💖💖 *NIHAAD* 💖💖 By Khaleesat Haiydar📖✍🏻 ~ 1 All thanks to Allah SWT for giving me the ability and privilege to present to you this book. My mother Hajiya Hajarah Allah ya karo farin ciki da kwanciyar hankali da arziki me amfani, Allah ya saka maki da gidan Aljanna, 👏🏻 my special greetings to my own Barrister KH, Allah ya jibanci lamarinka, ya kara bude hanyoyin arzikin da xa ayi ma addini hidima💖 and My lovely aunt Rukayya Allah ya raya su Lil Khaleesat ya kara maki kwanciyar hankali.. And then my fans, i am who i am as a result of u guys, i love you all for the support always, Allah ya baku farin cikin duniya da na kiyama.... As usual support ur writer and may God bless u. Tun da ta ji furucin wan Abbanta na karshe ta sakar masu kuka me karfin gaske, ta kalli Mahaifiyarta dake goge hawayen dake sauka idonta, babu alamar dai xata ce komai, Ta kalli Abba da fuskarsa ke hade tamkar hadari, shi ma bata samu courage din ce masa komai ba, yayyinta maza biyu dake parlon babu wanda yace komai cikinsu, ta dinga kuka da shesheka ta kalli Umma warce tayi tagumi, kallon Kakarta dake girgiza kafa tayi cikin rawan murya ta kamo hannunta tace "Don girman Allah kice su yi hakuri sharrin shaidan ne, don Allah kice su yafe min, ni ban san wanda yayi min haka ba..." Kakar ta warce hannunta tace "Ja can, Ke har kinsan sharrin shaidan alhalin kece shaidaniyar Nihad, ai kafin ki dauko mana abun kunya gwara tun wuri mu kunyata ki, ki ce lalle ke sai kin xama mutuniyar banxa abinda kaf xuri'a babu? Me yake burgeki da rayuwar 'ya yan iska har wannan abu ya same ki haka?" Kuka kakar ta saki tace "Allah mun gode maka, ka haifi ɗa ne kawai baka haifi halinsa ba, yanxu meye wannan kika mana Nihad" Mikewa Nihad tayi tana kuka sosai ta fice daga parlon, direct dakinta ta nufa don tasan ko me xata ce a parlon nan babu wanda xae saurareta, tunda har Umma ma ta ki cewa komai to babu wanda xai ce komai, bayan ta shiga daki ta sa makulli ta fada kan gado tana rusa kuka kamar ranta xai fita, is this actually happening to her? yanda ta ga rana haka ta ga dare, gashi ta kasa sallah ko da raka'a daya ne, gaba daya ta fice hayyacinta, she wish all this is nothing but a dream, she wish xata farka taga mummunan mafarki kawai take, da asuba aka murda kofar dakin ta daga idonta da suka kumbura tana kallon kofar amma bata da niyyar tashi ta bude, har aka gaji da Knocking aka bar wajen. Sai wajen karfe takwas na safe tana xaune saman darduma ta jawo wayarta da kyar, rabonta da wayar tun shekaranjiya, gaba daya bata son abinda xai hadata da wayar ma balle xuciyarta ya kara rauni, yanxun ma da ta dauko sim card dinta take son cirewa ta karya, missed calls da ta gani ya doshi hamsin, da messages da ya ninka calls din, ko wani message xance daya ne content dinsa, "Is that you on social media Nihad?" "Nihad what came over u?" "Nihad what is happening?" "Nihad something is wrong somewhere, ur Video is all over the internet" Fita tayi daga Inbox din hawaye me xafi na sauka idonta, ta bude WhatsApp shi ma dai duk messages din ne har da videos... Kashe wayar tayi ta ciro sim card din ta karya kamar yanda tayi niyya sannan ta jefar da wayar saman gado tana goge hawayen da ya ki tsaya mata, wayyo ina ka xata farka taga mafarki kawai take da gaske, tun shekaranjiya take wish din nan, amma taki farkawa wanda hakan ke kara tabbatar mata da gaske ne duk abinda ke faruwa, babu wani xancen mafarki, Knocking din kofa aka yi, ta kalli kofar sai kuma ta mike a hankali ta nufi kofar ta bude, Umma ta gani tsaye, nan da nan wasu sabbin hawayen suka ciko idonta, Umma ta shigo dakin ta kulle kofar, Nihad ta bi ta da kallo har ta xauna gefen gado, Nihad ta karasa inda take ta durkusa kasa cikin sanyin murya tace "Umma don girman Allah ku rufa min asiri kar ayi min haka, wllh xan iya mutuwa, talk to Abba plss" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "It's too late Nihad, tun da har Alhaji Abubakar ne ya yanke hukuncin nan kema kinsan babu me ja da wannan hukunci nasa, ke dai naki addu'a, mu ma kuma muna nan muna taya ki da shi, it's okay to make mistakes as long as we learn from them, so ki kwantar da hankalinki everything will be alright, kuma koma waye ya aikata maki haka sai dai mu ce Allah ya shiryesa" Ta rushe da wani kuka cikin tashin hankali take cewa "Na shiga uku Umma, yanxu baxa ki iya ce ma Abba komai ba? auren dole fa xa su min, Umma ya xan yi da raina idan hakan ya faru, na shiga uku na..." Mikewa Umma tayi ta nufi kofa ta fita ta kulle. Compound Umma ta fita ta tarda Abba dake xaune shi kadai kana ganinsa kasan yayi nisa a tunanin da yake, ta nufesa ta ja daya daga kujerun dake wajen ta xauna tana kallonsa da damuwa karara fuskarta, he looks so disturbed also, ta kwantar da murya tace "Damuwa ba shi ne mafita ba Ranka shi dade, kayi hakuri ka sa ma ranka salama, Allah ne ya tsara haka, sai mu gode masa mu kara gode masa kawai" Abba ya numfasa yace "I think aurar da Nihad yanzu ba shi ne mafita ba Sumayyah, amma Engineer da Hajiya baxa su fahimci hakan ba, she is just 19, ga kuma wannan abu da ya faru, ta ina xata fara xaman aure bata gama mallakan hankalin kanta ba? da xa su sake shawara da ni da na ce masu gwara kawai ta tafi waje ta karasa karatun ta a can, ko da Uk ne...." Umma dake ta kallonsa tace "Wannan gaskiya ne, aurar da Nihad is not a way out, amma ni dai shawarata kar ka tofa naka a issue din nan Yallabai, duk yanda Yaya yayi da Nihad dai dai ne don 'er sa ce, kuma ran Hajiya xae 6aci idan ka bijiro da wannan batun na taje waje tayi karatu, gani kawai xa su yi kana ma goyon bayanta ne, naka kawai ido sannan kayi mata fatan alkhairi duk yanda suka yi da ita er su ce, kuma baxa su yi abinda xai cuceta ba, tunda suka ce aure mu xuba masu ido duk yanda suka yi dai dai ne, shawara ta biyu kuma kada ka kuskura Yaya yace xai hada Nihad da daya daga 'ya yansa balle ma bana tunanin xa ayi hakan kawai in case xa a bijiro da wannan gaskiya ka nuna a'a, don in har aka yi hakan zumunci xae tarwatse kasan su waye 'ya yan nasa da iyayensu, yara ne masu ji da kansu wa enda ba sa rayuwa a kasar, don haka kar ka soma yarda... don walakantattciya xasu mayar mana da er mu, ni yallabai yanda video din nan nata ya tafi viral gwara kawai a samo wani da ba kowa ba, bawan Allah wanda ba ma shi da abun duniya, shi kadai xai iya aurenta ya rufa mata asiri su xauna lafiya ba tare da ya goranta mata wataran ba, bai kuma walakanta mana ita ba, kyau ace ma a karkara yake rayuwarsa yallabai" Abba ya daga kai yana mata wani kallo babu ko kiftawa, tace "Atoh Allah ya baka hakuri, ka samo wani d'an senator ko Attajiri ka hadasu kawai, hakan ma dai dai ne...." Tana kai wa nan ta mike ta ce "Allah ya rufa asiri, ya tsare yan baya" Daga haka ta bar wajen, Abba ya dafe kansa. Umma ta saka Abba tunani iri iri bayan ta bar sa a wajen, ta wani bangaren she is damn right, abinda ta fada gaskiya ne, babu wanda xai yi ma tayin Nihad ya amsa da farin ciki ko dadin rai, Nihad is nothing but a disappointment to him, bai taba xaton hakan daga gareta ba kuma yayi da ya sanin fifitata da yayi cikin duk 'ya yansa, yayi da ya sanin nuna mata so karara da yayi kan sauran 'ya yan sa, amma Alhmdlh tunda abinda tayi ya tsaya iya haka, shawaran da Umma ta basa kuma shi xai yi amfani da... Mai gadi ne ya bude gate jin ana horn, Abba ya bi motar da ta shigo compound din da ido har yayi parking, yana xaune aka samesa cikin ladabi ya mika masa ledan dake hannunsa yace "Ga aiken Alhaji" mikewa Abba yayi yace "Mu je can parlor daga nan ka kwashi takalman da xa ayi min polish ka ba mai gadi" Abba na gaba yana biye da shi a baya har suka shiga cikin babban parlon gidan, sannan main parlor din Abba, Abba ya xauna yace "Ka ɗan jira xan yi waya, xan sake aikenka ne" Mai gadi ne xaune a position dinsa tare da driver, mai gadin yayi kasa da murya yace "Ka ko ji abinda ke faruwa kuwa??" Drivern yace "Me ke faruwa?" Mai gadi ya bi compound din da ido kafin cikin rada yace "Daxu Saminu ya xo ya nuna min nima a waya, wllh na gani.." Driver yace "Me ka ga?" Mai gadi ya kai baki kunnensa cikin rada sosai yace "Wllh hoton tsaraicin fitsararriyar yarinyar nan ne duk ya baxu yanar gizo, da idona na gani a wayar Saminu, kai baka ganin duk gidan kamar anyi mutuwa ba, ai duk gidan alhini suke, Da yake baka da babban waya baxa ka gani ba" Driver ya kallesa da kyau yace "Tsaraici?" Mai gadi ya kwashe da dariya yace "Yo tsaraici mana, yar kamfai da rigar mama kawai ne a jikinta kuma hoto me motsi aka mata, duk halittar jikinta babu wanda bai fito ba malam, abun dai ba a cewa komai, ni Alhaji ne ma ke ban tausayi don ya shiga damuwa sosai" Yana kallon mai gadin yace "Kai a ina ka gani??" Mai gadi yace "Toh jira ka ga ikon Allah" yana fadin haka ya nufi boys quarters da sauri, ba a dau lkci ba sai gashi ya dawo rike da wayar saminu, ya mika masa, amsa yayi ya danna play a video din, ko second goma bai yi da kallon ba ya ajiye wayar gefensa yana kallon Mai gadin, Mai gadin ya kwashe da dariya yace "Toh dada, muma duk haka muka gani, Allah kadai yasan iyakar inda abun nan yaje, shi ma a wani gruf ya gani wai, har fesbook yace min ya gani, kaga daga yanxu sai dai ta daga ma wasu kai ba mu ba kuma" Dariya mai gadin ya kyalkyale da, Driver ya mike yace "Ga takalma in ji Alhaji a ba shoe shiner" Daga haka ya tafi boys quarters. Nihad na kwance edge din gadonta ta kafa ma agogon dake manne bangon dakinta ido, xuwa yanxu kam ta hakura da kukan da take, but she is so weak, har ta mance rabonta da wani abinci, babu wanda ke bin ta kanta a gidan banda Umma dake shigowa dakin nata lkci lkci, she still don't have the courage to go to her mother, Bude kofar dakin aka yi ta daga kai da sauri, Husnah ce ta shigo dakin da sallama fuskarta dauke da damuwa, ta karasa kusa da ita ta xauna gefen ta amma ta kasa cewa komai, Nihad din ma dai bata ce mata komai ba, Husnah ta sauke ajiyar xuciya tace "Kar ki sa ma kanki wani ciwon kawata, duk abinda ya faru da mutum a rayuwa dama Allah ya tsara hakan, kiyi hakuri da kaddaranki, kiyi hakuri kiyi accepting with good faith" Lkci daya hawaye ya kawo idon Nihad, Husnah da ita ma har hawayen ya cika idonta tace "Pls have faith don Allah Nihad, koma waye yayi maki wannan abun Allah baxai bar sa haka ba, tun a duniya Allah xai bi maki hakkinki, ya saka maki" Nihad ta mike xaune ta fashe da kuka tace "Ji nake kamar in kashe kaina Husnah" Husnah ta rufe bakinta da sauri tace "Kiyi istigifari, who are u not to be tested by Allah?? Kar ki kuma fadin hakan, kowa da irin tasa kaddaran a rayuwa, ki dau naki with good faith nace maki, in sha Allah xaki cinye wannan jarabawan, muna nan muna maki addu'a, Allah ya rufe abun cikin gaggawa a daina yawo da shi a media" Nihad ta share idonta a hankali tace "How will i mend this damage?" Husnah tace "Allah will, ke dai ki ci gaba da addu'a, wllh kawata tunda naga abun nan Allah ya sani baccin kirki for the pass 3 days ban yi ba, amma koma waye yayi mana haka xai ga sakkaya daga wajen Allah, sai Allah ya saka mana" Nihad ta sunkuyar da kai a hankali tace "Kuma fa wai aure Uncle dina da Inna suka ce xa ayi min" Husnah ta xaro ido tace "What?? Aure?? Which of ur uncle are u talking about? Abbansu Hamid??" Nihad ta gyada mata kai, Husnah ta rike ha6a tace "But sorry to say Nihad yanxu duk rashin jin da su Zeenat da Pinky ke yi bai gani ba sai naki? Duk runz din da suke yi babu wanda ya hango nasu sai naki? Lallai kam ance laifi tudu ne, Kawai sbda wani axxalumin yaje yayi posting dinki halve naked shine xa ace xa a maki aure? Wa enda ma aka saki hotunansu fully naked ba ace xa a masu aure ba sai ke da naki nafila ne, Tabdi... to wai wa suka ce xa su aura maki?" Nihad tace "I don't even know, but i am thinking of running away" Husnah tace "Nima nayi wannan tunanin, kada ki wani tsaya a cuceki a...." Bude kofa aka yi duk suka yi shiru suka juya suna kallon kofar, Yaya Farooq ne ya shigo dakin, Nihad sai da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta don bata mance dukan tsiyan da yayi mata shekaranjiya ba, banda ma Umma ta masa jan ido ta kwaceta a hannunsa, Ya wani murtuke fuska yana kallon Husnah cikin daga murya yace "Ke, Uban wa ya baki permission din shigowa gidan nan, ta ina ma kika shigo don uwarki??" Husnah ta mike tana sissinne kai jikinta na 6ari, Ita dai Nihad banda faduwa babu abinda gabanta yake har ta fara kallon bandaki ko can xata shige ta kulle, Ya daka ma Husnah wani raxanannen tsawa yace "Xo ki fita kar in karya ki in karya banza" Jakarta ta dauka ta nufi kofa da sauri har tana tuntube, Tana fita ya doka ma Nihad wata harara yace "Kin ga result din bin ire iren kawayen nan ai..." Cikin rawar murya tace "Yaya ita Husnah ai babu ruwan..." Haureta ya kai kafa xai yi ta kauce, ta fashe da matsanancin kuka dai dai shigowar Umma, Umma na ganinsa, tana tafe hannu tace "Wato duk warning din da na maka bai isheka ba ko Farooq? Duk jan kunnen da nayi maka kar ka sake dawowa hanyar dakin nan watsi kayi da shi sbda ban isa ba ko?? To uban naku ma da ya ga abun nan ko nunata da yatsa bai yi ba balle ya kai mata hannu, kai ko zagi bai hadasa da ita ba, to wai shin ma ina ruwanka farooq? Meye naka? To wllh ka shiga hankalinka ka fita harkarta a gidan nan, ka shiga hankalinka nace, Shi Usman da yake ba mahaukaci bane ai nasiha kadai ya hadasa da ita, tun daga sannan ma a ina ta sake saka sa a ido, abun nan dai naga ba yaki bane, kai iskancin da kake sani ake yi balle a tsawatar maka?? To ahir dinka farooq kar ka kuskura in nuna maka bacin rai na wllh" Ita dai Nihad shessheka kawai take, shi kam banda kallon mahaifiyarsa babu abinda yake, ji yake kamar ya karya Nihad ko xai ji sauki a ransa, juyawa yayi ya fice daga dakin kamar xai tashi sama, Umma ta bi sa da harara, sai kuma ta ja tsaki tace "Rabu da shi, ba kanki farau ba ai" Daga haka ita ma ta fice daga dakin. Bayan magrib Nihad ta dake ta fita dakinta for the first time tun da gari ya waye, part din mum dinta ta nufa, duk gaba daya jikinta a sanyaye yake, ta bude kofar parlon a hankali Mumy na xaune parlon da sisters dinta biyu, tun jiya suke gidan amma ko bin ta kanta su ma basa yi, abun duniya duk ya ishesu barin da suka ga damuwar da yayarsu ta shiga, Nihad dai tunda Umma ta kwace ta a hannun Aunty Jamila rabonta da su sai kuma yanxu, banda faduwa babu abinda xuciyarta ke yi, Mumy ta nuna mata kofa alamar ta fita, kuka ta sakar mata ta xube nan bakin kofar cikin rawan murya tace "Don Allah Mumy kiyi hakuri ki yafe min, wllh i don't know how all this happen, i don't know who did this to me, mumy ba halina bane don Allah ki saurareni" Mumy tace "Fita nace Nihad" Kallon Aunties dinta tayi tana girgiza kai wasu sabbin hawayen na sauko mata tace "Aunty Jamila don Allah ku ce Mumy ta yafe min" Ganin Mumy ta mike, ta tashi da sauri ta fice daga parlon xuciyarta na bugawa, kuka take sosai bata da option ta nufi dakin yayanta farooq, bata tadda shi a dakin ba ta rakube jikin kofa tana shessheka, ba a dau lkci ba ya shigo dakin daga masallaci, yana kokarin kulle kofar ya ganta, kan yace komai ta hade hannunta with tears tace "Ya farooq don Allah ka saurareni, only u will understand and listen to me, wllh i knew nothing about that video, ban san wa yayi min ba, ban san yaushe aka min ba, ban kuma san wanda ya fitar ba" Kuka take sosai, ya daure fuska yace "Shaye shaye kika fara da har baki san when and where aka maki video din ba Nihad??" tace "Believe me yaya Farooq, wllh ban sani ba, yanda ku ka gansa haka nima na gansa" Yace "Na rabaki da bin kawaye barkatai Nihad, na rabaki da yawace yawace da xuwa parties, har night party nasan kina xuwa don Sadeeq saw u, na maki magana kika karyatasa kamar bai san me yake ba, u are just different from every other child in this house, just look at the disgrace u have caused to our family, u have tarnished the reputation of our home, how will i face my frnds da suka sanki, my own blood with such act? Oh no, Subhanallah" Ta dinga girgiza masa kai tace "Don Allah ku yi hakuri yaya, i wish my life can end now because of all this, i regret everything" Xaunawa yayi gefen gado ransa a dagule, ita dai ta dinga goge hawayen da ya ki tsaya mata tace "Yaya farooq i need one favor from u plss" Yace "U don't deserve that favor Nihad" tace "Plss yaya abu na karshe da xa ka iya min a rayuwa shine don Allah kar ka bari Abba su yi min auren dole, wllh xan iya mutuwa kaga har na gaya maka" Yace "What did ur boyfriend say about the video?" A hankali ta sunkuyar da kai tayi shiru, ya hade rai yace "Tambayarki nake" Cikin rawan murya tace "Yayi blocking dina...." Farooq ya gyada kai yace "Good" ta hade hannunta tace "Don Allah yaya, kasan consequences din auren dole kar ku bari ayi min, na yarda a min ko wani hukunci amma banda auren dole, idan ma xa a ce for the rest of my life baxan sake fita waje ba, sannan babu ni babu karatu har abada i agree but kar ayi min auren dole sbda wannan mistake din nawa, ka taimaka kayi ma Abba magana" Umma ce ta shigo dakin duk suka daga kai suna kallonta, tace "So kike ki kara tunxura Abbanki Nihad? Duk shirun da yayi maki bai isheki ba sai kin tunxurasa, Ba na baki shawaran kar ki ce komai a kan batun auren nan ba, so kike ki fusatar da Abbanki yayi maki abinda bai ta6a maki ba?" Faruq yace "Noo wannan ba magana bace Umma, we don't even know da wanda xa a hadata, ko ma me tayi ai da gatanta and she still have her right, su gani suke auren shine way out, whereas it's not" Umma tace "Toh tunda kai ka haifesu ai sai ka gaya masu way out" Ya girgiza kai yace "Umma idan ma auren ne ba sai a bari komai ya lafa ba, ta yaya abu na xafi xafi a shigo da maganar aure, waye xai aureta? Noo bata yi deserving wannan auren ba gaskiya" Umma tace "Ko ma wa xai aureta wannan ba damuwarka bane sai ka xuba ma iyayenka ido, su ai sun san abinda ya kamata, ko so kake ka nuna masu goyan bayan abinda tayi kake?" Ya dinga kallon Ummar tasa, Mikewa yayi ya fice daga dakin, ta bi bayansa, Nihad ta bi su da kallo, sai da suka sauka stairs Umma tace "Farooq" ya juyo yana kallonta, tace "Naga kamar so kake ka ja ma kanka bakin jini gun Kakarku da Engineer, sannan nima hakan ya shafeni, kawai so kake ka ja min maganan da ba shi da ranan mutuwa gun tsohuwar nan, don haka kar ka sake tofa komai a kan lamarin nan, ita kanta uwar da ta haifeta taki cewa komai har yanzu, me magana dama daga ni sai kai, kuma a hakan ma haushinmu ake, don Usman ma bai tsoma kansa ba balle a ga nasa, to ba Uba daya ba, ko ciki daya ku ka fito da Nihad ni dai nace ka janye bakinka daga issue din nan domin a samu masalha, daxu Abban naku ma ya kirani wai ya tafi karkara neman wanda xai hadata da, to idan ana son asiri ya rufu ai sai dai hakan dama, to wa xai yarda ya aureta a nan dai cikin gari? don haka nake kara gargadinka, kar ma ka fara cewa a fasa aure" Faruq yace "Karkara kuma?" Umma tace "Ehh nan fa, ko ka ga alamar Nihad xata samu miji cikin gari ba karkaran ba nace, da wannan mummunan abin da ta aikata wa xae yarda nasa ya aureta?" Yace "Ah haba, karkara kuma, noo ba dai karkara ba, waye ya ba Abba wnn muguwar shawaran? Karkara fa kike ce Umma" Strictly Umma tace "Farooq" ya daga kai ya kalleta tace "I am giving u this serious warning, kada ka kuskura ka sake tofa naka a wannan lamarin, kaji abinda nace maka??" Bai ce mata komai ba, tace "To na dai gaya maka" daga haka ta bar wajen ya bi ta da ido. 💖 *Bitter Rivalries*💖 And i came really prepared...... 🤗 Contact me directly via👇🏻 07087865788✍🏻 💖💖 *NIHAAD*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📖✍🏻 ~~ 2 Dumbin gaisuwa da fatan alkhairi xuwa ga iyayen gidan Khaleesat's Palace, my die hard fans🥰😍 Su Hajjaju Chamo me gwala-gwalai duk da jarin ya karye amma take ta bobboye mana, Hajiya Aunty Zahra mai siyar da harawa, Hajiya Nafisa Mom twins, Su Hajiya Aunty Maryam, Uwar Nabeela, Mrs Jay, Hajiya Inna, Hajiya Deejah, Hajiya Zeenaru, Nanisa Zero Zero, Hajiya Bilkisu, Hajiya Rabia, Damsel, Uwar Yusrah, Ummu Zainab, Uwar gidan Barrister wato Khaleesat me siyar da tayoyi, kai duk wanda bai ga sunansa a nan ba ya biyo ni da sunan xai gansa a next page😜 amma fa ko kun ki ko kun so sai nayi sharing link dinku, ku tanadar ma sabbin fans ruwa da cin cin ehe.🤓 Da daddare Abba na xaune parlonsa tare da Yayansa Alhaji Abubakar.... Alhaji Abubakar yace "Ae duk ba sai ka sanar masu komai ba, kawai gobe idan an daura auren kowa ma sai ya sani, i don't think u owe anybody explanation to this" Abba ya numfasa yace "Toh shikenan" Alhaji Abubakar yace "Yea i think that's okay ba sai kace ma kowa komai ba for now, a ina kace xa su xauna? I mean which of ur houses are they staying?" Abba yace "I don't think i can keep her where she will in any way feel comfy, i wish xai koma can karkarar tasu su xauna in basa enough jari, idan noma xai yi ma yayi employing workers su yi masa a can ko ni xan dinga biya, cause i want her to learn a bitter lesson of her life, ina son ta san wata rayuwar bayan rayuwa cikin daula" Alhaji Abubakar ya girgiza kai yace "No... There is no need for all that, duk abinda ya kamata kayi kar ka fasa, ka basu inda xa su xauna comfortably" Bayan Alhaji Abubakar ya bar gidan, Umma ta shigo parlon Abba, ganin basu ta6a abincin da ta ajiye masu ba tace "Haba yallabai, ko abincin baka ci ba har yanxu?" Abba yace "Kawai ayi min black tea" Umma tace "Toh shkkn" Tashi tayi ta dau abincin ta fita, ba a dau lkci da fitarta ba Farooq ya shigo parlon, waya ya tadda Abbansa ke yi, wanda da jin yanda yake amsa wayar kasan magana ce aka kirasa a kan Nihad kuma abokinsa ne me kiran nasa, Farooq ya sunkuyar da kansa duk jikinsa yayi sanyi, har Abba ya gama wayar ya jinginar da kai da kujera bai ce masa komai ba, a hankali Farooq ya dago yace "Barka da dare Abba" Abba ya amsa, Farooq yace "Throughout ina ta kiranka but couldn't reach u on phone" Abba yace "Ehh wata er tafiya nayi, is there any problem?" Farooq yace "Ya gajiyan hanya" Abba yace "Alhamdulillah" Farooq yayi kasa da murya yace "Abba magana ce dama a kan Nihad?" Dai dai nan Umma ta shigo da mug din black tea dake ta kamshi, Da hannu Abba yayi masa alamar ya aka yi, Farooq yayi shiru, Abba yace "Maganar me a kan Nihad Umar?" Farooq ya d'an fara kame kame, sai kuma dai kawai yace "Abba a kan auren nan da aka ce ne, is it not better a yi hakuri a janye, idan ya so..." Dakatar da shi Abba yayi yace "Idan wannan maganar ce ta kawo ka, ka je kawai i need rest Umar, kaga ban dade da shigowa gidan ba" Umma dai na xaune kan one sitter, pleadingly Farooq yace "Pls ka saurareni Abba" Abba yace "I said i need rest...." Umma tace "ka je yace xai huta ko kuwa?" Mikewa Farooq yayi ya fice daga parlon, Umma ta kalli Abba tace "Kayi hakuri Yallabai, xan so ka cire wannan damuwar a ranka, in sha Allah everything will be alright, kar kaje ka sa ma kanka wani ciwon bayan hawan jinin da kake fama da" Abba yayi sigh yana girgiza kai yace "A kalla ba a kirani a rana ba xa a kirani sau goma a kan Nihad, the video is trending day by day.... Me yafi wannan bakin ciki Sumayyah? A reputable person like me, noo Nihad tayi tarnishing image din gida na" Da damuwa Umma tace "To ya xa ayi Yallabai haka Allah ya kaddaro mana, sai dai kawai mu rungumi kaddara, amma akwai wani malami bawan Allah, tun ranan da abun ya faru Hajiya Sukhaina tace ko shi xa ayi ma magana yayi addu'a Allah ya kawo karshen trending din abun, shiru xaka ji kamar ba ayi ba wllh, neman video din ma xa ayi a rasa" Abba ya mata wani kallo yace "Malami? Wani irin malami?" Umma ta gyara xama tace "Ba boka fa nace ba Alhaji, amma dai shkkn kawai, ina ce akwai malamai bayin Allah wa enda..." Mikewa Abba yayi bayan ya dau mug din black tea dinsa ya wuce daki ya kulle kofa. Washegari friday ana sauka sallan juma'a, Abba ya tafi tare da yayansa da cousins dinsa biyu xuwa garin da aka daura ma Nihad aure, a kan sadaki dubu hamsin wanda shi ya bayar. Sai kusan la'asar suka dawo gida, nan kuma ya sanar ma Umma su fara shirye shiryen kai ta, Umma tayi shiru cike da jimami, sai kuma ta sauke ajiyar xuciya tace "To wani gidan kenan xa a kai ta yallabai?" Abba yace "Wannan gidan da aka gama na Rijiyar zaki, it's already furnished" Umma tace "Allah sarki, ina laifin