nidan Allah ka kaini ko nawane Zan baka.

Ikon Allah mutum yace kafin ya qaremin kallo Yana cewa' yarinya wannan anguwan babu Wanda ya Isa ya shigeta yanzu nayi saurin zaro Ido Ina cewa' sabida me? Yau da safe na baro wurin yanzu kake gayamin haka.

Shiru yayi yace inshiga napep din naqi muna cikin haka saiga malaman mu sun fito nemana suna ganina suka riqeni lokacin harna fara kuka Ina cewa sai an kaini gida.

Kiyi hakuri yarinya sabida tin safe fada ya barke tsakanin fulani da jama'ar anguwa gabadaya sun kashe mutanan wurin malamin mu ya fada' sai Mai napep yace' wani abin haushi harda Mai taimaka musu suka kashe wani ake kiransa malam ya'u bakina na karkarwa na maimai sunan inajin jini na daukana haka suka sani cikin adaidaita aka kaini babban asibitin dake garinmu' muna zuwa Naga gawawwakin mutane wasu kuma anyanke musu kafa wasu da ciwo a jikinsu' Ina ganin haka naji duk wani ciwo na warke na riqa Shiga cikinsu Ina duba fuskokin mutane ko Allah zaisa nima Naga nawa iyayen .


Ina cikin dubawa naji wata kawata ta kwalamin kira' hauwa ya'u zokigani' kinga mamanki ta fada tana kuka' da gudu na qarasa gurin mama na rungume gawarta Ina kuka Ina tsinewa fulani aka aka dauketa akayimata jana'iza ita da sauran Yan uwana da jama'ar anguwa har akayi aka gama babu gawar mahaifina' hakan yasa aka Koma anguwar gabas ana neman sauran mutane ciki harna nawa mahaifin' ana zuwa akaga yadda suka cinnawa gidanmu wuta ga gone qurmur..

Ranar munyi kuka harmun gaji' tin da wannan lokacin na rasa gatana sai wannan Mai napep din ya tafi Dani gidanshi acan nayi rayuwa har Allah ya hadani da mahaifinku mukayi aure.

Kunji wannan shine labarina da dalilin dayasa na tsani fulani na kuma saina duk wata alaqa da zata hadani da fulani har nakeji Zan iya rabuwa da Koma waye muddin ya hada alaqarsa da jinin fulani.

Sai gashi Allah buwayi gagara misali ya nunamin mahaifina bayan shekara 35 hakan ya bani mamaki sai nake ganin kamar bashi ba' Amma danaji ya Kira sunana na tabbatar da shine mahaifina.

Juyawa tayi inda malam ke zaune tana cewa' malam garin Yaya ka kubuta daga sharrin wadannan fulanin harkakoma rayuwa a cikinsu?


Murmushi malam yayi Yana cewa' haqiqa rashin sani yafi dare duhu to maganar gaskiya hauwa'u niba fulani ne suka wulaqantani ba......


Tashi tsaye mummy tayi gabanta na faduwa tace..........*'yar sadaka book 2*


Ki siya kafin ki karanta ta wannan number 09038049272..


Tsaye mummy ta tashi gabanta na faduwa tace' malam duk gari ya dauka fulanine suka aikata wannan ta'addancin tayaya yanzu zakace Basu bane' Dan Allah malam...


Hannu malam ya daga mata Yana cewa'

Hauwa'u ki yadda da abinda na gayamiki' lokuta da Dama ana aikata barna da ta'addanci baza'ayi bincike Mai kyauba sai a Dora laifin kan fulani'

inaso kisani dayawa daga cikin wasu abubuwan ba fulani ke aikatashi ba ana alakari da halin wasu daga cikinsu sai a yanke musu hukunci' hakan ba daidai bane.

Gumin fuskanta ta goge tana cewa' to malam Ya abin yake?

