Tashi sauran surukanta da yaranta da suka zo biki kowa ya tashi' a tare suka fito kowa ya Shiga motansa' mummy ta Shiga wata motan daban' driver ne ke tukin.
Karfe 8 daidai kowa ya halacci gurin' ango da amarya na zaune cikin Mota kawaye' da abokan ango na jere Suna jiran fitowansu.
Yasmeen ce ta Kalli mashkur daya kafeta da ido hannunsu hade Sai faman murzawa da shafasu yake tace' Dan Allah baby ka rufamun asiri agama komai lfy' murmushi mashkur yayi yace haba baby anfa Gama Amma Sai Jamin Rai ake anqi akaiki Nima Na huta' ka qara hakuri mana' ana gamawa za'a kaini gidan mummy daga can zaka daukeni' Kaji tsiyar ba mashkur ya fada '' wayace gidan mummy za'a kaiki? Ko haka musulumci yayi ayi?' dariya Yasmeen tayi tace' Nima haka naji yayar mama Na fada Wai sunyi waya da aunty lateefah take gayamata'' tsaki mashkur yayi yace naji, shiru tayi tana roqarin bude qofa ta fita yasa hannu ya qara janyota jikinsa Yana cewa ance ki tafi ne kona sallameki?' Bata qara motsi ba yasa hannu a cikin aljihun wandansa ya fiddo kudi bandir yan dubu ɗaya sabbi dal ya miqa mata' amsa wannan kisa a jakarki dasu kawayenki zasuyi mana liqi kema kiyi' lumshe ido Yasmeen tayi ta bude tace mufa muna da kudi a gurinmu' daddy ya bamu masu yawa' ido ya zuba Mata Yana cewa ki amsa Kawai banasan musu Ko angayamiki kudin liki Suna yawa'ah ah tace tasa hannu biyu ta amsa tana godiya.
Bude motan yayi ya fita itama fita tayi' atare kawayen amarya Dana ango suka shigar dasu ciki' Suna Shiga aka fara kida nan aka Kira mama ta bude guri da addua kafin afara shagali' wakar amarya da ango Wanda gwanja ya rera' kawayen amaryane suka fara bude Fili da rawa' Sannan aka Kira ango da amaryarsa agaban fili' Suna fitowa mummy ta Shiga nan ta fara yimusu leqi tana juyawa su aunty lateefah da matar abbakar suka fiso Suna taka rawa sosai mashkur ya bude bakin aljihu Yana musu barin kudi' ba'abar mama ba itama ta fito ta ɓalle jaka tana zuba kudi..
Taro yayi taro kowa ya chi ya sha an girgije abokan ango dana amarya"Yan uwa da abokai ba Wanda be taka rawa yayi liqi ba.an kwashe awanni da yawa ana shagali kafin a tashi' motaci suka kwasa jama'a Sai gidan mummy sabida mummy ta rigime tace a gidanta za'a dauka amarya' haka kuwa akayi mama ta samu ta Zille da kyar ta tafi gida ita da sauran kawayen ta yayinda danginta Dana daddy zasu wuce kai amarya.

Tinda aka fara tafiya Yasmeen take Neman mama sedai haryanzu Bata Ganta ba' Tashi takesanyi mashkur ya riqe hannunta' a hankali yace ina Kuma Zaki?
Idon Yasmeen fal da hawaye tace' ni mamanah nake nema banganta a gurin nan ba tinda tayimana liqi ta fita' ya bude baki kenan zeyi Magana aunty lateefah ta zo ta riqe hannun Yasmeen tana cewa' Malam ka fita mana kai Ko kunya bakaji ka riqeta a gaban mutane ga abokanka can Na jira'murmushi mashkur yayi ya sake hannun Yasmeen Yana dage Mata gira.
Kallan lateefah tayi tana hawaye tace' aunty ina mama nifa banganta ba?
Kinganta can a Mota ke ake jira' da haka tayi Mata wayo ta Sata a mota' dama ita kadai ake jira tana Shiga aka tafi da ita gidan mummy.

Tinda Yasmeen ta kyalla ido ta Ganta a gidan mummy ta fara kuka tana Kiran daddynta' dakyar 'aka rarrasheta kannin daddy suka kaita gurin mummy nan suka Bata amananta tare da yimata nasiha tabi mijinta.
Karfe Goma motaci suka kwashe 'yan kai amarya suka maidasu gidan mama.

