ya mujaheed ka fita inasan shiryawa kaga idan aunty husna ta gani fada zatamin ta qare maganar cike da sanyin jiki.

Siririn tsaki yaja Mara sauti ya tashi tsaye Yana cewa' kedai wallahi anyi bigidajiya daga ke har husnan ita dai nijlah Bata qara cemasa komai ba harya sa qafa ya fita a dakin Yana bin santala santalan cinyoyinta da kallo tare da mita qasa qasa .

Yana fita nijlah ta sauke sassanyar ajiyar zuciya ta cigaba da hirinta' cikin sauri ta gama kwalliya duk da ba iyawa tayi ba ta yafa mayafi ta fito' dakin aunty husna ta shiga nan ta sameta zaune bakin gado tana ba Ayman abinci' sunkuyawa nijlah tayi tace aunty Ina kwana?
Lfy qlau amarya husna ta amsa tana murmushi' sosa Kai nijlah tayi ta nemi guri zata zauna' dasauri husna tace' kefa nagayamiki daddyn Ayman Yana kiranki tashi kije idan kin dawo saiki zauna kinsan basan jira yake ba?

To nijlah tace' Jikinta babu kwari ta tashi tana tafiya kamar wacce kwai ya fashewa ta fita a dakin' falo ta dawo ta Sami daddyn Ayman zaune Yana latsa computer' akasa ta zauna ta gaishesa' nan ya amsa Mata cikin sakin fuska kafin ya gyara zama Yana kallanta.

Ya jima Yana nazarinta kafin yace' nijlah Kinga abinda Allah yayi ko' Allah ya kaddara Zaki zauna damu sedai zaman naki ya zame Mana alkairi tinda gashi yau za'a daura aurenki da Dan uwana Wanda sanin kanki ne ya nuna Miki soyayya irin wacce ta dace' dakyar ta iya daga masa Kai alamar eh' nan yacigaba da magana' nijlah idan har kika riqemin amanar Dan uwana to babu shakka Zan sakamiki da abinda Baki taba tinani ba' kuma da an daura auren Zan nemo danginki kafin ki tare a gidanshi.

Ina fatan zakiji dadin haka' da kyar ta bude bakinta tace eh' to nagode Allah yayi Miki albarka tashi kije Naga lokaci yayi zamu je sallah daga nan za'a aura auren.

Kanta a sunkuye ta fita' sedai tana fita taji wasu hawaye masu zafin gaske na zuba daga cikin idanunta Wanda ta rasa dalilin zubarsu' Bata iya tafiya a hankali ba saima gudu data sa ta fada dakinta' kuka take Mai cin rai Wanda takejinsa kama zuciyarsa zata tsage sabida tsabar tashin hankalin datake ciki' sosai ta zurfafa cikin kuka gami da tunanin halin datasa kanta a ciki taji an turo kofar dakin' Bata iya dagowa ba balle taga me shigowan haka Bata Dena kukan da take ba .

Tsaye husna tayi jikin kofa tana mamakin kukan da nijlah take gashi har daddyn Ayman da mujaheed da sauran 'yan uwa wadanda suka zo daurin auren harsun wuce masallaci' bare wani ya tayata rarrashi ko tambayanta abinda ya sata kuka.

Ganin kukan nata na qara yawa yasa aunty husna qarasawa bakin gadon ta Kira sunanta a hankali' nijlah? Nijlah Bata amsaba saima qara gunjin kuka data sa tana Kiran sunan kaka Wanda ta Dade Bata kira ba..




Muyi hakuri ku qara hakuri'da rashin jina' kunsan rashin mahaifi ba abune Mai sauqi ba' shiyasa haryanzu banajina daidai na kuma kasa cigaba da typing Amma yanzu insha Allahu nadawo kullum muna tare zaku riqa jina indai ba akasi akasamu irin na rayuwa ba'nagode sosai da soyayyarku gareni' Naga Kira masu turo text duka nagani Allah ya bar kauna.


Fatan zaku cigaba dasa mahaifina cikin addu'oinku' Allah yajiqansa da rahama.