wannan gidan na kusa da mu yallabai, ai xa su fi sakewa a nan..." Abba yace "Ban yi niyya ba" Umma tace "Rijiyar zakin ma yayi ai, Allah ya saka da alkhairi" mikewa tayi ta fita don xuwa sanar ma Mum din Nihad da Yan uwanta dake can bangarenta abinda Abba ya ce, nata side din ta fara shiga, first daughter dinta Kamila na xaune parlon sai second daughter dinta Amina, sannan kanninta mata biyu da suka xo daga Jigawa daxu, Umma tace "To duk ku shirya kai amarya an daura mata auren yau dai" Kamila ta riƙe ha6a tace "Har an daura?? yanxu Umma Abba bai fada maku da wa aka yi auren ba, ni kawai sai xuciyata ke bani Hamid ne ko Saif" Umma ta saki baki tace "Hamid? Ita uwar Hamid din karen hauka ya cijeta xata yarda a hada shi da Nihad? Ko kuma shi Hamid din mahaukaciya ne da zai amince da auren Nihad, Kai har shi Uban Hamid din da ya kirkiro auren ba yarda xai yi ayi auren da ɗan sa ba karewa kenan, haka ita ma Innar, wani can dai Abban naku ya samo a karkara, hakan kuma kadai ne rufin asirinta a dai abin nan da ya faru" Amina ta mika ma Umma wayarta dake ring, Umma ta amsa ganin autarta ce ke kira ta daga ta kai kunne da murmushi tace "Hello auta, duk yau kin ji ni shiru ko" lkci daya ta hade rai tace "Ki zo kiyi me kina karatun ki Nihal? A kan wani dalili xaki taho kuna tsaka da karatu? To wllh kar ki fara idan ba haka ba yanxun nan in kira Farooq in gaya masa, me xuwanki xai sa a fasa, bayan har an daura auren ma, duk sanda ku ka yi hutu idan kin dawo sai kije ki ga dakin er uwar taki ba shikenan ba, amma ki wani ce xaki kamo hanya kamar ana yaki" a kufule Umma da ta gama sauraronta tace "To wai uban meye na wannan kukan da kike, so kike ki ja ma kanki wani ciwo ne ko ko? Bata da waya yanxu a hannu, idan na fita yanxu xan bata sai ku yi magana, amma ta ina xaki baro Zaria da yamman nan ba hutu ku ka yi ba, kuma dama kin ta6a dawowa gida ke kadai ne banda gulma da daura ma kai wahala Nihal?? Ni dai sai anjima ban san shashanci" Katse wayar Umma tayi, Aunty Laraba tace "Wai tahowa xata yi daga Zarian?" Umma tace "Ehh wai, kinji wata gulma dai, ko uban me xata xo tayi oho" Aunty Laraba tace "To wai ita tace ma Abban nasu bata son Maryam Abatcan da er uwar ke xuwa ne?" Umma tayi murmushi tace "Aa haka dai yayi niyya ita ya turata federal dai dai ita, ita kuma Nihad dama Private ne dai dai da ita inji uban, wato Maryam Abatcha, option ma ya bata ta xabi Private uni da take so shine ta xabi Maryam Abatcha" Aunty Maimuna tace "Ai ko ga Maryam Abatcha ana ta gani a soshiyal media" Umma dai bata ce komai ba, sai kuma tace "Allah dai ya shirya mana zuri'a kawai" daga haka ta fita xuwa bangaren mum din Nihad, a corridor ta hadu da matan Alhaji Abubakar su biyu sun shigo gidan, suka gaisa da fara'a ana kara jajanta lamarin da ya faru, Hajiya fatima tace "Daxu Abbansu Hamid ya dawo gida yake sanar mana ai har an daura aure, nace shine babu labari ko daga gare ku Hajiya" Umma tace "Wllh abun ne ya xo a haka Hajajju, kinsan muna ta tunanin xa su hakura a fasa auren a nemo wani solution, to kin san halin mazan namu da kafiya, wllh sun ki, kawai fatan Allah ya basu xaman lafiya da ko ma waye mijin" Hajiya Zuwaira tace "Shikenan addu'ar, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi a gareta, Allah kuma ya duba yan baya" Duk suka amsa da Ameen, Umma tace "Mu je dama bangaren Maryam din xan je" a tare suka tafi part din Mumy, bayan an gaisa an kara jajantawa, Mumy dai bin su kawai take da kallo bata cewa komai, Umma ta sanar mata abinda Abba yace sannan ta fita daga dakin. Bayan magrib xa a kai Nihad, kafin Magrib din Abba ya tara gaba daya matan nasa da 'ya yansa, Usman, Farooq, Kamila, Amina, Nihal ce kawai bata nan a yaran Umma, yaran Mumy kuwa Nihad da kanninta biyu wa enda duk maza ne, daya me shekara tara da kuma me shekara shidda duk basa parlon, Bayan duk sun hallara a parlon Abba ya nisa yace "Ina fatan duk kun ga abinda ya faru da yar uwarku Nihad, Nihad is nothing but a disappointment to the family, kar ku ga Nihad tayi wannan mummunan laifin na bada ita ga wanda nayi niyya without bothering ko ya cancanceta ko bai yi ba, to wllh wllh if anything of such should happen again in my family infact ko wanda bai yi kusa da hakan ba idan ya faru a family dina wllh i will prefer to shoot that person" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Allah Ubangiji ya tsare, ya kare mana zuri'a Alhaji" Abba ya kalli Mumy da bata cewa komai tun faruwan abun, amma kana ganinta kasan she is heartbroken, her first child, habaa ko bacci bata iya yi tunda wannan lamari ya faru, da tasan Nihad xata girma ta yi irin wnn rashin jin da Allah bai raya mata ita ba, tun faruwan hakan ita ma ta kashe wayarta sbda kiran yan uwa da abokan arziki da suka san Nihad, Abba yayi gyaran murya yace "Ban ga laifinki ba Maryam don ni nasan kinyi iya bakin kokarin ki na ganin kin ba ma Nihad tarbiya yanda ya kamata, u tried ur best, matsalar kawai u didn't make Nihad ur frnd aside mothering her, amma dai babu komai, kawai dai kafin Nihad ta dauko mana abinda xuciyarmu xai kasa dauka nan gaba tun wuri ni da yayana da yan uwana mun mikata, kusan xance na bada sadakarta" Abba na fadin haka ya ciro sadakinta dake aljihunsa ya mika ma Umma yace "Sai ki damka mata ku da xa ku kai ta" Umma ta amsa cikin sanyin murya tace "Yanxu Yallabai mun yi deserving a bada er mu ba tare da mun san wanda aka ba ma ba? Ai hankalinmu baxai taba kwanciya ba, tun jiya nake bin ka kaki gaya min, ai yana da kyau a sanar mana mu sani don muna da hakkin sani, idan ma ni bani da hakkin in sani mahaifiyarta fa?" Abba ya ɗan yi shiru, sai kuma ya dau wayarsa yayi dialing number snn ya kai kunne, ana dagawa yace "Ka shigo nan parlor ka sameni yanzu" daga haka ya katse wayar, duk kowa yayi shiru ya xuba ido ya ga wanda xai shigo parlon barin Farooq da Umma. Da sallama ya bude kofar parlon, ganin su Umma ya dakata daga bakin kofar bai shigo ba, Abba na kallonsa yace "Karaso" ya karasa shiga cikin parlon kansa a kasa, duk occupant din parlon kallonsa suke with full shock, Abba ya nunasa yace "Shi na ba auren Nihad, shine mijinta" Mikewa Farooq yayi yana kallon Abba baki bude, Mumy ta hadiyi wani kullutu da taji ya tokareta a makogwaro, Umma kuwa sae kallonsa take daga sama har kasa babu ko kiftawa, ta ma rasa yanayin da take ciki ita, Kowa na parlon ya kasa cewa komai, tsabar silence din parlon da allura xai fadi xa a ji karar faduwarsa, shi kam dai yana ta tsaye ya sunkui da kai har sannan, Abba yayi breaking silent din yace "Je ka" Juyawa yayi ya fita daga parlon, Usman ya kalli Abba yace "Haba Dad? Yanxu shi ka aura ma Nihad?" Farooq yace "No Abba, u should have given her a choice, bata yi deserving ayi mata dole ba sbda wannan kaddarar tata, but Abba...." Kasa cewa komai yayi ya koma ya xauna, shi ma ya rasa yanayin da yake ciki, but he don't think it's still bad after all, just dat.... Girgiza kai kawai yayi, Umma tace "Haba Alhaji...." Abba ya mike yana bin kowa da kallo yace "No one have the right to query my authority" Yana fadin haka ya bar masu parlon ya shiga bedroom dinsa, suka dinga kallon kallo a tsakaninsu a parlon, Usman ne ya fara mikewa ya fice daga parlon, Mumy ta mike ta bi bayansa ita ma tana share idonta, Umma ta sauke ajiyar xuciya tana kallon Farooq, ita gaba daya ma kanta fa ya kulle, Abba really took them unaware, jinginar da kanta tayi da kujera Farooq ya mike ya fice daga parlon shi ma. Ana idar da magrib yan kai amarya suka fara shirye shiryen kai ta, Nihad bata ta6a shiga irin tashin hankalin da take ciki ba a wannan moment din, ko video dinta bai tada hankalinta kamar yanxu ba, gashi nobody is there to console her, Nihal na schl, Husnah kuma taki xuwa gidan sbda Farooq, gashi bata da numberta a kai balle ta amshi wayar wani ta kirata, su kamila da Amina tamkar ma farin ciki da abinda ya sameta suke don uban kwalliya suka ci har da kashe dauri Hajiya Zuwaira ce ta kai ta gun Mumy tayi mata fada ta sa mata albarka, sbda takaici da bakin ciki Mumy ta ki cewa komai daga karshe da aka tilastata sae cewa tayi Allah ya tsare, Alhaji Abubakar ne kawai yayi mata fada, Abba kuwa tun da aka idar da magrib ya ki shigowa gidan dama, a haka dai aka tattara ta da akwatunan kayanta uku wanda Umma da Kamila suka hada mata wasu kayayyakinta a ciki, kuka take kamar xata shide, har addu'a ta dinga yi Allah ya dau ranta kafin a karasa da ita gidan, tana ganin an shiga gidan ta kara sautin kukan da take a haka har aka shigar da ita daki, gida ne bungalow madaidaici me dakuna uku, ko wani daki da bandaki, sae bandakin dake parlor sai kitchen, anyi furnishing gidan babu laifi sai dai furnitures din ba masu tsada bane, Nihad ta dinga kuka tana cewa ta shiga uku, masu bata bakin ma har sun gaji sun daina, karfe tara saura suka fara shirin tafiya, Nihad ta rike hannun Kamila cikin kuka tace "Aunty ynxu tafiya xa ku yi ku bar ni, don Allah kar kuyi min haka..." Kamila tayi dariya tace "Ae ko dole xa mu yi maki haka tunda mun kawo ki gidan mijinki kinga ni ynxu sae na koma xan dau jakata inyi driving xuwa gida, kawai kiyi hakuri ki bi mijinki ku xauna lafiya ko hakan xai goge wannan ta6on da kika ma kanki" Daga haka ta fice daga dakin don dama ita ce karshen fita, Nihad ta silalo kasa ta xauna tana kukan takaici, tana jin duk suka fice daga gidan ta daina jin hayaniyar kowa, nan kuma tunanin ta ya tafi gun wanda xata gani a matsayin mijinta, tsoho ne, yaro ne, baki ne, fari ne, kato ne, siriri ne, mummuna ne, kyakkyawa ne, infact duk wannan tunanin ne suka baibaye ranta gabanta ya dinga faduwa hankalinta ya kara tashi, daga karshe ma daina kukan tayi banda bugawa babu abinda xuciyarta yake, ta fi minti ashirin a haka taji an bude gate, da sauri ta mike ta tafi gun window ta bude labule amma sai taga ba ta nan gate din ma yake ba balle taga me shigowa, komawa tayi ta xauna can karshen gado tana jin yanda kirjinta ke heaving, to waye wannan da ko mota ba shi da, bayan wasu mintuna taji an shigo parlor, daga karshe ta ji kamar an bude wani daki an shiga, mikewa tayi ta jingina da window with so much fear, har ta gaji da tsayuwa bata ga alamar xa a shigo dakin ba, komawa tayi ta xauna gefen gado, a kan idonta karfe sha daya tayi, bacci take ji amma taki kwanciya sbda fargaba, kafin sha biyu bacci barawo ya saceta. Ba ita ta bude ido ba sae da hasken rana ya sauka saman fuskarta washegari da safe, a firgice ta mike xaune, sae kuma ta sauka daga saman gadon ta shige bandaki da sauri, bayan ta idar da sallah ta mike a hankali ta nufi kofar dakin ta bude ta fita xuwa parlor, ta dinga bin ko ina da kallo xuciyarta na bugawa, kofar da take tunanin kitchen ne ta nufa ta bude kofar a hankali, wani kara ta saki ba tare da ta shirya ba ganin mutum a tsaye yayi backing kofar kitchen din ga ruwa ya daura saman gas, juyowa yayi suka yi ido hudu da ita, wani irin shock ne ya bayyana a fuskarta ta dinga komawa baya tana kallonsa bakinta ya kasa furta komai, can ta nunasa da yatsa nan ma words suka yi failing dinta, juyawa yayi ya kashe gas din don ruwan ya fara tafasa ya juye cikin mug sannan ya bi gefenta ya fice daga kitchen din ba tare da ya sake kallonta ba, makalkalewa tayi jikin kofa jikinta na 6ari tana ganin abun kamar a mafarki, sae a sannan bakinta ya bude ta fasa wani raxanannen ihu, sai kuma ta fara ganin kitchen din na juya mata lkci daya ta sulale kasa.... _8 months earlier_ Contact me directly via👇🏻 to gain access to the book 07087865788 ✍🏻 3 💖💖 NIHAAD💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 ~~~ Gaisuwa da fatan alkhairi xuwa ga sauran membobi yan gurmin Khaleesats Palace, don gurminsu ya hana in saka sunansu jiya inga ta tsiya, Su Hajiya Aisha Bela, Hajiya Suwaiba, Hajiya Safiyya Usman😂 Hajiya Mardiyya mandy rice😜, Hajiya Sadiya uwar Hanan, Uwar Sa'eed, Hajiya Farida me kayan en gayu, Amzaj, Hajiya Zaarah, Wata ana ce mata me kayi nayi, Hajiya Aisha Macika, Hajiya Billy, Uwar Habee, har dai da wata me gawayin dare, duk na gaisheku kyauta... Sauran da basu ga sunansu ba a tsakiyar rubutu xa su gani😁 8months earlier... Zaune yake saman farar kujera dake kusa da dakin mai gadi, ya fi awa daya xaune wajen, lkci lkci yake goge zufan fuskarsa da handkerchief din hannunsa, karamar waya ya fiddo aljihunsa yana duba agogo dake nuni da karfe biyar da rabi, ya juya ya kalli mai gadi dake xaune gefensa da radionsa a hannu, xai yi magana aka danna horn, da sauri mai gadin ya ajiye radion ya mike ya isa bakin gate din gidan ya bude, wata rantsantsiyar mota ce ta shigo compound din, mutumin dake xaune ya bi motar da ido har ta isa kantamemen space da aka tanadar don parking a compound din, mai gadin ya dawo bayan ya maida gate din ya rufe yace "Bari in sanar masa kana ta jira kar ya shige ciki kuma" Daga haka ya nufi parking lot din ya jira har dattijon dake cikin motar ya sauko yana gyara babban rigar jikinsa, da ladabi me gadin ya risina yace "Barka da isowa Alhaji" Alhaji Ibrahim yace "Yauwa Aminu... " Mai gadin yace "Alhaji dama Habibu ya taho da baƙon tun daxu, shi har ya ma tafi yace yau xai koma, baƙon kuma gashi can yana jiranka tun karfe biyu" Alhaji Ibrahim ya kulle motar tasa yace "Ohk, to ya karaso" Mai gadi ya koma gun mutumin dake xaune saman farar kujera da sauri yace "Kaje nayi masa magana" Tashi mutumin yayi ya nufi parking space din, yana isa ya duka har kasa yana kallon Alhaji Ibrahim yace "Barka da yamma Alhaji" Alhaji Ibrahim na kallonsa yace "Yauwa kai ne wanda Habibun ya kawo kenan?" Mutumin yace "Eh ni ne" Alhaji yace "Ya sunanka?" Mutumin ya sauke idonsa daga kallonsa yace "Sunana Ibrahim" Alhaji Ibrahim ya jinjina kai yace "To madallah, amma ya ku ke da Habibun?" Mutumin yace "Garinmu daya da shi, ga gidanmu ga gidansu, babana aminin mahaifinsa ne" Alhaji Ibrahim yace "To ba laifi, ai har garin naku naje watanni da suka wuce" Shi dai mutumin bai ce komai ba, Alhaji Ibrahim yace "Shkkn babu damuwa, amma kayi karatu ne?" Mutumin ya girgiza kai yace "Aa iyakata sakandari, shi ma ban zana waec ba" Alhaji Ibrahim ya daga kafada yace "Ohk, xuwa kake ganin xaka dinga yi kullum ko kuma yaya tsarin naka yake?" yayi kasa da kai yace "Duk yanda ka tsara haka xa ayi Alhaji" Alhaji Ibrahim yace "Kaje dai gobe da safe ka dawo, ni yanxu xan shiga ciki in huta ne, dawowata daga aiki kenan..." yace "Toh nagode kwarai Alhaji, Allah ya kara girma" Tuni Alhaji Ibrahim ya nufi main entrance din shiga gidan nasa, ya mike ya bi sa da kallo, sannan ya kalli building din gidan wanda duplex ce gari guda, juyawa yayi ya koma gun mai gadi, mai gadin na ganinsa yace "Ya ake ciki?" yace "Yace in dawo da safe" Mai gadi yace "Ahaf ai ka ma samu, tunda ta hannun Habibu ka biyo, ai Alhaji sun fi shekara goma sha biyar da Habibu, har kauyensu ya je daurin aurensa kwanaki, in dai baka da rawan kai sannan uwa uba ace kana da nutsuwa gun aikinka to wllh tuni Alhaji xai ja ka jiki ka xama kamar d'an gida, ba ga mu ba duk mun dawo kamar yan gidan banda dai ba halinsu daya da wasu daga ahalin gidan nasa ba, to ya sunan naka?" Mutumin yace "Sunana Ibrahim" Mai gadi ya rufe baki yace "Yo ai sunan Alhajin kenan" yace "Allah sarki, Sai goben in sha Allah, xan tafi ynxu" Mai gadi yace "Allah ya kai mu" Gate ya nufa ya fita daga gidan. Alhaji Ibrahim ne xaune parlonsa, daga gefensa matarsa kuma amaryarsa Hajiya Maryam, Wasu yan mata ne biyu xaune daga kasa saman lallausan carpet dake malale parlon, Hajiya Maryam tace "Ayi hakuri Alhaji in sha Allah hakan ma baxai sake faruwa ba, ita ma Hajiya nasan bata fahimce su bane, amma xa su je su bata hakuri" Alhaji Ibrahim na kallon yan matan yace "Ku tashi ku bani waje" Duk a tare suka ce kayi hakuri Abba, yace "Ku fita nace..." Mikewa suka yi a tare suka fita daga parlon, daya daga cikin yan matan tace "Gaskiya ni ki daina ja min Nihad, ko me kika yi sai a hada mu a mana fada, da na sani da ban biki ba jiya, haba don Allah" Tsaki er uwar tayi mata ta bi wani corridor tayi gaba abunta irin ko damunta abun bai yi ba. Wata mata ce da baxata haura hamsin da bakwai ba xaune wani lafiyayyen parlor da ba a cika da kaya masu hayaniya ba, cike da ɓacin rai tace "Toh banda ma fitina da neman magana irin naku dole ne sai kun je? Me yasa baxa ku xauna inda Allah ya ijiye ku ba, maganinku kenan" Nihad tace "Ae wllh daga yau ko Abban ne yace mu je ni dai sai dai in fita inyi using opportunity din in xaga gari in sha iska in dawo abu na, i don't care... baxan sake xuwa ba gaskiya" tana kai wa nan ta mike ta dau wayarta dake caji ta fita daga parlon, Hajiya Sumayyah tace "Atoh dai, da ya fi maku, don dama magana ta ce kawai bakwa ji banda haka na hanaku xuwa tun ba yau ba" Ita dai er uwar Nihad na kwance saman kujera bata ce komai ba, Hajiya Sumayyah ta bude kofar bedroom dinta ta shiga ta kulle. Washegari asabar kasancewar yan matan gidan basu da lectures duk suka yi shirin tafiya islamiyya amma banda Nihad dake kwance parlon step mum dinta tana aikin danna waya, Hajiya Sumayyah da suke kira da Umma da tace "Ke Nihad kina kallon lkci kuwa, ko baxa ki islamiyyan bane yau ma?" Nihad tace "Umma sai gobe i have something important to do" Umma tace "To ita Nihal ma cewa tayi ba xata ba?" Bata rufe baki ba sai ga Nihal ta shigo har ta gama shiryawa, Umma ta kalli Nihad bata dae ce komai ba ta ci gaba da abinda take, Nihal tace "Hope u are been cautious of time Nihad?" Tashi Nihad tayi ta fita daga parlon tana cewa "Ni sai gobe" Mai gadi ne tsaye tare da mutumin da ya xo jiya, bayan sun gaisa mai gadin yace "Yanxu xaka ga Alhajin ya fito xai tafi gun motsa jiki, don ma yau bai fito da wuri ba, amma dai bari in sanar masu a ciki kar kuma ka yi ta jira haka babu dadi" mutumin yace "To nagode" Xaunawa yayi kan farar kujera yana bin compound din da kallo don ya kayatu da kyawawan shukoki na flowers har ma da artificial flowers, daga can wani gefe wani karamin water fall ne me ban sha'awa ruwa na ta xuba ga artificial crocodiles da kifaye a ciki, ba a dau lkci ba mai gadin ya dawo yace "Ka ga wancan yar barandar?" ya kalli inda yake nuna masa yace "Eh na gani" Mai gadin yace "Toh kaje can kayi jiran alhajin, akwai kujeru ma a wajen" Tashi yayi ya tafi wajen yana bin ko ina da kallo, bayan kujeru masu kyau har da carpet grass malale a kasa daga gefe, ga artificial flowers da ya kawata wajen, ya xauna saman daya daga kujerun wajen surveying everywhere with his eyes, bayan kusan minti sha biyar aka bude kofar parlon, tsaye tayi tana kallonsa daga sama har kasa a bit flabbergasted, ya kalleta yayi kasa da kai yace "Ina kwana" tace "Wa kake nema Malam? Daga ina haka?" Yace "Mai gidan nake jira" ta fi minti daya tana masa kallon sama har kasa, ta ma rasa me xata ce, sai kuma ta sauka kasa xuwa compound din ta tafi gun mai gadi da sauri, yana gaisheta ta ki amsawa tace "Aminu waye wancan aka bar sa xaune a kofar shiga parlor? Waye wannan?" Yace "Ranki shi dade baƙon Alhaji ne wanda Habibu ya kawo jiya, shine sabon...." Ta gwalo ido ta dakatar da shi da sauri tace "Haba Aminu, Haba Aminu, yanxu kai rashin hankalin naka ya kai haka, a tunaninka ya kamata a bar sa yaje har can ya jira Abbanmu, privacy din mu ne can din fa? ga dai kujeru a compound amma har sai yaje balcony kamar xai shiga parlor, a ina aka ta6a haka?" Aminu yayi kasa da murya yace "Wannan gaskiya ne Hajiya, ayi hakuri anyi kuskure kam, ayi hakuri" Tace "To tun wuri ka tafi kace ya dawo nan kusa da kai ya xauna ya jira Abban" Aminu yace "Toh Hajiya" tabe baki tace "Ni dama tambayarka xanyi hope jiya baku mance feeding din tsuntsaye na ba?" Ya washe baki yace "Haba dai Hajiya, ai kullum safe rana da dare sai Saminu ya basu, yau ma da asuba ina kallo yaje ya xuba masu" tace "Yauwa toh nagode, bari in je in duba su, shekaranjiya da jiya duk bama nan ban gansu ba" Yace "Da yake sai dare ku ka dawo jiya din ma" Tace "Eh fa" daga haka ta wuce ta xaga ta inda tsuntsayen suke a backyard din gidan wanda nan dinma duk shuke shuke ne, ta fi minti bakwai tana kallon kyawawan tsadaddun birds din nata ko wani breeds a cage dinsu daban, birds din iri hudu ne ko wanne me kyau har kuma da Aku a ciki, ta tafi gun akun da aka yi Seperating da sauran tace "Hello cutie" The bird was only chirping and flying around the little cage alamar he appreciates seeing her, bayan wani lkci ta bar wajen xata koma cikin gida, tsaye taga Abba a balcony bakon nasa kuma ya sauka daga saman kujera ya durkusa kasa yana sauraren Abba, kallonta kawai Abba yake da mamaki yace "Nihad ke baxa ki islamiyyan bane?" Tayi gathering courage tayi kasa da murya tace "Abba assignment nake typing anjima xan yi submitting via...." Abba ya dakatar da ita yace "Why are u skipping Islamiyya this days Nihad, last week ma na ga baki je ba ko, hakan ba dai dai bane dear" Sunkuyar da kanta tayi bayan few seconds ta dago, kallon mutumin dake kallonsu ita da Abba tayi, ta wani daure fuska wondering why he was looking at them, tana tafiya a hankali ta shiga parlor ta kullo kofar, bayan minti shidda aka sake bude kofar, har sannan Abba na tsaye speaking with the man, su uku ne duk sanye da hijab din islamiyya har kasa, Abba ya kallesu, sai kuma yace "Ke xaki yi driving din?" Tace "Eh Abba ga makullin" Amsa yayi ya mika ma mutumin dake durkushe gabansa yace "Ka ajiyesu a makaranta, xan jira ka har ka dawo" Ya amsa da ladabi yace "Toh Alhaji" shi ya fara sauka Balcony din, Autan Mumyn Nihad da ake kira da Sudais yace "Abba is he our new driver" Abba yace "Yes he is sweetheart" Duk suka yi ma Abbansu sallama suka sauka xuwa parking lot, sai da suka tsaya dai dai motar xuwa makarantarsu sannan drivern ya nufi motar shi ma, bayan ya bude duk suka shiga back seat, ya shiga ya tada motar yana warming, shi dai Abba na tsaye balcony har sannan yana kallonsu, Drivern na warming motar yaji ance "Ina kwana" ya daga kai yana kallonta ta madubi da mamaki, sai kuma yace "Ina kwana" Bayan wasu yan mintuna ya ja motar suka bar gidan xuwa islamiyyan nasu with Fadil and Sudais directing him. Parking yayi bakin gate din islamiyyan, Nihal ta bude motar ta sauka su Fadil ma duk suka sauka, bayan ta kulle motar ta kallesa tace "Sai anjima" Yace "Sai anjima Hajiya" Suka shiga makarantar, reverse yayi ya bar wajen har sannan bai daina mamaki ba. Yana isa gidan bayan mai gadi ya bude masa gate ya shiga yayi parking ya kashe motar ya sauka, gun mai gadin ya nufa ya xauna, Mai gadin yace "Inji ka yi kumallo dai?" Driver yace "Aa" Mai gadin yace "Toh bari inyi ma mai aikin gidan magana in amso maka" Daga haka ya nufi backyard din gidan xuwa kofar kitchen dake baya, Drivern dai na xaune yana ta juya makullin motar hannunsa sai ga mai gadin ya dawo da plate din dankali da kwai da kofin shayi, ya amsa yace "Nagode sosai" slice din bread ne biyar a gefen irish din da kwai wanda aka matsa ketchup a gefe shi ma, irish din ya fara ci yana dangwalawa da ketchup din, Mai gadi yace "Amma xaka dinga tafiya ne da daddare ka dawo da safe ko gidan nan xaka tsaya?" ya kallesa yace "A ina xan tsaya a nan din?" Mai gadi yace "Ka ji ka, Yo ai har Habibu ya gama yayinsa a gidan nan kafin Alhaji ya bude masa shagon da ya bude masa na tayoyi a gidan nan yake komai nasa, duk tare muke, ga can boyis kwata, su Saminu da Shafi'u masu gyaran pulawa da sharan tsakar gida da Isiya me wanki da guga ai a nan suke duk" ya dau cup din shayin ya kurba yace "Dakin babba ne?" Mai gadin yayi dariya yace "Wai daki, to har parlor akwai a ginin, sannan dakuna uku ne ko wanne da bandaki, kai har ma da kitchen a nan din" yace "To shikenan" Aminu mai gadi yace "Kai ma kayi xamanka kawai a nan xa ka fi gane kan albashin naka, kaga babu xancen kashe kudin abun hawa xuwa da tafiya sannan xa a ciyar da kai a nan ba sae ka siya komai da neran ka ba, duk abinda yan gida suka ci a nan shi mu ma muke ci" Shi dai bai ce komai ba ya gama cinye irish din tass sannan yace "Toh xan xauna nan din in sha Allah, nagode da kulawa" Ganin ya ajiye plate din Aminu yace "Ya haka, naga baka ci kwan ba? Yanxun nan fa ta soya maka" Ya girgiza kai yace "Bana so" Aminu ya dau plate din yana kokarin cin kwan yace "Allah sarki, wasu haka suke basa cin kwai sai suce yana masu karni, mu dai kam ko danyensa ne baxa mu ki ci sha ba, wa yaƙi dadi" Sai da Aminu ya cinye