first 3months din kawai ya dawo gida,Mubeen ba karamin murna yayi da hakan ba,se yaki gayawa kowa nasa randa ze dawo.Tun asannan ne ya soma k'irgen ranakun daya rage masa ah Indiar.Ayanxu haka sati guda cur! kawai ya rage masa ya dawo.
****
watarana bayan mun gama morning lectures,sae kawai naji ina jin bak'on al'amari ajikina,zazzabi meh k'arfin gaske naji yana nemar rufeni,nayiwa Ash sallama na nufi office din Mahmood.Yana ganina ya taso arud'e yana fadin"My Zahmood yaya dai? Meya sameki?"
Amai shine ya biyo bayan tambayoyinsa,amai nake kamar zan amayo hanjin cikina,duk yabi ya rud'e.Students din da suke cikin office din sae ce min suke "Sorry ma,it shall be well with you.... "
Saida Mahmood ya wanke min fuska,wani student ya taimaka yayi clearing inda nayi amai.Ya daukeni kamar wata 'yar baby yana fadin"Dolene muje asibiti Zahmood jikinki yayi zafi sosai.... " cikin tashin hankali ya fice dani ahannunsa,ni kuwa babu damar kwatar kaina don gabaki daya jikina ya mutu.Ya umarce wani acikin students din daya rufe masa office,ya rufe ya mik'a masa makullan.
Yace dasu"Am sorry for the inconvenience..... Wen I get back I will attend to u all properly,buh for now I hav to take care of my wife... "
. yayi gaba da sauri yana fadin"My Zahmood sannu kinji insha Allah it shall be well with you.Mutane kuwa sae binsu ake da kallo cike da shaawar wannan soyayyar tasu.
Babu bata lokaci ya Isa ga motarsa ya fice daga makarantar aguje,ahankali na furta"Dear nah I think am carrying ur baby........ "
Cike da murna yace"Wayyyo Allah Zahmood are you serious? Da gaske kike na kusa zama uba? Yanxu nima an kusa kirana da baba kenan? "
Juyawa nayi ina kallon yadda yake zuba sambatu,hawaye na gangarowa Saman kuncinsa,abin gwanin ban tausayi,sae nima naji kawai hawaye ya ziraro min tare da jin sonsa na qaruwa acikin xuciyata.
Asibitin mah haka aka kara tabbatar masa da lallai ina dauke da juna biyu na tsawon sati uku.Har k'yauta sae da Mahmood ya baiwa likita na wannan albishir daya masa.
Wani sabon tattalina yake daga ni har babyn tamu,na musamman ya dauki hutun sati guda yana kula dani,don rashin kunya Mahmood har kiran yan'uwansa yayi akan an samu karuwa,babu wanda yakai Momi murnar samun wannan karuwar,alast ta kusa ganin jikokinta daga bangaren babban danta.Bayan kwana biyu kuwa sae ga mutan kano anzo dubiyata hadda su 'yan gidan Baba mu'azzam,har gidanmu saida Mahmood yakaisu hadda Hajiyarsa don sada zumunci,ita kuwa Ummana Sau daya tazo da kannena,Suhaima mah haka,ita kuwa Ash tayi zuwa har sau hudu kenan.Aranar suka koma Kano.bayan sati guda na ware,na danji dan dama-dama har na soma zuwa makaranta,amma ko kadan Mahmood baya bari ina aiki,duk abinda nakeso shike tashiwa ya dauko min ita,wai shi baya son na wahalar masa da babynsa,nace ai kuwa idan baya bari ina dan motsa jiki toh kuwa haihuwar tana iya zuwar min da dan gaddama,shine fa yadan soma barina ina dan taba wani aikin amma ba sosai ba.
****
**BAYAN SATI GUDA**
Akace rana bata k'arya sede uwar diya taji kunya,sannu-sannu bata hana zuwa sede adade ba'a kai ba.Ayau misalin qarfe biyu Mubarak ya diro Nigeria,ta Lagos suka sauka,suka sake shiga jirgin da ze saukesu akano.Bayan 1hr 40mins suka iso Kano ta dabo tumbin giya.Be Sanar da kowa batun dawowarsa ba balle yasa ran za'a taho daukarsa,babu b'ata lokaci yayi shatar adaidaita.Har kofar gidan aka kawoshi.