Ki zauna yanzu Zakiji komai hauwa'u' zama mummy tayi tana cije yatsa idanunta akan malam tana sauraransa' zuciyarta na azalzalata da sanjin labarin.


Hauwa'u lokacin da kika tafi makaranta Allah ya Aiko da ikonsa akanmu wasu 'yan ta'adda suka kawowa fulanin kusa damu hari' muna cikin gida nida mamanki mukafarajin ihu da harbe harben bundiga' da gudu na fito mamanki na riqeni ahaka muka qaraso bakin get' Mai gadi muka gani kwance cikin jini kafin muyi Yinqurin wani Abu Yan iskannan sun hauro Mana cikin gida' da zuwansu suka samin bindiga suna cewa'


Ka fitomana da jauro ko yanzu mu aikaka lahira?

Cikin tashin hankali mafara rantsewa wadannan mutane Amma Basu saurareni ba suka harbe mahaifiyarki akan idona tana salati ahaka Allah yamata cikawa na kurma ihu Ina qoqarin zuwa kan gawarta suka Dora bindiga a kaina zasu harbeni na runtse Ido Ina Kiran sunan Allah saika jauro ya fado ta katanga ya riqeni muka bace suka daina ganinmu ' ganin sun rasa jauro yasa ransu ya qara baci suka kunnawa gidanmu wuta tare da kashe sauran mutanan da suka rage..


Ban tashi tsintar kaina ba sai a wani tsuburin kauye Wanda za'a kiranshi da ruga ta fulani' gida biyu ne a gurin sai wajen kiwan shanu daya zagaye.


Salati nake Ina tambayan jauro yanda wannan abun al'ajabi ya faru? Bai iya gayamin ba sedai yace turosu akayi su kasheshi' nan muka zauna mukayi kuka na rashin iyalinmu da duk wata kadara tamu.


Bamu San kowa a wannan kauyen ba haka muka Samu itatuwa da Kara muka hada tamu bukkan tinda mukafara Yan gari suka zo suka Samu a gaba' sun so hanamu hada bukkan Allah ya kawo kaka ita ta nuna tana buqatar a taimaka mana' dakyar suka Bari muka zauna.


Kaka ke zuwa gidansu tana kawomana kanzo da fura ahaka har tasa aka bamu aran Gona muka fara noma muna tayasu kiwo' shekaranmu daya da zuwa Allah yama jauro rasuwa sabida hawan jini daya kamashi a haka na cigaba da zama ni daya Ina tunaninki wata Rana haka Zan kwana Ina kuka.

Ganin yadda nake zaune ni kadai yasa mahaifin kaka ya bani auren ta batare dayasan dangina ba' tinda na auri kaka muke zaune lafiya' sedai duk haihuwan da kaka' zatayi yaran basa zama sai babban yaranmu shi dayane ya rayu har mukayi Masa aure shekaransu daya da aure suka Samu hadari a hanyarsu ta zuwa tallan nono sai yarinyarsa guda itace nijlah..


Dasauri mummy ta dago Kai tana kallan nijlah hawaye na qara zubowa akan fuskanta.

Malam ya cigaba da cewa' kasancewar niba wani Abu na Tara ba yasa muka Shiga gararin rayuwa' har ta Kai abinda zamusa a bakinmu Yana Mana wahala ga nijlah tayi girmanta yakamata ace muna kula da ita Koda abincine' sedai Allah bai horemana ba sai mu kwana uku bamu Dora tukunya ba hakan yasa na yanke shawaran auren da ita ko Allah zaisa ta Samu inda itama zata huta' Allah yasa mashkur ya amsa aurenta a qarshe ya zo da itanan..


Kallan mashkur mummy tayi da idanunta daya canza kala tace' auta mayyasa baka gayamin taimakon nijlah kayi ba? Meyasa baka gayamin halinda iyayenta suke ciki ba? Kasa na kuntatawa rayuwarta nayi watsi da maraicinta.