Rungume Yasmeen mama tayi tana Bata hakuri' kiyi hakuri kinji kyata' Nima mahaifiyarki ce zakiji dadin Zama Dani kinji' Kuma Duk abinda mashkur yayi Miki ki gayamin zanyi masa hukunci idan kece baki kyautaba kema ba kyaleki Zan ba' da kyar Yasmeen tayi shiru a jikin mummy tana sauke ajiyar zuciya.

Maryam' ke Maryam da sauri Maryam ta shigo' falon tace mummy gani' ina kika shiga Sai faman Kira nake baki zo ba' mummy ina qarasa kai kayan abinci dinning shiyasa' toki kawo Mata abinci nan ba'a dinning zata ciba' to Maryam tace tana turo baki ta fita.
Haka Kawai Sai wahala nake Akan wannan banzar' Duk da nasan sabida ita ake wulaqanta nijlah gashi ta tafi Har yanzu bamu gantaba' tana Mita ta Gama kawo kayan abinci' Ko ruwa Bata kawo ba ta fita seda mummy ta qara kiranta kafin tazo ta ajiye.
Tana fita mashkur ya shigo Dakin da sallama' mummy ce ta amsa ya nemi guri kusa da ita ya zauna' kallan kayan abinci yayi yace' mummy wannan fa?
Abinci amarya ne Sai taci zaku tafi banaso ta kwana da yinwa.
Marairai cewa mashkur yayi yace' eyyah mummy Nima bazan barmiki ita da yinwa ba' ga Kaji can a Mota da Madara ta Tashi muje su Nasir nacan suna jiranmu ya qare maganar Yana sosa kai.

Daguwa mummy tayi masa kafin tace'dan gidanku Ni kake Gaya kaji zataji toba inda zakuje saitaci ta koshi anan Kuma ka fita ka Gaya abokan Naka nizan kaita dakinta da hannuna sabida haka kowa ya wuce nasu gidan dare yayi' Wanda sukayi mun gode.
Zaro ido mashkur yayi yace mummy haba Dan Allah hakafa akewa kowa idan zeyi aure shikenan Kuma ni Sai ki hana' Sai yanzu Yasmeen ta dago kai tana satar kallansu tayi sa'a suka hada ido da mashkur tayi saurin yimasa gwalo' kwafa yayi kama qaramin yaro Yana dire diren qafa yace' mummy kinganta Ko?
Kallan Yasmeen mummy tayi kafin tace ni banga tayi komai ba yarinya Ko kallanka batayi ba' to kaga Ni bara naje Da saina gayamusu' Dan ba Baku Yasmeen zanba' ah ah mummy zanje' harya fita ya juyo Yana cewa' ke Kuma kiyi sauri kici ni bacci nakeji.

Dariya Kawai mummy tayi ta fara zuba Mata abinci' farfesun kifi ne da dankali Sai kunun madara' tana zubawa tace to Yasmeen zauna daidai ki cinyeshi duka ina kallanki!
Cikin murya irin ta me Kuka tace mummy Allah naci abinci Kuma naqoshi' mummy Bata Kuma Magana ba ta Tashi ta koma kusa da ita' cokali ta dauka ta dibi abincin ta kai wa Yasmeen bakinta' sunke da kai Yasmeen tayi tanaji kunya' mummy tace dagowa Zaki kici tinda kinqi ci da hannunki' cike da shagwaba Yasmeen tace ah ah mummy zanci.