Momi itace wacce ya soma hangowa ah tsakar gidan tana baiwa kajin da take kiwo abincinsu.
"Assalamu alaykum warahmatullahi ta'ala wa barakatuhu..." Ya fadi hakan alokacin daya shigo cikin gidan sosai.
Momi ce ta amsa sallamar tare da dago kanta,afirgice ta jefar da kwanon abincin kajin dake hannunta,tace"Wah nake gani haka agabana kamar d'ana Mubarak? "
Murmushin k'arfin halin ya sakar mata kana yace"Abin mamaki yanxu Momina dan naki ne kika kasa shaidawa kai tsaye?ko don na k'ara baki da kuma 'yar ramar danayi ne? "
Da rawar murya tace"Eh fah hakane kam,ashe ba cewa kayi sae bayan watanni shidda zaka dawo ba? Ko kuwa bakada lafiya ne shine ka tashi ka kamo hanya ba tare da saninmu ba? "
"Momi hankalina zefi kwanciya idan ina kusa da Hauwa'u,idan ina ganinta zanfi jindadi,dama ko kadan banso wannan tafiyar ba sabida irin lalurarta ta laulayi meh tsanani,amma sabida matsa min da akayi shiyasa na tafi,koda naje can hankalina yaki kwanciya akanta shine oganmu yace kawai na dawo...... "
Cike da fargaba Momi tace"Ai kuwa cikin nata da sauki sosae don bayan kwana bibbiyu Dr.Basira ke xuwa dubata,kuma ta tabbatar mana da cewar baby da mamanta lfy qalau suke,kuma she has about 70% assurance na cewar wannan k'aron da kanta zata haihu basai an barkata ba,eyyah Mubarak ai daka tsaya abinka ka gama abinda yakaika....... "
Murmushi kawai yayi yace"Bari na shiga ciki Momi... " kafin ta k'ara magana ya shige ciki jaye da trolley dinsa.Dif! duk wani network meh aiki ajikin Momi ya tsaya cak! ya dena aiki.Tana nan tsaya se tunane-tunane take,ahakan Usee ya shigo gidan yana cire earpiece akunnensa,cike da tashin hankali yace"Momi daga nesa na hango wani ya sauka daga cikin adaidaita har ya shigo cikin gidan nan kamar Yah Mubarak..... "
"Shine ba wai kama ba...... "
Salati Usee ya saki tare da aza hannu duka biyun aka kamar wanda aka yiwa mutuwa.Wani irin zabura Momi tayi kamar wacce aka jonawa electric shock,tayi gaba da sauri sauri tana cewa"Usee taimaka ka kwashe min abincin kajin nan dana zubar,bari na kira Abbanku Mu'azzamu na fada masa cewar ya dawo....... "
"Toh" kawai ya iya cewa.Ta shige ciki,ada dakinta take da niyyar shiga don dauko wayarta amma se kuma ta Samu kanta da son yiwa su Mubarak lab'e.Da hanzari kuwa tayi dakin da aka sauki Hanan,ajikin kofar dakin ta lab'e tana sauraron maganarsu.
Kuka ta jiwo Hanan tana yi tare da rokansa"Haba mijin Hauwa'u yanxu har xuwa wannan lokacin baka cire Zahra aranka ba?aganina ya kamata ka shafeta daga cikin rayuwarka don I think Zahra ta maka nisa ba kadan ba...... "
Wata uban tsawa ya doka mata,yace"Shut up! Jiddah..... Yanxu har ke kin isa kice na cire Zahra araina? Kin kuwa san yadda nake sonta kuwa?toh ayau ina son ki san cewar duk wani numfashi da nake shak'a tare nake shak'arsa da soyayyarta,bana tsammanin ko Momi mah wannan k'aron zata iya dakatar dani daga aurenta...."