Daga mashkur har Abba kallan mummy suke cike da mamaki' a hankali mashkur yace' mummy a lokacin idanunki sun rufe Baki tsaya na gayamiki ko ita wacece ba burinki bai wuci nijlah ta bar Miki gidaba' Amma duk da haka Ina qoqarin gayamiki Baki amsa uzurina ba.

Magana zatayi Abba yace' yanzu dai magana ya qare' gashi yarinyar da kika tsangwama kika wulaqanta tayi sanadiyyar ganin mahaifinki gashi kuma abinda kike zargi ba haka bane' yanzu Ina Zaki Kai haqqinta da kika dauka?


Kuka mummy ta sa'ta miqa hannu tana Kiran nijlah' nijlah ta maqale kafada tana kallan mashkur' alama yayi Mata dataje ta matsa cikin sanyin jiki mummy ta rungume ta tana kuka' tana cewa'

Haqiqa ke alkairi ce a gareni nayi watsi da hakan' Nijlah ki yafemin' Ashe ke jininace Allah nagode ma dakahada Dana dake badan hakana bansan ta inda zanga mahaifina ba.

Murmushi nijlah tayi tasa hannu tana goge hawayen fuskan mummy.


Mummy ta riqeta tana cewa'Nijlah bakice kinyafemin ba?

A hankali nijlah tace' mummy nibakimin komai ba wallahi bantaba riqeki a Raina ba Dan haka nayafemiki kema Dan Allah ki yafewa mashkur sabida sabamiki daya riqayi Akaina.


Shafa kanta mummy tayi tasa hannu ta riqo Yasmeen tana cewa' Allah nagode ma dakasa yarana suka hada kansu Allah ya muku albarka' da ameen suka amsa kowa na farincikin ganin Dan uwansa' kaka ko ta kasa rufe Baki sabida murna haka kowa ya riqa sa albarka tare da neman yafiyar juna.

Malam ne yace' yakamata mu Koma sabida gobe da sassafe zamu Koma kauye.

Kallansa mummy tayi tana cewa' malam kayi hakuri da zaman kauye ku dawo nan mucigaba da zama' dasauri nijlah tace' eh wallahi mummy Nima inaso su zauna a kusa damu.


Murmushi malam yayi Yana kallansu daya bayan daya' kafin yace' hauwa'u kiyi hakuri da wannan batu Dan a gaskiya bazamu zauna anan ba kibari muqara sauran rayuwarmu acan' Abba najin haka yafara roqon malam Amma fur malam yaqi yadda haka suka hakura.

Ganin karfe 1 na dare yayi suka kwana gabadayansu a gidan mummy duk da kusan Rabin kwanan a zaune sukayi shi' washe gari mashkur yace' nijlah ta shirya su koma gida taqi yadda tace ita a gurin kaka' zata zauna kuma abincinta takeso.

Mummy ce ta riqe hannun nijlah tana cewa' Kai auta dagaske diyar tawa cikine da ita?

Murmushi yayi ya kasa magana nijlah ko jikin kaka ta Koma tana cewa' aidai bani da komai ko kaka' shafa kanta' kaka tayi tana murmushi farin ciki Dan gani take tafi kowa farin ciki..

Babu yadda mashkur ya iya haka mummy tace dole saiya bar nijlah a gida har zuwa ranar dasu kaka zasu Koma kauye.

Karfe 10 na safe Abba ya tafi da jama'a batare da kowa ya sani ba sukaje kauyen kankan nan yasa aka rushe gidan malam akayimusu gini na zamani' cikin kwana uku aka kammala ginin batare da kowa ya sani ba..


Tinda mashkur ya Koma gidansa yake fama da Yasmeen sabida ragwanta irin nata' dakyar take iya Bari Yana biyan buqatarsa wani lokaci har kuka take sabida gajiya da jarabarsa' Allah Allah yake nijlah ta dawo danya fuskanci ita Bata Masa qaddama duk da itama yana Bata wahala dauriya kawai tafi Yasmeen..