kwan ya mike yace "Mu je ka ga Boyis kwatan" shi ma ya tashi, yana biye da shi, suka tafi far end of the main building in which stood a Beautiful Chalet, mai gadi ne ya fara shiga, shi ma ya cire takalminsa bakin kofar shiga Chalet din kamar yanda mai gadin yayi sannan ya shiga ciki, ba laifi parlon na da girma, sannan ga kujeru har ma da tv, kaya ne ko ta ina a parlon ga wani tashi da parlon yake, everywhere looks very untidy, isiya ne tsaye parlon yana ta faman guga a ironing board, Aminu yace "Ashe kana ta guga shi yasa baka fito ba, ina Saminu?" Isiya dake ta kallon wanda Mai gadin ya shigo da yace "Suna can daki" Aminu yace "To ga bako, kun samu karuwa a nan, shine ya maye madadin Habibu a gidan nan yanxu" Mutumin ya gaida isiya, isiya ya amsa yana ci gaba da gugansa, Aminu na kallonsa yace "Mu je ka xabi dakin da xaka xauna ko" Isiya yace "Ka dai san dakin dake daga dama ni ne a ciki, na hagu kuma Saminu, wanda ke jikin na hagun Shafi'u ne a ciki" Shi dai kallonsa kawai mutumin yake, Aminu dake kallon Isiya shi ma yace "To ya xa ayi kenan" Saminu da Shafi'u ne suka fito daga dakunan su, Isiya yace "Toh ai parlon ma na da girma sai kawai ya maida nan din wajen kwanansa ko" mutumin ya gyada kai yace "Ohk to shikenan" Isiya yace "Yauwa" Aminu ya kalli su Saminu yace "Sabon direban gidan ne shi ma kuma nan xai xauna, sunansa Ibrahim kun ga sunan Alhaji ne...." Saminu yace "To sannun sa da xuwa" Tuni ya juya ya fita daga parlon ya bar mai gadi, Aminu na ganin haka ya bi bayansa da sauri... Suna tafe mai gadi yace "Amma kasan da nauyi mu dinga kiran sunan Alhaji gatsau, baka da wani sunan ko inkiya da xa mu iya dinga kiranka da?" kallonsa yayi yace "Khalil Mahaifiyata ke kirana" Aminu yace "Allah sarki, to ai mu ma sai mu ce khalil din, suna me dadi kamar na larabawa wllh" Bayan sun koma mazaunin mai gadi sun zauna, Mai gadin ya kallesa yace "Yanxu kawai kayayyakin ka xaka je gida ka debo, aikin naka ma fa ba wani me wahala bane, kaga yan makaranta motar makaranta ce ke xuwa daukansu da safe, Yan matan nan biyu kuma daya a zaria ma take karatu, dayar ce ke karatu a nan, ita warce ke karatu a nan din sai ta kai karfe biyu ma bata tafi makarantar ba, Alhaji kadai xaka ajiye karfe tara gun aikinsa, ban ki ba dae Nihad don gantali gareta kamar ta ci kafar kare, kuma sae ta fake da makaranta, a takaice dai kai Alhaji wajen aikinsa da safe shine ainahin aikinka sauran duk masu sauki ne" Khalil da har ya gaji da surutun Aminu ya gyada masa kai kawai, for the next 30mins Aminu bai yi shiru ba, Khalil har ya daina tanka masa don ya ma yi nisa a tunanin da yake, dai dai nan Alhaji ya fito, Mai gadi yayi kasa da murya yace "Da alama yau baxai je motsa jikin ba kenan tunda har gashi sha daya ta yi" Sai kuma ya mike, Khalil ma ya mike yana kallon Alhajin a bit surprised at who is standing next to him, Khalil yayi kasa da murya yace "Yan makarantar har sun taso ne?" Mai gadi ya kalli Khalil da sauri yace "Ka je yana maka magana ne" Khalill ya nufi Alhajin da hanzari, Alhaji yace "Mu je xaka ajiye mu 3 streets away from this" Khalil yace "Toh" Motar da yayi parking bayan ya ajiye yan makaranta ya nufa, Abba yace "Wancan motar ba wannan ba" Khalil ya tafi gun motar da Abba ya nuna masa, Bayan sun fita gidan Mai gadi ya kulle gate, driving Khalil yake a hankali, lkci lkci yake kallon Nihad dake zaune bayan mota da Abbanta tana danna wayarta. Ganin Khalil a layin da Alhajin yace ya ajiye su, Alhaji Ibrahim yayi mamaki sosai, don shi ya ma mance ba Habibu bane ke jan sa, bai yi masa kwatancen inda xai kai su ba ya dai ce masa 3 streets.... Ganin yayi slow down Alhaji Ibrahim yace "Noo ci gaba da tafiya, gida na uku xaka tsaya" Dai dai gidan Khalil yayi parking, Alhaji yace "Kayi horn kawai" yana yin horn mai gadi ya leko ganin motar ya koma ya bude gate din da sauri, Khalil ya shiga ciki ya samu waje yayi parking , Alhaji Ibrahim yace "Maa sha Allah, kayi jirana har in fito" Khalil yace "To Alhaji" Nihad ta sauka ta daya side din wayarta kare a kunnenta, Alhaji Ibrahim ya sauka ya nufi entrance din gidan, Ta side mirror Khalil ke kallonta amma sai yaga kamar wannan fara ce ai, Nihad dake ta xagaye da waya a kunnenta da sunan she is making call, whereas she is not kawai bata son Abba yace su shiga ciki tare ne, tana ganin Abban nata ya shiga gidan ta turo baki ta tafi can karkashin wani Thatch dake compound din wanda aim dinsa wajen shan iska, xaunawa tayi a wajen. Khalil ya sauka daga cikin motar ya tafi gun mai gadin gidan suka gaisa, Mai gadin na kallonsa yace "Ko kai ne madadin Habibu" Khalil yace "Eh nine" Mai gadin yace "Maa sha Allah" Xaunawa khalil yayi yana bin compound din da kallo, wanda shi ma yayi haduwan karshe, ya d'an juya ya kalli Side din da Nihad take, she was so engrossed with what she is doing on her phone.... U can contact me directly via👇🏻 07087865788✍🏻 4 💖💖 *NIHAAD*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 ~~~~ Gaisuwa da fatan alkhairi xuwa ga manya manyan fans dina irinsu.. Fatima Arebia, Aisha Abubakar, Maman Shukrah (Banatsapparel and more) Khadijah Dutse, mu'azatu😂, infact da duk wani member na Khaleesats palace da ban ambato ba a nan ku sani ina son ku har raina, ina yin ku, ina maku fatan alkhairi Allah ya dafa maku a duk lamuranku, My respect to many of my fans da suka fara patronizing Nihad without even waiting for the end of free pages, yawancin ku ba biyan littafin ku ka yi ba kyauta ce kawai kuke min, kuma ina alfahari da ku, ina maku fatan alkhairi da Zuri'a dayyiba. Allah ya bar xuminci, ya saka da Alkhairi ya karo maku yalwataccen arxiki, na kuma sadaukar da page din nan gare ku. Bayan minti talatin da biyar Nihad ta gaji da jiran Abbanta don har sannan bai fito daga gidan ba, ga kiran da Husnah ke ta yi mata taki dagawa don bata son tace mata bata gida tasan baxata jira ta ba, kallon agogon dake makale hannunta tayi ganin sha biyu har da minti goma ta tashi daga kan kujerar da take ta nufi khalil, Babu yabo babu fallasa tace "Hey xan koma gida kayi dropping dina yanxu" Sai da ya fara kallon mai gadi dake gefensa kamar dai da mai gadin take, ta daure fuska tace "Malam da kai fa nake?" Sai a sannan ya kalleta ya d'an kara kunnensa gaba yace "Na'am" Rasa ma me zata ce masa tayi saboda bakin ciki, har sannan fuskarta a daure tace "Ina ga dai kana da matsalar ji, dalla malam ka tashi ka maida ni gida" Yace "Naga ai Alhajin bai fito ba" Tana masa wani kallo tace "Eh na fi ka sanin bai fito ba" Yace "To kar ya fito ya tarar bana nan" Ta rike kugu cike da masifa tace "Sai ka maida ni, idan ka maida ni xaka iya dawowa idan ka ga dama" Ya dauke kai yayi shiru bai ce komai ba, shi dai mai gadi sai mazurai yake da ido babu damar ya kwaba ma khalil, shi tsoronsa ma kada wnn ɗan abin ya sa ya rasa aikinsa, yana ga kamar Khalil bai ta6a aiki gidan masu hannu da shuni bane shi yasa har ya tsaya suna ja in ja da Hajiya karama banda haka ina shi ina biyeta, ai duk abinda tace haka xa ayi, tsawar Nihad ne ya dawo da mai gadin reality don sai da ya tsorata, "Dalla Malam kana bata min lkci, are you even okay, how dare u query my order? Ko dai kana shaye shaye ne???" Khalil ya ɗan kalleta, sae kuma ya mike ya nufi motar, ta ja wani dogon tsaki ta bi bayansa kamar xata tashi sama tana harararsa, duk sai taji ranta yayi mugun baci, bayan mota ta bude ta shiga, tuni mai gadi har ya wangale gate yana daga mata hannu alamar Allah ya tsare, Khalil yayi reverse ya fita daga compound din, cikin mintuna kadan ya isa gida da ita, yana parking dai dai gate ta ja tsaki ta bude motar ta fice without closing the door, da ido ya bi ta har ta shiga gate din gidan, ya fi minti biyar tsaye da motar, daga bisanni ya sauka ya kulle door din motar, sannan ya shiga yyi reverse ya bar layin ya koma can gidan da Abba yake. Nihad na shiga gida bangaren Umma ta nufa, jefar da jakarta tayi saman kujeran parlon tana kallon Umma tace "Umma wani irin driver ne wannan Abba yayi employing, who even linked them? wllh yaron bai da kunya ko kadan Umma, kinga abinda yayi min kuwa??" Umma ta ajiye kayan hannunta tana kallonta tace "Me yayi maki?" Nihad tace "Wllh rashin kunya yayi min, ni babu wani wanda ya ta6a min haka ma tun da nake, wai yaron ya maida ni gida yaki fa" Umma tace "Aa abu me sauki sae ayi ma Abban naku magana ya sallamesa, halan d'an kauye ne?" Nihad tace "Toh ae dama su ne masu wannan tsagerancin da rashin ta idon, wllh Umma wannan idan yayi wata daya a gidan nan daina kai mu duk inda xa mu xae yi, Allah cewa xai dinga yi baxae je ba kansa tsaye idan ma bai hada mana da zagi ba, gwara kawai Abba ya dawo ya sallamesa a samo wani dama ni bai min ba from the start, irinsu ne idan an shigo da su inuwa su maida mutum rana, wai kinga me yayi min ne, jayayya fa muka tsaya muna yi da shi" Daga haka ta fice daga parlon ta tafi dakinta don ta shirya xuwa inda xa su hadu da Husnah, sae dae tana tsaka da shiryawa ta dinga kiran wayar Husnah ta ji a kashe, lkci daya ranta ya baci, kaddai har tayi tafiyarta, ta zauna gefen gado tana ta trying din layin amma ya ki connecting. Ana kiran sllhn Azahar Abba ya fito daga gidan tare da wata tsohuwa, Khalil ya mike tsaye ganinsu, suna karasowa inda yake Abba yace "Sabon drivern da na dauka kenan Hajiya, yau ya fara aiki..." Tsohuwar ta kallesa daga sama har kasa tace "To ba laifi, kuma da ganinsa xae fi Habibu kwazo duba da halittarsa, kawai dae sai mu yi fatan Allah ya sa ya fi Habibu nutsuwa, don Habibu ni kadai nasan ɗan iska" Khalil yayi kasa da kai tare da risinawa yace "Ina yini Hajiya" da fara'a tace "Lafiya lau, amma kai buzu ne koh?" Ya murmusa yana girgiza kai, Tsohuwar tace "Toh a dai kula da dukiyar mutane ka ji, kai ma sai kaga Allah ya kula da kai, baka ga motar da Habibu ya ajiye kafin ya tafi ba, duk ta fita hayyacinta daga karshe konden konden aka siyar ma, su ma din dai a walakance suka siya, ya sunanka?" Yace "Ibrahim" Buda baki tayi tace "Ikon Allah, Kai ae kawai ka zama d'an gida abun ka daga yau ka ji, babu me raina ka ko waye shi, kanka tsaye kar ka yarda da hakan, ae sunan Uban gidan naka kenan, kuma ni na haifesa, Allah yayi maku albarka gaba daya" yana murmushi yace "Ameen" Abba yace "Toh ki koma haka Hajiya, ni xan tafi" Tace "To Allah ya tsare, idan Habubakar din ya dawo xan tattauna da shi" Yace "Ba laifi, sae anjima" daga haka ya nufi motar, Khalil na biye da shi a baya. Yana ajiye Abba a gida, Abba yace "Ka tafi islamiyya ka dauko yara nasan sun tashi ynxu" Khalil yace "Toh in sha Allah" hanyar makarantar ya nufa, yana parking bakin gate sae ga Nihal, sannan Fadil da Sudais, Amina ce karshen fitowa duk suka shige bayan motar, ita kuma ta xauna gaba, ta madubi yake kallon Nihal, tace "Barka da rana" xai amsa Sudais da Fadil suka gaishesa su ma, amsa masu yayi gaba daya sannan ya maida hankalinsa kan driving din da yake. Nihad na tsaye bakin parlon Abba tana jiran ya amsa sallamar da tayi, yana amsawa ta shiga, ta karasa parlon ta xauna saman kujera tace "Abba ina yini" yace "Nihad me yasa kika ki shiga ku gaisa da inna da mutanen gidan?" Ta langwabar da kai bata ce komai ba, glasses dinsa ya saka yana maida dubansa kan laptop din gabansa, tace "Abba i came to report this new driver to you" Sake kallonta yayi yace "What about him?" Tace "Abba kawai don nace ya maida ni gida i am press shine mutumin nan ya ki, infact yi yayi kamar bai ji abinda nake cewa ba ya bar ni a tsaye" Abba yace "Is that so?" Tace "Wllh Abba, and it's not as if i was rude to him, kawai cewa nayi don Allah ka maida ni gida ina son xan koma, kawai sai yayi min banxa, wllh Sagir mai gadi ne shaidata" Abba dai yayi shiru yana kallonta, bude kofar parlon Abba aka yi sai ga su Sudais da Fadil sun shigo gaida Abban nasu ganin motarsa a gida, Nihal ce ta shigo bayansu, Abba yace "Welcome Nihal, tell the driver to wait me at the balcony...." Juyawa tayi ta fita, ba a wani dau lkci ba sai ga ta ta dawo tace "Abba na gaya masa" Abba ya ajiye laptop din kafarsa ya mike ya nufi kofa, Nihad taji wani dadi har cikin ranta dama babu abinda xata ce ma Abbanta tana so da baya yi, mikewa tayi da sauri ta bi bayansa Nihal ta bi ta da kallo, Abba na kallon Khalil bayan ya zauna saman daya daga kujerun dake wajen yace "Ibrahim me yasa tace ka maido ta gida ka ki?" Khalil ya durkusa kasa yace "Yallabai ban ki ba, ce mata nayi kar ka fito ka tarar bana nan kace inyi jiranka, amma daga karshe na daukota na dawo da ita gidan" Nihad dake jikin kofa ta hade rai jin abinda yace, Abba ya juya ya kalleta yace "Is that so?" Tace "To Abba sae fa da ya ja min rai, maimakon ina gaya masa kawai ya tashi ya kai ni gida" Abba ya kalli khalil yace "Je ka" Mikewa Khalil yayi yana kallonta yace "Kiyi hakuri, ban san haƙan xai bata maki rai ba" Wani shegen kallo tayi masa ta juya tayi wucewarta ciki. Bangaren Umma Nihad ta koma, Kamar xata fashe da kuka tace "Umma kin ga Abba bai dauki ko wani action ba dai ko?" Umma tace "Sai yace masa me?" Tace "Ba abinda yace masa, ni wllh sai dai duk abinda xai faru ya faru, da kaina xan dinga driving kaina, gashi gobe ina da lectures karfe goma a haka xai kai ni schl din? Nooo i will prefer to drive my sef" Umma tace "To idan kika tafi da motar da wanne xa a dauko kannenki daga makaranta?" Tace "Ba ga motar yaya Farooq ba ko yaya Usman" Bata jira me umma xata ce ba ta fita daga parlon xuwa kitchen, Aminu mai gadi ta gani a windown kitchen din ta baya, mai aikinsu Hafsah tana xuba wani abinci a plate, kallonta tayi tace "Abincin waye wannan?" Kafin tayi magana Aminu yace "Na sabon dreba ne" Buda baki tayi tace "Shi ma din sai an dinga basa abincin a nan? Waye yace haka?" Daga mai aiki har mai gadin suka yi shiru, tace "Ohh kawai ku kuka tsara hakan sbda ku ke siyan kayan abinci?? To Abba bai ce haka ba, ni ma kuma bance ba, saboda haka ajiye abincin nan dake hannunki baxa a kai ba, kai kuma Aminu ka kama gabanka, ba shi da portion din abinci a gidan nan" juyawa Aminu yayi ya bar wajen a sanyaye, Hafsah ta nemi plate ta rufe abincin ita ma a sanyaye, tsaki Nihad tayi ta dau plate ta debi abinda xata deba ta cika nama sannan ta fita, tana fita Nihal ta shigo kitchen din ita ma xata xuba abinci, ganin wanda Hafsah ta rufe tace "Hafsah wannan wa ya ci ya rage?" Hafsah dake wanke wanke tace "Aa ban dade da xubawa ba, Aminu ne ya xo amsar ma sabon dreba abinci Aunty Nihad ta hana" Nihal tayi shiru da mamaki, can tace "To saboda me?" Hafsah tace "Nima ban sani ba wllh" Nihal ta buɗe abincin tana kallo, can ta rufe ta kalli Hafsah tace "Ki kai masa" Hafsah ta xaro ido tace "Ta fa hana Aunty Nihal" Nihal bata kuma cewa komai ba ta dau spoon ta daura saman abincin ta fita daga kitchen, xaune ta tadda Khalil bakin gate da mai gadin, mai gadin ya dauko masa wani guntun bread dake ta ajiye dakinsa da pure water ya basa, kallonta suke gaba daya, shi dai Khalil yana kokarin gane wacece, don kamarsu ta ɓaci da Nihad, sai da ta karaso ya gane ba Nihad bace don Nihad ta fi ta haske har ma da tsayin hanci, amma both suna da dimple, ta mika masa abincin tace "Ga abincin" Amsa yayi ya d'an yi murmushi wanda iyakarsa Lips yace "Nagode" Juyawa tayi ta koma ciki, Mai gadi yace "Kaga er albarka, muna ganin abubuwan al'ajabi fa a gidan nan, halaye iri iri in gaya maka, kaga Nihal din nan da kake gani, ko kadan bata yi halin uwarta Hajiya ba, yarinya ce nutsatssiya ga sanin ya kamata, uwa uba ga girmama d'an adam ko da kuwa almajiri ne, ba dai ka ganta da kawaye ba kuma, uwarta kuwa ban ta6a ganin mace mara kirki mara mutunci irinta ba duk nan hakuri muke da ita, gashi bata da aiki sai shige ma matan manya manyan kasar nan, sannan ita kadai ce bata yarda Habibu ya ja ta a mota ba, duk sanda xata fita sai ta bari Alhaji ya fita sannan ta ja mota ita ma, bata dawowa kuma sai dab da magariba motar nan kaga duk yayi butu butu da laka malam, tana dawowa kuma xata sa Habibu ya wanke motar, ita kuma wancan Ja'irar da ta hanaka abinci ban ta6a ganin me kirki irin uwarta ba, wato matar Alhaji ta biyu kenan, ga dai ita ce ta fari gun uwarta, tsakaninsu da Nihal kwana daya tak, shi sa xaka gansu kamar yan biyu, sai kuma Allah ya basu kama daya, komai nasu iri daya ne, to wllh Hajiya Mumy uwar Nihad mace ce me mutunta mutum babu ruwan baiwar Allahn nan da duniya, sai gashi Allah ya hadata da shaidaniyar yarinya, bata da aiki sai na bitar kawaye da rashin daraja ɗan adam, to haka Allah yayi ikonsa a gidan nan, kyansa ace Nihad uwarta Umma, ita kuma Nihal uwarta Mumy kaga dai dai kenan, amma Allah bai tsara hakan ba, ni fa da rana daya aka haifesu sai muce canja su aka yi a asibiti, amma Nihal aka fara haifa er baka da ita washegari aka haifi Nihad ita kuma fara tass, kaga ko ai ba ayi canje ba" Khalil dake kallonsa yana sauraronsa attentively yace "Ita Umman yaranta nawa?" Mai gadi ya gyara xama irin abun nema ya samu din nan, yana kirga su da yatsa yace "Kaga Farouq shine ɗan ta na fari, a Habuja yake aiki, ya kan yi wata biyu ma bai leko gidan nan ba, ba laifi yana da kirki da faram faram da jama'a, shi ma kuma bai yo halin uwarsa ba gaskiya, sai Usman shi kuma kadaran kadahan, shi ba a ma gane alkibilarsa, yana da kirki oho, bashi da kirki oho, atoh a haka na san sa gaskiya, sai Kamila warce tayi aure shekara biyu kenan, wani shegen mai kudi Umman tasan yanda tayi ta hadata da ta aura, sai Nihal sannan autarsu Amina, amma fa ta fi ji da Nihal din don ita ma auta take kiranta, ita wannan Aminar ma mara kunya ce gaskiya amma fa akwai son karatun addini, tana ajin karshe na sakandari, Nihal kuma ABU Zaria take, ita Nihad makarantarta ance yayi Miliyan biyu xuwa uku, haka naji su Saminu ke cewa, Maryam Abatcha naji suka ce sunan makarantar" Khalil yace "Toh ita me xuwa Maryam Abatcha din su nawa ne gun Mamarta" Mai gadi yace "Ai ita ce ta fari, sai kanninta biyu duk maza, Sudess da Fadil" Khalil bai ce komai ba ya bude abincin hannunsa ya dau spoon ya fara ci. Nihad na gama cin abinci ta tafi bangaren Mum dinta, shiryawa ta sameta tana yi hankalinta a d'an tashe, Nihad tace "Mumy me ya faru?" Mumy tace "Yanxu Jamila ta kirani wai kanwar mijinta ta rasu" Nihad ta dafe kirji tace "Kaddai Aunty Salma?" Mumy tace "Ita" Salati Nihad ta saki tace "Allah sarki, Allah ya ji kanta, Mumy in sa Hijab mu je" Mumy tace "Ki sameni a waje, drivern bai fita ba dai ko?" Nihad tace "Mumy kiyi driving din mana ko kuma ni inyi" ko tanka ta Mumy bata yi ba ta dau handbag dinta ta fita, bangaren Umma ta fara shiga ta sanar mata rasuwan, Umma tace "Allah Ubangiji ya ji kanta, in sha Allah idan xaki koma gobe sai mu je muyi gaisuwa mu ma, Allah ya ji kan musulmi" Mumy tace "Ameen, Allah ya kai mu goben" Part din Abba ta nufa, shi ma ta sanar masa rasuwan daga haka ta fita compound, Mai gadi yayi kasa da murya yana ma Khalil magana yace "Yauwa kaga Hajiya Mumyn ita ce uwar Nihad, ina ga fita xata yi" Muryar Mumy suka ji tana cewa "Aminu Drivern ya fita ne?" Mai gadi ya mike da sauri yace "Aa gashi nan Hajiya a kusa da ni" Khalil ya mike ya gaisheta da ladabi, Mumy ta amsa cikin mutuntawa tana kallonsa daga sama har kasa, sai kuma tace "Shi ne Drivern?" Khalil yace "Ni ne Hajiya" Mumy tace "Don Allah xaka ajiye ni nan Hotoro ne idan ba damuwa" yace "Toh Hajiya" Makullin motarta ta mika masa, ya amsa da ladabi Aminu ya nuna masa motar Mumy, gun motar ya nufa, Mumy ta daga wayarta dake ringing ta kai kunne, Nihad ce ta fito ita ma sanye da Hijab har kasa, tana ganinsa cikin motar Mumy ta wani daure fuska, bayan yayi warming motar ya karaso da motar har inda Mumy take ya tsaya, Mumy ta bude bayan motar ta shiga, Nihad ma ta bude baya xata shiga mumy tace "Baxa ki xauna a gaba ba" Without looking at her mum tace "No, i will be more comfortable at the back" Kulle motar tayi ta bude handbag dinta ta ciro tsadadden shade dinta ta saka, Khalil ya ja motar Mai gadi na daga masu hannu har suka fita compound din ya kulle gate, cike da nutsuwa Khalil ke driving din xuwa hotoro da Mumy tace daga Nasarawa GRA. Suna isa dai dai family house din mijin kanwarta Jamila ta sa yayi parking, Mumy ta fara sauka daga motar tana kallonsa tace "Ko xaka je ka dawo xuwa bayan magrib ka daukemu, kar a bar ka kayi ta jira a nan" Yace "Aa babu komai xan jira daga can tsallaken in sha Allah" Jin haka Mumy tace "Toh shkkn" Daga haka ta juya ta shiga gidan rasuwar Nihad na biye da ita a baya. Nihad bata yarda ta xauna cikin jama'a da suka fara taruwa gidan ba ana koke koke, ta nemi waje at the far end of the compound ta inda generator din gidan yake ta xauna ita daya a wajen, Iphone dinta ta ciro a jakarta, taga missed calls din Husnah da Naf, da sauri tayi dialing Number Husnah, yana fara ring Husnah ta daga tace "Ina kika shiga ne babe" Nihad tace "Wllh mun fita tare da Abba ne, and i left my phone at home, what's up kun fitan ne?" Husnah tace "Tun yaushe, ke in gaya maki akwai labari wllh" Nihad tace "Yanxu dai kuna ina?" Husnah tace "Tahir guest palace, kiyi kokari ki taho yanxu kar ayi ba ke" Nihad tace "Husnah Hijab fa ne a jikina, mun xo wani gaisuwa da Mumy a hotoro" Naf ta amshe wayar don a handsfree Husnah ta sa, tace "Haba dai minti nawa kin shiga boutique Nihad" Nihad tace "Toh shkkn bari in amshi makullin motar Mumy a hannun driver in taho kawai, nasan before magrib xata koma gida kafin nan na dawo" Naf tace "Shkkn xa mu jira ki a Tahir din be fast pls" Katse wayar Nihad tayi tana bin compound din da ido trying to figure out where her mum is, har ta kare xaga tsakar gidan da idanuwanta bata ga mumy ba alamar dai ta shiga cikin gidan, tashi tayi da sauri ta nufi gate ta bude ta fita, nan ma ta dinga waige waigen inda xata hango drivern, tun da ta fito ya ganta, don yana xaune daga tsallaken bakin titi wajen mai siyar da Fruits, hada ido suka yi ta tsallaka da sauri ta nufesa babu yabo babu fallasa tace "Hey ka bani makullin mota xan mika sako in dawo yanxu" Kallon me siyar da fruits din yayi kamar dai da shi take, nan da nan Nihad ta harxuka cikin tsawa tace "Malam da kai nake fa kake kallon wani" Ya kalleta sai kuma ya kara kunnensa gaba yace "Na'am?" Nihad was soo mad at him, xuciyarta ya dinga tafarfasa ta rasa abun ce masa, shi ma kuma bai kuma cewa komai ba sae ma dauke kansa da yayi, ruwan da ta gani cikin roba gun me siyar da fruits din ta fixgo a fusace ta juye masa gaba daya tun daga saman kansa, duk mutanen dake wajen suka kame a inda suke baki bude suna kallonta da mamaki, Tana huci cikin bacin rai tace "Kai din banzaaa kana driver din gidanmu har xan dinga maka magana kana mayar ni mahaukaciya, who do u think u are?? Waye kai??" To gain access to the book, contact me directly via👇🏻 07087865788✍🏻 5️⃣💖💖 *NIHAAD* 💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 ~~~~~ Tun da Nihad ta kwara masa ruwan bai dago kansa da ya sunkuyar ba, lkci daya kamanninsa suka sauya, sae kuma dai ya daga kai ya kalleta, Tana hararansa tace "To wllh kaji ka sani, ka rasa aikinka a karkashin mu daga wannan moment din, yau ba sai gobe ba xan sa Abbana ya dau wani sabon driver din ya sallameka, baka yi deserving aiki a gidanmu ba..." Mai fruit din na girgiza kai rai bace yace "Amma baki da mutunci, baki da kirki, baki san darajan da Allah yayi ma d'an Adam ba, kuma uwa uba baki da tarbiya wllh..." Tayi masa wani matsiyacin kallo tace "Kai kuma wa ya sako da kai Malam? Kai a wa xaka sako min bakinka cikin lamarina? Ina ruwanka? Ko xaka tilasta ni in san darajan d'an Adam din ne??" Wani tsaki ta ja tana harararsa, Wani mutumi a wajen ya karbe a fusace yace "Xa ki samu dai dai dake a duniya wllh, ke yanxu irin tarbiyar da aka maki a gidanku kenan? Tir kuwa da tarbiyan gidan nan naku, tir da tarbiyan da iyayenki suka maki, idan haka arxikin ke sa mutane a hanyar halaka Allah ya hanamu..." Nan kowa na wajen yayi mata caaa, ko wanne na gasa mata magana son ransa har da masu xaginta, abun da tayi ya basu mamaki sosai ya kuma ta6a su, barin yanda suka ga khalil yayi shiru yaki ce mata komai, har da masu ce mata arxikin ma sai sun nemesa sun rasa, da surutunsu ya isheta ta ja dogon tsaki tace "Duk ku ji da abinda ya dame ku malamai, bani da ikon hukunta driver din gidanmu aka ce maku, ina ruwanku da abinda na masa banda sa ido irin na mutane" Tana fadin haka ta