*Masu San siyan labarin Yar sadaka ku jira sai na gama Free pages nagode.*


Momn sultan ce💘💘 *'YAR SADAKA 2.*💘💘



*BOOK 2.*



*STORY & WRITING...*
*BY*
*MOMN SULTAN*


*NA KUDI*

*Wannan labarin na kudine' ga mai so zata Biya 200 naira kachal ta karanta' Zaki Tura katin MTN ta wannan number 09038049272,,Ko ta account number, 0089110527, suwaiba Hussaini zakirai, access bank.*

*'yan Niger su tuntubi wannan number,, +22789520047.*


*Free page*


6️⃣



Meya faruwa nijlah? Kike irin wannan kukan ko so kike akaiki gidanki da ciwan kai' nijlah kimin bayani meya daki kuka?
Kamar bazata iya magana sabida kukan yaci karfinta husna ta qara tambayanta da dabara da komai nijlah ta fara magana cikin muryan wacce kuka ya gama ratsa tasa hannu ta riqe aunty husna tana cewa' aunty taba zuciyana kiji' daf take da fashewa tabar gangan jikin' Dan Allah aunty kimin Rai kada a daura wannan auren wallahi zamu halaka gabadaya.

Cike da firgici gami da gigita husna take magana'ke nijlah nutsu' ki nutsu nace ki gayamin abinda kikesan fada'tin tini nasan akwai abinda kike boyemin Amma kin kasa fito dashi'yanzune kike da damar da Zaki gayamin kafin me afkuwa ta afku adaura auren' ki gayamin mace husna ta fada da qarfin tana jinjiga nijlah?
Ganin yadda aunty husna ta rikice yasa nijlah karaya ta langwabar da Kai tana cewa' aunty ni Dan Allah kisa a fasa daura auren har zuwa lokacin da Zan buqata da kaina; Zaki buqaci me Kinga nijlah ki fita a idona ' Yar metsitsiyar yarinya dake kin iya zurfin cikin tsiya' wallahi badan kina da daurin gindi a gidannan ba saina kusa karyaki' abin haushinki yayi yawa wallahi ta qare maganar tana dungurinta.
Naji abinda kikace Amma Dan Allah kisa a fasa wallahi bazan iyaba' juyawa husna tayi da niyyar barin dakin nijlah tayi saurin riqeta tana kuka tana makiya akan tasa a janye daurin aure.
Haushine yasa husna ture ta ta fita a dakin' da sauri ta shiga dakinta' ta dauka waya' number daddyn Ayman tayi dealing zuciyanta na Kuna tare da tinanin irin kalaman da zatayi amfani dasu gurin ganar dashi abinda nijlah take nufi duk da itama ba sani tayi ba' be dauka ba sabida a lokacin suna sallah' bayan sun idar suka fara shirye shiryen daurin auren' daddyn Ayman shiya zama waliyin amarya nijlah yayinda qanin babansu mujaheed ya zama walin ango.
Ganin irin Kiran da husna tamasa yaqi amsata yasata tayi saurin rubutamasa sako ta tura.
Za'a daura auren daddyn Ayman yaji shigowan text cikin wayansa' dasauri ya bude ganin sunan husna ga tarin miss calls daya gani' Yana dubawa gumi yafara karyo masa Yana cewa' malam ku dakata' kar a daura auren.
Dasauri mujaheed ya tashi tsaye Yana cewa' sabida me yaya meyasa zaka Hana a daura' kaga malam a daura auren daga baya Koma menene sai ayi' cikin tsawa irin Wanda yayan nasa be tabayimasa yake magana' ganin haka yasa mujaheed komawa gefe Yana hawaye tare da sallamawa zuciyar da samun farin ciki' daddy Ayman be jira maganan da ake ba ya fita da sauri' ko mota be shigaba kasan cewar gidansa da masallaci ba nisa.

Ko sallama be iya yiba ya shiga dakin nijlah' tsaye ya samesu gaba dayansu sunci cirko cirko' husna na ganinsa tayi kansa tana cewa' badai a daura auren ba ko?
Cikin sanyin jiki daddyn Ayman yace' ba'a daura ba' alhmdllh husna tace' a fili yayinda nijlah ta sauke ajiyar zuciya.
Jikinsa a sanyaye yace'husna kince akwai matsala kar a daura aure' gashi kuma nazo na sameku lfy' ki gayamin meke faruwa?
Cike da tsoro husna tace' Nima bansani ba' sedai ka tambaya Nijlah tinda kuka tafi take kuka Kai kace uwarta da ubanta ne suka mutu'yayi tambaya harna gaji'a qarshe ma cewa tayi a fasa auren Bata shirya ba.
Dasauri daddyn Ayman ya maida kallansa ga nijlah Yana cewa' what sai kuma ya juya yana tafiya yana cewa ku sameni a bangarena daga ke har ita' Naga alama kunasan Raina Mana hankali' sai dana yara jama'a Zaki kawomin zancen banza da wofi' to wallahi baku isaba sedai yau dinnan kibarmin gida tinda ba gidan ubanta bane' sosai daddy Ayman yake taka steps Yana masifa' tsaye yake yakasa zama Banda zagaye dakin babu abinda yake' gaba daya hankalinsa Yana masallaci sabida sanin halin daya bar mujaheed.