Yauma kamar kullum ya shigo gidan mummy ya samesu zaune suna hira' daya bayan daya ya bisu Yana gaishesu saida ya gama nijlah ta saci kallanshi tana cewa' ya mashkur sannu da zuwa' be amsataba saima hararanta da yayi ya tashi ya Shiga dakinsa Yana cewa' mummy kinada paracetamol.


Kafin ta bashi amsa' harya Shiga dakinsa mummy ta kalli nijlah dake zaune kusa da ita tace' tashi ki Kaiwa mijinki magani keko murna bakiyi mijinki yazo.


Dariya kaka tayi tana cewa' idan Bata iya kula dashi Niba saina kwace Shiba Dama Dani ya dace.

Nijlah batace komai ba ta tashi cikin sanyin jiki ta dauka paracetamol da ruwan faro..

Da sallama ta Shiga dakin nan ta sameshi kwance ya daga Kai sama yana kallan fan' zama tayi kusa dashi Yana cewa' ya mashkur baka da lafiya ne?


Bansani ba yace ya tashi zaune ya amsa ruwa da maganin' bayan ya Sha ya zuba Mata Ido yana cewa' gabadaya kin tare a gidannan sabida Kinga mummy na shagwabaki nikin barni sai Shan wahala nake sabida Baki damu Dani ba..

Shiru tayi harya gama ta bude Baki a hankali tana cewa'dan Allah kayi hakuri kuma ai Zan dawo.

Kiyi zamanki kawai.

Turomasa Baki tayi ta tashi zata fita tana cewa' tobaga aunty Yasmeen ba Naga tana kula dakai.

Zonan meyasa Ina magana kina qoqarin fita?

Naga bani ka Kira ba mummy ce tace na kawoma.


Cije lebe yayi kafin yayi magana nijlah tayi saurin fita a dakin.


Tsaki yayi ya tashi ya fita Yana Mai tausayamata a duk ranar data shigo hannunsa.


Yau su malam suke Shirin komawa kauye yayin da dangin Abba da maman Yasmeen su husna da sauran Yan uwa suka zo Dan su rakasu' saida kowa ya Shiga mota ana Shirin tafiya mashkur yazo yana cewa.

Ina nijlah?

Mummy dake Shiga mota tace' gatanan a motan gaba ta zaune kusa da kaka' mashkur beyi magana ba ya zagaya ya bude motan fuskanshi a tamke yake kallan nijlah kafin a hankali yace' fito muje badake za'ayi tafiyan ba.


Zaro Ido tayi tana kallan kaka' dasauri kaka' ta dauke kanta tana kallan gefe.

Ki fito nace kafin kisa na' bai qarasa ba nijlah ta fito tana sakin kuka a hankali.

Fitowa mummy tayi dasauri ta qaraso kusa dasu tana cewa' Yaya haka?

Mummy bada ita zaku tafi ba.

Meyasa dacan baka gayamata ba saida ta shirya akasa kayanta a mota zakazo da shirmen zancenka?

Shiru yayi Yana riqe da hannunta tana kuka.

Dallah saketa ka kuma bacemin da gani mummy ta fada cikin fada'.

Hannunta ya saki da gudu nijlah ta Koma cikin mota malam ya fito Yana cewa'

Tashi kije nasan tinda ya hanaki zuwa Yana da dalili' kuka nijlah take tana sauke ajiyar zuciya haka ta fito a motan tana kuka tana komai suka tafi.


Mashkur na dagawa Yasmeen hannu taqi kulashi sabida haushin Hana nijlah zuwa.


Suna tafiya yasa hannu biyu ya dauketa tana wutsil wutsil ya Shiga da ita cikin.