juya, sai ta kara jin ranta ya wani baci, yanxu ya xata yi da xuwa wajensu Husnah, kwata kwata bata son hawa adaidaita, duk k'uran duniya ya kare ma mutum, kuma ma ai ba girmanta bane taje Tahir guest palace a adaidaita Sahu, bata sake bi ta kan mutanen wajen ba ta tsallaka titi abun ta, bin ta da kallo kawai Khalil ke yi, mutanen wajen sai hakuri suke basa, wani dattijo dake tsaye shi ma wajen a kan idonsa aka yi komai ya dafa khalil cike da jimami yace "Kayi hakuri yaro, rayuwa ce, amma bari in baka shawara wannan aiki ba shine xai kai ka aljanna ba balle ka ji shakkun barinsa, ka ajiye masu makullinsu, da dai wannan axababben walakancin gwara ko dako ne kayi ka ci abinci, balle siffarka bai yi kama da ta rago ba, ga ka namiji har namiji, ka nemi wata sana'ar sai Allah ya dubeka, ni ko duk arxikin duniyar nan xa a tattara min amma a hada min da walakanci to wllh na hakura da arxikin gwara inyi ta xama da talauci na, balle irin wannan walakanci da cin fuskar da yarinyar da aƙalla xaka bata shekaru sha uku ko sha hudu tayi maka a kan titi a bainar nasi babu kunya babu tsoron Allah, sannan babu ladama a tattare da ita, aa gaskiya ka sake duba lamarin nan dai, Allah Ubangiji ya saka maka wannan cin xarafi da cin mutuncin da tayi maka" Wani matashi ne da gidansu ke nan bakin titin ya fito da wata jallabiyarsa yana kallon khalil yace "Ga wannan mu shiga wancan shagon sai ka canxa, Allah ya saka maka abinda tayi maka" Mikewa Khalil yayi ya amshi rigar yana kallon mutumin yace "Nagode sosai" shagon da ya gwada masa ya nufa, duk mutanen wajen suka bi sa da kallo cike da tausayi barin ma da suka ga ya ki cewa komai, ya shiga shagon, me shagon ya basa waje ya canxa kayansa, wayarsa dake aljihunsa ya fara cirowa ya dinga jujjuya wayar kafin ya ajiye gently a saman bench, canxa kayan yayi, me shagon ya taho masa da babban leda don ya linke tasa kayan ya sa a ciki, amsa yayi ya masa godiya sannan ya linke ya saka a ledar yana rike da ledar ya fito shagon, mai shagon ya kalli wayarsa da ya bari kan bench, ya d'an bude ido yana sake kallon wayar sannan ya kalli khalil da har ya wuce, da sauri yace "Malam ka bar wayarka" Dawowa Khalil yayi da sauri ya dau wayar, ya zira a aljihun jallabiyar, yana ɗan murmushi yace "Nagode kwarai" daga haka ya fita me shagon ya bi sa da kallo kamar me naxari. Mumy ce tsaye bakin gate ta dalilin kiranta da aka yi ganin Nihad can tsallake ga jama'a a tsattsaye sun taru an sa ta a tsakiya, Mumy na kallon Nihad tace "Lafiya Nihad, me ke faruwa?" Nihad ta rungume hannunta tace "Mumy ko ba wancan driver din bane, wllh bashi da kunya ko kadan" Mumy tace "Me yayi maki?" Nihad tace "Wai fa Sajida ce tace min tana anguwan nan, dama akwai wani textbook da nake son amsa a wajenta, shine nace ya d'an ajiye ni, can gaba ne ba nisa, shine fa yake gaya min maganar banxa, shi wai baxai je ba" Mumy tace "Sai aka yi yaya?" Nihad na yatsina fuska tace "Shikenan, su kuma wa encan bansan me yasa suka taru haka ba" Mumy tace "Ina drivern?" Nihad ta kalli tsallaken titin ta ga ya fito wani shigo da jallabiya, Kafin ta ce komai Mumy tace "Mu je wajen nasa" Da sauri Nihad tace "Aa Mumy kyalesa kawai, ni ai ban biyesa ba, haka yayi min daxu ma a gidan Baffa, aa kawai dai ki bar sa" Mumy tace "Tsallaka mu je nace, bana son surutu" Nihad tayi shiru ganin Mumy ta tsallaka ta bi bayanta, amma gaba daya she isn't comfortable, Mumy ta nufi driver, yana ganinta yace "Hajiya har kin fito?" Tace "Aa ya sunanka?" Yace "Ibrahim" Tace "Ohk, ya ku ka yi da Nihad?" Gaba daya mutanen wajen kallonsu suke, Nihad dai na tsaye ta ki karasowa ta wani sha kunu, Mumy ta kalleta tace "To karaso mana Nihad" tana tafiya a hankali ta karasa inda suke tsaye da Umma ce baxa ta ji wani shakku ba xata biyo amma Mumy bata da tabbas, Mumy na kallon khalil tace "Ina jin ka" Nihad ta amshe tace "Na fa gaya maki abinda ya faru Mumy, nan nan wajen Sajida xai ajiye ni in amso textbook shine yake min maganar banxa har sa zagina, ni ko biyesa ban yi ba" Mai fruit dake tsaye shi ma ya saki salati yace "Wllh karya take Hajiya, ba haka aka yi ba, ai ina nan a xaune, bokiti guda na ruwa ta dauka ta kwara masa kawai ba laifin tsaye balle na xaune, baki ga ya canxa kaya ba, duk a kan idonmu aka yi komai" Mumy bata bari me fruit ya rufe baki ba ta tsinka ma Nihad mari, Nihad bata gama recover ba ta kuma sauke mata wani, wanda hakan ya ba mutane da yawa dake wajen mamaki, dama ashe ana hukunta 'ya yan masu kudi, hakan ya kuma mugun burgesu, fuska daure Mumy tace "Wuce ki basa hakuri" Nihad da tunda aka haifeta tana jin ba a ta6a marinta ba ta dinga ganin dishi dishi, ta dafe kuncinta, wani tsawa da Mumy tayi mata sai da ya dada hargitsa ta, Mumy tace "Tafi ki basa hakuri nace kar 6allaki a nan" Bata san sanda ta nufesa ba ta tsaya a gabansa hawaye cike idonta cikin rawan murya tace "Kayi hakuri" Shi dai kallon Mumy yayi yace "Hajiya kiyi hakuri duk bai kai haka ba" Mumy ta bude handbag dinta fuska a murtuke ta fiddo dubu biyu ta jefa mata nan kasa tace "Ki tsayar da Tricycle ki kama hanyar gida yanxun nan, kuma ina nan biyo ki a baya, dama don kiyi displaying bad altitude dinki kika biyo ni kenan, xan yi maganinki" Kuka kawai Nihad take tana jin kamar ta kwanta nan kasa tayi ta birgima ko xata ji sanyi, ko damuwa da mutanen dake kallonta wajen bata yi ba, Mumy na kallon khalil tace "Kayi hakuri don Allah Ibrahim, ita kuma xa mu hadu a gida" Daga haka Mumy ta tsallaka ta koma cikin gidan rasuwa. Nihad ta bude jakarta tana kuka sosai ta ciro wayarta tayi dialing number Abba, yana fara ringing Abba ya daga ta kara rushewa da kuka me karfi tace "Abbaa" Sai ta xama abar kallo a wajen, Abba yace "Subhanallah what happen Nihad?" Kin cewa komai tayi banda kuka babu abinda take rera masa, Abba ya katse wayar ya kira Mumy, tana dagawa yace "Where is Nihad?" Mumy tace "What about her?" Abba yace "Ta kirani yanxu tana kuka, and she is not responding to my questions" Mumy tace "Ka rabu da ita, ai muna tare, sai anjima" Daga haka Mumy ta katse wayar. Sai bayan magrib Mumy ta dawo gida, Khalil yayi parking ya sauka daga motar, Mumy ma ta sauka, da ladabi ya mika mata makullinta, ta amsa tace "Nagode, kuma kayi hakuri da abinda yarinyar nan tayi maka ka ji" Ya d'an yi murmushi yace "Ba komai Hajiya, nagode" Juyawa tayi ta shiga cikin gidan, shi kuma ya nufa gun mai gadi. Umma na jin shigowar motar Mumy ta shigo main parlor, Tana tsaye tana jiranta har ta shigo, Umma tace "Kin bani mamaki Maryam, yanxu a kan wani shegen driver xaki kama yarinya a titi cikin mutane ki doka sbda rashin sanin ciwon kai?" Bata ba Mumy space din magana ba ta ci gaba rai a bace, "Wallahi kin ban mamaki da gaske, ke a dole sai kin xama me kirki me mutunci a idon duniya? yanxu menene amfanin abinda kika ma Nihad a bakin titi a kan wani matsiyacin talaka ɗan iska can? To wllh in dai ba Ibrahim ne ubansa ba sai ya bar gidan nan yau, aikinsa ya kare a gidan nan, idan yayi ma Nihad ya ci bulus har kuma da tsaraban mari da duka da ya ja mata to wllh babu er da xai ma hakan a gidan nan ya kwana kalau, ba a haifi Ubansa yace xai ma Nihal ko Amina haka ba, don haka yau ba sai gobe ba xai kama gabansa, mu bama hulda da yan iska, sau biyu kenan duk a yau ta kawo min kararsa, ashe d'an iska Habibu ya turo ma Alhaji ba a sani ba, to kuwa xai kama gabansa yanxu yanxun nan, kwanansa daya dubi isa da mulki da yake gwadawa ya yanmu?, nan gaba ai har Alhajin ma cewa xai yi baxai tuka a mota ba" Mumy bata kuma tsayawa ta saurareta ba ta wuce part dinta. Mai gadi na kallon Khalil bayan ya gama shanya kayan da Nihad ta xuba masa ruwa yace "Hakuri kawai xaka yi, amma lallai yarinyar nan shaidaniya ce a siffar mutum..." shi dai khalil bai ce komai ba, mai gadi yace "Ga can abinci da aka kawo mana, na debar maka naka na ajiye" Khalil yace "Aa na koshi, yanxu wanka nake so xan yi" Mai gadi yace "To mu je in raka ka bangarenku" A tare suka nufi boys quarters din bayan mai gadi ya dauko wata er jakar kayan Khalil da ya bari a dakinsa tun xuwansa da safe, suna shiga parlon banda warin kartin maza babu abinda yake, ko ina soo dirty and unkept, ga saminu yayi bake bake kan 3 seater yana kallo ga plate din abinci da ya ajiye saman kujeran, Isiya na one sitter yana shan rake da yake tarawa nan kasa gefensa, Shafi'u kuma na 2 seater ga tasa plate din abincin ya gama ci ya bari saman kujera, Mai gadi ya nufi Saminu yayi kasa da murya yace "Saminu ko xaka ɗan sam masa waje ya dinga kwana a dakinka, ka gansa bashi da matsala wllh..." Ko rufe baki Mai gadi bai yi ba Saminu yayi saurin cewa "Aa nima dakin yayi min kadan" Mai gadi ya kalli Isiya dake jin abinda ya ke cewa, kafin mai gadin yace masa komai yace "Toh wai ba falo kace xai dinga kwana ba" Shafi'u yace "Shi dai na gani, Duka dakunan kaga ai babu waje, wa ke son takura" Khalil ya amshi jakarsa dake hannun mai gadi, mai gadi yace "Ko xa mu je can dakin nawa ka dinga kwana" Khalil yace "Aa kar ka damu, kayi komawar ka bakin gate" Yana fadin haka ya nufi space da aka tanadar domin dinning area a parlon, Kofar da ya gani ya bude ya ga kitchen ne, ya dinga kallon yanda suka mayar da kitchen din kamar na mahaukata duk da ba girki suke ba, tsintsiyar da ya gani wanda bai ga alamar ana amfani da shi ba ya dauka, ya hau share dinning area din, mai gadi ya juya ya fita daga parlon da sauri jin kamar ana horn. Cikin yan mintuna khalil ya gama gyara area din har da mopping, yana gamawa sai ga mai gadi ya kawo masa wani yakunannen zanin gado, amsa yayi ya shimfida a saman tiles din wajen, sannan ya bude window, ya shiga bandakin dake parlon, still yayi yana bin bathroom din da kallo, ko public toilet is far far better and neater than this, fita yayi ya koma gun mai gadi don ya amshi omo. Abba yayi shiru yana sauraron Mumy, Mumy ta ci gaba tace "Kawai ita Hajiya duk wani abu na cin mutunci da cin fuska shine dai dai a wajenta, ai wannan ba rayuwa me kyau bane, har take cewa ka sallamesa, da yayi me? Ruwa fa ta dauka gun me kayan marmari ta watsa masa a jiki, kawai dai ka haifi yaro baka haifi halinsa ba, haka ta sa Habibu a gaba daga baya ta gaji ta saukar da kanta, mai aikin gidan nan ba dadin Nihad take ji ba, Nihal kuma ba haka take ba, na rasa wannan baƙin hali irin na Nihad ni kam, ni dai ba haka taga nake mu'amala da jama'a ba balle tace, kai kanka ba haka mu'amalar ka da jama'a yake ba, to halin wa ta yo haka, idan ba shiga hakki ba wllh kar ka fara ce ma bawan Allahn nan komai, a kan me xata ce sai ya bata makullin motata ta tafi gantalinta da yamma sbda rashin kunya ma bata yi shakkar cewar motar tawa bace, kuma naga ai ba ita ta basa makullin ba ni na basa, to a kan me xai bata..." Abba dai yayi shiru bai ce komai ba, ganin ta gama fadin abinda xata fada yace "But that doesn't warrant u to slap her publicly Maryam, why not ki bari idan kuka dawo gida ki hukunta ta?" Mumy tace "Wato na goyi bayanta kenan Yallabai, ai yanda tayi rashin kirkinta a bainar jama'a gwara nima na hukuntata a cikin jama'ar dai dai kenan, ni fa i am not in support of walakanta d'an Adam Yallabai, kuma babu wani da ya fi wani a wajen Allah sai wanda yafi tsoronsa, idan ma xaka share xancen nan ka je ka huta to gwara ka share" Abba bai kuma cewa komai ba, Mumy tace "Can i excuse my self?" Yace "Alright" ta mike tayi masa sai da safe sannan ta fita, Umma ta fito daga bedroom din Abba don duk ta ji yanda suka yi da Mumy, tana ta6e baki tace "Yau ni naga neman suna kiri kiri gun talakawa, ita a neman sunan ma ta rasa inda xata dinga yi sai wajen talaka? Ai kamata yayi ta dinga kutsa kanta cikin manyan mutane ana yi da ita, ta nan ne neman suna xai mata rana, amma ke kice duk abinda talaka yayi dai dai ne, a dole sai kin burge?" Abba ya mike ya fita daga parlon, compound ya fito, dai dai nan khalil ya fito daga dakin mai gadi ya amshi omo, ganin Abba ya nufesa ya gaida shi da ladabi, Abba ya amsa yana kallonsa yace "Ibrahim, a dinga hakuri da yaran nan don Allah, sannan duk sanda Nihad ta sameka da batun amsan makullin mota kana da number ta ka kirani, idan wanda xaka bata ne sai ince ka bata, don ba wai bata iya driving ba, tana driving to where ever she wants to, just sbda security purpose ne bana barin suyi driving din da kansu, so kar kayi zaton bata iya driving din bane, and u gat respect them all kamar yanda xaka yi respecting dina ka ji" Khalil da kansa ke kasa a hankali yace "Toh in sha Allah Alhaji" Abba yace "Sun baka daki a can boys quarters din ko? Don nasan akwai empty room da Habibu ya bari" Khalil yace "Ehh an bani" Abba na kallon omon hannunsa yace "Wanki xaka yi da omo?" Yace "Eh xan wanke bandaki ne" Abba yace "Ohk good, wannan ai yayi kadan, no problem xa a kawo maka daga cikin gida yanxu" Yace "To nagode Alhaji" daga haka Abba ya juya ya koma cikin gida, khalil ya koma can boys quarters din. Abba na komawa part dinsa ya kalli Umma yace "Ki ba ko Sudais ne blanket with some detergents ya kai boys quarters" Umma tace "A kai ma wa a can?" Abba yace "Driver" Umma tace "Aa da dai kaje gun uwar dakinsa ta bada a kai masa, ni kam bani da old blanket, kaji Alhaji da wani xance, shine yace ka basa blanket din?" mikewa Abba yayi ya fita, ya tafi bangaren Mumy, tana daki ya sameta yace "Maryam blanket xaki ba Sudais with some detergents ya kai ma driver din can" Mumy tace "Sudais ai yayi bacci yallabai" Abba yace "To bani" Wani blanket dinta ta dauko, sannan ta dau pack din omo da sabulu with toothpaste ta hada ta ba Abba, Abba ya amsa ya fita dakin, a stairs ya hadu da Nihal xata dakinsu, tace "Abba where are u going with the blanket" Yace "Boys quarters xa a kai ma drivern can" Nihal tace "Ohk, bari in kai Abba" Abba yace "Good" Amsa tayi daga hannunsa don dama da Hijab a jikinta ta juya ta koma downstairs ta nufi kofar fita main parlor, boys quarters din ta nufa, tayi Knocking duk da kofar a bude take, isiya ne ya karaso ganinta ya gaisheta da ladabi xai amshi blanket din yace "Wanki ne Hajiya?" Tace "Aa, ina sabon driver yake?" Jin haka Khalil dake bandaki xai fara wankewa ya fito ya nufi kofar, kallonta ya dinga yi don da farko ya xata Nihad ce, amma sai yaga ba itan bace don wannan fuskarta bai rabo da murmushi, ya amshi abinda take mika masa, yace "Nagode sosai" Juyawa tayi ta sauka chalet din, ya koma cikin parlon yana kallonsu Isiya yace "Ku yi kokari ku bar barin kofar nan a bude sbda sauro" Da ido duk suka bi sa, lkci daya suka kya6e baki, ya ajiye blanket din ganin omo, sabulun wanki da na wanka sannan ga Toothpaste ya kwashe su gaba daya ya wuce bandakin, ya bata fiye da minti talatin yana wankin bandakin don sae da omon yayi rabi, lkci daya bandakin ya dawo hayyacinsa, wanka yyi ya fito, ya kulle bandakin da makulli sannan ya cire makullin ya koma dinning area, ya shimfida babban bargon wanda laushinsa ba a cewa komai, ya bude window dake wajen sannan ya kwanta ya rufe ido, bayan minti sha biyar yaji ana magana, ya bude ido ya ga Saminu tsaye a kansa, shiru yayi yana kallonsa, Saminu yace "Makullin bandaki da ka kulle xaka bada" Khalil yace "Ohk, dama kuna amfani da bandakin kenan?" Saminu yace "Yo me xai hana" Khalil yace "Ohk, shine ku ka bar shi yanda na samesa?" Bai jira Saminu yace komai ba, yace "Amma dai kamar babu bandaki a dakunan naku iya wannan kadai ne ko?" Saminu yace "Akwai mana, amma wannan din muke shiga gaba daya ai" Khalil ya ciro makullin da ya ajiye a aljihun gaban rigarsa ya mayar aljihun wando sannan ya gyara kwanciyarsa ya rufe ido, xuwa yanxu daga Isiya har Shafi'u na tsaye parlon suna kallonsa gaba daya, Saminu yace "Toh wai kai gayen nan me kake nufi tukunna ma dai" Mikewa Khalil yayi ya tsaya sai ga Saminu ɗan tsut a gabansa, Khalil na kallonsa da kyau ya tsaya dab da shi yace "Baxan bada ba nake nufi" Shafi'u ya koma ya xauna haka ma Isiya suna kikkifta ido, sui sui Saminu ya bar dinning area din shi ma yana gwaggwale ido. 07087865788✍🏻 6️⃣ 💖💖 *NIHAAD* 💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 ~~~~~~ Washegari Monday har karfe tara Nihad na ta kwance a dakinta, karfe tara da rabi aka bude kofar dakin, ta juya ganin Umma ce ta shigo ta mike xaune a hankali, Umma tace "Baxa ki makarantar bane Nihad, naga yau Monday" Nihad tace "Lectures din karfe goma ne, Nihal ta tafi islamiyya?" Umma tace "Tun yaushe, ke dai kam na san ba xa ki ba" Nihad bata ce komai ba, Umma ta juya ta fita, sauka tayi daga saman gadon ta shiga bandaki, nan ma sai da ta bata kusan minti arba'in sannan ta fito, shiryawa tayi cikin tsadadden bakar Abaya, wurin shirin ma ta 6ata kusan minti talatin, banda kamshi babu abinda ke tashi a ko ina na jikinta, sosai Abayar ta amshi farin fatarta kai kace balarabiya ce, ta dau karamin handbag ta sa flat shoe sannan ta fito daga dakin bata kulle ba don Hafsah xata shiga tayi mata gyaran dakin sannan ta wanke mata bandaki, tana tafiya kamar bata son tafiyar ta tafi part din Mumy ta bude kofar parlon, xaune ta ganta parlon tana waya, ta cire takalminta nan bakin kofa ta karasa ciki a hankali, ta xauna saman kujera fuskar nan nata babu yabo babu fallasa, har Mumy ta gama wayar sannan ta gaisheta, Mumy ta amsa mata ita ma a dakile without looking at her, mikewa tayi tace "Xan tafi makaranta" Mumy tace "Allah ya tsare" fita tayi daga parlon ta wuce part din Umma, Umma tace "Ashe dai za ki, toh Breakfast din fa?" Tace "Xan yi a makaranta" Umma tace "Toh Allah ya tsare" Kamar xata yi kuka tace "Umma ni gaskiya baxan iya shiga mota daya da wannan yaron ba" Umma tace "Toh yanxu ya xa ayi, idan na tafi na amsar maki makullin kin san anjima xa a dauko yara a makaranta" A hankali Nihad tace "Toh pls Umma zaki bani makullin motar ya Farooq" Umma ta rike ha6a tace "Farooq, to bari dai in dauko maki" cike da farin ciki Nihad tace "Yauwa Umma, karfe hudu xan dawo in sha Allah baxan wuce haka ba" Mikewa Umma tayi ta fita daga parlonta ta wuce dakin First son dinta, makullin dake jikin kofar ta murda sannan ta bude ta shiga ciki ta dauko makullin motarsa ta fito, farin ciki sosai Nihad tayi ta mashi makullin tana murmushi tace "Umma nagode" Umma tace "Toh ki tafi a hankali dai, kar ki kwarzane masa mota mu shiga uku" Nihad tace "A hankali xan tafi Umma" Daga haka tayi ma Umma sallama ta fita daga parlon cike da murna, ta fitowa compound taga mai gadi xaune tare da Khalil, lokaci daya ta wani murtuke fuska, ta nufi mai gadi tana juya makullin hannunta tace "Hey Bude min gate xan fita" Tashi yayi da sauri ya tafi xai bude gate din, ta nufi motar yayanta, ta gefen ido khalil ya bi ta da kallo, har ta shiga motar, bayan ta gama warming tayi zoom off out of the compound duk don ta tada k'uran interlock, Mai gadi ya daga mata hannu yace "Allah ya tsare Hajiya" ko kallonsa bata yi ba balle ta tanka, ta ja motar tayi gaba, kulle gate din yayi ya dawo yana kallon khalil yace "Hajiya ce xata bata motar Farooq da yake baya gari, kuma ina tabbatar maka uwarta bata sani ba, dama Umman ke daure mata tayi ta abinda ta ga dama a gidan nan ai, kai kam huta roro" Khalil yayi murmushi yace "Yanxu ina xata haka?" Mai gadi ya xauna yace "Wai Makaranta mana, kasan jami'arta shegen tsada ke garai" Khalil yace "Ita er uwarta fa?" Mai gadi yace "Baiwar Allah, ba daxu ka ajiyeta a islamiyya ba, hutun makaranta ta dawo, amma kaga kullum sai taje islamiyya abunta..." Khalil yace "Wacce makarantar take ita?" Mai gadi yace "Ba nace maka a Zaria take, Ahmadu Bello" Khalil bai kuma cewa komai ba. Nihad na driving tayi dialing number Husnah, Yana fara ringing Husnah ta daga, Nihad tace "Kin shiga school ne?" Husnah tace "Me yasa kika kashe wayarki jiya bayan munyi dake kina tahowa?" Nihad ta sauke ajiyar xuciya tace "It's a long story, but ya na ji muryarki haka, are you okay?" Husnah tace "Partially" Nihad tace "Where are u at now?" Husnah tace "Ni'ima guest palace" Nihad tace "Really? To bari in taho nan kawai, nima I'm not even in the mood of attending lectures today" Husnah tace "Sai kin xo" Katse wayar Nihad tayi ta dau hanyar Ni'ima guest palace din. Nihad na isa tayi parking ta kirata, nan Husnah ta sanar mata room number dinta, Nihad ta sauka motar ta shiga ciki, Knocking tayi kofar dakin, Naf ta bude, Nihad ta d'an buda ido ganin Husnah a kwance ta lulluba, ta kalli Naf tace "Is she okay?" Naf tace "Shigo in kulle kofa" Nihad ta shiga ta karasa gun Husnah, ta xauna gefen gadon tana kai hannu jikinta tace "Ya dai Husnah?" Husnah ta mike xaune tana ta6e baki tace "Ashe Yaks d'an iska ne duk bamu sani ba" Nihad ta ɗan bude ido tace "Me ya faru?" Husnah tace "Kawai yaje ya sha kwayoyinsa jiya in gaya maki yayi assaulting dina" Nihad ta xaro ido tace "Really?" Husnah tace "Wllh ke dai in gaya maki, ban da abunsa ai i wouldn't have denied him" Nihad tace "Where was Nafee then?" Husnah tace "Ita suna tare da saurayinta, kin san shi ma ya zo" Da mamaki Nihad tace "Yaks??" Husnah tace "Ai kuwa baki ga yanda ya dinga tambayarki ba, nace kina hanya duk ya damu baki iso ba, ke gwara ma da baki xo ba din, kilan rashin xuwanki ya sa haka ya faru," Nihad tayi shiru, can tace "Tabdi, kuma a Tahir guest palace din?" Husnah tace "Wane Tahir, ai ba a can muka yi birthday din ba, ke kinga haduwar birthday din nan kuwa Nihad?? Gaskiya na jima ban ga birthday da yayi haduwar na Maska ba, it was light" Nihad tace "Ni xancen yaks ne ya tsaya min a rai, Shi yasa fa kike ganin bana kula clique dinsu, bana harka da maza marasu aji" Husnah tayi dariya tace "Ni kawai way of approach dinsa ne ya kona min rai, amma what's there? norms ne ai, someone that i have been crushing on from day one" Nihad tace "To karfe nawa ku ka bar wajen?" Husnah tace "Kai dare yayi fa sosai, ke ni fa wllh gwara ma da Allah ya hanaki xuwa nace maki, don da ban san ya xan yi da ke ba a wajen ga uban daren da muka yi, cabb to wa ma xai saurareki, gaskiya birthday din nan yayi armashi, ai da naga daren yayi sosai shine na fasa komawa hostel kawai muka kama daki a nan ni da Surayya, ita Naf fa sai yau da safe ta xo nan ta same mu" Nihad ta kyabe baki ta ajiye handbag dinta tace "I am jet hungry banyi breakfast ba, me suke siyarwa a nan?" Husnah tace "Ke bamu dade da waya da Ayman ba xai taho mana da abinci yanxu, bari in kirasa ince plate uku xai kawo, shi ma jiya ya dawo daga Egypt" Daga haka Husnah ta kirasa ta sanar masa ya dado wani plate din, bayan ta ajiye wayar tana kallon Nihad tace "Amma jiyan me ya hanaki xuwa don Allah?" Nihad ta sauke wani ajiyar xuciya irin na takaici tace "Husnah in gaya maki wani sabon driver Abba ya dauka, kin san ai ya bude ma Habibu Shago" Husnah ta gwalo ido tace "Don Allah, kina nufin yanxu babu Habibu? Allah sarki, kai amma xaki yi kewan Habibu, sau da yawa fa da shi kike hada baki, gashi duk inda kika ce ya kai ki kai tsaye yake kai ki, har ma ya jira ki" Nihad ta marairaice tace "Ke dai bari, ai ni aka yi ma da Habibu ya bar driving, sau nawa yake kai ni Tahir ko Bristol or prince hotel, kuma ya jirani komin dadewar da xa mu yi, sau nawa xa mu fita in amshi mota a hannunsa shi ya tafi harkar gabansa nima inyi tafiyata, sai na gama xan kirasa mu hadu a busstop mu koma gida, Yawanci ba shi nake aika ya siyo min duk abinda nake bukata ba, ai har kuka sai da nayi da naji Abba ya bude masa shago, Habibu ai mutum ne" Husnah tace "Amma fa ya ci kudinki ba karya" Nihad tace "I wish Allah xai ta6a xuciyar Abba ya dawo mana da Habibu kawai" Husnah tace "Toh shi sabon da aka dauka fa?" Nihad ta gyara xama tace "Ai shi xan baki labari yanxu, wato wani tatattcen d'an iska, mara kunya Abba ya dauko mana as driver Husnah, kinsan jiya a kansa sai da Mumy ta mareni har sau biyu a titi cikin jama'a? Husnah as i am talking to u now i am boiling inside, tun shekaranjiya nake cikin ɓacin rai da bakin cikin mutumin nan, daga fara aiki shekaranjiya har ya raina ni baya girmama ni, ina masa magana sai yayi min banxa ko kuma ya kalle wanda ke kusa da shi irin dai kamar ba da shi nake ba da na kusa da shi nake, ko kuma ya kara min sheggun kunnuwansa gaba, irin dai na raini da tantiranci, Husnah yayi mugun raina ni wllh, yanxu maganar da nake maki motar ya Farooq Umma ta bani makulli na fito da shi, baxan juri xama a mota ni da shi yana driving dina ba...." Tuni har hawaye ya cika idonta, Husnah dake ta