Kallo daya husna tayi ma nijlah dake zaune ta rafka uban tagumi tana tinanin abinda zata tambayeta tace'ki samemu a daki yanzu' a firgice nijlah ta dago Kai tana kallanta kafin tayi magana husna ta fita a dakin ta hau sama, gaban nijlah na faduwa ta tashi tana tafiya a hankali tabi bayansu.

Tsaye ta gansu yayinda daddyn Ayman keta safa da marwa a dakin, bakin nijlah na rawa tace' daddyn Ayman gani' cikin fushi yake kallanta lokaci guda ya daure fuska yace''nijlah Ina son sanin abinda yasa kikace kinfasa wannan auren' bayan nidake saida muka zauna mukayi magana Amma yanzu Zaki tsiro da abinda ze tarwatsamin farin cikin Dan uwana?
Shiru Nijlah tayi tana Jada baya sabida mugun tsoran daya shigeta' jikinta' na karkarwa bakinta na rawa sedai duk da wannan tsoran takasa bude Baki ta bashi amsa.
Tsawa ya dakamata Wanda tasata tashi da gudu ta rungume aunty husna tana kuka' a hankali husna ta janye jikinta tana cewa haba nijlah kiyi magana' ni a wannan lokacin' bazan iya kareki ba gaskiyar abinda yasaki fasa auren kawai Zaki fada sai hankali ya kwanta.
Kanta daddyn Ayman yayi Yana cewa' waiba dake nayi magana ba?
Nijlah Bata iya magana ba saima fitsari data saki tana karkarwa' tare da sakin saban kuka' wayyo Allah nah'wayyo kaka zasu kasheni niku kaini gurin kaka' malam kana ina? Ihu sosai nijlah take tana Neman taimako hakan datayi ba qaramin dagawa daddy Ayman da husna yayi ba, cikin sauri daddyn Ayman ya bude Mata kofa Yana cewa' zoki fita kije can ki nemi inda asararrun iyayen naki suke saiki musu shagwaba acan' kallansa husna tayi idonta taf da hawaye yayi saurin katseta' idan kikace tak kema saikin bita yau ni Naga bala'i' yarinya saikace aljana ya qare maganar Yana huci kamar wani Zaki.

Da gudu nijlah ta fita a dakin tana waiwaye steps take takawa idonta a rufe Bata ko kallan hanya' tana sauka ta fito' a falon tana kuka jikinta' sai digan fitsari' cin Karo sukayi da mujaheed yasa hannu yayi saurin tare ta Yana Tambayanta? Nijlah meya faru waya tabamin ke' ita dai nijlah Bata iya magana ba sai nuna Masa sama take tana karkarwa' mutane ne wadanda suka rako mujaheed gida sabida gajiya da sukayi a masallaci suna jira daddynr Ayman be dawo ba suka bisu da kallo' ganin yadda duk ta birgice ta rikice tana Neman zautar dashi yayi saurin daukanta ya daga ta sama Yana tafiya da ita' Bata hanashi ba sabida Kota fita batasan inda zatajeba' sama yake qoqari hawa da ita sukaji muryan daddyn Ayman Yana cewa' karka kuskura ka hawomin da ita daki Dan Banga amfanin zamanta damu ba' ka saketa ta tafi can ta qarata tinda bazata aureka ba' cigaba da tafiya mujaheed yayi da ita a hannunsa yayan nasa ya daka Masa tsawa irin wacce be tabaji yayi Masa ba' gaba daya jikinsa ya dauka rawa har saida nijlah ta kusa fadowa daga hannunsa' Yana kuka Yana magana' shikenan Dan uwana tinda haka kace nizan bita zanbi nijlah muje can muyi rayuwa da ita' Yaya bazan iya rayuwa ba tare da nijlah' ba' kayi hakuri Nina zabi zama da ita hankali na zefi kwanciya Yana gama fada ya juya' da sauri husna ta Sha gabansa tana cewa babu inda zakace daddyn Ayman kayi magana kana kallo Yana Shirin tafiya idan ya tafi Ina zeje?