Ya sassauta murya yace"Haba jiddan Mubarak ke kanki kin san nayi kokari sosae ba kadan ba da har nakai tsawon lokacin nan ah India ba tare da jin halin da Zahrata ke ciki ba,kullum idan munyi waya dake sae na gaya miki cewar har yanxu banji daga gareta ba,shine yanxu kike cewa na haqura da ita? Never! Wallahi,tashi ki dauko min makullin motata na kama hanyar Zaria yanxun nan kuwa...... "
"Haba Mubarak ko hutawa bakayi ba balle kasa koda ruwa ne acikinka shine kake tunanin kama hanyar Zaria ayanxu?ka bari ka huta mana..... "
Wani uban tsawa ya doka mata wanda hakan ba karamin firgitata yayi ba musamman mah Momi wacce har saida ta dan buge da k'ofa don tsananin firgici😁
Xuciyarsa ce ta bashi cewar kamar ana musu lab'e don haka da sauri ya nufi kofar yana fadin"Uban waye ne ke mana lab'e anan?" Azatonsa Usee ne don beyi tsammanin cewar Momi bace.
Ita kuwa Momi jin abinda ya fada ya sanyata hanzarin rugawa da gudu xuwa falo xuciyarta kamar zata fad'o waje don tsananin fargaba,tana iya cewa tunda take aduniyarta bata tab'a shiga irin wannan tashin hankalin ba kamar na yau. (Hahahah! Major general of soldiers ya dawo).😀😂
Ita kuwa Hanan har fitsari saida ta saki don tsananin tsoro.Koda ya lek'a sae yaga wayam!babu kowa,xuwa yayi ya lek'a falon,sae yayi ido hudu da Momi wacce sae faman sauke ajiyar xuciya take,jikinsa ne yayi sanyi qalau kamar kankara don jikinsa ya bashi cewar itace ta musu lab'en.
"Mubarak zoka zauna muyi magana..... "
Gabansa ne yaji ya bada rass!,wato kenan Momi taji xantukansa da Hanan kenan?toh taji din mana shide walhi bata isa ta hana masa auran Zahra ba don ba itace ta haifeshi ba balle tace idan tayi masa baki yana iya kamashi.(Anya mubarak? Matar data raineka tsakaninta da Allah ne kake tunanin idan ta maka baki bazai kamaka ba? Ina ganin kawai ka zauna ka sake tunani).
"Ina son kadan bani aron juz 1hr acikin lokacinka so nake muyi magana.... " ta fadi da rawar murya don har ga Allah tsoron Mubarak din ma take.
Arayuwarsa ta duniya momi ita kadai ce macen da baze ya musa mata magana ba,amma akan Zahra wannan k'aron sede ta nemi wani Mubarak din amma bashi ba.
"Toh" kawai ya iya cewa don kwarai yana son yaji ta bakinta kafin ya amayar da tasa.Samin gu yayi ya zauna,se alokacin Usee ya shigo suka gaisa da yayan nasa,har yake tambayarsa ya hanya? Ba yabo ba fallasa ya amsa masa.
Hanan kuwa ta fito sae kuka take rik'e da key motarsa ahannunta,wuri guda ta tsaya cak! tama kasa karasa gareshi sae shesshek'a take,shi kuwa kallo daya yayi mata kana ya dauke kansa daga gareta.
Momi ce tayi mata ido,ai kuwa da hanzari ta shiga cikin taitayinta tare da samin hannun wata kujera ta zauna.Momi ta shige dakinta,da rawar hannu ta lalubo wayarta ta latso Baba Mu'azzam take gaya masa cewar ai Mubarak ya dawo,yace gashi nan tafe yanxun nan kuwa kada akuskura abari Mubarak din ya fita,ta de amsa masa da "insha Allahu" ne,don idan ya nemi fitar tasan ko ita ayanxu bata isa ta hana masa fita ba yadda idanuwansa suka rufe da tashin hankalin nan.Ta latso su Mahmood shima ta gaya masa,yace gasu nan tafe suma,duk 'ya'yanta mata saida ta kirasu suma Cike da tashin hankali sukace gasu nan tafe.Tace kada asake ataho da yara abarsu ahannun masu aikin gida,tama gode Jasmin na gidan Meema don haka komai zaizo musu da dan dama dama don bata qaunar yara su gigice da wannan tashin hankalin da suke shirin fuskata............... 📝
A/N
Tofa! bilhaqqi yau ake yinta,fire on the mountain kadan-kadan,ku agaza musu da taimakon gaggawa ta yan fire service 😁
Last episode coming soon ending of diz week insha Allah!!