sauraronta da mugun mamaki ta gyara xama tace "What?? Shi ordinary driver din yake duk wannan abinda kika lissafo min kuma kika kyalesa? Ta yaya kika basa wannan fuskar ya rainaki daga fara aikinsa Nihad? Waye shi haka, kuma a ina Abba ya samo sa?? Wai ma garin yaya kika yi creating room for this bullshit" Nihad na shessheka tace "Baxa ki gane ba, wllh irin yan iskan nan ne yaron, cikin ruwan sanyi yake raininsa da rashin mutunci, idan kin gansa ma xa kiyi xaton baya magana nan ko katon ɗan iska ne, yanda fa kika san motarsa haka yake jin kansa daga fara aiki" Husnah ta rike ha6a tace "Tabdi... to kuwa xa mu yi maganinsa, but what did Abba say about it? Ko baki kai kararsa ba har yanxu?" Nihad tace "Babu wani action da Abba ya dauka tunda Mumy ta zuzzuga sa, har Umma ma ta saka baki amma Abba yaki daukan kwakkwaran action, the painful part of it is that Mumy supporting dinsa take kamar ta ta6a saninsa, kinsan yanda take abubuwanta dai, to wllh a kansa ta gaggaura min mari jiya a tsakiyar Hotoro dalilin da yasa na fasa xuwa Tahir palace kenan, to wannan ne har xan dinga basa kudi yana kai ni duk inda nake so ba tare da yayi casting dina ba wataran? Ina ai baxai yiwu ba, bana harka da fitsararrun yara ni...." Husnah tace "Calm down besty, shi karamin kwaro ne wllh, kuma xa mu yi maganinsa, Clique dinmu kadai mun ishesa" Naf dake ta sauraronsu ta kyabe baki tace "Lallai wnn ɗan iska ne number 1, daga wani kauyen aka samo maku shi halan? Shi a yan kauyen ma shege ne fa" Nihad tace "How will i even know, wlh d'an rainin wayo ne na karshe, gashi baya wani magana nake gaya maku, yanda kuka san kurma, cikin ruwan sanyi yake rashin mutunci da raini, ga wani ji da kai, to kana aiki karkashin mutane kana driving ina wani ji da kai??" Kwankwasa kofar aka yi, Husnah tace "Ayman is here..." Naf ta nufi kofar ta bude, wani matashi ya shigo dakin rike da takeaway uku with many drinks da bottle water, Ya ajiye ledan yana kallon Nihad yace "Manyan mata, ashe dai kina kasar nan Nihad?" Nihad tace "To an zuga Abbana ya ki kai ni UK karatu ba dole a gan ni a kasar ba" Dariya yayi yace "Gaskiya ne, to ya kwana da yawa, kinsan ku manya ne ba kowa ku ke replying ma chat ba both WhatsApp and IG" Nihad tace "Not at all" Husnah ta mike ta dauko takeaway daya ta ajiye ma Nihad, Ayman na kallon Husnah yace "I think bari in kama wani dakin kawai" Husnah tace "Ohk then" Daga haka ya fita daga dakin, Naf ta ja tsaki tace "Sai shegen girman kai, wato jira yake in fara masa magana ko" Husnah tace "Ke dai kowa sai kice yana da girman kai bayan kema kina fama da naki, duk fa Salman ne ya hura maki kunne ki daina kula kowa sai ki dinga fakewa da ana maki girman kai" Naf tace "Ni fita ma xan xo in yi yanxu, amma xan dawo later" Husnah tace "Ina xa ki? Baxa ki ci abincin ba?" Tace "Idan na dawo xan ci" Husnah tace "Kar fa ki ki dawowa Naf, saboda ke naki gayyato Zully nan fa" Naf tace "Ke wllh xan dawo, wani Alhaji ne ke ta damuna da kira ya shigo kano, to yayi min alkawarin waya dama, shine xan je" Husnah tace "Ahh, to maza ki je, Allah ya sa mu ga latest iphone" Naf ta dau figigin gyalenta tace "Toh Allah ya sa bari in je, Nihad idan na dawo xa mu tsara yanda xa ayi da ɗan kauyen can shi kuma" Nihad tace "Toh sai kin dawo" Daga haka Naf ta fita daga dakin, Husnah tace "Tabdi, yau ni naga karfin hali wai barawo da sallama, wannan idan yayi wata daya a gidan ai sai dai kuma ya koma rayuwa cikin main building ya bar boys quarters kawai" Nihad tace "Sai yanzu rashin barina in xauna a hostel da Mumy tayi ke kara damuna sosai, kinsan da na hakura amma tun da aka kawo wannan drivern damuwan ya dawo sabo" Husnah tace "To ko xaki kara gwada yi ma Abba magana?" Nihad tace "Babu yanda Umma bata yi da shi ba, amma da yake Mumy da ya farooq sun hure masa kunne ya ki amincewa, sae dae kawai yayi ta bani hakuri wai there is time for everything" Husnah tace "Gaskiya in har ba sallaman driver din nan aka yi ba xaki takura sosai, gashi Abba baxai baki mota ba ko" Nihad tace "Ba fa ruwan Abba, Mumy ce matsalar gidan nan sae yaya Farooq, amma ae Umma tayi kokarin ganin an bani motar kwanaki hakan bai yiwu ba" Husnah xata yi magana wayarta ya fara ring, tana dubawa taga Ayman ne, dagawa tayi tace "Ya? Wani room number kake?" Yace "102... Pls Nihad ta bani minti goma mu yi magana mana" Husnah tace "Ohk over there?" Yace "Yeah" katse wayar tayi tana kallon Nihad tace "Ayman wants to speak to you" Nihad tace "Ohk kin katse wayar kuma" Husnah tace "No, yana room 102" Nihad tace "Ina ga ya sha kwaya, nice xan bi sa dakin??" Husnah tace "C'mon, minti nawa xa kiyi ki fito, he said just 10 mins, behave like the big girl u are mana" Nihad tace "Look, ya bar ni ma inji da damuwata i don't have that strength to talk" Husnah tace "Don Allah kiyi hakuri ki je Nihad, minti goman nayi ko bai gama magana ba ki fito kawai, ko albarkacina ya ci mana, yana ganin idan na gaya maki xaki ji shi yasa ya biyo ta wajena, ki je ki dawo ki ji yanda xa mu yi da wancan ɗan kauyen shi kuma" Nihad ta d'an kyabe baki, sai kuma ta mike tana gyara veil din abayanta tace "Wani room ma kika ce?" Husnah ta gaya mata, daga nan ta fita xuwa dakin. Kwankwasa kofar dakin tayi, sai gashi ya bude yana kallonta da murmushi fuskarsa yace "Welcome Nihad" gefensa ta bi ta shiga dakin ta xauna saman one seater dake dakin tana kallonsa har ya dawo ya xauna gefen gado sannan tace "I am all ears" shiru yayi yana kallonta, ta langwabar da kai tace "Kayi shiru" Ɗan murmushi yayi yace "Donno where to start from, kinsan kina da wani kwarjini na daban Nihad" Ta kalli agogon dake wrist dinta, sannan tace "Then just start from d end" Dariya yayi sannan yace "Ohk, a takaice kawai ina son ki bani dama let date" Tace "Sorry but i don't double date Ayman" Yace "What's d big deal about double dating Nihad?" Ta girgiza kai tace "Tsari na kenan, i have my boyfriend, and yana sona kamar yanda nima nake son sa, so what's d need of dating else where?" Shiru Ayman yayi, can ya mike ya koma kan kujerar da take ya xauna a hannun kujeran xai kama hannunta ta fixge ta matsa gefe sannan tace "I am sorry Ayman, ina da saurayina kuma duk kun sani" Yayi kasa da murya yace "Yeah i know, but pls Nihad... even if it's once a while, i will always provide u with all ur needs, i am not talking about petty needs" Da mamaki tace "What's that u are talking about?" The way he was looking at her directly in the eyes yasa ta mike tana kallonsa da kyau tace "Seems Husnah bata ta6a baka labarina ba ko?? Kawai kana ganin mu tare, duk inda take xaka gan ni, Ohk get this Ayman, my obstinacy have limit, it hasn't attain to this extent, sorry" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice daga dakin ta kullo masa kofar. Tana komawa wajen Husnah, Husnah ta katse wayar da take ta ajiye, Nihad tace "Baki ta6a gaya ma Ayman wacece ni ba ko?" Husnah bata ce mata komai ba, Nihad ta nemi waje ta xauna, Husnah tace "Toh wai meye a ciki, kawai kin bi kin makale ma Aliyu da definitely kinsan yana da yan mata iri iri shi ma, ni wllh Aliyun nan haushi yake bani, ga shegen ji da kai kamar ɗan jinin sarauta, duk abinda ya daura ki a kai shi kike yi, ga samari iri iri ko wanne na sonki amma kince ke sai Aliyu, to Aliyun me" Nan da nan Nihad ta hade rai tana kallon Husnah, can ta ja tsaki ta dau jakarta ta mike ta nufi kofa, Husnah tace "Tun da an ta6a numfashin ki ba dole ki nufi kofa ba, to baxa ki tsaya ki ji yanda xa mu yi da sabon drivern naku ba" Ko sauraronta Nihad bata yi ba har ta fice daga dakin, Husnah ta ta6e baki tace "Kawai ki makale ma mutumin da yan mata ke rububi a kansa, ki dauki son duniya ki dora masa, shi kuma yayi ta yin kamar bai san kina yi ba, da ma yana baki lokacinsa yanda ya kamata ne abun baxai dameni ba" Husnah ta ja tsaki ta jawo abincin gabanta ta bude..... Contact me directly via👇🏻 07087865788 WhatsApp only. 7️⃣ 💖💖 *NIHAAD*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 ~~~~~~~ Sai bayan la'asar Nihad ta iso gida, bayan ta fito daga wajen Husnah school kawai ta wuce tayi attending lectures daya, mai gadi na bude gate ta shiga gidan ba tare da ta saurari gaisheta da yake ba, tayi parking dai dai inda motar take ta kashe, sauka tayi ta kulle motar tana kallon inda mai gadin ke xama ko xata ga Khalil, ai ko yana xaune, ko da wasa bai kalli inda take ba, sai ma danna torchlight phone dake hannunsa da yake with full concentration, nan da nan taji har ranta ya fara baci, wai wa yayi ma wannan mutumin hanyar xuwa neman aiki a gidansu? har ta juya xata wuce ciki sai kuma ta dawo, fuskarta daure ta nufesu, Mai gadi na ganin ta doso inda suke ya mike daga xaunen da yake yana gaisheta, Babu yabo babu fallasa ta amsa sannan tace "Aminu kuna canza ma tsuntsaye na abinci da ruwa kuwa??" Yace "Ehh Hajiya ko daxu da kaina naje wajen na basu abinci da ruwan" Mai gadi ne ke mata magana amma banda hararan khalil babu abinda take with hatred, how dare him baxai gaisheta ba ma, wani dogon tsaki ta ja tace "Aminu ka sameni wajen tsuntsayen" Daga haka ta wuce fuuu xuwa bayan gidan inda cage din birds din nata suke, Aminu ya kalli khalil sannan ya bi bayanta da sauri, sai a snn Khalil ya daga kai ya bi su da kallo, suna isa wajen tsuntsayen tace "Aminu in tambayeka mana" Yayi kasa da kai yace "Toh Hajiya" Tace "Wai waye ya kawo wancan yaron gidan nan da sunan ya nemi aikin driving?" Aminu yace "Hajiya Habibu ne ya kawosa ae" Da mamaki tace "Habibu??? Habibu dai?" Aminu yace "Kwarai Hajiya" Juyawa tayi ta wuce ta bar sa tsaye a wajen, gida ta shige, Aminu ya dawo bakin gate ya xauna yana kallon khalil dake kallonsa shi ma, yayi kasa da murya yace "Wai tambaya take wa ya kawoka, to ban san ko na kwabsa ba da nace Habibu, kasan fa Habibu mutuminta ne, har makudan kudi tana basa, to duk inda xata kai tsaye yake kai ta har ya jirata, ya sha gaya min maganganu amma yace kar in gaya ma kowa" Khalil yace "Wani magana?" Aminu ya gyara xama yace "Ae otal daddaya ne a garin nan da wajen shakatawa irin ta manya bai ta6a ajiyeta ba... Kai duk dai wani otal dake kano da ya amsa sunansa otal xuwa take, wani lkcn tun safe sae dare xae je ya daukota, Khalil dake ta kallonsa da mamaki yace "Hotel?? Me ke kai ta can?" Aminu yace "Ahaf ka ji ka da wani xance, me ake zuwa yi otal, kuma kaf babu wanda ya sani a gidan nan sae Habibu sae kuma ni da yake gaya ma, kai wani lkcn har Habuja tana xuwa kuma ta dawo a ranan, kasan sha'anin jirgi, peee ta tafi peee ta dawo ita da kawayenta, babu wanda xae sani, duk kowa tunaninsa tana makaranta, ita ce Kaduna, Ita ce legas, patacot.....kai manyan garuruwan kasar nan dai da ka sani babu inda yarinyar nan bata xuwa, babu abinda Habibu bai sani ba game da ita ai, ina ga shi yasa taji haushin barin dreba da yayi" Khalil dai yayi shiru, Mai gadi yace "Atoh ni kallonta kawai nake kyar" Khalil yace "Allah ya kiyaye" Mai gadi yace "Ameen dae" Nihad na shiga bedroom dinta ta ajiye jakarta da mayafi ta dau wayarta tayi dialing number Habibu, yana fara ringing ta nemi gefen gado ta xauna babu bata lkci ya daga hade da sallama yace "Hajjaju Hajjaju ina yini" Tace "Lafiya lau Habibu" Yace "Ya kwana biyu kuma?" Tace "Lafiya lau, Kana ji na?" Yace "Ina ji Hajiya" Tace "Wannan drivern da ka kawo ma Abba, a ina ka san sa?" Habibu yace "Wani abu ya faru ne Hajiya?" Tace "Tambayarka nake kana tambayata" Yace "Ehh Hajiya na san sa, d'an uwa na ne, garinmu daya" Nihad tace "Bana son karya ta ina ya xama ɗan uwanka kana baƙi yana fari??" Habibu yace "Ayya Hajiya ai in dai ka fito kauye daya da mutum ku ka shigo maraya dan uwanka xaka kirasa, haka abun yake ki tambayi kowa ma" Ta kyabe baki tace "Toh abu daya nake so da kai yanxu" Yace "Toh ina ji Hajiya" Tace "Ko nawa kake so xan baka Habibu, in dai kudi ne kar ka ji komai" Shi dai yayi shiru, tace "Kana ji na?" Yace "Ehh ina ji Hajiya" Tace "So nake ka kira Abba ka 6ata sa a wajensa, ka kirkiro wani babban laifi kace yayi a garin naku ashe dalilin da ya sa ya bar garin kenan, kai baka sani ba sai yanxu wani ɗan garin naku ke sanar maka" Jin shirun da Habibu yayi tace "Kayi min shiru?" Da sauri yace "Ehh ina jin ki Hajiya, ina sauraronki" Nihad tace "Good, yaushe xan saurareka?" Yace "Xuwa gobe in sha Allah" Tace "Ohkk" daga haka ta katse wayar ta mike ta nufi window tana jin wani relieve a ranta. Khalil na shigowa parlon chalet din da suke ciki dab da magrib ya dinga bin parlon da kallo, tun safe da ya fito bai sake shigowa ba sai yanxu, kuma kafin ya fita tass ya share ko ina, amma yanxu parlon wani sai yace yara kanana sun shiga sun yi wasa da rana, beside that every where is so untidy, nan kayan wanki, can kayan guga da Isiya ke yi, ga plate din abinci da cups a tsakar parlon, kofar ma a wangale ake barinsa sauro su shiga yanda suka ga dama, Ya dinga kallon Saminu, Isiya da Shafi'u da ke parlon, Kafin ya ce komai Shafi'u yace "Ana ta kiran wayarka tun daxu fa" Kallon direction din da jakarsa yake yayi, sai kuma ya kallesu yace "Amma nace ku yi hakuri ku bar barin kofa a bude sbda sauro, tunda a parlor nake kwanciya ko" Isiya yace "Baka ga fankar ya lalace jiya ba, AC dama tun da ka xo ai baya yi, shhkn sbda sauro sai mu ki bude kofa iska ya shigo" Khalil ya dinga kallonsa, Saminu yace "Haba kai tun da ka zo sai kayi ta abu isa isa da gadara don kaga muna maka shiru, mu kafin ka zo haka muka saba barin kofa gaskiya" Khalil bai kuma ce masu komai ba ya nufi gun kayansa, ya dau jakarsa da blanket, sai tsintsiya da parker da yake shara, hanyar dakuna uku dake chalet din ya nufa, duk suka bi sa da ido har da waigawa, sai da ya bude ko wani daki sannan daga karshe ya shiga na dama, ajiye jakarsa da blanket yayi, duk wani ghana must go da jaka da ya gani a dakin sai da ya cilla sa waje, sannan ya cire dukunannen zanin gadon dake kan gadon shi ma ya cilla masu waje, tas ya share dakin, sannan ya shiga bandaki nan ma ya wanke, ya fito ya bude jakarsa da makulli ya dauko Harpic da hypo ya koma bandakin, bayan ko ina ya dawo yanda yake son ganinsa, yayi wanka ya dauro alwala ya fito, har xai kulle jakarsa sai ya tuna wayarsa ya dauko ya ga miss calls din Habibu kusan 7, ya gama kare ma number kallo sannan ya ajiye wayar ya mike ya fita daga dakin ya sa makulli, ya zira makullin a aljihun jallabiyan jikinsa, babu yabo babu fallasa ya fito parlon ya nufi kofa duk suka bi sa da kallo babu wanda ya iya cewa komai har ya fita. Bayan khalil yayi sallah yana xaune gefen mai gadi sai ga Hafsah ta kawo ma mai gadin abinci, Mai gadi na kallonta yace "Shi ma ki kawo masa tasa abincin nan kawai" Tace "Toh" sannan ta juya ta koma ciki, Khalil ya mike yace "Xan dau wayata da ka sa a caji" Daga haka ya shiga dakin mai gadin ya dauko wayar ya dawo ya xauna, yayi dialing number Habibu ya kai kunne, ba a dauki lokaci ba Habibu ya daga yace "Ranka shi dade" Khalil ya gyara xama yace "Ya kake" Habibu yace "Lafiya qlau wllh, ya aikin?" Khalil yace "Alhamdulillah" Habibu yace "To madallah, kana ji na" Khalil yace "Ina ji" Habibu yace "Wani abun ya hadaku da wannan yarinyar Nihad ne?" Khalil yace "Wani abu kamar me?" Habibu yace "Aa wai ko sa'insa, ko dai makamancin hakan" Khalil yace "Ko daya" Habibu yace "Tohh, akwai fa matsala" Khalil yace "Ta me kenan" nan Habibu ya sanar masa yanda suka yi da Nihad daxu, Khalil yace "xan kiraka anjima" Daga haka ya katse wayar ya amshi abincin da Hafsah ta kawo masa yace "Nagode" Nihad ta fito daga wanka kenan da daddare Mumy ta shigo dakinta, sunkuyar da kai tayi tana goge jikinta tace "Ina yini" Mumy tace "Wa ya baki makullin motar Farooq daxu?" Nihad ta kalleta da sauri, sai kuma ta marairaice tace "Umma ce ta bani" Mumy tace "Ke yanxu Nihad duk wata hanyar da xaki bi ki sani magana shi kike nema a rayuwarki ko?? Kwata kwata baki daukeni bakin komai ba, duk abinda xai 6ata min rai shi kike rawan jiki kiyi, ki kama ki dau mota ki kama hanyar makaranta without i and ur dad knowing ko Nihad" Nihad ta fara shessheka tace "Mumy u don't want to be considering me, ni baxan iya shiga mota daya da wancan sabon driver din ba shi yasa na amshi makullin motar ya Farooq gun Umma" Mumy tace "A saboda meye baxa ki shiga mota daya da shi ba? Saboda shi ba mutum bane? Kawai don bai baki makullin mota kin tafi gantali ba shine kika dau karan tsana kika daura ma mutumi? He is only trying to protect his job don ai ba a basa umarnin ya baki makulli ba ko" Kuka Nihad take sosai tace "Ko me nace Mumy baki supporting dina, wllh yaron ba shi da kunya, ya raina ni kawai" Mumy tace "Wato yaro ne ma?? Me yasa ita Nihal bata complain a kansa, ina ce shi ke dropping dinta a islamiyya kullum, i even ask her ko taga yana da matsala tace min he is so friendly, me yasa ke baxa ki sauke kanki yanda er uwarki ke yi ba" Nihad ta hade rai tace "Wannan wawiyar me ta sani, ko bai mata magana ba ma ai washe masa hakora xata yi ita tayi masa, baxa ma ta jira ya gaisheta ba ita xata fara gaishesa sbda bata da hankali, pls mumy ki daina sa Nihal a cikin mutane" Mumy tace "Ki bi duniya a sannu Nihad, babban matashi irin wannan sbda yana aiki karkashin Abbanki kice baxa ki gaishesa ba sai dai ke ya gaisheki, me yasa baxa kiyi koyi da Nihal ba, me yasa kika dau duniya da xafi haka" Nihad tace "Ni dai Mumy kiyi hakuri ki bani makullin motar ki yau wllh ina da lectures karfe goma, Ni kuma baxan juri shiga mota daya da shi ba" Mumy tace "Toh xa mu gani kuwa, kuma wllh kika sake xuwa gun Hajiya kika amshi makulli sai na 6abbalaki a gidan nan" Nihad tace "Shikenan ni baxan je makarantar ba kawai" Mumy tace "Ohk ni kike gaya ma wannan ko" Ta fashe da kuka sosai tace "Toh Mumy ya kike son inyi, ni naga kamar ma kin fi son driver din nan a kaina kawai" Mumy tace "Ehh na fi sonsa a kanki, kuma wllh kar ki kuskura ki bari karfe goma yayi maki a gidan nan, sannan shi din xai kai ki, idan kuwa ba haka ba xaki sha mamakin abinda xan maki, tunda ke kin dau girman kan duniya kin daura ma kanki" Daga haka Mumy ta fice daga dakin, Nihad tayi kukanta ma'ishi, taji ta tsani wannan bawan Allah, ta tsanesa... Babu yanda ta iya haka ta tashi ta shirya, karfe goma saura minti biyar ta fito compound, atamfa ce jikinta da wata mitsitsiyar mayafi da ta rataya a wuya, hannunta rike da laptop dinta da jaka, fuskarta a daura ta nufi can inda ta hango Driver din a xaune da Aminu, tana masa wani matsiyacin kallo, cike da isa da gadara tace "Tasowa xaka yi kayi dropping dina a school idan ka ga dama, kai kuma Aminu sai ka gaya masa makarantar tamu" Daga haka ta juya ta bar wajen ta tafi can gun motar, murya can kasa kasa Aminu yace "Iko sai Allah" Mikewa Khalil yayi ya nufi motar, Har xata bude back seat sae kuma ta fasa ta xaga ta bude seat din gaba ta shiga, yanda ta hade rai sai kayi xaton ko dariya bata ta6a ba, shi ma ya shiga motar, suna fita compound Aminu ya daga masu hannu, AC din motar Nihad ta kunna, shi dai bai nuna yasan abinda tayi ba, suna hawa saman titi tayi connecting phone dinta ta kure waka a motar, shi dai driving dinsa kawai yake, bayan kusan minti talatin suna tafiya, ganin tafiyar tasa babu direction, ta wani juya ta kallesa tace "Wai malam baka san inda xaka kai ni bane, ko Aminun bai gaya maka ba?" Tafiyarsa kawai yake pretending he didn't know she is talking duk da yana jinta, rage volume din wakan tayi can kasa, a fusace tace "Malam da kai nake" Ya kalleta yace "Ohk magana kike, wakar ki ce ta hana inji" Ta yi masa wani kallo tace "Da yake kai kurma ne ba dole waka ya hanaka ji, Aminu wai bai gaya maka inda xaka kai ni ba?" Yayi slow down sannan yayi parking yace "Ina ta sauraren kice ga inda xaki ne ai" Buda baki tayi tana kallonsa, Cikin daga murya tace "Aminu bai gaya maka bane?" Yace "Toh ai ban ga Aminu cikin motar ba" She couldn't stop looking at him, ita ba abin ta sauka ba, dakewa tayi tace "Saboda ba kai ke xuba fetur a motar ba shi yasa kake ta yawo da ni a cikin garin kano ba tare da kasan inda xan je ba ko?" Bai bata amsa ba, bata kuma ga alamar xai ce komai ba, wani dogon tsaki ta ja, ta gyara xama tace "Dama harka da ɗan kauye ya gaji haka, idan kaga dama Maryam Abatcha American University of Nigeria xaka kai ni" Without looking at her yace "Ohk sai kin dinga min kwatance" Tace "Ban gane sai an maka kwatance ba, kai dama babu inda ka sani a kanon ka xo ka nemi driving a gidanmu?" Yace "Ehh idan aka ci gaba da nuna min wajajen xan sani ai" Tace "Amma wllh baka da amfani" Tsaki ta ja tace "Ai sai ka juya kan motar idan dai ba garinku xa mu je ba" yace "In kince aje can din ma ai sai aje" Bude baki tayi, sai kuma tace "Wallahi yaron nan ka raina ni" Sai a sannan ya juya ya kalleta jin abinda tace, ta galla masa wani harara tace "Malam kana bata min lkci xan je makaranta" Yace "Na xata garin namu xa mu" Daga haka ya juya, rai a bace ta dinga gwada masa inda xai bi har suka iso makarantar, ganin yayi parking a waje tace "Malam tada motar nan ka shigar dani ciki, ko duk nan akwai wanda kaga anyi dropping a titi?" ya ci gaba da driving din slowly, dai dai gate din makarantar ya tsaya ya sauke glass din motar, gaishesa security din suka yi, ya amsa ya amshi pass ya shiga cikin makarantar yace "Ina?" Rudely tace "Duk inda ka ga wancan jan motar ta bi kai ma ka bi, bani da lkcn yi maka wani kwatancen" Bai ce mata komai ba, ya ci gaba da driving dinsa, Dai dai wajen da motar ta tsaya ya samu waje yayi parking shi ma, ta ciro wayarta ta kira Husnah, Husnah na dagawa tace "Kin shigo school?" Husnah tace "Ehh, ke kina ina?" Nihad tace "Ku fito parking space ke da su Naf ku sameni yanzu yanzu, ki tabbatar har da Zully xa ku taho" Husnah tace "Ke kika yi driving din yau ma?" Nihad tace "Ke dai nace ku zo sharp sharp" daga haka ta katse wayar, ta zuge zip din jakarta ta fiddo chewing gum ta jefa cikin bakinta tana tauna a hankali, Shi dae gabansa kawai yake kallo, Bayan few seconds ya kashe motar ya zare makullin ya ajiye nan kusa da ita without looking at her, ya bude motar xae sauka, da mamaki tana kallonsa tace "Heyy, meye hakan kake yi? Waye xaka bar ma motar?" Still bai kalleta ba yace "Masu shi" Daga haka ya kulle motar ya juya ya bar wajen, kasa cewa komai tayi sbda mamaki, can ta sauka motar tana bin sa da ido baki bude, sae ga Husnah da Naf with Zully da wata kawar Zully, Husnah ta karasa kusa da ita da sauri tace "Nihad what happened, ya da bude baki haka" Nihad ta kalleta tace "I don't think this guy is okay, ji tafiya yayi ya bar min motar fa Husnah" Husnah tace "Wa??" Nihad tace "New driver din, kiranku fa nayi wai ku gansa, mu yi masa tijara..." Husnah tace "Wai wancan me bakar rigar dake tafiya?" Kasa bata amsa Nihad tayi don da gaske mamaki ne kawai ya cikata, Naf tace "Kawai haka nan ya kama ya tafi babu magana?" Nihad tace "Not at all, ajiye min makulli yayi kusa da ni, nace wa xai bar ma motar, wai masu shi.... kawai ya saka kai yayi tafiyarsa" Lkci daya Husnah da su Naf suka kwashe da dariya har da kyakyatawa, Nihad ta hade rai, Husnah tayi dariya me isarta sannan tace "Gaskiya wannan drivern dan duniya ne, ni ko na so in gansa wllh, ya iya bada amsa dai dai da tambaya" Nihad ta hade rai tayi locking motar ta bar su wajen a tsaye ta wuce aji, bin ta suka yi har sannan suna dariya, a lecture room suka sameta, Husnah ta xauna kusa da ita tace "Anya ba ajiye aikin yayi gaba daya ba" Nihad tace "Toh ni ya kamata ya ba makulli? Ko dama ni na basa makullin?" Husnah ta fashe da dariya har da kife kai. *Know the frnds of ur kids* To gain Access to the book Nihad Contact me directly via👇🏻 07087865788 _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp 💖💖 *NIHAAD* 💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 8...... Throughout the day's lecture mood din Nihad was so dull, gaba daya she wasn't her self, Husnah tace "Nihad mu je mu ci abinci ni dai na fara jin yunwa" A takaice tace "I am not hungry" Husnah tace "C'mon babe, wai me ke faruwa ne? Gaba daya you look dull today, don Allah ki gaya min me ke faruwa" Nihad ta sauke ajiyar xuciya tace "Wai har ni mutumin nan xai ma walakanci ya ajiye ma makulli ya wuce Husnah?" Husnah ta ja wani dogon tsaki tace "Ohh this? Wai wannan ne ya canxa maki mood throughout? Lallai ma, To wai meye abun damuwa, kika sani ko barin aikin ma yayi? Ni na fi tunani ya