Cikin fada dadin Ayman yace' ki matsa husna' matsa nace yaje duk inda zashi' badai ya zabi mace Akaina ba'' nijlah dake hannun mujaheed haryanzu tayi wani irin zillo ta fado tana kallansu daya bayan daya' tace' kuyi hakuri niba nayi haka Dan na Bata muku Rai ba nayi hakane sabida samun zaman lafiya' sedai hakan be Samu ba' nizan barku a hakama nice da godiya bisa irin kulawar da kuka bani' koba komai nasamu ilimin rayuwa daku' tana gama fada ta juya' da gudu mujaheed yabi bayanta Yana cewa' sedai muyi rayuwa a jeje dadai narasaki' Mara musu baya daddyn Ayman yayi da gudu Yana Kiran mujaheed.
Aunty husna ta sauke ajiyar zuciya ta daga hannunta sama tace' ya Allah ya kawomana dauki .



______________


A firgice Yasmeen take kallansa bakinta na rawa ta maimaita sunan nijlah' nijlah fa kace haba mijina yaushe zaka manta da wannan aljanar yarinyan' nice fa ni kake Kira da nijlah saita saki kuma Mai cin rai ta durqusa a gurin tana kuka' tinda tafara magana mashkur ya safke kansa kasa danshi kunya yakeji ya dago Ido su hada da Yasmeen ni kansa yasan yamata na daidai ba kuma ba qaramin cin mutumci bane ka taba matarka ka kuma kirata da sunan wata matar' hannu yasa ya dafe kansa Yana tinanin ta inda ze fara rarrashinta' a hankali ya tashi ya matsa inda take tare dasa hannu ya janyota jikinshi tana kwacewa tana komai ahaka ya zaunar da ita Yana shafa bayanta' muryarsa a sarqe ya Kira sunanta Yasmeen" Yasmeen Bata amsaba saima qoqarin kwatar kanta take tana cewa' Nika sakeni banaso' kaje can ka taba nijlah tinda ita kakeso bani b' saurin hade bakinsu mashkur yayi Yana binta da salo Mai rikitarwa' tin tana qin amsa har saida Yasmeen ta sakar Masa jiki ya cigaba da shafa boobs dinta tare da aikamata da sako Mai wuyar fassara narkewa tayi a jikinsa Yana fidda numfashi dan baqaramin dadin abin take jiba ganin Yana Neman zuge Mata zip din Riga yasa tayi saurin riqe hannunsa tana cewa' pls baby bafa mu kadai bane' mama tana ciki kuma ga 'yan biki ni wallahi harka fara bani tsoro'
Kallanta yayi da jajayen idanunsa Wanda ya rine da fitinansa ya kuma kafeta dasu tare da matseta a jikinsa Yana cewa' gayamin tsoran me kikeji?
A shagwabe Yasmeen tace ni Allah tsoro kake bani' niba bani da San wahala ' murmushinsa yayi me qayatarwa yace' zakiga wahala indai nine gwarama ki shirya amsar gwarzon namiji' Bata qara magana ba sai turo masa Dan qaramin bakinta tayi' suna zaune mubeena tayi sallama' ta shigo' kallo daya tayi musu tayi murmushi tace' ango ka ara Mana amarya lokacin kwalliya yayi baka bamu amarya ba' Sosa Kai mashkur yayi yace' ayi hakuri gatanan zuwa inaso muqarasa magana' ah ah fa mashkur minti nawa ya rage agogon hannunta ta duba tana cewa' yanzu karfe 5 na yamma nan da karfe 10 zamu kaima amaryarka har gida' Dan haka ka bamu ita muje gurin party da wuri nasan kaima su Nasir suna can ana nemanka kazo nan ka maqale' duka Yasmeen takai Mata tana cewa' ah ah mantawa kikace ba maqalewa yayi ba' kashe Mata Ido mubeena tayi ta riqe hannunta tana cewa' kabani aronta ko' babu yadda mashkur ya iya haka ya riqa daga Kai kama dolo Shima ya tashi suka fito a tare .






Gargadi'Idan kinsan Zaki fitarmin da novel karki siya' ban amince ki siya ki tura a wayan kawa ko group ba' Abu daya na yarda dashi' Zaki iya bada wayarki a karanta a ciki Amma Banda turawa.....