A dakinsa yayimata masauki Yana murmushi ya zauna Yana kallan yadda take kuka tana Kiran kaka da malam' kafin ta Koma Kiran mummy.*Wannan shafin na kudine'karki karanta idan baki siya ba' ga mai so zata Biya 200 naira kachal ta karanta' Zaki Tura katin MTN ta wannan number 09038049272,,Ko ta account number, 0089110527, suwaiba Hussaini zakirai, access bank.idan Baki siya ba karki karanta..*

*'yan Niger su tuntubi wannan number,, +22789520047.* D

*Garabasa ga duk Wanda ta siya labarin 'yar sadaka' Zaki karanta wayafi sonta na mmn fareesah 200 naira' Wanda be siya 'yar sadaka ba zai karanta 300 ko da kudinki sai da rabanki*


A rikice Nasir ya juyo Yana kallan mashkur tare Kiran sunan nijlah da karfi' nijlah kece? Nasir ya qara tambaya a rikice?
Karkarwa jikin nijlah ya dauka a yayinda mujaheed ya zuba musu ido Yana kallansu daya Bayan daya.

Gabadaya jikin mashkur ya sake yayi sanyi' Banda tafarasa da zuciyarsa keyi.' soyake yasake dago ido ya kalleta sedai baze iya Hakan ba sabida ingizashi da zuciyarsa take Akan mujaheed' iska mai zafi ya furzan ya dago idanunsa a hankali ya saukesu Akan nijlah Wanda zuwa yanzu hawaye sunfara wanke Mata fuska' shiru yayi Yana kare Mata kallo Mai dauke da tambayoyi iri iri' qara runtse idanunsa yayi ganin yadda nijlah ke qoqarin kwace jikinta' sedai Haryanzu mujaheed be saketa ba Saima qoqarin sauketa yake Akan jirgin Yana Mata sannu tare da duba kowacce gaba ta jikinta.

Dasauri mashkur ya runtse ido ya sake budesu yanasan tabbatarwa kanshi gaskiya' mafarki yake Ko kuwa a gaskene nijlansa yake gani Manne a qirjin wani wato bashi ba?


Ya Jima kafin ya bude idanunsa' sedai Yana budewa suka qara sauka akansu' cikin zafi da bugawar zuciya mashkur yayi kansu dasauri Nasir Na kiransa' Amma Beji ba.

Yana zuwa ya fizgosu' a tare nijlah da mujaheed suka zube qasa wanwar' be kyalesu haka ba Seda yabi mujaheed Yana duka' cikin lokaci kalilan fuskan mujaheed ya kumbura' gefe nijlah ta koma ta hora hannu akanta' ihu taje tare da Neman masu taimako' take gurin ya cika ana ba mashkur hakuri be cikasa ba Seda ya hadawa mujaheed jini da majina kafin ayi nasaran kwacesa a jikinsa' Yana sakin mujaheed ya saki wani irin Kuka Mai ciwo Yana dafe saitin zuciyarsa' a hankali bakinsa ke furta nijlah ni zakici Amana menayi Miki? kika zabi hukuntani da wannan mummunan abun' namiji fa? Namiji nagani rungume dake.

Dasauri Nasir ya sake hannun nijlah yayi Kan mashkur Yana jinjigasa ganin yadda numfashinsa ke barazanar dauke' Duk yadda mujaheed ya bugu Amma kunnuwansa Basu denajin sautin Aman muryan mashkur ba.

Da kyar ya dago Yana kiran nijlah' ba musu nijlah ta tafi gurin mujaheed jikinta Na karkarwa ganin yadda jini ke daukansa' tana zuwa ta zube a gabansa tana Kuka tare da Kiran sunansa.

Ambulance aka Kira ta daukesu zuwa asibiti Mafi kusa da gurin' Nasir ke kula da mashkur' nijlah na kula da mujaheed sedai gabadaya hankalinta nakan mashkur ta Rasa abinda ke Mata dadi' gashi an hadasu daki daya' jinta take a mugun takure Dan bazata iya daga kai ta Kalli inda mashkur ke kwance' fitsari takeji Amma bazata iya Tashi ba' ganin yadda take matse matse yasa mujaheed zuba Mata ido' a hankali yace'nijlah fitsari kikeji Ko?