ajiye aikin ne, ba gashi da kika tambayesa wa ya bar ma motar yace maki masu shi ba, probably yayi quitting ne" Nihad dake ta kallonta tace "Sai ya rasa wanda xai ajiye ma aiki sai ni, me yasa bai kai ma Abba makullin ba, salon ayi xaton ni ce na koresa? dama babu wanda ke considering dina a gidan banda Umma, kawai so yake ya kara ja min bakin jini wajen Mumy" Husnah ta ja tsaki tace "Soo what? Idan ma ajiye aikin yayi ai hakan ke kika fi so, abinda kike ta so ne ya faru fa, karkari su gama surutunsu na kwana biyu su yi shiru, sannan a samo wani driver din wanda xa ki juya yanda kike so, ba shikenan ba?" Nihad ta taɓe baki ta mike tana harhada material din karatunta tace "Xan tafi gida" Husnah tace "Gida kuma? Da wuri haka? Ke da nace maki xa mu je guest inn din su Bill yanxu, Kai Nihad yau da kike da full control din mota an bar maki kiyi yanda kika ga dama shine xa ki wuce gida da wuri, haba yan mata, ki bari wajajen six ki koma gidan mana" Nihad tace "Ni kawai gida xan tafi duk raina a bace yake" Husnah ta juya ido tace "Toh ai shkkn, bari in raka ki gun motar" Tare suka isa inda motar yake, Nihad ta ajiye jakanta da kayan karatunta a bayan motar, sannan ta zaga ta shiga driver seat, Husnah na tsaye har ta tada motar ta fara tafiya..... Nihad na isa gate din gidansu tayi horn, mai gadi ya fito da sauri ya bude gate din, ta shiga gidan tayi parking, sannan ta kashe motar ta sauka, kallon inda mai gadin yake tayi, ta ga shi kadai ne a wajen, ta nufi cikin gida ba tare da ta dau material din makarantar ta dake bayan mota ba, Mumy na xaune parlor da Nihal, sai Umma dake parlon ita ma duk suna kallo, ta gaida su xata wuce, Mumy tace "Bani makullin da kika amsa wajen driver daxu" Tsayawa tayi cike da mamaki tana kallon Mumy tace "Mumy wa yace ni na amsa makullin?" Umma tace "Atoh, nima dai nace baxa kiyi haka ba, amma shi algungumin yace kin amshi makulli, kuma sun yarda" Nihad tayi narai narai da ido tace "A yaushe na amshi makulli wajensa? Wllh Umma sharri yayi min" Mumy tace "Ban tambayeki ba'asi ba, makulli nace kawai ki bani, xa kuma mu hade a daki" Nihad ta fashe da kuka tace "Ni wllh Allah ya isa wannan sharrin da yayi min, Allah ya isa tsakanina da shi munafuki kawai, ajiye min makullin fa kawai...." Throw pillow Mumy ta dauke ta jefa mata tace "Tafi ki bani waje, ga ki nan munafuka, wllh tunda haka kika xaba xa mu sa kafar wando daya dake a gidan nan, kuma daga yau kika sake driving da kanki sai dai ki canza wata uwar bani ba" Umma tace "Wai ya kike haka ne Maryam? Shikenan kai da ɗan ka baxa ka ja sa jiki ba komai ya fada maka sai ka karyatasa baxa ka goyi bayansa ba, me yasa kike fiffita bare akan naki? Wannan wace irin rayuwa ce? Ki bar ta tayi bayani ma kin ki sbda rashin adalci" A fusace Mumy tace "Bana son bayaninta, wani bayani xata min sai kace bani na haifeta ba, ko kuma ban san halinta ba, wllh daga ni har ubanki babu me irin wannan mugun hali naki don ma kiji, in har kince ke sai dai ki tuka kanki to wllh ki nemi wata uwar, kuma ai kin saba cewa a baki makullin ba wnn ne karo na farko ba, don haka babu abinda xa ki gaya min in yarda" Kuka kawai Nihad take xuciyarta na suya, ta ajiye makullin motar nan saman kujera tace "Allah ya isa karyan da ya laka min, Allah ya isa tsakanina da shi..." Tashi Mumy tayi, Nihad na ganin haka ta wuce sama da gudu, Mumy tace "Tsaya dai ki min rashin kunya" Mikewa Umma tayi ta fita daga parlon, tana fita compound ta kwalo ma Aminu kira ya taho da sauri, tace "Ina dreban nan yake?" Mai gadi yace "Ya fita ya ɗan amso abu" Tace "Toh xai dawo ya sameni" Daga haka ta juya fuu ta koma ciki. Nihad na shiga dakinta ta sa makulli ta dinga rusa kuka ta dau wayarta tayi dialing number Abba, yana fara ringing ya daga yace "Hello Dear, ina meeting i will get back to you" Ta fashe da kuka tace "Abba ni dai kawai a canza driver din nan, bana son ganinsa kuma, i can't withstand the sight of him any longer, kawai ni dai Abba ka sallamesa" Abba ya ɗan yi shiru sai kuma yace "Why did u ask him to hand over the key to you da ya kai ki makaranta?" Nihad ta xaro ido tace "Abba wllh sharri ya min, ta yaya xan ce ya bani makulli, wllh karya yake min ni ban ce masa haka ba" Abba yace "Idan na dawo gida xa mu yi magana yanxu muna meeting ne" Daga haka ya katse wayar, kuka ta dinga yi, nobody is getting her banda Umma, wato dawowa gida yayi ya laka mata wannan uban sharrin gashi kowa ya yarda, number Farooq tayi dialing, yana dagawa shi ma ta rushe masa da kuka yace "Lafiya??" Cikin kuka tace "Yaya dama Abba ne ya dau wani sabon driver, yaya tun da ya fara aiki yake laka min sharri iri iri, yana sa Mumy na kara tsanata, wai daxu ya kai ni schl shine ya ajiye min makulli yayi wucewarsa, da ya dawo gida shine ya je yace ma su Abba da Mumy ni nace ya ajiye min makullin" Farooq yace "To ai halinki ne wannan, amsan makulli a wajen drivers kiyi driving da kanki, ke ko wani driver sai kin samu matsala da shi, haka Habibu farkon da ya fara aiki a gidan nan, why are u always having issues with everybody? Me yasa ita Nihal bata ce an mata ba" Lkci daya ta hade rai, yace "Shi wannan din yaushe ya fara aiki har kika fara samun matsala da shi Nihad?" Kin cewa komai tayi, yace "Ki min magana ko in kashe wayata" Murya can ciki ciki tace "Sallah xan yi" Katse wayar yayi, ta jefar da nata wayar, wato nobody is even supporting her, then xata dau action da kanta. Tana kwance bayan tayi wanka tayi sallah wayarta ya fara ring, ta jawo wayar ganin number da ke kiranta ta mike zaune ta daga tana wara ido tace "Shine baka ce min xaka dawo ba bayan ko jiya mun yi magana" Yace "How are you?" Ta lumshe ido tace "I am fine, ya hanya?" Yace "Alhamdulillah, yaushe za mu hadu? I will be leaving for Abuja next tomorrow" Tace "Wai yau kake nufi xa mu hadu?" Yace "Toh shikenan tunda ba yau ba" Da sauri tace "Noo ba haka nake nufi ba, i only asked, okay yanxu xan shirya in fito in sha Allah" Yace "Where are we meeting?" Tace "U suggest" Yace "How about Royal park..." A hankali tace "Kasan fa an canza mana driver" Yace "Ohh really, when?" Tace "Kwanan nan" Yace "So u are not use to the new one ko?" Ta taɓe baki tace "Aa wannan dan rainin hankali ne, i don't think we can eva get use to each other" Yace "To yanxu ya za mu yi? Sbda ke na sauka kano fa" Tace "For now pls mu hadu ko a wellcare ne, dama xan ɗan yi shopping..." Yace "Nahh, baxan iya fita don kawai in je wellcare ba, kina nufin a tsaye xan ganki sannan mu rabu?" Tace "No pls, after today i will plan where we will be meeting, ba kace next tomorrow xaka koma ba" Yace "Karfe nawa xa ki wellcare din?" Tace "Kawai shiryawa xan yi yanxu" Yace "Drivern ne zai kawo ki?" Tace "To ya xan yi shi din xai kawo ni, dama kuma Abba ya bani kudin shopping kawai dai ban je nayi ba ne har ynxu" Yace "Okay idan xa ki fito ki kirani" Tace "Tohm, i will call you" Daga haka ya katse wayar. Sosai taji xuciyarta yayi sanyi duk wani bacin rai dake tare da ita ta nema ta rasa kawai muryarsa da ta ji. Bayan ta shirya ta fito ta tafi bangaren Mumy, Tana tsaye a parlon tace "Abba ya turo min kudin shopping, cream dina da sabulu sun kare, ina son xan je in siya yanxu, sai driver yayi dropping dina a can" Mumy tace "Gobe Nihal xata je shopping xata koma makaranta, sai ki bari ku tafi tare" Nihad da gabanta ya fadi tace "Mumy bani da cream din da xan shafa ne fa, let me get even if it's just the cream today idan ya so goben sai mu je tare, ina gama siyan cream din xa mu dawo gida" Mumy tace "Allah ya tsare, sannan kuma ki yi masa abinda kika saba, ki tabbatar tare xa ku dawo gidan nan da shi" Nihad dai bata ce komai ba ta juya ta bude kofar dakin sannan ta fita. Tana fita compound taga bata ga drivern ba, ta tambayi mai gadi yace "Yanxun nan ya bar nan, ya shiga can bangarensu.... " Chalet din ta nufa, ta hangosa zaune saman matakalan dake wajen waya kare a kunnensa, yana hangota ya katse wayar kuma ya ki kallonta, ta karaso babu yabo bbu fallasa tace "Hey idan ka ga dama zaka ajiyeni a well care yanxu yanxu" tana fadin haka ta juya ta bar wajen. Da ido ya bi ta, sai kuma ya mike ya ciro makullin a aljihunsa ya bi bayanta, tana tsaye compound din ta kira Aliyu, ta sanar masa gata nan xata fito, bayan ta gama wayar ta karasa ta shiga bayan motar, sai da suka hau saman titi sannan yace "Kwatance xa ki yi" Ta hade rai tace "Kai ko ina sai kace baka sani ba sai an maka kwatance, baka da Google map ne??" Yace "Ban da" Tsaki ta ja, haka ta dinga gwada masa inda xa su bi har suka iso well care, parking yayi a space da ake parking din, tayi dialing number Aliyu, yana dagawa tace "Are u inside?" Waige waige ta fara yi jin abinda yace, tace "I am also outside, where did u park?" Sauke glass tayi, lkci daya ta hangosa, murmushinsa me kyau ya sakar mata yana kallonta, xata katse wayar yayi saurin cewa "Waitt" sai ta fasa kashewa tana sauraronsa, yace "What if idan an ɗan basa wani abu mu ce ya jira mu a nan, mu je eatry... i am jet hungry" Rasa abinda xata ce masa tayi, don ta ce ma Mumy baxata dade ba, can ta saci kallon Khalil ta ga idonsa a kan Aliyu yake ko kiftawa bai yi, duk da glass din a dage yake, kuma tinted ne ba me duhu can ba, a ranta tace wannan ma yayi kama da wanda xai amshi abu idan an basa, bude motar tayi ta sauka ta nufi inda Aliyu yake, shi dai Khalil bai daina kallon Aliyu ba kamar ya ga wani halitta na daban, tana karasawa gun motar Aliyu dake ta kallonta underneath his breathe yace "Waow, baby kin kara kyau fa, tell me what is d secret" Tayi masa murmushi wanda har dimple dinta sai da ya lotsa, sauke idonsa yayi kasa, can ya zaro dollar 100 a aljihunsa yace "In bashi wannan ya jira mu a nan?" Tana kallon kudin tace "Toh kasan dai ba wai mun saba da shi bane, snn bashi da kirki fa wllh" Aliyu yace "Kudi ne baki fara basa ba shi yasa baku saba ba, yana ganin wannan yanxu xaki ga kun dawo kun dai daita kun saba" Bude motar yayi ya fito, walking majestically ya nufi motar, Nihad ta bi sa da kallo, Waige waige khalil ya fara yi da sauri, as if looking for an alternative kafin Aliyu ya karaso gun motar, lokaci daya kawai yayi locking motar kafin ya iso, Aliyu na karasowa ya bude motar yaji a kulle, kwankwasa glass din motar yayi, Khalil ya kauda kai duk da Aliyun ba ganinsa yake ba, Sau biyu Aliyu na kwankwasawa kafin ya daga kai ya kalli Nihad, ta buda masa hannu alamar i told u dama, mamaki ne ya cika Aliyu ya dinga kallon motar, can ya sake Kwankwasa glass din, tace "Dear just leave him ka bar wajen kawai, ba nace maka ɗan iskan yaro bane" Aliyu da ransa ya gama baci yace "Who did he think he is, da driving din da yake yi ake biyansa yake takama ko me? Waye shi yana matsayin just driver xai kulle mota yana jin ana kwankwasawa ya ki budewa, kuma ba wai bai gan ni bane" Nihad tace "Ai ban ta6a ganin mutum me karfin hali irin yaron nan ba" Aliyu yace "Look Nihad idan kika shiga school gobe xa mu hadu, i can't stand here any longer, mood dina ya baci seriously, ba a ta6a ci min fuska irin yau ba" Nihad tayi shiru tana kallonsa duk jikinta yayi sanyi, don kana ganinsa kasan ransa yayi mugun baci da gaske, tafiya ya fara yi kawai ya koma gun motarsa ya shiga ya tada yayi zoom off, da ido khalil ya bi sa har ya hau saman titi, Nihad ta dinga kallon motar tana jin kamar ta rushe da kuka ko xata ji sauki a ranta, mutumin da tayi wata da watanni bata gani ba, shine wannan drivern xai 6ata ma rai har ya tafi?? Ta fi minti biyu tsaye kawai kallon motar take with different thought running her mind ga wani kullutu da ya tokareta a makogwaro sbda bakin ciki da takaici, a duk abubuwan da yake mata bata jin akwai wanda ya mata ciwo ya ta6a har karshen xuciyarta irin wannan, she is trying her best not to cry, don har idonta ya cicciko, kiris ya rage ta fashe da kuka a wajen, Khalil dake ta kallon duk expression da reaction dinta ya shafa kansa, sai kuma ya sauke both glasses yace "Naga kamar kin fasa siyayyan, kuma ga hadari, ni kuma bana tuki cikin ruwa ko in baki makullin in yi tafiyata??" Wani matsiyacin shegen kallo tayi masa, ta bude back seat ta shige motar ta kulle da karfi tana kara danne kukan dake cin ta, tada motar yayi, yayi reverse ya dau hanyar gida, har suka isa gida Nihad danna kukanta take, bayan yayi parking ta bude motar ta sauka ta tafi gun driver seat ta tsaya tana nunasa da yatsa tana huci tace "Sai kayi da ka sanin abinda kayi min yau wllh, kuma ni ce sanadin barin ka gidan nan, banza mahaukaci kawai talaka" Kashe motar yayi ya sauka yana kallonta ya kara mata kunne gaba yace "Kamar kina magana?" Da wani bakin ciki ya mamayeta bata san sanda ta cakumo kwalarsa ba duk da uban tsayinsa tsaurin idonta bai sa taga hakan ba, tana jijjigasa da duk karfinta hade da kunduma masa wani mummunan zagi, mai gadi dake ganin komai ya karaso da gudu jikinsa na bari yana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Subhanallahi... " Khalil dai kallonta kawai yake baya ko kiftawa, cikin nutsuwa yace "Cika ni" Ta buga wani uban tsawa tana dungure masa goshi tace "An ki a cika ka din, kayi uban da xaka yi in ga, kai har ka isa kana aiki ƙarƙashinmu kana matsayin Drivern gidanmu ka dinga kawo min raini? Ni ce ma zaka raina? Kasan wa ka walakanta daxu?? To wllh ko kaff zuri'arka xa a siyar idan har Aliyu ya daureka kudin da aka siyesu bai isa yayi bailing dinka ba" Nihal ta fito cikin gida da kawarta xata mata rakiya ganin abinda ke faruwa ta karaso da sauri xata ta janye Nihad tace "Nihad what's this u are doing, don't u have manners? Meye wannan kike yi?" Nihad na huci ta bangajeta a fusace tace "Eh ban da shi, sai ki ara min naki ke me shi, a kan matsiyacin nan xaki ce min bani da manner, kin san abinda yayi min ne?" Nihal na kallon Khalil cike da damuwa tace "Don Allah kayi hakuri" Yana warware rigarsa da Nihad ta cakuikuye yace "Ba komai... fita xa ki yi ne?" Nihal dai duk jikinta yayi sanyi ta kasa cewa komai, yace "Ko ba fita xa ki yi ba?" tace "Aa Kawata xan raka bakin titi" ya kalli kawartata dake tsaye ita ma tana kallon abun mamaki, yace "Ohk to, ta hau sai na ajiyeta a gida, xan jira ta a waje...." Yana fadin haka ya koma motar ya tada ya bar wajen, mai gadi ya tafi da sauri ya bude gate, Nihad bata san sanda ta fashe da kuka ba, da hanzari ta shige cikin gida tana kuka sosai. Bayan ta ci kukanta me isarta ta dau wayarta ta kira Aliyu, har ya katse bai daga ba, ta kuma kiransa nan ma no response, hawaye ne ya dinga sauka idonta, bayan kusan awa daya ta mike ta gyara idonta ta fita, bangaren Mumy ta tafi sai taga kamar tana da bakuwa, hakan ya sa ta bar wajen ta tafi gun Umma, Umma tace "Lafiya me ya sami idonki Nihad?" Cikin rawan murya tace "Umma Aliyu ne ya dawo shine muka yi da shi xa mu hadu a wellcare, bayan mun hadu sai ya sauko daga motarsa yace bari su gaisa da driver ai ko in gaya maki mutumin nan yayi masa walakanci mafi muni, ya kulle motar ya kuma ki ya sauke glass, banda Abba da ya ja mana ina Driver xai ma tsaya same place inda nake balle Aliyu? Yasan waye uban Aliyu a kasar nan, kaskantar da kansa fa yayi ya tafi su gaisa maimakon shi drivern ya sauko ya taho har inda yake ya gaishesa amma ya masa wannan mugun walakancin" Umma dai sakin baki tayi tana kallon Nihad, can tayi kasa da murya tace "Wai har yanzu kuna tare da Aliyun nan ne dama?" Nihad ta gyada mata kai tana matsar kwalla, Umma tace "Ba kince min kun rabu ba kwanaki?" Nihad tace "We came back together 1 month ago" Umma tace "Ke dai bakya ji Nihad nace ki fita harkan yaron nan, ba mutunci ne da familynsu ba kin ki, nace ki rabu da shi in kina son sama ma kanki mutunci kina son ki tsira da mutuncin ki, ina ke ina Aliyu banda dai yaudaran kai Nihad? Kika san wasu irin yan mata yake hulda da? 'ya yan shugaban kasa yake hulda da fa" Nihad taki cewa, Umma tace "Gaskiya kar ki sake kulasa ni dai na gaya maki, yana son ki ne ko sau daya bai ta6a takowa ya xo gidanku ba? Sai dai soyayya a titi da makaranta, kema kinsan yaudaran kanki kike don Aliyu ya fi karfin ki, me ma xai kawosa gidan nan? waye ubanki a inda ubansa yake, inaa ai nisan ma yayi yawa, balle ma duk yan iska ne yaran masu kudin nan wa enda idonsu ya yage har kunne, banda lalata yara da bata masu rayuwa babu abinda suke" Nihad still ta ki cewa komai, Umma tace "Kin min alkawarin xa ki rabu da shi kiyi blocking dinsa kamar yanda kika yi blocking din Ahmad yanxu?" Nihad ta turo baki tace "Ni dai ina sonsa Umma, shi ma kuma yana so na ai, da baya so na baxai dinga kirana ba har yace mu hadu a wani waje, dama ce maki xanyi xan je gidansu Baffa ko da Mumy ta tambayeni" Daga haka tayi ficewarta daga parlon Umma ta bi ta da ido ko kiftawa babu, Nihad na sauka downstairs ta fito compound, fuskar nan nata a murtuke ta nufi gate, mai gadi dai ya kauda kai da sauri don tare suke da Khalil, shi dai ya rasa kan wannan abinda ke faruwa tsakaninta da Khalil, yana mugun ganin karfin halin Khalil da baya nuna shakkarta kamar su, har ta fita gate ta dawo tana kallon mai gadi fuskar nan nata babu rahama tace "Kai in ji dai kuna kula min da tsuntsaye na? Don idan har wani abu ya samesu wllh kaf gidan nan duk sai kun raina kanku ban cire kowa ba kuma" Da ladabi yace "Ko daxu sai da naje can da kaina Hajiya" Ficewa tayi daga gate din bayan ta maka ma khalil da bai ma san tana yi ba harara, Mai gadi ya kalli khalil yace "Sai fargaba nake kar tace xaka kai ta wani waje" Khalil yayi murmushi yace "Meye a ciki, sai a kai ta ai..." Da yake babu wani nisa da kafa Nihad ta bi ta cikin anguwanni har ta isa gidan yayan Abbanta, Hamid na xaune compound tare da wani abokinsa, kallo daya tayi masu ta kara gaba abunta, Abokin nasa yace "Wannan ba cousin din nan taka bace, naga ta wuce bata ce maka komai ba, and kamar kuna good time da ita ai" Hamid yace "Noo, step sisters dinta ne muke good time, wannan ai yar iska ce" Abokin yace "Shit but sun yi kama sosai, kamar har ya wuce misali" Hamid yace "Toh wannan da kake gani ji take da girman kai da rainin wayo, sannan runz girl ce..." Abokin ya wara ido yace "Waow dai dai mu kenan, ka hadu mu to" Hamid ya masa wani shegen kallo yace "Ai da manyan mata ake runz ba kwailaye ba, kwailar ma fitsararriya irin wannan" Tuni Nihad ta shige gidan, direct part din Kakarta ta nufa, tana bude kofar dakin ta shiga, inna tace "Aa, daga ina haka, Ibrahim din ya shigo ne" Nihad tace "Ni kadai ce" Inna tace "Aa naga sai ya taso keyarki kike xuwa shi sa abun ya daure min kai, ina ce tare ku ke" Nihad ta nemi waje ta xauna, Inna tace "Baki da lafiya ne?" Nihad ta fashe da kuka kamar jira take tace "Inna wani sabon driver Abba ya dauka, yaron ba shi da kunya ya raina ni inna, ba irin rashin mutuncin da baya min" Inna da ta saki baki tace "Shi Dreban?" Nihad ta gyada mata kai tana goge hawayen idonta, Inna tace "Ko ba wani gansameme ba yana tafiya gansan gansan?" Nihad tace "Shi" Inna tace "Toh ai Ibrahim din ya kawo sa har nan ya gaisheni, amma ni na xata ɗan arxiki ne, don har kasa ya duka ya gaida ni" Nihad tace "Wllh na munafurci ne...." Nan ta labarta ma inna abinda ya faru kamar yanda ta gaya ma Umma, Inna tace "Ba lafiya, shi dreban??" 07087865788✍🏻 💖💖 *NIHAAD*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 9..... Nihad na shesshekan kuka tace "Wllh shi inna, kawai an bar sa yana ta abinda ya ga dama a gidan kamar gidan ubansa, duk ya gama rena ni, ko gaisuwa bata hadani da shi" Inna tace "Duk ba wannan ba, yanxu kin kira Aliyun??" Nihad ta daura kanta gefen gadon inna hawaye na sauka idonta tace "Bayan ya ki dagawa" Inna ta dauko wayarta ta mika mata tace "Kirasa da nawa" Nihad tace "Ae idan ba shi da numberka baxa ka iya samunsa ba, ya sa layinsa a Private" Inna tace "Wai ko ba dai Aliyu ɗ'an wajen janaral Habubakar jikamshi ba?" A hankali Nihad tace "Shi..." Inna tace "To wannan dreba duk yanda aka yi tsinanne ne, ko don nace masa ya saki jikinsa yasa ya sake kamar gidan ubansa? to ai ni na xata yaron arxiki ne" Salati inna ta saki tayi tagumi tace "Yau naga dreban jaraba, ashe duk ni na ja komai da nace ya saki jikinsa, to a kira min Ibrahim din tun yamma bai yi ba ya sallamesa" Nihad ta dau wayar inna da sauri ta fara neman number Abba tayi dialing, Inna ta bude baki ta rike ha6a tace "To shi kuma Aliyun banda abunsa garin yaya xai ce sai yayi ma dreba magana mutumin da ba ajinsa ba, ai abinda bai sani ba talakawan nan haka suke da dacin rai kamar mutum ne ya doro masu talaucin, ina shi ina wani basamuden buzun dreba can? To ko a almajiri dai baxa su yarda su ajiye wannan mutumi a gidansu ba balle dreba, su da tun daga titin da ya yanka unguwarsu xaka fara ganin dirka dirkan sojoji har da motocinsu...." Nihad ta turo baki tace "Abba bai daga ba" Inna tace "Ina xai daga, ya tashi ya kawo wani kato gansameme kamar mutanen farko ya dau mota ya basa, ni wllh ranan da na fara ganinsa sai da na tsure, sai fa ya daga mutum ya nanasa da kasa sau biyar bai gaji ba, irinsu ai gadin dogon banki ya kamata a basu ba wai motar mutane ba" Nihad dai tayi tagumi don abinda ya dameta daban, ita yanxu ta ya xata fara shawo kan Aliyu, da yaya ma suka dawo soyayyar, Inna tace "To ko kin san inda ya sauka ki rakani mu je in basa hakuri" Nihad ta kalleta tace "Ji ki kuma, kawai don ki ja min raini?" Inna tace "Wani raini mutumi na nema ya kubuce, wa ke ta wani raini Nihad, idan ma baxa ki shiga ba ni ki rakani ki nuna min hanya in je in samesa" Nihad tace "Aa ke dai kawai duk yanda xa kiyi kiyi Abba ya kori driver din nan kawai" Inna tace "Yo sai ma kin fada, abu har ya kai yana korar ma jikokina samari" Hamid ne ya bude kofar dakin ya shiga yana kallon Nihad yace "Ke don uwarki ni sa'anki ne xaki wuce ni da abokina baki gaishemu ba" Nihad ta turo baki ta koma gefen Inna, Inna dai bata ce komai ba, Yace "Mahaukaciya kawai, uban wa xaki dinga daga ma kai?" A fusace Nihad tace "Kina dai gani babu abinda na masa ya xo ya fara xagina ko inna, ni fa shi yasa bana son xuwa gidan nan wllh, kowa yaje yaji da mugun halinsa" Cikin xafin nama ya nufeta, Inna ta mike ta wangale hannu tana tare Nihad tace "Dokeni to, Hamidu nace ka dokeni" Huci yake yana kallonta, Inna tace "Ai dama ka saba dukan nawa yanxun ma ka duka, ranan da ka biyo Bilkisu ai ni ka jibga ba ita ba" Nihad ko kallonsa bata yarda ta sake yi ba, Yayi wani kwafa ya fice daga dakin, Inna ta kulle dakinta tace "Kinsan korosa aka yi daga can kasar wajen wai wa'adinsa ya kare a can, to kuma sai kayi ta hucewa kan ya yan mutane" Nihad bata san lkcn da ta kyalkyale da dariya ba, Inna tace "Allah haka uban yace min, duk a booth din jirgi aka kwaso su aka dawo" Nihad dai bata ce komai ba, Inna tace "Yanxu ko kin boye number ki baxai daga wayar ba?" Nihad ta mike tace "Ni dai xan tafi inna dama anjima da daddare kice Hamid din ya kawoki nan gidanmu ki samu Abba da kanki" Inna tace "Toh shkkn ma, kawai bari inje in riskesa a gidan ba sai mun yi waya ba, idan ma ya kama ko shi sai ya kira Aliyun ya basa hakuri" Bude baki Nihad tayi, can ta kyabe bakin tace "Ni dai sai kin zo" Daga haka ta fita daga dakin, A bakin gate abokin Hamid ya tare ta da ya faki idon Hamid ya biyota, yana fara magana ta dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu tana yatsine fuska tace "Ina wasa da kai ne malam?" Daga haka ta ja tsaki tayi ficewarta daga gate din, ya bi ta da kallo baki bude, dama Hamid ya gaya masa ya ki ji. Nihad na komawa anguwansu ta yi ido hudu da Khalil dake xaune kan dakali a kofar gida wayarsa na kare kunnensa, yana ganinta bai sake cewa komai ba a wayar da yake kuma bai cire wayar a kunnensa ba, har ta isa dai dai inda yake, tayi masa wani harara ta ja tsaki ta shige cikin gida tayi banging gate din. Abba na tsaye balcony bayan magrib Khalil ya karaso da ladabi yana kallonsa yace "Gani Alhaji" Abba yace "Yauwa pharmacy xan aikeka ka siyo min magani yanxu" Khalil yace "Toh, ya sunan maganin?" Abba na duba wayarsa yace "Yanxu likitana ya turo min ta message bari dai in duba" Abba na shiga message din har ya fara pronouncing sunan maganin kawai ya fasa kar khalil yaje ya masa shirme, yace "Bari kawai xan rubuta maka a takarda kaje ka siyo, idan ka siyo sai...." Abba ya dakata ganin mai gadi na bude gate, sai ga motar Hamid ya shigo compound din, Abba yace "Je ka xan rubuta sunan maganin