Saikin amsa na hannuna mummy ta fada tana kai Mata Shi bakinta' ba yadda Yasmeen ta iya haka ta bude baki mummy ta zuba Mata abincin' Kamar magani haka takejinsa a cikin bakinta' Duk da irin dadin dayayi' Sai yanzu takeji zafin rabuwa da iyayenta Ashe haka rabuwa da iyaye yake ka tafi gidan aure' hawayene masu zafi suka fara zuba a fuskanta' hannu biyu tasa tana gogewa' da ido mummy ta Bita tana mamakin yadda take Kuka a daidai wannan lokacin Duk da ita shaidace Akan irin soyayyar da sukewa juna ita da mashkur' hannu mummy tasa ta cire nata hannun ta riqa goge Mata hawayen da nata' kafin a hankali ta Kira sunanta' cikin nutsuwa Yasmeen ta amsa Kanta a qasa' mummy tace' Yasmeen meyasaki Kuka Ko mune bakisan Zama damu Ko Kuma wani abu akamiki?
Girgiza kai Yasmeen tayi bakinta Na rawa tace' mummy' daddy' daddy na nakesan gani.
Dariya taba mummy ganin Ko kwana Yasmeen batayi ba tafara kira daddy Toma me akayi da maza' itako zata so taga irin Zaman da za'ayi tsakanin Yasmeen da mashkur sabida ta lura gaba dayansu Yan shagwaba aka hada' tsaki tayi data tuna da nijlah ya tinawa da irin Tata shagwabar' Sai Kuma ta kawar da tinanin tayi tafara rarrashin Yasmeen Har tayi shiru' Maryam mummy ta Kira ta kwashe kayan abincin' Maryam Na fita mummy ta Kira aunty lateefah' lateefah' zo mana? Ko Harkin fara bacci.
Lateefah da bacci yafara dauka Taji Kiran mummy Kamar a mafarki' dakyar ta iya Tashi ta Shiga Dakin tana hamma' mummy kirana kike ta fada tana Zama kusa da Yasmeen' ah ah mana keda aka Kira ina kikaga ta zama' Tashi Zaki ki kai Yasmeen Dakin Baya ta kwanta' Naga bajin Dadi take ba idan Allah ya kaimu da safe Sai auta ya dauketa su tafi' zaro ido lateefah tayi tace haba mummy mashkur fa jira yake Ku Gama ya dauki matarsa' cikin fada mummy tace' Toni ga abinda nace Zaki kaita koni Na kaita da kaina' tashi lateefah tayi tana dariya ta kama hannun Yasmeen' Banda murna Babu abinda abinda Yasmeen take tabi Bayan lateefah' lafiyanyan gadone a dakin Sai yar qaraman wardrobe da mudubu' bude wardrobe lateefah tayi ta dauko rigan bacci ta aje Kan gadon tana cewa'gashinan kisa saiki kwanta'idan kina buqatar wanka ga toilet' cike da kunya Yasmeen tace to aunty nagode' lateefah Na fita Yasmeen ta fada toilet.
Gajiya da jira mashkur yayi ya dawo cikin gidan Bayan ya sallami abokansa' Yana zuwa yaga mummy Na Shirin rufe kofa' tsayawa yayi Yana sosa kai' fuska a tsuke mummy tace'Yaya auta' lfy naganka cikin dare? Dama Baka tafi ka kwanta ba? Ta jera masa wannan tambayoyin.

Kamar baze amsa taba yaga zata rufe qofan Sai yayi saurin cewa mummy Yasmeen fa?
Tayi bacci kaima ka wuce dare yayi' Bata jira amsar Saba ta rufe qofanta tana mita Niko nace Ikon Allah da mummy ta damu auta beda lfy yanzu Kuma yayi aure an kwace matar lolxx..

Kama yayi Kuka haka yaji' ya Dade tsaye a kofan kafin ya dawo falo' Zama yayi Yana ta zabga uban tsaki ganin Hakan bame Yiwu bane ya Tashi Yana duba dukkan Dakin dake gidan Yana Allah Allah yaga Dakin da amaryarsa take Dan yau yaci alwashin seya kwana da matarsa.


________________


Gudu nijlah take tana haqi ahaka harta zo bakin get' mujaheed ne ya daka Musa Mai Gadi tsawa Yana gudu Yana cewa kada ka bude Mata kofa' wallahi idan ta Bata kaima saina batar dakai'musa najin haka ya Tashi da sauri ya koma bakin get tare da riqe get din gam da hannunsa' tsaye nijlah tayi tana kuka' ahaka mujaheed ya qaraso inda take' beyi mata Magana ba ya fara Janta yanasan maida ita ciki' cike da tsiwa nijlah take qoqarin fizgewa tane cewa ka sakeni Na tafi banaso Na haifar Ma masifa a cikin gida Domin Na tabbata daura wannan auren ba qaramin mafisa bane da tashin hankali.
Zazzafar ajiyar zuciya mujaheed ya safke Yana bin nijlah da kallo' kallanta yake tindaga Sama Har qasa be iya Magana ba Har saida daddyn Ayman ya qaraso inda suke Shima ya tsaya Yana haqi Yana kallansu.

Nijlah nawa kike? Ke bakisan aure rahama bane' meyasa kike kiransa da mafisa' haba nijlah tah wallahi idan kika barni mutuwa zanyi' Na tabbata bazan qara moruwa ba' ki tallafi rayuwa Dan Allah.
Murmushi nijlah tayi tace' tabbas aure rahama ne Domin shiyasa Na Zama haka Har kaima kasanni dako a hanya ka ganni Na tabbata ba zaka taba sha'awar Aure na ba.
Indai Har kin yadda aure rahama ne nijlah ki amince a daura aurenmu? nijlah ko bakya Sona yaudarata kikazo Yi?