Idan kin biya kituromin shaidan biya ta wannan number 09038049272 WhatsApp.



Momn sultan ce💘💘 *'YAR SADAKA 2.*💘💘



*BOOK 2.*



*STORY & WRITING...*
*BY*
*MOMN SULTAN*


*NA KUDI*

*Wannan labarin na kudine' ga mai so zata Biya 200 naira kachal ta karanta' Zaki Tura katin MTN ta wannan number 09038049272,,Ko ta account number, 0089110527, suwaiba Hussaini zakirai, access bank.*

*'yan Niger su tuntubi wannan number,, +22789520047.*

*Garabasa ga duk Wanda ta siya labarin 'yar sadaka' Zaki karanta wayafi sonta na mmn fareesah 200 naira' Wanda be siya 'yar sadaka ba zai karanta 300 ko da kudinki sai da rabanki*


*last Free page*



7️⃣



Tinda suka fito Yasmeen ta Bata fuska tana hararan mubeena' mubeena Na ganinta sedai Bata tanka ba Har suka Shiga falon da kawayensu ke cike masu kawalliya da dauka selfie nayi' da ido suke bin Yasmeen harta samu guri kusa da zee ta zauna tana yatsina fuska' dariya zee tayi tace' kai kawata haka kuke da jaraba keda angon naki' Baku iya hakuri dare yayi' murguda baki Yasmeen tayi ta cigaba da latsa wayarta tana cewa' to uwar 'yansa ido me kukayi' shewa suka sa zee tace ke bakiji irin kamshin dake Tashi a jikinki ba' kowa yasan lalubar juna akai' kafin ta qare Magana mubeena tace' hhhh zee naso ace ke kikaje Kiran Yasmeen da kinga abin mamaki hararan da Yasmeen ke binta dashi yasata saurin rufe baki tana dariya.

Kunya da takaici sune suka Hana Yasmeen Magana Saima cigaba da kallan waya tayi' nan suka cigaba da tsokalanta wasu nacewa zasu zo gashin jiki gobe da takaici ya isa Yasmeen saita Tashi da niyyan fita a dakin' Khadija ce ta riqo hannunta tana cewa' dawo kawata ayi kwalliya kinga lokaci Na tafiya' maqale kafada Yasmeen tayi Khady tace barni dasu Zan rama Miki idan lokacinsu yayi' dakyar suka lallabata ta zauna aka fara tsara Mata kawalliy.
Ba qaramin kyau tayi ba haka kawayen da Yan uwa suka fara daukanta photo kowa nasa Mata albarka.

Mama ce zaune me kwalliya tanayima' Babar yayarsu aunty maimuna ta shigo' da mamaki take kallan mama kafin tace' yanzu Maman Yasmeen menene amfani wannan partyn tinda an daura aure Akai yarinya gidan mijinta zaku tsaya wani fi'ila!
A hankali mama ta dago tana kallan Yayar tata kafin tace' Dan Allah Yaya kiyi hakuri ayi wannan party kinsan halin daddyn Yasmeen yanzu ze saukewa kowa Akan wannan yarinyar gwara kibari a rabu lfy dashi.
Toni zanyi masa Magana Yana ina' baza'ayi wani party yanzu ba' dasauri mama ta Tashi tana Bata hakuri' kiyi hakuri Yaya bafa daddyn Yasmeen yasa ayi party ba' daga gidan ango mamansa ta shirya kinga be dace mu hanasu ba!
Sabida me zakice be dace ba Naga Dai bamu Basu 'yar ba haryanzu a hannunmu take' dariya mama tayi kafin tace' kai Yaya kin manta an daura aure Sannan shine auta a gidansu' mummy nason mashkur shiyasa ta Hada wannan partyn sabida nasan aikin tane bana kowa' to ai shikenan nayi tinanin kece da wannan aikin Yaya ta fada tana Neman gurin zama.


Acan gidan mummy ma Haka abin yake kowa ka kalla da kawalliya a fuskanshi aunty lateefah ce zaune kusa da mummy tana gyara Mata daure' mummy tace' ke lateefah Wai Sai dare ya tsala zaku.kaimu gurin paryn' haba ayi Abu ido nagani mana?
Dariya lateefah tayi tace mummy yanzu za'a tafi nafiso Sai ango da amarya sunje gurin saimu ma mu tafi' ah ah kinga Ni Tashi mu tafi cewar mummy tana daukan mayafi' mummy Na
Showing 9001 words to 12000 words out of 65321 words