a kawo maka yanxu" Yace "Toh Alhaji" daga haka ya nufi boys quarters, Inna ce ta sauka daga motar ta nufo balcony, Abba dai na tsaye yana ta tunanin ko lafiya, Tana isowa ganin yanayinta yace "Lafiya inna?" Tace "Ina fa lafiya, mu je parlor baxan iya tsayuwa ba" Sai da ta fara shiga parlon Abba ya bi ta, kanta tsaye ta tafi parlonsa duk yana biye da ita, ta nemi waje ta xauna shi ma ya xauna yace "Ina yini Inna?" Tace "Ibrahim a ina ka samo wannan gansamemen dreban naka?" Abba yace "Wani abu ya faru ne?" Tace "Meye baxai faru ba, ya kora ma Nihad saurayi, d'an wajen Janaral Jikamshi, har yaron ya goge numberta yanxu haka da nake maka magana" Abba yayi shirui yana kallonta as if confused don ya kasa fahimtar xancen nata, Inna tace "A kara min Ac, xafi ya isheni" Abba ya dau remote ya kunna Ac din, yace "Ban fahimta ba Inna" Nan inna ta xauna tayi ma Abba tsari da abinda Nihad ta fada mata da ma wanda bata fada mata ba duk ta dire ma Abba, Abba yace "Ikon Allah, ke yanxu wa ya sanar maki wannan?" Inna tace "Har gida ta sameni tana kuka kamar ranta xai fita, hankalina yayi mugun tashi shine nace da kaina xan taho da daddaren nan, sannan a kira min dreban in ji uban da ya aikosa wajenmu, ni dama ina ganinsa na sha jinin jikina ban yarda da shi ba kawai nayi shiru ne, wa yasan adadin binne binnen da yayi maka a gidan nan yanxu? Huhuhu kana wasa da buzun mutum, Ai irinsu xuwa suke su tarwatse gida kai har ma su talauce mai gidan su saci abinda xa su sata su gudu su koma Nijar, to Ibrahim ko motar nan ma ya gudu maka da shi ai ya cuceka, to yanxu ni dai a kira min shi ko in tafi in samesa da kaina" Abba yace "Aa ba sai kin samesa ba, ai sallamarsa kawai xanyi ya tafi ba sai anyi wani tashin tashina ba" Inna tace "Aa ko xagi ne a bari in masa kafin ya tafi ai" Abba yace "Ke dai nace ki bar komai a hannuna, bari Hamid ya xo ya maida ki gida dare yayi" Tace "Ai Habubakar ne ya sa ya kawoni banda haka waye ubana Hamid xai kawoni, tun fa da aka korosa daga kasar wajen yake jin haushin kowa, to ni nasan sanda ya koma can da xama balle sanda aka korosa, kawai gani nayi ya dawo da manyan jakunkuna, ji yake kamar duk ya kashe mu yanxu haka" Abba yace "Ke wa yace maki an korosa, don Allah ki bar fadin wnn magana a xata da gaske ne" Mikewa yayi ya fita daga parlon ya kira Hamid dake main parlor yace "Zo ka maida Hajiya gida" Yace "Toh Abba" Har mota ya rakata, bata ce xata shiga wajen matansa ba shi ma bai ce ta shiga ba, don da suka fito parlor ma yace Nihal ta kirasu su gaisheta ta hana, yana tsaye compound din har motar ta fita, yana kallon mai gadi dake kulle gate yace "Kai ina Ibrahim?" Aminu bai kai ga bada amsa ba sai ga khalil da mota, Aminu ya kara bude gate din Khalil ya shiga compound din da motar sannan yayi parking a parking space Abba dai ya bisa da kallo, yana sauka daga motar ganin Abba a tsaye, ya nufesa da ledan pharmacy a hannunsa ya ɗan risina yace "Ga maganin Alhaji" Abba yace "Wani Magani?" Khalil ya kallesa yace "Da kace a siyo" Abba yace "Na gaya maka maganin da zaka siyo min ne?" Khalil ya kalli ledan hannunsa da sauri, kawai sai ya rasa abinda xai ce, Abba ya amshi ledan ya bude maganin sannan ya bude wayarsa ya shiga message din da Dr dinsa ya turo masa yaga maganin ne Khalil ya siyo, Abba ya daga kai yana kallonsa daga sama har kasa, kafin yace komai khalil yayi saurin cewa "Ai ka fada min sunan maganin, rikewa nayi a kai" Abba dai bai ce komai ba sai kallonsa yake, Khalil kam ya kasa barin su hada ido, Can Abba yace "Ban gaya maka sunan maganin fully ba" Da sauri khalil yace "Ka tambayi Habibu a can garinmu akwai wani likita da ya bude Kemist na siyar da magunguna, na fi shekara takwas ina jire masa shago yana bani wani abu duk wata, Allah ya bunkasa masa shagon sosai, rasuwa Allah yayi masa shine yaransa suka rufe shagon bayan sun bada sarin duk magungunan da ya bari, wannan dalilin ne ma har yasa da Habibu yayi min tayin wannan aikin na taho kano don ina xaune babu abinda nake, don haka babu wani magani da ban sani ba yanxu haka sai abinda ba a rasa ba..." Abba yace "Allah ya rufa asiri.... Yau kuma me ya hadaka da Nihad?" Khalil ya sunkuyar da kai yace "Bani da masaniyar na mata wani laifin yau, kawai dai abinda na sani saurayinta ya zo zai bani kudi yau da na kai ta babban shago xata yi siyayya, sai na nuna baxan amsa ba, shkkn abinda na sani kenan Alhaji" Abba yace "Kaje xa mu yi magana gobe" Daga haka Abba ya nufi cikin gida, Khalil ya koma gun mai gadi ya zauna letting out a deep breath. Washegari da safe Nihad ta leka window ya fi sau goma wai taga ko driver ya fara harhada kayansa xai bar gidan, amma sai taga ya kai su Sudais da Amina school, kuma da ya dawo taga ya ci gaba da zama bakin gate, kasa samun sunkuni tayi, ta dau wayarta tayi dialing number Inna, yana fara ringing ta daga, tace "Ina kwana inna" Inna tace "An tashi lafiya" Nihad tace "Inna wai jiya ya ku ka yi da Abba da kika xo ne?" Inna tace "Yace xai yi masa koren kare, ai shi bai san haka yake ba, da kyar ma in ya kwana a gidan ki bincika ki ga" Nihad tace "Wani bincike bayan ga mutum can a zaune ina kallonsa" Inna tace "Atoh, Kilan sai yau xai tafi, ai na gaya ma Ibrahim maganganu masu ta6a xuciya jiya, yace min in sha Allahu xai sallamesa, ina jin sai yau din xai koresa don jiya kinga ai dare yayi kar ace mutum bai da imani yayi kora cikin dare" Nihad tace "Sai anjima" Katse wayar tayi ta bude kofar daki ta fito, a parlor ta hadu da Nihal, Nihal tace "Kinsan in two days time xan koma school" Nihad ta tsaya ta kalleta tace "Toh ai baki gaya min ba" Nihal tace "Toh yanxu na gaya maki" Nihad tace "Toh yanxu da Habibu baya nan waye xai kai ki Zaria?" Nihal tace "Ni ma ban sani ba, sai Abba yayi magana" Nihad tace "Don kinga wannan drivern sallamarsa xa ayi yau" Nihal dake ta kallonta tace "Okay" Nihad tace "Ko dai har kinyi shopping din ki?" Nihal tace "Aa probably today or tomorrow, sai yanda Abba yace" Nihad tace "Okay ki min magana sai mu je har da ni" Nihal tace "Okay, baki da lectures yau?" Nihad tace "Toh ko ina da lectures ai babu driver da xai kai ni, but karfe tara nake da lectures" Bata jira cewar Nihal ba ta nufi kofar fita parlon ta fito compound, Backyard din gidan ta nufa kai tsaye gun tsuntsayenta su Saminu na gaisheta duk tayi kamar bata ji su ba, tsaye tayi bata motsin kirki tana kallon cages din birds din da duk suke a bude kuma babu birds din a ciki sai roban abincinsu da ruwa, duk cages din guda hudu a bude suke har na parrot dinta, Dawowa tayi da gudu cikin gida tana kallon Saminu dake shara Shafi'u na watering flowers din gidan cikin tashin hankali tace "Saminu ina tsuntsaye na aka kai min?" Saminu ya mike da sauri haka Shafi'u da yayi dropping watering can din hannunsa, Saminu yace "Suna can cikin kejinsu Hajiya" Ta gwalo ido tace "Wani cage din??" Duk suka nufi inda birds din suke, sai ga su sun dawo suna wuri wuri da ido, Saminu na in ina yace "Wllh Hajiya ko jiya sai da muka xuba masu abinci da ruwa...." Da sauri ta juya ta bar wajen ta nufi gun mai gadi cikin rawan murya tace "Aminu ina aka kai min tsuntsaye na?" Aminu yace "Suna can keji Hajiya" Cikin daga murya tace "Wani Cage din, abinda naje na tarar a bude babu komai ciki" Mai gadi ya mike da sauri yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, babu komai ciki?" Shi dai Khalil na xaune yana danne danne da torchlight phone, Aminu ya nufi inda birds din suke da sauri, Nihad da har kanta ya sara mata ta bi bayansa gabanta na faduwa, can ba a dau lkci ba sai ga ta ta dawo tsakar compound ta rusa wani uban ihu ta daura hannu a ka uwa warce aka yi ma mutuwa, Nihal ce ta fara fitowa a guje ta nufota tace "Nihad what happened?" Nihad ta fashe da matsanancin kuka tace "Wani yaje ya bude min cage din birds dina duk sun gudu, wayyo Allah na na shiga uku, wllh har sun saba dani Nihal, Parrot din har kiran sunana yake yace good morning" Su Aminu da Saminu dai na can gefe a tsaye sai wuwwurga idanuwa suke, Umma ce ta fito compound din Mumy na biye da ita a baya, Hankali tashe Umma tace "Lafiya Nihad, me ya faru?" Nihad ta nufeta tana kuka sosai ta kamo hannunta tace "Umma wani yayi releasing din min birds dina duk sun gudu babu ko daya" Umma ta saki salati tace "Waye da wannan danyen aikin, yanxu babu ko daya wa ennan tsadaddun tsuntsayen da Abbanki ya siya maki" Nihad na gyada kai cikin kuka tace "Wllh duk sun gudu, bude masu cage din aka yi don su gudu" Mumy dake kallonta tace "Shine xa ki 6ara baki haka ki daga mana hankali Nihad?" Umma ta kalli Mumy tace "Haba Maryam, ko don ba ke kika bada kudin siyan tsuntsun ba, kinsan yanda dabba ke da shiga rai kuwa" Mumy tace "Toh waye ya budesu har suka gudu? Sannan ita me yasa bata xuwa dubasu a kai kai yaushe rabon da taje inda suke" Cikin kuka Nihad tace "Wllh ina xuwa dubasu ki tambayi Aminu, kullum sai naje dubasu" Nihal tace "Toh ko da aka basu abinci ne aka mance ba a kulle cage din ba" Nihad ta durkushe wajen tana kuka kamar ranta xai fita tace "Ni wllh ko ma wa yayi min haka Allah ya isa ban yafe ba, Allah ya tsine ma koma waye, Allah ya isa, shi ma sai an nemasa an rasa wataran yanda na rasa tsuntsaye nahhh" Juyawa Mumy tayi ta wuce cikin gida, Umma ta dagota tace "Ai ba Allah ya isa xa kiyi ba, koma uban wa yayi wannan aika aikan dole a ganosa a hukuntasa, ki bar komai a hannuna kawai" Nihad na shessheka tace "Umma wanda yayi mun haka ya tsaneni ne shi sa yayi haka kuma sai Allah ya tsine masa albarka ya daidaice, Allah ya isana" Nihal tace "Ki daina cewa haka baki san ko..." A fusace Nihad ta mike ta hankadeta har sai da ta kusa faduwa, tace "Shut up plss if have nothing good to say" Bude baki Umma tayi, sae kuma ta kalli Nihal tace "To wuce ciki" Nihal ta ta6e baki ta juya ta koma ciki, Umma ta juya ita ma ta bar wajen, Nihad ta hade rai ganin yanda ma'aikatan gidan ke kallonta, cikin tsawa tace "Uban meye kuke wani kallona munafukai yan iska, ai har da hadin bakin ku aka sakar min tsuntsaye suka bi duniya, to ku sani wllh daga yau sbda ku ni xan dinga shiga kitchen sai in ga d'an iskan da xai xubo maku abinci ya kawo maku, for one week ba ku da abinci wllh a gidan nan tunda har aka sakar min tsuntsu suka gudu" Tana fadin haka ta juya fuuuu ta wuce ciki. Da yammacin ranan Farooq ya shigo gidan daga Abuja, Nihad da abun duniya ya isheta don har sannan Aliyu isn't picking her calls, ga kuma har yanxu bata ga Driver ya bar gidan ba, kuma babu ma wata alamar da ta nuna xai bari, yana nan a xaune tare da mai gadi, ko makaranta bata je ba sbda damuwa gashi har test Husnah tace mata anyi, ta mike daga xaman da take ta yi a parlor ta fito compound jin motar Farooq, tamke fuska tayi ganin Khalil da Aminu sun nufi Farooq, Khalil ya fara basa hannu da ladabi, suka gaisa, farooq dai sai kallonsa yake, Aminu dake ta rawar kafa yana washe baki yace "Ae shine sabon dreban gidan tun bayan tafiyar Habibu, yau kwanansa biyar ina jin a gidan nan" Farooq ya kara kallon Khalil daga sama har kasa, sai kuma yace "Driver??" Sai kuma yayi saurin cewa "Ohk maa sha Allah, ya sunanka?" Khalil yace "Ibrahim" Farooq ya gyada kai yace "Maa sha Allah...." Tuni Mai gadi ya dau jakar Farooq ya nufi cikin gida da shi, Nihad dake tsaye balcony ta hade rai tace "Toh ajiye kayi tafiyarka ko ka aikesa ne??" Aminu ya ajiye jakar ya juya sui sui ya bar wajen, Farooq ya amsa gaisuwan da Nihal ke yi masa ya nufi Nihad yace "What happened Nihad?" Kamar jira take ta fashe da matsanancin kuka, yace "Meye haka?" Cikin kuka tace "Ya Farooq wani axxalumin da baya tsoron Allah ya bude ma tsuntsaye na cage duk sun gudu har parrot din" Bude baki Farooq yayi yace "Garin yaya?" Ta karasa ta rungumesa tana kuka sosai, ta gefen ido khalil ya kalleta kafin ya juya ya bar wajen, Farooq ya dago kanta yace "But how did it happen" Tace "Kawai yau da safe naje basu abinci naga ba komai cikin cage din" Yace "Ow that's bad, bari anjima sai mu je ki siyo wasu" Ta marairaice tace "But how will d parrot get to know me just as the old one?" Yace "Yanda wancan din ya sanki sabon ma haka xai san ki" Daga haka ya kama hannunta suka shiga gidan tana share idonta. Bayan ta amshi nata tsaraban da farooq ya kawo mata ta wuce sama xuwa dakinta, wayarta ta dauka ta sake kiran Inna, yana fara ring Inna ta daga, Nihad tace "Inna har yanxu fa driver din na nan babu inda ya tafi don ma in gaya maki" A fusace inna tace "Ke raba ni da wani shegen dreba an shigo an kwashe min yan canjina wai barin gidan da nayi jiya da magariba, kowa sai ce min yake ba shi bane, to ni na saci abina koko?" Nihad ta tabe baki ta katse wayarta, sai kuma ta ja tsaki tace "Dama ba a abun arxiki dake..." Da daddare tana dakin farooq dake kallonta yace "Toh sai in ce masa me idan na kirasa?" A hankali tace "Kawai hakuri xaka basa a kan abinda driver din yayi masa" Farooq yace "Ba kince layinsa a kulle yake ba?" Tace "Aa ya ta6a saving numberka a gabana ai, ka tuna sanda ya kiraka da baka da lafiya?" Yace "Oh, ohk" Daukar wayarsa yayi ta kira masa number Aliyu yayi dialing, a kashe suka ji wayar, yace "It's switch off" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Ki je kawai, gobe sai in kirasa" Mikewa tayi tace "To sai da safe yaya....." Saura how many page free pages ya kare??? 07087865788✍🏻 💖💖 *NIHAAD*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📖✍🏻 10...... Khalil na xaune yana waya a bakin gate mai gadi ya karaso wajen daga boys quarters, Khalil ya saka wayar a aljihunsa bayan ya gama, Aminu da har ya xauna ya mike yace "Aa bari in baka waje ka ci gaba da wayarka...." Khalil yace "Na gama" Aminu ya dawo ya xauna yana kallonsa yace "Na lura baka son kayi waya a gaban mutane saboda hayaniya ko?" khalil yace "Haka ne" Aminu yace "Ina can tare da su Saminu muna ta jajanta lamarin tsuntsayen nan da suka gudu, abun da mamaki da al'ajabi, sun kusa shekara daya da rabi fa a wajen ba a ta6a nemansu an rasa ba sai yau" Khalil yace "Ai gwara da suka gudu kar xunubanta ya dinga shafarsu su ma" Aminu ya kyalkyale da dariya yace "Wllh baka da dama, ni tashin hankalina abincin da tace xa a hanamu, in an hanamu abinci ya xa mu yi? Ba fa kanta kenan, duk da nasan uwarta baxata yarda da hakan ba, amma makira ce tana iya biyomu ta kwace idan an kawo mana" Khalil yayi murmushi kawai, Aminu yace "Amma fa kana bani tsoro da mamaki yanda kake nuna mata baka shakkarta, akwai wani littafi da na ta6a saurara a shafa labari, kaga yanda ta sa ka gaba haka? To haka ita ma yarinyar littafin ta sa mutumin gaba yana aiki a kampanin babanta ita kuma ita ce manaja a kampanin, tayi ta masa walakanci da rashin mutunci daga baya ta xurma sonsa in gaya maka, To sai...." Dakatar da shi khalil yayi yace "Me kake nufi?" Aminu ya gyara xama yana washe baki yace "Toh wa ya sani ko hakan xai iya faruwa wataran, barin taga sambalele me dogon hanci, ka fa san matan nan ba alkibla garesu ba...." Khalil yace "Ta wahala.... banda abun ka ina ita ina talaka? Sai dai kuma bata san wani talakan ma ko da kudi aka hadasa bazai saurareta ba, in dai kamar ni talakan yake wllh ko kallonta baxai yi ba" Aminu ya gwale ido, sai kuma ya tuntsire da dariya yace "Yanxu kana nufi misali yau ace maka gata nan ka aura baxa ka aura ba?" Khalil yace "Misalinka ba me yiwuwa bane har duniya ta nade, don kuwa da in aureta gwara na aura Krista, ko kuma in dauwama ba auren, kai kasan darajan da Allah yayi ma ɗan Adam kuwa? To bari kaji ko da kudi wannan yarinyar baxata tsaya inda budurwata take ba, ga ta dai yar talakawa kamar ni amma ita wannan fitsararriyar baxata tsaya inda xata tsaya ba wllh...." Aminu yace "Aa dole xaka ji haushinta wllh, nima kuma ina taya ka jin haushinta kullum, ji tijaran fa da tayi maka daxu, banda yanayin rayuwa a ina xata ganka har ta cakume kwalar rigarka tana dungure kanka tana maka munanan xagi, a ƙalla ai xaka bata kusan shekara goma na sani, amma ta maka wnn cin mutunci da tijara gaban Nihal da kawarta, ba ma wannan ba ji yanda ta dau bahon ruwa gaba daya ta juye maka a cikin jama'a" Khalil yayi wani Murmushi bai dai ce komai ba, Aminu yace "Ni dai yau ace min ga ta in aura xan yarda in aureta ko don kudin babanta da kuma halaccinsa, sai kuma in saita mata xama...." Daga sama har kasa khalil ya kalli Aminu, bai san sanda yayi dariya ba yace "Kai ta kudin kake kenan" Aminu ya washe hakora, Khalil ya girgiza kai yana Murmushi, Aminu yace "Wllh ni fa naji dadin bude kejin nan da aka yi tsuntsayen suka gudu, Allah ne ya bi min hakki na abinda ta min jiya a kan su" Khalil yace "Ku kuka bar mata tsuntsayen suka kai har warhaka a gidan ai" Daga haka ya mike ya bar Aminu a wajen xai je yayi alwala kafin a kira isha'i. Nihad na komawa dakinta taga missed calls din Husnah da yawa, ta xauna gefen gado ta kirata, yana fara ringing Husnah ta daga, Nihad ta dinga jin hayaniya tace "Kina ina haka?" Husnah tace "Mozida suite" Nihad tace "Me ake yi a nan?" Husnah tace "Wllh na manta ban gaya maki ba shekaranjiya a schl, Abokin saurayin Naf ne ke birthday, nayi ta kiranki tun daxu baki daga ba dama wai in gaya maki" Nihad tace "Toh ai tun jiya ya kamata ku gaya min, kuma yanxu kinga dare yayi" Husnah tace "Kashhh, kinga ke matsalarki kenan Nihad, karfe takwas din ne dare?" Nihad tace "Toh ta yaya ma xa ayi in taho babu me kai ni, kinsan wawan nan har yanzu Abbanmu bai koresa ba wa yasani ma ko asiri yayi ma yan gidan duk suke supporting dinsa, Umma ce kadai ke bayana a ko da yaushe, throughout na xuba ido yau in ga ko xai tafi ban ga ya tafi ba" Husnah tace "Kinsan abinda zai faru?" Nihad tace "Aa" Husnah tace "Yanxu xa mu fita mu karo wasu wine, kawai ki san duk yanda xa ayi ki fito mu hadu a wannan katon supermarket din na anguwarku" Nihad tace "Kar fa ku bar ni inyi ta jira Husnah" Husnah tace "Haba wani jira, bayan gashi nan yanxu ni da Naff da Sumy za mu fito" Nihad tace "Okay, bari a shiga masallaci sbda yan sa ido, sai in fito" Husnah tace "Sai mun hade, kar kuma kice ban gaya maki ba, A abokan celebrant din har da 'ya yan gwamnoni, shiga ce ta kece raini xa ki yi, duk da nasan ki ba wasa" daga haka Husnah ta katse wayar. Nihad ta mike ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje jin ana kiran isha'i, ta dauro alwala ta fito da sauri, tada sallah tayi bayan ta idar ta fito da wani ubansun gown dinta ja wanda Aliyu ne ya siyo mata daga kasar waje ta saka, ko make up bata yi ba duk ta harhada kayan make up din da turarruka a wani babban jakarta da xae iya daukan hijab da takalmi da tarkace da yawa, tana jin an tada sllh sae da ta jira aka yi raka'a daya snn ta fita da sauri bayan ta sa ma dakinta makulli, tayi surveying parlor don tabbatar da babu kowa a ciki, ko wa na dakinsa, dama kuma gidan ana magrib kowa ke shigewa daki babu me shiga privacy din wani, sai kuma washegari idan an hadu wajen breakfast, yawanci da yake a bangaren Umma dakinta yake, Umma kan shigo taga ko tana waya kuma da wa take wayar, to dai ta sa ma dakin makulli ko taje xata shiga xata ji sa a kulle, da sauri da sauri ta fito compound nan ma ta ci sa'a babu kowa, duk suna masallaci, kan kace me ta bar compound din ta kama hanyar inda supermarket din da Husnah tace ta jirasu yake, tana isa wajen ko minti biyar ba ayi ba sai ga motarsu Husnah suka dauketa suka wuce, Husnah tace "Yanxu da Habibu na nan nasan da kansa zai xo ya daukeki idan aka gama partyn ko karfe sha biyun dare ne, yanxu dole kinga sai mun ajiye ki a nan after the party in ba dai saurayi kika yi a can ba" Nihad dai ta xuge jakarta ta fara gyara fuskarta xata yi light make up. Wajen partyn ya hadu iya haduwa kamar yanda Husnah ta fada ai kam ya yan manya ne suka cika wajen, very dim light ne kunne a inda suke birthday din, babu abincin da babu da abun sha tun daga ruwa, lemo, wine, alcoholic drinks, kai komai da akwai a wajen, gasassun rago biyu aka bankare wajen, ga manya manyan pepper chicken... cake din da budurwarsa tayi masa ma kadai abun kallo ne... duk hayakin cigarette ya turnike wajen, an sha shagali iya shagali a birthday din nan, abinda Nihad bata yarda da shi ba shine ta sake ma maza fuska a wajen, xata dai shige cikin kawayenta mata amma bata xama cikin maza, ko da kana ta shisshige mata ma banxa xata yi da kai tayi ta danna waya, Husnah ta kwankwade glass din wani alcoholic wine, glass na biyu kenan ta sha, su Naf da sauran yan matan wajen su ma duk wine din suke sha, Husnah na kallon Nihad dake rike da cinyar kaza da wani can drink a gabanta tace "Wllh ki ɗan dana wine din nan ya fi na wancan ranan dadi sannan shi wannan babu abinda xa ki ji idan kika sha, wllh soo cool" Nihad tace "Aa baxan sha ba drink din nan ya isheni" Zully tace "Ke dadina dake kwabsin ki yayi yawa, don Allah ki ɗan kurba idan bai maki ba sai ki bari kar ki sha, nima kinsan ai ban fiye son wines haka ba, amma tunda kika ga ina shan wannan ya kamata kisan ba karya" Nan duk suka mata caaa akan cewa ta ɗandana idan bata ji dadinsa ba sai ta bari, Husnah ta cika mata glass din gabanta tace "Kiyi sipping first ki ji" Nihad ta dauka ta kai baki ta kurbi kadan, bayan few seconds ta wara ido tana kallonsu tace "Waow its really nyc, it tastes good" Husnah ta kyalkyale da dariya tace "Ba na gaya maki ba da kin tsaya kin kwabsawa" Nan Nihad ta kwankwade wine din, Husnah ta kara cika mata glass nan ma ta shanye, Naff sai dariya take tana cewa "Wllh ki bar ta haka Husnah tam ni dai na gaya maki" Husnah tace "Toh meye a ciki ai baya wani bugarwa" Haka dai Nihad ta sha wine tayi nak, party din da ba a karasa da ita ba kenan tayi ta masu layi a wajen, banda dariya babu abinda suke mata, Husnah tace "Kaii amma jininta ma bai da karfi wllh, ɗan wannan wine din shine xai bugar da ita" Nan suka ci gaba da shagulgulansu, Nihad kuwa ta kife kai a wajen sai bacci, ba a tashi birthday din nan ba sai karfe dayan dare, Husnah ba irin tashin da bata yi ma Nihad ba amma ta ki tashi, da ta dagota xata koma ta kife kai, wani abokin celebrant din yace "Na kama daki a nan why not kawai ku barta ta kwanta ta huta" Husnah tace "Aa nasan halinta tana farkawa xa mu samu matsala da ita, kawai dai kamata yayi mu ma a kama mana dakin dama dare yayi ba lallai a bari mu shiga schl ba yanxu, idan ya so duk sai mu kwana a nan" Ba don ransa ya so ba haka nan ya kama masu dakin, suka ciccibi Nihad sai dakin suka kwantar da ita saman gado, Husnah dai na ta kaffa kaffa da Iphone din Nihad a wajen tunda ta san halin wasu daga yan matan dake wajen. Sai kusan biyu suka kwanta a dakin bayan duk sun yi wanka. Karfe hudu da rabi Nihad ta farka da wani axababben ciwon kai, da kyar ta mike xaune tana bin dakin da kallo, sai kuma ta sauka tana layi ta nufi kofar dake dakin wanda bandaki ne, ta kuma sani tunda sun saba lodging a wajen ita da su Husnah, tana shiga bayin bayan tayi fitsari taji wani amai ya taho mata, nan ta dinga kwarara aman tana rike da cikinta dake juya mata, da kyar ta wanke bakinta bayan ya lafa mata ta fito, bata sake komawa baccin ba sbda ciwon kai me tsanani da ya takurata, ganin biyar ya kusa ta ta6a Husnah da kyar, ta fi minti goma tana tada Husnah dake xuba minshari kamar wani kato, kafin ta bude ido cikin magagin bacci tace "Wai ya aka yi Nihad?" Da kyar Nihad tace "Don Allah wa xai yi dropping dina gida kafin yan gidanmu suyi noticing bana nan, asuba ya riga yayi" Husnah ta ja tsaki tace "Tsakar daren nan wa xai wani kai ki gida kowa na bacci, ki bari gobe kawai" Nihad tace "Ke asuba fa yayi ki duba agogo ki ga, wllh na manta yayanmu na gida zai iya xuwa bedroom dina yace xai tasheni inyi sallah, idan yana gari duk yana tashin mu...." Husnah tace "Ohh God Nihad ki barni inyi bacci mana, haba" Daga haka ta juya ta ci gaba da baccinta, tashi Nihad tayi da kyar ta bude jakarta ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta bude kofar dakin ta fita, babu kowa reception din hotel din sai tv dake aiki, ta fita haraban wajen, wani mutumi ta gani xaune yana ta xukar ta6a a waje, ganinta ya kashe ta6ar, ta nufesa tana kallonsa ganin bahaushe ne tace "Bawan Allah idan babu damuwa ina son taimako wajenka don Allah" Daga sama har kasa yake kallonta yace "Taimakon me?" Tace "Nasarawa GRA nake son ka ajiyeni pls, kawayena da muke tare da su bacci suke ni kuma ban xo da motata ba" Yace "Ohk babu damuwa, bari