Ko kusa ya mujaheed bani da niyyan yaudaranka' sedai aurene tsakanina dakai a yanzu baze taba yiwuwa ba!

Fizgo ta mujaheed yayi ya hadata da qirjinsa Yana cewa' taba ki taba nan nijlah' taba kiji yadda zuciya take halbawa Kamar zata bar gangar jiki nah nijlah ki temaka a daura aurenmu yanzu Dan Allah kiceto rayuwata' nijlah Ni maraya ne banida uwa bani da uba' bantaba San wani abu Bayan Dan uwana ba Sai ke nijlah karki Bari Na zauce Akan sanki' ke tawace Babu Wanda ya isa ya kwaceki koya rabani dake.
Dakyar nijlah ta iya bude baki tana Magana sabida yadda ya shageta ya mannata da qirjinsa ga wani irin zafi dataji jikinsa ya dauka tafara magana.
Kayi hakuri mujaheed Nima inasonka sedai' matse bakinta mujaheed yayi Yana cewa karkice ah ah kawai kice kin amince' yanzu ke bakiyi mamakin yadda Na zube a gabanki ina roqonki ki amince ba Duk da qarancin shekarunki'nijlah karki sani a Rana Dan Allah kice eh?

Dasauri nijlah tace ah ah nace' nace ah ah kayi hakuri mujaheed akwai lokac' luuuuuuuuuuuuuuuu mujaheed yayi daddy Ayman daya daskare a tsaye yana sauraranau yayi saurin tare sa ya fada jikinsa' da gudu nijlah tayi kansu tana cewa' dan Allah ka tashi Kaji idan ka mutu Nima mutuwa zanyi nan tafara fulatanci ta Zama Kamar mahaukaciya' Musa Musa bani ruwa da sauri ka bani' da gudu Musa ya dauko kwanan ban ruwan fulawa cike da ruwa suka fara zuwa mujaheed Amma abanza Danko mutsawa beyi ba.

Cikin gida ya koma da gudu ya dauka makullin Mota ya fito qoqarin daukar mujaheed yake' nijlah dake riqe da shi ta birkice taqi sakinsa'

Tass tasss Tass daddy Ayman ya dauketa da mari Har guda 3 Yana cewa' ki sakeshi nace Dan uwarki' Kuma ki tabbata idan Dan uwana ya mutu kema saikin bishi daga haka yasa mujaheed a Mota Shima ya Shiga ya jata da mugun gudu ya tafi standard hospital dashi.......



Wadan suka shirya siyan labarin zasu turo kudi su yanzu haka idan sungani' sabida Na Gama free page.

Ina qara fada idan kinsan Zaki fitarmin da novel karki siya.

Kuturo shaidar biyan ta wannan number 09038049272.


Mon sultan💘💘 *'YAR SADAKA 2.*💘💘



*BOOK 2.*





*Wannan labarin na kudine' ga mai so zata Biya 200 naira kachal ta karanta karki karanta idan Baki siya ba' Zaki Tura katin MTN ta wannan number 09038049272,,Ko ta account number, 0089110527, suwaiba Hussaini zakirai, access bank.* 8

*'yan Niger su tuntubi wannan number,, +22789520047.*

*Garabasa ga duk Wanda ta siya labarin 'yar sadaka' Zaki karanta wayafi sonta na mmn fareesah 200 naira' Wanda be siya 'yar sadaka ba zai karanta 300 ko da kudinki sai da rabanki*