Longest chapter so far!!
*HAFNAN CE💞*
Showing 42001 words to 43707 words out of 43707 words
****
watarana bayan mun gama morning lectures,sae kawai naji ina jin bak'on al'amari ajikina,zazzabi meh k'arfin gaske naji yana nemar rufeni,nayiwa Ash sallama na nufi office din Mahmood.Yana ganina ya taso arud'e yana fadin"My Zahmood yaya dai? Meya sameki?"
Amai shine ya biyo bayan tambayoyinsa,amai nake kamar zan amayo hanjin cikina,duk yabi ya rud'e.Students din da suke cikin office din sae ce min suke "Sorry ma,it shall be well with you.... "
Saida Mahmood ya wanke min fuska,wani student ya taimaka yayi clearing inda nayi amai.Ya daukeni kamar wata 'yar baby yana fadin"Dolene muje asibiti Zahmood jikinki yayi zafi sosai.... " cikin tashin hankali ya fice dani ahannunsa,ni kuwa babu damar kwatar kaina don gabaki daya jikina ya mutu.Ya umarce wani acikin students din daya rufe masa office,ya rufe ya mik'a masa makullan.
Yace dasu"Am sorry for the inconvenience..... Wen I get back I will attend to u all properly,buh for now I hav to take care of my wife... "
. yayi gaba da sauri yana fadin"My Zahmood sannu kinji insha Allah it shall be well with you.Mutane kuwa sae binsu ake da kallo cike da shaawar wannan soyayyar tasu.
Babu bata lokaci ya Isa ga motarsa ya fice daga makarantar aguje,ahankali na furta"Dear nah I think am carrying ur baby........ "
Cike da murna yace"Wayyyo Allah Zahmood are you serious? Da gaske kike na kusa zama uba? Yanxu nima an kusa kirana da baba kenan? "
Juyawa nayi ina kallon yadda yake zuba sambatu,hawaye na gangarowa Saman kuncinsa,abin gwanin ban tausayi,sae nima naji kawai hawaye ya ziraro min tare da jin sonsa na qaruwa acikin xuciyata.
Asibitin mah haka aka kara tabbatar masa da lallai ina dauke da juna biyu na tsawon sati uku.Har k'yauta sae da Mahmood ya baiwa likita na wannan albishir daya masa.
Wani sabon tattalina yake daga ni har babyn tamu,na musamman ya dauki hutun sati guda yana kula dani,don rashin kunya Mahmood har kiran yan'uwansa yayi akan an samu karuwa,babu wanda yakai Momi murnar samun wannan karuwar,alast ta kusa ganin jikokinta daga bangaren babban danta.Bayan kwana biyu kuwa sae ga mutan kano anzo dubiyata hadda su 'yan gidan Baba mu'azzam,har gidanmu saida Mahmood yakaisu hadda Hajiyarsa don sada zumunci,ita kuwa Ummana Sau daya tazo da kannena,Suhaima mah haka,ita kuwa Ash tayi zuwa har sau hudu kenan.Aranar suka koma Kano.bayan sati guda na ware,na danji dan dama-dama har na soma zuwa makaranta,amma ko kadan Mahmood baya bari ina aiki,duk abinda nakeso shike tashiwa ya dauko min ita,wai shi baya son na wahalar masa da babynsa,nace ai kuwa idan baya bari ina dan motsa jiki toh kuwa haihuwar tana iya zuwar min da dan gaddama,shine fa yadan soma barina ina dan taba wani aikin amma ba sosai ba.
****
**BAYAN SATI GUDA**
Akace rana bata k'arya sede uwar diya taji kunya,sannu-sannu bata hana zuwa sede adade ba'a kai ba.Ayau misalin qarfe biyu Mubarak ya diro Nigeria,ta Lagos suka sauka,suka sake shiga jirgin da ze saukesu akano.Bayan 1hr 40mins suka iso Kano ta dabo tumbin giya.Be Sanar da kowa batun dawowarsa ba balle yasa ran za'a taho daukarsa,babu b'ata lokaci yayi shatar adaidaita.Har kofar gidan aka kawoshi.