in dauko makullin motata" Tace "Toh Nagode, nima xan dauko jakata" Daga haka duk suka koma ciki, ta shiga dakinsu, shi ma ya shiga nasa, ta tattara komai nata a jakarta, wayarta ne kawai bata gani ba, zaro ido tayi lkci daya hankalinta ya tashi ta fara tashin Husnah a rikice tace "Husnah ina wayata??" Da kyar Husnah dake ta snore kamar doki ta bude ido, a fusace tace "Ohh my God Nihad ki kyaleni mana inyi bacci, me yasa kin fiye takura ne wai" hankali tashe Nihad tace "Dalla can ina wayata??" Husnah ta ja wani dogon tsaki ta daga pillow dinta ta zaro wayar ta ajiye mata a gefe sannan ta ci gaba da baccinta, Nihad ta sauke ajiyar xuciya sannan ta dau jakarta da wayar da sauri ta fita, Tsaye ta gansa a haraban hotel din yana jiranta jikin motarsa, bayan ta shiga motar shi ma ya shiga, suna fita daga suite din yace "Ku ne ku ka yi birthday jiya?" Gyada masa kai tayi kawai, yace "Gaskiya ne, birthday din na manya ne" Duk surutun da yake Nihad ba tankasa take ba, banda tashi babu abinda xuciyarta yake, she was so uncomfortable, a haka ta dinga daurewa tana masa kwatance har suka isa dai dai inda su Husnah suka dauketa daren jiya, yace "Ina gidan naku?" Ta nuna masa wani layi dake a rufe tace "xan karasa da kafa, kaga gate din a kulle yake" yace "Ohk amma ya sunanki?" Cike da karfin hali tace "Aysha" yace "Maa sha Allah, Aysha ki bani digit dinki mana" ta gyada masa kai kawai, ya mika mata wayarsa ta amsa tayi dialing wani old line dinta dake a kashe tace "Wayar a kashe yake sai na shiga gida na kunna" yace "Toh shkkn nagode Aysha ni sunana Mustapha" tace "Nagode, sae anjima" daga haka ta bude motar ta sauka, cike da karfin hali take tafiya don jiri ke dibanta, ta shiga layin da ta nuna masa, sae da ya ga tayi nisa sosai a layin sannan yayi reverse ya bar wajen, tana waigowa taga ya wuce, ta juya da sauri ta dawo ta fita daga layin sannan ta dau hanyar nasu layin, gani tayi kamar an idar da sallah bayan ta iso kusa da gate din gidansu, da sauri ta bude karfen inda aka xagaye da flowers a kofar gidan nasu ta shige bayan flowers din ta buya tana maida numfashi, don har an fara fitowa daga masallaci, tana jin aka shiga cikin gida aka kulle gate, Sai kuma ta sake jin an bude gate din, Muryar Abbanta taji yana amsa gaisuwa nan bakin kofar gate din, sai da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta, ta kara yin lamo a cikin flowers din duk da ant da taji suna cizonta bata damu ba, ta fi minti bakwai a haka bata sake jin motsin kowa ba bakin gate din, hautsinewa cikinta ke yi taji amai na taho mata, kokarin fitowa take yi daga flower din don ta samu ta shige cikin gida, kawai taga mutum xaune a dakalin dake kusa da inda take labe, sai da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta don duk xatonta ya Farooq ne don shi ma ya kan xauna a waje idan aka idar da sallah, ya daga kai jin motsi, sai kuma ya mike tsaye da sauri, komawa baya yayi yana kallonta with surprise, ita kuwa tsabar tsorata aman da take rikewa ya taho mata, ta durkusa ta dinga kwarara aman a wajen, kauda kansa yayi bayan yayi perceiving din aman da take yi, ya sake kallonta this time around da wani expression a fuskarsa, duk sae da ta amaye sauran liquor din cikinta sannan ta mike da kyar, ko kallonsa bata yarda tayi ba ta shige gate din gidan, ya bi ta da kallo babu ko kiftawa, ko second ashirin ba ayi da shigarta ba sae ga mai gadi da gudu ya fito waje yana kallon Khalil yana zare ido yace "Ina me tabbatar maka bata kwana gida ba, dawowarta kenan daga duk inda ma taje wllh" Khalil dai bai ce komai ba, mai gadi ya yamutse fuska yace "Ni warin giya ma nake ji, ko kai baka ji ba don Allah?" Khalil ya juya ya shiga gate din gidan ya xauna nan saman bench dake gefen dakin mai gadi with numerous thought running his mind, mai gadin ma ya shigo ya zauna yace "Ni fa sai nake ganin ma kamar warin giya take ko kai baka ji ba?" Khalil ya kallesa yace "Amma baka wanke bakin ka ba ko?" Mai gadi ya ɗan zaro ido, sai kuma yayi yake yace "Ai shi xan wanke ma na fito yanxu..." Tashi yayi da sauri ya shige dakinsa, Khalil ya kalli hanyar gate din, sai kuma ya mike ya fita, jakanta da ya hango cikin flowers da ta bari ya dauko ya shige cikin gidan sannan ya nufi chalet dinsu, A parlor ya tadda Su Saminu sun yi dai dai duk suna bacci, ya ciro makullin daki a aljihu, ya bude dakin sannan ya shiga ya kulle kofar, xaunawa yayi gefen gado ya bude jakar, takalma heels ya fara cirowa da kayan kwalliya da turarruka, sai iphone dinta da ya gani, ya dinga jujjuya wayar don a lock yake, sai kuma ya ajiye ya ci gaba da ciro sauran kayan jakan, bai san sanda ya bude baki ba ganin kwalban Codeine, can ya ajiye a gefe, ya bude wani zip dake cikin jakar, still yayi ya dinga kallon abinda ke wajen babu ko kiftawa, ya kai hannu a hankali ya cirosu gaba daya yana jujjuyawa, prophylactics ne na maza da na mata, ya ajiye su a gefen gado ya mike ya nufi window din dakin yana kallon waje babu ko kiftawa. Nihad na fitowa daga wanka aka bude kofar dakin, sae da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta don tsoro, Umma ce ta shigo dakin ta rufe kofar murya can kasa tace "Daga ina kike Nihad?" Nihad ta daburce tace "Ni Umma?" Umma tace "Aa ban son karya ba yanxun nan naga giftawarki ba na fito daga parlon Abbanku?" Nihad tayi narai narai da ido tayi shiru, Umma tace "Gaya min gaskiyan inda kika je" A hankali tace "Wata kawarmu ce ke birthday Umma" Umma tace "Ki dai nutsu, in ma xaki birthday ae sai ji gaya min ni baxan hanaki ba, amma baxa je makarantar yau ba bacci xa kiyi ko?" Tace "Aa xan je" Umma tace "Toh sai kiyi ki shirya karki makara" Daga haka Umma ta juya ta fita, Nihad ta sauke ajiyar xuciya, sai yanxu da ta sake wani aman da xata yi wanka taji ta ɗan fara dawowa dai dai, kanta ya daina juya mata, tana gaban madubi tana shafa mai ta tuna da jakarta, xaro ido tayi ta mike da sauri ta dau hijab dinta gogagge ta saka sannan ta fito daga dakinta, downstairs ta sauka ganin Farooq a xaune dining area tace "Yaya ina kwana?" Yace "Kina jin ina Knocking ki ka ki bude kofa daxu?" Tace "Aa yaya ina bandaki ne, ai na tashi sannan ma" Bai ce komai ba, ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ta bude kofa, yace "Ina xa ki?" Ta marairaice tace "Xan je in duba ko Allah xai sa tsuntsayen sun dawo" Murmushi kawai yayi ta juya ta fita, da sauri ta nufi gate, taji dadin ganin mai gadi baya bakin gate din, sannan khalil ma baya wajen, tana bude gate ta samesu su biyu xaune kofar gidan, suna hada ido da khalil ta daburce, sai ta hau kame kame, bata amsa gaisuwar da mai gadi ke mata ba tace "Aminu a layin nan babu inda zan samu katin waya?" Aminu yace "Inaa, Hajiya ai sai an fita can supermarket" Tace "Ohk" Da gefen ido ta dinga lekan cikin flowers din dai dai inda ta buya amma bata ga alamar jaka ba, nan hankalinta ya tashi sbda wayarta na ciki, bata san lkcn da ta karasa wajen ba tana kara dubawa da kyau, Aminu yace "Wani abu kike nema ne Hajiya?" Wani shegen kallo tayi masa tace "Toh ina ruwanka?" Khalil dai na ta danna er karamar wayar hannunsa, ta saci kallonsa. 07087865788✍🏻 💖💖 *NIHAAD*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 11 Juyawa Nihad tayi daga karshe ta koma cikin gidan don ko kallon inda take Khalil bai yi ba, to wai wa ya dau jakarta? lkci daya jikinta yayi sanyi hankalinta ya tashi fiye da da, haka nan ta shiga gida jiki ba kwari ta koma dakinta ta shirya, Hijab har kasa ta saka ko powder bata shafa a fuskar ba, ta fito ta tafi bangaren Mumy, xaunawa tayi saman kujera ta gaisheta sannan tace "Mumy xan tafi makaranta ina da lectures karfe takwas" Mumy ta kalli agogo ganin bakwai da rabi tace "Kinyi breakfast ne?" Tace "Xan yi idan na sauka" Mumy tace "To ko ke fa da kika sa Hijab yau, kinga yanda yayi maki kyau, amma kullum in ta maki magana daya a kan shegun mayafan nan da kike sawa ba kya ji" Nihad ta ɗan kirkiri murmushi ta mike tace "Sae na dawo" Mumy tace "Toh Allah ya tsare, kiyi addu'a kafin ki fita" Nihad ta amsa da "Toh" sannan ta fita. Gaba daya Nihad neman appetite dinta tayi ta rasa, daga karshe nan ta bar abincin tayi ma Umma dake parlor sallama ta fita gidan, mai gadi kadai ta samu xaune bakin gate, ta nufesa tana tsaye dab da shi tace "Aminu don Allah baka ga min jaka a bakin gate ba? Kamar a nan na yar jiya da daddare, ko da safe nan don Allah baka gani ba??" Yace "Subhanallahi jaka Hajiya? ae ko wllh tllh ban gani ba, kema kin san da na gani ae xan adana maki" Nihad ta rasa abun cewa tayi shiru, iphone dinta fa na jakar yanxu ta ina xata fara? Wani xufa ta ji na keto mata, can ta dake tace "Ina driver din?" Aminu yace "Ya tafi yayi wanka" Tace "Sae kaje kace masa ya fito ya kai ni makaranta ni dai" Aminu ya mike da sauri yace "Toh Hajiya" daga nan ya nufi chalet din. Bayan Aminu ya shiga har dakin da khalil ke ciki ya sanar masa abinda Nihad tace, khalil dake zaune gefen gado yana combing kansa yace "Ta saba xuwa makaranta karfe bakwai da rabi dama?" Aminu yace "Atoh dae, nima ban ta6a ganin ta fita da safe xuwa makaranta ba wai kuma ran asabar, amma kai dai kawai ka fito kaje ka kai ta kar ta kara maka wani fitsarar" Khalil ya kallesa bai dae ce komai ba yana ci gaba da combing din kansa, Aminu ya bi dakin da kallo yace "Wai!!! amma kana kokarin gyara dakin nan, dubi fa dakin kamar a can daya bangaren, ba dauda ba wari ba tarkace, wannan ai idan na kwanta a nan sai in makara al-qur'an...." Khalil ya mike yace "Mu je..." Aminu ya kasa kunne yace "Ba waya bace ke wannan rurin?" Khalil yace "Mu dai je" Aminu ya mike ya fita dakin, Khalil ya bi sa da kallo kafin ya dage duvet din da ya lullube jakar Nihad da shi a saman gado sannan ya bude jakar ya ciro wayarta dake ta vibrate alamar kira, Husnah ya kara gani for the fourth time a jikin screen din wayar, tun daxu take kira, nannade wayar yayi da duvet don baxae iya silencing dinsa ba sbda security dake jiki, ya dau makullin mota ya fita daga dakin ya kulle sannan ya fita compound. Yanda xaka san abun duniya ya taran ma Nihad xama tayi a kan bench da mai gadi da Khalil ke xama, ita dai tana da yakinin dole Khalil xai hango jakar a bayan flowers kuma ai a bude ma ta bar karfen wajen, wai to don bashi da kunya sai kawai ya kama ya dau mata jaka, yaushe ta sake masa har xai kai hannunsa kan jakarta, wato yanxu jira yake sai ta tambayesa kenan? Cabdi... tana hangosu tayi maza ta mike ta sha kunu, Khalil dai ko kallon direction dinta bai yi ba ya tafi gun motar ya bude ya shiga, bayan yayi warming mai gadi ya bude masa gate, Sai da ya fita compound sannan Nihad ta fita ita ma tana tafiya a hankali ta bude back seat ta shiga ta xauna, Aminu ya dinga daga mata hannu alamar a dawo lafiya, ko kallonsa bata yi ba, Khalil ya ja motar suka bar layin, tunani take to yanxu dai tambayarsa jakarta xata yi? Cab gaskiya baxata yi hakan ba, m ta saci kallonsa ta madubi suka yi ido hudu, da sauri ta dauke kanta ta wani daure fuska ta zuge zip din wani jakar da ta dauko ta fiddo chewing gum ta bude ta jefa baki, shi dai driving kawai yake, sai da suka kusa makarantar tayi gyaran murya tace "Malam ka bude min Ac xafi ya dameni...." A takaice yace "Ke kika san meye shi" Tayi masa wani kallo tace "kace me??" Bai tanka ta ba, ta masa wani shegen harara ta ja tsaki kasa kasa ta ci gaba da taunar chewing gum dinta, suna isa makarantar dai dai department din nasu yayi parking, tana ta sauraron ta ji ko xai yi maganar jakar amma shiru, gabansa kawai yake kallo, ganin bata sauka ba, kuma kamar bata da niyyar saukan yace "Ko yau ma xa a bar maki makullin ne?" Ta galla masa wani harara tace "Ai ba ni na kawo motar ba balle ka bar min makullin" tana gama fadin haka ta bude motar ta sauka ta ki kulle door din tayi tafiyarta, ya bi ta da wani kallo, sai kuma ya sauka ya kulle sannan ya hau motar ya tafi.... Husnah na ganin Nihad tace "Shine nake ta kiranki kike danna min busy Nihad?" Nihad ta sauke ajiyar xuciya amma ta ki bata amsa, ta nemi seat ta xauna, wato dai a takaice drivern nan ne ya dau jakar tunda gashi har Husnah ta kira ana ta danna mata busy, lallai mutumin nan raini me karfi ya shiga tsakaninsu, bayan dauke mata jaka sbda guts har bude jakar ma yayi kenan, muryar Husnah ya dawo da ita daga tunanin da take, tace "Ina magana kin min shiru, dama ba komai bane ce maki xanyi ki taho da jakar da kika je birthday jiya da shi, don akwai abubuwana a ciki" Nihad ta kalleta tace "Abubuwanki kamar me?" Husnah tace "Kwalban Codeine dina da Naff na ciki, sai prophylactics, ni ina jin kamar ma har da lingerie dina a jakar, don na duba ban gani ba...." Nihad ta zaro manyan idonta tace "Duk a cikin ina???" Husnah tace "Jakarki mana, kinsan yana da girma" Nihad bata san sanda ta mike ta dafe kirjinta ba tace "Na shiga uku...." Da mamaki Husnah tace "Kin shiga uku kuma? Me ya faru?" Nihad tayi narai narai da tace "Wayyo Allah na, Me yasa xa ki min haka ki ajiye abubuwan nan a cikin jakata Husnah? Me yasa xa ki min haka? Gashi yanxu jakar ta fadi a bakin gate ban san wanda ya dauke min ba" Husnah ta gwalo ido tace "Kaiii, garin yaya kika yarda jaka a bakin gate Nihad?" Nihad da abun duniya ya isheta ta koma ta xauna ta cije yatsa tace "Na shiga uku" Husnah ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh kinsan wa ya dau jakar ne?" Ta kalli Husnah tace "Wallahi wannan driver din nake zargi don shi kadai ya gan ni sanda na dawo da asuba don a bayan flowers dake kofar gida na fara buya as a result of people coming out from the mosque after subhi prayer" Husnah ta rike ha6a tace "Ji tsiya, Driver kuma?" Nihad ta kasa cewa komai tayi tagumi, Husnah tace "Tabb shine kika yi shiru, to me kike jira da har yanxu baki tambayesa ba?" Nihad tace "Toh me xan ce masa? Bayan ban ga sanda ya dauka ba, Har wayata fa na cikin jakar, idan ba sata yake son yi ba ai xai ba Aminu ya ajiye min" Husnah tace "Ehh lallai wannan mutumin ya rika, shi ke ta ja min busy kenan? Wato dai har ya bude jakar" Nihad ta xaro ido tace "Na shiga uku, gashi kin xuba abubuwa kika ce cikin jakar" Husnah ta mata wani kallo tace "Ke dalla to meye, koma me ya gani cikin jakar ba shi ya ga duhu ba, kuma ma bansan uban me kike jira da har yanxu baki tambayesa jakarki ba, ko tsoronsa kika fara ji? ai ba ma tambayarsa xa ki yi ba wai ko ya ga jaka ko bai gani ba, kawai ce masa xa ki yi ya baki jakar ki da ya dauka kar kiyi masa rashin mutunci, kuma kada ya sake ta6a maki kayanki ko da kuwa a titi kika yar don baki aikesa ba" Nihad dai ta rasa abun cewa tunani iri iri ke yawo a ranta, Husnah ta kyabe baki tace "Ni dai ki adana min prophylactics din nan foreign ne ba na kasar nan bane kuma tsada ke garesu, Codeine din kuma shi ma nasan ba kya sha, kar ki je ki xubar ki adana mana gaskiya" Tashi Nihad tayi ta bar mata wajen ta koma seat din baya abun duniya ya isheta, yanxu mutumin nan duk ya ga abinda Husnah ta saka mata a jaka? To amma ya ma yi mugun rainata gaskiya, waye shi da har xai bincika mata jakarta?? A daddafe Nihad ta yi lectures daya tace xata tafi gida, Husnah tace "Ke don Allah ki saki ranki, ko Abba ne ya ga jakar nan ya dauka ya bincika ai sai haka, me xai dameki akan wani shegen driver dinku ya bude jakar ki? Ae rashin mutunci mafi muni xaki masa idan kin koma gida anjima, ni abinda ya fi damu na ma wayarki ne wllh, don matsiyacin sai ya iya dauka yace xai je ya siyar bai san wayar nan sai ta siye duk yan kauyensu ba, yanxu kawai ki xo mu je police station, cikin lokaci kalilan xa ayi tracking" Nihad ta zaro ido tace "In tona ma kaina asiri kenan, kin zata na gaya ma kowa cewar na yarda jaka da waya a ciki? To har Nihal bata sani ba" Husnah tace "In kince ayi cikin sirri babu tonon asiri ai sai ayi hakan, duk fa mutanena ne, amma wllh so nake a walakanta sa idan aka ga wayar a wajensa, a nakada masa shegen duka" Nihad tace "Husnah bari in je gida ko xan ji saukin abinda ke damuna, i can't endure anymore" Husnah ta ta6e baki tace "Wllh kina da sa ma kai damuwa, duk ki bada space din da lamarin driver xai dinga damunki haka, to wai shi wannan driver din daga ina ya xo yake abu isa isa da gadara haka?" Mikewa Nihad tayi tace "Duk yanda ake ciki xan kiraki da wayar Nihal ai tana da number ki" Daga haka ta fice daga hall din, tun da ta fara school din bata ta6a trekking da kafafuwanta har bakin titi ba sai yau, haka nan ta tsayar da adaidaita shi ma xata iya kirga iya sau nawa ta hau sa a rayuwarta, suna isa gida ta sauka ta bude jakarta ta basa kudi sannan ta shiga gidan, Aminu ne kawai bakin gate, ta ɗan bi compound din da kallo sai kuma tayi kasa da murya tace "Aminu baka tambayar min driver din can ko ya ga jakata ba kuma?" Aminu yace "Anya, don ina da yakini da ya gani xai nuna min, ai shi mutum ne me gaskiya da amana" Ta wani galla masa harara tace "Dallah Malam rufe min baki, duka duka kwananku nawa tare xaka san yana da gaskiya da amana, ashe kai dolo ne ma ban sani ba? To bari ka ji wayata ce ta kusan miliyan daya da rabi a jakar nan" Driver ya gwalo ido yace "Subhanallahi, subhanallahi...." Nihad ta saci kallon wanda ke tahowa ganin driver din ne ta daure fuska ta juya ta nufi cikin gida da sauri, xaunawa Khalil yayi gefen Aminu ganin yanda yake zaro ido kamar mara gaskiya yace "Me ya faru kake buda ido haka" Aminu yace "Ba nace maka ta yarda jakarta ba daxu har tana tambayata ko na gani, to wllh wai har da wayarta na miliyan biyu da rabi a cikin jakar" Khalil ya ciro karamar wayarsa yace "To ta huta..." Aminu yace "Atoh dai, Ta kuwa huta wllh, don yau tana sa uban a gaba ya siya mata sabo wallahi sai ya siya, sai dai uwarta ta hana amma tsaf in dai ita ce xai siya mata, kai kaji waya har miliyan uku, ni yanxu na samu irin kudin nan ai kauye xan koma in tada gini malam, inci me kyau in sha me kyau, sannan in kara mata biyu...." Khalil na kallonsa yace "Haba?" Aminu yace "Wllh tllh, albashin namu fa Hajiya ke amsowa a wajensa ta bamu, Ni dai ban san ko nawa yake bata ba amma dubu 50 50 take bamu, kuma da farkon xuwana akwai wani lkcn da ya ta6a bani da kansa wllh dubu 70 ya bani, to kilan dai har da kyautatawa ce irin tasa ban dae sani ba" Khalil dae bai ce masa komai ba. Nihad na shiga cikin parlor ta tafi dakinta direct, xaunawa tayi gefen gado ta rafka tagumi abun duniya ya isheta, tun da shegen mutumin nan ya xo gidan nan bata da kwanciyar hankali, bude kofar dakin aka yi Nihal ta shigo da sallama, Nihad ta daga kai tana kallonta, Nihal ta karaso ta xauna gefenta tace "Amma ba ki jira ku gama lectures din yau ba kika taho ko" Nihad ta yatsine fuska tace "I am tired, kawai shine na dawo" Nihal tace "Toh ki kwanta ki huta, xuwa yamma sai ki rakani shopping din, kinsan gobe sunday xan tafi fa" Nihad tace "Wa xai kai ki shopping din??" Nihal tace "Khalil" Nihad ta juya ido tace "Waye haka?" Nihal tace "Driver..." Nihad ta bude baki ta rike ha6a tace "Wai khalil? Shi uban wa ya basa wannan suna yana driver? Ni fa na xata kinyi wani saurayi ne Khalil ban sani ba, shi driver din ne yace maki sunansa khalil?" Nihal dai kallonta kawai take, Nihad ta gyada kai tace "Tabdi, ana iskanci a duniya, shi yasan ma'anar Khalil din ma kuwa?? Yau naga mutumi da karfin hali, ke kuma wawuya shine kika yarda sunansa Khalil, to wllh karya yake ba abinda ya hadasa da wannan sunan" Nihal tace "To ko ma dai meye sunan Abbanmu garesa, ko so kike in kira sunan Abba gatsau?" Nihad tace "Toh meye don kin kira tunda ba sunan Abban kika kira ba? Meye don kin ce masa Ibrahim ba shine sunan nasa ba? Wato dai ke kika makala masa khalil din kenan?" Nihal tace "Aa, yace haka ake kiransa dama, ni bani na sa masa ba" Nihad ta bude baki tace "Ji shegen karya, to karya yake munafuki, uban wa ke ce masa haka? Amma fa mutumin nan yayi mugun raina maki wayo ma dai, a kauye wa yasan wani khalil, dama Halilu yace shine xan yarda, to wai tsaya ma tukun, fira ku ke har yake gaya maki sunansa khalil??" Mikewa Nihal tayi tace "Woo na gaji da question and answer din nan, Ko ma meye sunansa ba abu bane da za mu tsaya muna bata lkci akai, ni dai anjima ki shirya mu je Sahad store din" Nihad tace "Allah ya kiyaye in dai can xaki wllh baxan je ba, ga wajaje irinsu wellcare kice min Sahad, ai kowa da kowa ke xuwa Sahad" Nihal ta juya ta kalleta, sai kuma ta girgiza kai kawai ta fita daga dakin. Nihad ta rike ha6a tace "Ji maye wai khalil, shi a lallai ya xo gidan masu kudi bari ya maida sunansa irin na yan gayu wai khalil, aa Khalo ba khalil ba" Ta ja tsaki ta mike ta shige bandaki. Ta a fitowa ta koma gefen gado da take xaune ta xauna, tunani ta shiga yi a ranta, to ko dai taje can chalet din da kanta ta duba jakarta ne? Ta kalli agogo lkci daya ta mike ta fito main parlor Umma tace "Aa har kin dawo er baba" Nihad ta gaisheta sannan ta fita balcony har sannan taga yana xaune tare da Aminu a bakin gate, komawa ciki tayi ta shiga kitchen sannan ta bude kofar kitchen din da xai sada ka da back yard din gidan wanda ta nan ma xaka iya xagawa har xuwa Chalet, ganin yanda Hafsah ke kallonta ta sha kunu tace "Ya dai da kallo haka ke kuma?" Hafsah ta kauda kanta, Nihad ta fita da sauri ta xaga ta baya sai Chalet, bata ga takalmin kowa a bakin kofar ba alamar su Isiyan ma duk basa nan kenan, a hankali ta bude kofar tana leka parlon sannan ta shiga, da sauri sauri ta fara dudduba parlon, har xuwa dining area bata ga alamar jakarta ba, har bandakin dake parlon sai da ta bude, wanda sai da ta kusa amai, ta kullo da sauri tana yatsina fuska ta yi hanyar dakunan chalet din, duk dakuna biyun dake a bude sai da shiga tana tottoshe hancinta tsabar tsami da doyi, na ta bincika kaf Ghana must go da ta gani a dakunan amma bata ga jakarta ba, dakin da khalil ke ciki ta murda ta ji a kulle, to ko dai nan dakin aka ajiye jakar nata shine har da kullewa da makulli, tunanin inda xata fara nemo spare key ta shiga yi, can ta zare key din dake jikin kofar su Isiya ta juya ta fita da sauri ta xaga ta koma kitchen, sai da ta wanke hannunta da morning fresh ta hada har key din tana yatsina fuska sannan ta shigo parlor, har wani tashi taji xuciyarta ke yi sbda warin da ta dinga inhaling, kazami irin wannan har shi xai takura mata a gidan nan ya dinga shiga gonarta, dubi wajen da suke kwana wanda ita ko pig take rearing baxata bari yayi rayuwa a irin wannan kazantaccen wajen ba, tana wannan tunanin ta faki idon Umma dake waya ta shige bangaren Abbanta, direct dakinsa ta wuce bayan ta shiga parlor, nan ta hau bude duk wani drawer da ke dakin, a bedside drawer ne ta ga bunches of spare keys na gidan, tayi murmushi ta kalli na hannunta sannan ta hau duba irinsa, kaf irinsu guda uku dake wajen duk sai da ta dauka incase of necessity sannan ta mayar da drawer din ta kulle ta mike ta fice daga dakin, kitchen ta sake bi ta xaga xuwa Chalet din, da sauri ta shiga ciki ta nufi hanyar rooms din, dakin dake kulle tayi facing, ta hau gwada makullen hannunta da sauri da sauri, lkci daya ta bude dakin, wani farin ciki ne ya lullubeta, ta shige ciki ta kulle tana bin ko ina da kallo gabanta na faduwa? Banda kamshi babu abinda ke tashi a dakin, rigarsa da ta gani saman gado ya sa ta gane shine a dakin, rike ha6a tayi.... to gidan uban wa ya samo wannan turaren da ya xuba a dakin haka, bata daina bin dakin da kallo ba ta karasa middle of the room, the room look so different kamar ba a chalet din ba, babu tarkace da kaya kamar irin na su isiya sannan everywhere looks so neat and tidy, ta kyabe baki without bothering ta hau yin abinda ya kai ta dakin, Duvet ta gani kamar an rufe abu da shi ta tafi da sauri ta daga sai ga jakarta a ajiye saman gadon, xaro ido tayi wani farin ciki ya lullubeta, ta bude jakar tana bincikawa da sauri, banda abubuwan da Husnah ta xuba mata a jakan sai nata tarkacen bata ga alamar wayarta a ciki ba, nan kuma ta marairaice tana bin dakin da kallo, a ina to ya ajiye mata wayar?? Sake jakar tayi ta nufi tasa jakar kayan dake dakin, sai bin jakan take da kallo kafin ta durkusa ta xuge zip din, ko karasa bude zip din bata yi ba tayi ido hudu da wayarta, babu bata lkci ta dauka, dai dai nan kuma aka bude kofar dakin, tsabar rudewa da tsorata da tayi bata san sanda ta mike ta saki wayar jikinta na rawa tace "Wayyoo... Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" 07087865788 ✍🏻