Guda daddyn Ayman yake sosai bana wasa ba'Amma duk da haka gani yake mota tsaye take' gabadaya hankalinsa ya gama tashi musamma idan yasa hannu a hancin mujaheed yaji babu numfashi' Allah ne kadai ya kaisu asibitin lafiya' suna zuwa likitoci suka shiga ciki da mujaheed' tsaye daddyn Ayman yayi ya rasa inda zesa rayuwarsa yaji dadi' addu'arshi daya mujaheed ya tashi domin ya daukarwa kansa alwashin daukar fansa Akan nijlah mundin Shima ya rasa gudan jininsa.
Likitoci sunyi iya bakin qoqarinsu Amma haryanzu mujaheed be farka ba' daya daga cikin manyan likitocin ya matsa waje daya Yana goge gumi' seda ya Samu nutsuwa ya dauka wayansa' wata number da akayi saving da Dr yayi dealing' second daya zuwa biyu aka dauka' Dr na dauka Dr Ahmad yayi saurin cewa' likita Dan Allah kazo munada patient munyi iya kar qoqarinmu akansa sedai haryanzu be farfado ba' beyi magana. Ba ya kashe wayan tare da tattare takaddun dake kan table' cikin saurin yasa glass dinsa ya fita a office' minti biyu kachal ne ya Kai shi inda mujaheed ke kwance' Yana zuwa sauran likitoci suka bashi guri' be dauka lokaci me tsayi akansa ba numfashinsa mujaheed ya dawo daidai' mujaheed na farkawa yafara Kiran nijlah' nijlah karkimin haka wannan iya shegen naki yayi yawa zuciyana bazata iya dauka ba' ki tallafi rayuwa kar zuciyana ta buga' gajiya daddyn Ayman yayi da jira ya shiga cikin dakin sabida jin muryan mujaheed Yana Kiran wannan yarinyar da ayanzu yake ganin tafi hadarin jirgin sama a gurinsa' Yana shiga daya daga cikin likitocin suka ce ya Samu ya rarrashesa yayi shiru kuma dole sai an kawo yarinyar dayake Kira kafin asan abinyi' da to daddyn Ayman ya amsa ya Sami guri' gefen gadon ya zauna Yana qarewa Dan uwana nasa kallo.
Jan jiki mujaheed yayi ya kwantar da kansa jikinsa Yana cewa' Yaya ka temaka kada na mutu wallahi bazan iya rayuwa ba nijlah ba' daddyn Ayman be iya magana ba saima hannu dayasa ya rufewa mujaheed Baki Yana girgiza masa kai' bude idanunsa mujaheed yayi Yana kallan Dan uwan nasa da haryanzu ya kasa magana sai girgiza masa kai yake' zuciyarsa na dokawa da matsanincin karfi' yace Yaya kayi magana Dan Allah Ina nijlah?
Juya Masa baya daddyn Ayman yayi Dan a yanzu yafara gajiya da wannan iskancin da mujaheed ke Masa akan yarinyar daya tabbata ya haifeta yace' kaga mujaheed kadena yaudaran zuciyarka' ka aje maganar nijlah ka dauka wata abace data zo ada kuma ta tafi.
Jikin mujaheed na wani kyarma ya qanqameshi' wasu sabbin hawaye na zuba daga cikin idonsa' bakinsa na rawa yafara magana har haqoransa na haduwa da juna yace' dangirma Allah Yaya kadena gayamin haka ka kiramin ita ko Zan sami sauqin abinda nakeji' Yaya nine fa Dan uwanka da kake nunawa soyayya da kauna kada ka bari ka rasani akan abinda kake da iko a kansa ya qare maganar zuciyarsa na bugawa da karfi' runtse Ido daddyn Ayman yayi Yana sauraran dan uwan nashi' lokaci guda ya tinana amanar da iyayensu suka Dora akanshi ta fado Masa cikin zuciya dasauri yasa hannu yasa y tallafi fuskan mujaheed cike da tausayawa ya Sanya kwayar idonsa cikin nashi ya zuba Masa Ido yana kallan zallar soyayyan da Dan uwan nasa kewa nijlah' narkewa mujaheed yay a jikinsa yana San yin magana likita ya shigo' a hankali daddyn Ayman ya janye jikinsa ana mujaheed ya fita' Yana fita mujaheed ya ruqe hannun Dr Yana cewa' Dr haryanzu basu kawomin nijlah ba' nasan Kai kasan abinda nakeji kasa Baki ko Zan Samu sauqi dajin dadin rayuwa' murmushi Dr Ahmad yayi yace ka kwantar da hankalinka kasha wannan maganin anjima kadan itama zasu kawo ta' banaso likita wanne irin maganine wannan' wallahi baku da maganin damuwa ta' nijlah ce kaidai samun sauqi na kudena wahalar da kanku' nan ya birkice Yana surutai to ganin yadda jikin nasa ya qara rikicewa ga zazzabi Mai zafi gaske daya qara rufeshi yasa Dr yimasa alluran bacci' minti biyu dayin alluran bacci me nauyi ya daukesa.
Lullubesa yayi ya fito dasauri daga office' Yana fita ya kalli daddyn Ayman' shi dinma kallansa yake yace' abdallah inaso kaje gida kayi saurin dauko yarinyar nan kafin mujaheed ya farka ko kasa a kawo ta' idan ba hakaba to akwai matsala babba' cike da firgici da tsoro daddyn Ayman ya dafa kafadar Dr Ahmad Yace'aboki na Dan Allah kayi duk yadda zakai kada na rasa Dan uwana' Shima dafasa yayi yace abdallah? Rayuwar Dan uwanka ba'a
Showing 12001 words to 15000 words out of 65321 words