Momi itace wacce ya soma hangowa ah tsakar gidan tana baiwa kajin da take kiwo abincinsu.
"Assalamu alaykum warahmatullahi ta'ala wa barakatuhu..." Ya fadi hakan alokacin daya shigo cikin gidan sosai.
Momi ce ta amsa sallamar tare da dago kanta,afirgice ta jefar da kwanon abincin kajin dake hannunta,tace"Wah nake gani haka agabana kamar d'ana Mubarak? "
Murmushin k'arfin halin ya sakar mata kana yace"Abin mamaki yanxu Momina dan naki ne kika kasa shaidawa kai tsaye?ko don na k'ara baki da kuma 'yar ramar danayi ne? "
Da rawar murya tace"Eh fah hakane kam,ashe ba cewa kayi sae bayan watanni shidda zaka dawo ba? Ko kuwa bakada lafiya ne shine ka tashi ka kamo hanya ba tare da saninmu ba? "
"Momi hankalina zefi kwanciya idan ina kusa da Hauwa'u,idan ina ganinta zanfi jindadi,dama ko kadan banso wannan tafiyar ba sabida irin lalurarta ta laulayi meh tsanani,amma sabida matsa min da akayi shiyasa na tafi,koda naje can hankalina yaki kwanciya akanta shine oganmu yace kawai na dawo...... "
Cike da fargaba Momi tace"Ai kuwa cikin nata da sauki sosae don bayan kwana bibbiyu Dr.Basira ke xuwa dubata,kuma ta tabbatar mana da cewar baby da mamanta lfy qalau suke,kuma she has about 70% assurance na cewar wannan k'aron da kanta zata haihu basai an barkata ba,eyyah Mubarak ai daka tsaya abinka ka gama abinda yakaika....... "
Murmushi kawai yayi yace"Bari na shiga ciki Momi... " kafin ta k'ara magana ya shige ciki jaye da trolley dinsa.Dif! duk wani network meh aiki ajikin Momi ya tsaya cak! ya dena aiki.Tana nan tsaya se tunane-tunane take,ahakan Usee ya shigo gidan yana cire earpiece akunnensa,cike da tashin hankali yace"Momi daga nesa na hango wani ya sauka daga cikin adaidaita har ya shigo cikin gidan nan kamar Yah Mubarak..... "
"Shine ba wai kama ba...... "
Salati Usee ya saki tare da aza hannu duka biyun aka kamar wanda aka yiwa mutuwa.Wani irin zabura Momi tayi kamar wacce aka jonawa electric shock,tayi gaba da sauri sauri tana cewa"Usee taimaka ka kwashe min abincin kajin nan dana zubar,bari na kira Abbanku Mu'azzamu na fada masa cewar ya dawo....... "
"Toh" kawai ya iya cewa.Ta shige ciki,ada dakinta take da niyyar shiga don dauko wayarta amma se kuma ta Samu kanta da son yiwa su Mubarak lab'e.Da hanzari kuwa tayi dakin da aka sauki Hanan,ajikin kofar dakin ta lab'e tana sauraron maganarsu.
Kuka ta jiwo Hanan tana yi tare da rokansa"Haba mijin Hauwa'u yanxu har xuwa wannan lokacin baka cire Zahra aranka ba?aganina ya kamata ka shafeta daga cikin rayuwarka don I think Zahra ta maka nisa ba kadan ba...... "
Wata uban tsawa ya doka mata,yace"Shut up! Jiddah..... Yanxu har ke kin isa kice na cire Zahra araina? Kin kuwa san yadda nake sonta kuwa?toh ayau ina son ki san cewar duk wani numfashi da nake shak'a tare nake shak'arsa da soyayyarta,bana tsammanin ko Momi mah wannan k'aron zata iya dakatar dani daga aurenta...."