Bata bashi amsa ba Seda yaqara tambayanta kafin ta dagamasa Kanta tana turo baki' Duk da irin zafi da radadin dayakeji haka ya Tashi dakyar ya kama hannunta.

Bandaki suka nufa ita dashi mashkur ya yinqura ze Tashi Nasir ya riqesa' dakyar ya samu ya koma ya kwanta kafin ya juyo Yana kallansu ransa a bace yace' ke nijlah baki da hankali agabanmu Zaki Shiga toilet da wani qato?
Dama yawan karuwanci kika fito bamu sani ba?

Karuwanci Kuma mujaheed ya tambaya?
Bansani ba gatanan ka tambayeta Nasir ya fada Yana hararansu.

Sakinta mujaheed yayi ya koma Kan gadon marasa lafiya ya zauna da mamaki fal cikin zuciyarsa.

Dakyar nijlah ta Shiga toilet Bayan tagama takasa fitowa ta tsaya tana tinanin halinda zata Shiga idan Har aka rabata da daya daga cikin masoyanta' Kuka takesanyi ta kasa da haka ta fito Kanta a qasa .

Da kallo suka Bita kowanne Yana mamakin abinda ta aikata masa.

A nesa dasu ta zaune daidai lokacin da wayar mujaheed ya fara ringing' dasauri mujaheed ya dauka Yana cewa' Yaya kazo Kaji Abu ina asibitin Amal Dan Allah kazo yanzu.

What mujaheed asibiti fa kace waye ba lafiya? Ya fada Yana miqewa tsaye, dasauri aunty husna ta juyo tana kallansa.

Cikin muryan Kuka mujaheed yace' Dan uwana ba lfy nidai Kawai kazo' daga haka ya katse Kiran yana Kuka hankali.

Kallansu mashkur yayi ya saki tsaki tare da cewa'
Keeee ?

Juyowa nijlah tayi tana kallansa yace' zonan.

Kasa zuwa tayi ta tsaya tana turamasa baki' Nasir ne yace' bakiji abinda akace ba?

Jikintane yayi matuqar sanyi ta juya a hankali tana tafiya harta qarasa jikin gadon ta jingina Kanta jikin Bango tana sauraransa.

Tashi mashkur ya zuba Mata ido' ya Jima Yana kallanta kafin a hankali yace' nijlah wanene wannan yafada Yana nuna mujaheed Wanda zuwa yanzu tsoro ya hanasa Magana.

Bata iya Magana ba Sai barin da jikinta ya dauka tana qoqarin matso hawaye a idonta.

Tashi mashkur yayi ya janyota jikinsa ya kwada Mata Mari Mai kyau Sai da jinta da ganinta ya dauke Na wani Yan daqiqu kafin ta dawo cikin hayyacinta mashkur ya fara Magana.

Karki Bari Na qara Magana baki bani amsar tambaya naba.
Qin Magana tayi mashkur ya Tashi tsaye a fusace yayi kanta' dasauri mujaheed ya cire Duk wani tsoro yasha gabansa Yana cewa'.

Dakata Malam kai uban tane kome' dazaka kamata da duka?

A fusace mashkur ya ture mujaheed Yana cewa' Ni nafi ubanta Kuma ka tambayeta kaji' Magana yake sanyi daddyn Ayman da aunty husna suka shigo ha hankalinsu a tashe.

Nijlah Na ganin husna ta tafi gurinta da gudu tana kuka.

Shima mujaheed Kuka yana kallan daddyn Ayman.

Mujaheed meke faruwa Naga jikinka da ciwo? Accident kukayi kome?

Yaya wannan' haka Kawai ya hauni a duka Yana zagina Har Suna Kiran matata da karuwa.

A tare mashkur
Showing 24001 words to 27000 words out of 65321 words