Ya sassauta murya yace"Haba jiddan Mubarak ke kanki kin san nayi kokari sosae ba kadan ba da har nakai tsawon lokacin nan ah India ba tare da jin halin da Zahrata ke ciki ba,kullum idan munyi waya dake sae na gaya miki cewar har yanxu banji daga gareta ba,shine yanxu kike cewa na haqura da ita? Never! Wallahi,tashi ki dauko min makullin motata na kama hanyar Zaria yanxun nan kuwa...... "
"Haba Mubarak ko hutawa bakayi ba balle kasa koda ruwa ne acikinka shine kake tunanin kama hanyar Zaria ayanxu?ka bari ka huta mana..... "
Wani uban tsawa ya doka mata wanda hakan ba karamin firgitata yayi ba musamman mah Momi wacce har saida ta dan buge da k'ofa don tsananin firgici😁
Xuciyarsa ce ta bashi cewar kamar ana musu lab'e don haka da sauri ya nufi kofar yana fadin"Uban waye ne ke mana lab'e anan?" Azatonsa Usee ne don beyi tsammanin cewar Momi bace.
Ita kuwa Momi jin abinda ya fada ya sanyata hanzarin rugawa da gudu xuwa falo xuciyarta kamar zata fad'o waje don tsananin fargaba,tana iya cewa tunda take aduniyarta bata tab'a shiga irin wannan tashin hankalin ba kamar na yau. (Hahahah! Major general of soldiers ya dawo).😀😂
Ita kuwa Hanan har fitsari saida ta saki don tsananin tsoro.Koda ya lek'a sae yaga wayam!babu kowa,xuwa yayi ya lek'a falon,sae yayi ido hudu da Momi wacce sae faman sauke ajiyar xuciya take,jikinsa ne yayi sanyi qalau kamar kankara don jikinsa ya bashi cewar itace ta musu lab'en.
"Mubarak zoka zauna muyi magana..... "
Gabansa ne yaji ya bada rass!,wato kenan Momi taji xantukansa da Hanan kenan?toh taji din mana shide walhi bata isa ta hana masa auran Zahra ba don ba itace ta haifeshi ba balle tace idan tayi masa baki yana iya kamashi.(Anya mubarak? Matar data raineka tsakaninta da Allah ne kake tunanin idan ta maka baki bazai kamaka ba? Ina ganin kawai ka zauna ka sake tunani).
"Ina son kadan bani aron juz 1hr acikin lokacinka so nake muyi magana.... " ta fadi da rawar murya don har ga Allah tsoron Mubarak din ma take.
Arayuwarsa ta duniya momi ita kadai ce macen da baze ya musa mata magana ba,amma akan Zahra wannan k'aron sede ta nemi wani Mubarak din amma bashi ba.
"Toh" kawai ya iya cewa don kwarai yana son yaji ta bakinta kafin ya amayar da tasa.Samin gu yayi ya zauna,se alokacin Usee ya shigo suka gaisa da yayan nasa,har yake tambayarsa ya hanya? Ba yabo ba fallasa ya amsa masa.
Hanan kuwa ta fito sae kuka take rik'e da key motarsa ahannunta,wuri guda ta tsaya cak! tama kasa karasa gareshi sae shesshek'a take,shi kuwa kallo daya yayi mata kana ya dauke kansa daga gareta.
Momi ce tayi mata ido,ai kuwa da hanzari ta shiga cikin taitayinta tare da samin hannun wata kujera ta zauna.Momi ta shige dakinta,da rawar hannu ta lalubo wayarta ta latso Baba Mu'azzam take gaya masa cewar ai Mubarak ya dawo,yace gashi nan tafe yanxun nan kuwa kada akuskura abari Mubarak din ya fita,ta de amsa masa da "insha Allahu" ne,don idan ya nemi fitar tasan ko ita ayanxu bata isa ta hana masa fita ba yadda idanuwansa suka rufe da tashin hankalin nan.Ta latso su Mahmood shima ta gaya masa,yace gasu nan tafe suma,duk 'ya'yanta mata saida ta kirasu suma Cike da tashin hankali sukace gasu nan tafe.Tace kada asake ataho da yara abarsu ahannun masu aikin gida,tama gode Jasmin na gidan Meema don haka komai zaizo musu da dan dama dama don bata qaunar yara su gigice da wannan tashin hankalin da suke shirin fuskata............... 📝
A/N
Tofa! bilhaqqi yau ake yinta,fire on the mountain kadan-kadan,ku agaza musu da taimakon gaggawa ta yan fire service 😁
Last episode coming soon ending of diz week insha Allah!!
Longest chapter so far!!
*HAFNAN CE💞*
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15