Jihar Zamfara, jiha ce mai tarin albarka, jiha ce mai cike da arziqi, na noma, na ma'adanai, da kiwo, Allah ya azurta Zamfara da mutanen kirki tun kafuwar ta, ya sanya ta zama qasa mai tarin albarka, da ruqo da addinin musulunci, jihar Zamfara na daya daga cikin jihohin Nigeria da suka yi tashe a tsaida shari'ar Musulunci shekaru masu yawa da suka gabata.
An san mutanen jihar Zamfara da son zaman lafiya, gaskiya, amana, juriya, jarumta,ilimi, kasuwanci, sana'o'i, sarauta, da dik wani abu na jin dadin rayuwa.
Zamfara gari ne na zaman lafiya a baya, gari ne da aka yanke shi daga jihar Sokoto,a zamanin General Sani Abacha, a 1st October 1996, shine shugaban qasar da ya ba ta 'yancin ta, ta zama jaha kamar sauran jahohi a qasar nan ta Nigeria.
Jihar Zamfara ta tara sarakuna, da shuwagabannin gwamnati masu adalci a baya, ta yanda qasar ta zamanto a koda yaushe cikin aminci take, kowanne dan jahar kuma kowanne yare, da addini ya ke zaune cikin kwanciyar hankali, ba fargaba, ba tashin hankali, balle tsoro.
Wannan ita ce jihar Zamfara a shekarun da suka gabata.
Garin Gusau shi ne babban birnin jihar zamfara, gari ne da ya qunshi al'umma kala kala, mabanbanta, yaruka daban_daban, da addinai daban-daban.
Gwamna Halliru Murtala Gusau, shi ne Gwamna mai ci, ya na zaune da iyalan shi a unguwar GRA, Gwamna Halliru ba shi da abin so a duniya sama da iyalin shi, dan haka komai ya ke yi a duniyar siyasa domin su ne, Hajiya Ikilima wadda aka fi kira da Hajiya Ikee, ita ce matar shi, sai yaran su biyu Sultan me shakara Ashirin da tara, da Sultana Mai shekara Ashirin da biyar,dikkan su sun yi karatu ne a University of Westminster London, in da Sultan na da BSc a Architectural Technology, Sultana Kuma na da BA a Arabic and linguistics.
Dikkanin su sun samu gata, kalar wanda in da za a hada su da sauran yaran gwamnonin Nigeria, za a yi wahala a samu ya su, kama daga dukiya,da tsaro, saboda tsaron da suke samu in Sun samu amincewar iyayen su har su ka fita, to sai mutum ya rantse Gwamna ne da kan shi ke yawo, motocin sojoji da 'yan sanda ne kawai mutum zai hango su na biye da su dik inda suka dosa.
Yau kusan sati biyu kenan, Sultana na roqar mahaifiyar ta da su bata dama ta fara aiki itama, dan kasar ta ta mori ilimin da Allah ya hore mata, yau ma kamar kullum, Hajiya Ikee shiru ta mata ta ci gaba da ɗaukan inibin ta ta na jefawa a baki, hankali kwance, qafar ta kuwa mai aikin su ce Me Buruji ke matsa mata, kan ta a qasa, saboda tsoron had'a ido da uwar gidan nata.
Cikin tausaya wa Sultana ta ce,
" Baaba je ki kitchen za mu yi magana da Hajiya"
"To ran ki shi dade"
A duqe ta miqe kamar wadda take a fadar matar sarki.
Da sauri Hajiya Ikee ta kalli Sultana ta ce,
"Na hwa san mi kike yi Sultana ,wato Ina Sanya Me Buruji wahala ko? Shi na kin ka kore ta, tau ki kiyaye ni, kar ki koma yi min haka nan, and da ki ke damu na akan ki hwara aiki,Ni misshamin kai da aikin ki? Daddyn ku ya ce ba za ku yi aiki ba, kuma na goyi da bayan shi, % saboda ku ba diyan talaka kuke ba, albashin ga dai in shi ki ka bida ana baki duk wata, dangi ma aka basu albashi ba tare da sun tai aikin komi ba balle ke? Daga yau kar ke ko dan uwan ki ku sake tunkara ta da wanga batu, kin ishen da d'umin banza, haba"
Cikin fushi ta tashi za ta bar tafkeke kuma qayataccen parlourn na su, wanda tsayawa ma fadin had'uwar shi, bata lokacin mai karatu ne.
Da sauri Sultana ta rungume Mahaifiyar tata ta baya, tare da dora kan ta a saman bayan ta, cikin kalamai masu sauqi Sultana ke magana.
"Mum Dan Allah ki hakuri, indai ni ta, ban koma yin magana akan aiki, zan hakura, ba zan sake maganar ba, ki dena hushi pls"
Juyawa ta Yi ta na Dan murmishi, sannan ta zauna a kujerar da ta tashi, sannan ta ce,
"Ni wallah mamaki kuke ban diyan ga, kamar ba kuyi karatu qasar waje ba, kamar wadan da sun ka yi cudanya da talakawa, Allah ya daukaka ku, amma kullum burin ku bai wuce ku ga kun wulaqanta kanun ku ba,"
Murmushin takaici Sultana ta yi, dan ta san in tai magana, yanzu ran mahaifiyar ta zai qara ɓaci.
Amma tabbas ko a dangi ana mamakin yanayin tarbiyyar su, wadda ta sha bam_bam da ta iyayen su.
Su kuwa ba su ga abun mamaki ba, dan sun san yanda akai suka samu tarbiyyar nan, sannan sun sani Ubangiji Allah ya na yin yadda ya so, a sanda ya so ba tare da neman izinin kowa ba, sun sani da izinin shi, da ikon shi ne suka zamo yara na gari, tarbiyyar da suke da ita ta sha banban da halayyar iyayen su.
Lokacin da aka kai su Sultana makaranta a qasar waje, sun kammala primary a nan Nigeria a Abuja, makarantar hade take da islamiyya, mai matuqar tsada ce, dan haka yara suna samun ilimi na kowane fanni, sun haddace qur'ani tun su na Nigeria, wanda iyayen su ma basu wani damu da hakan ba, fatan su su samu kyakkyawan result da zai kai yaran babbar makarantar gaba da primary, dake qasar turawa.
Kuma sun samu nasarar hakan, an kai su makarantar gaba da Sakandire a London,ba su samu damar ci gaba da karatun Islama ba, sai bayan da suka shiga jami'a lokacin hankali ya shige su, Sultan ya ga haddar su na zubewa, shi ne ya sama masu wani malami Bature ne,amma Musulmi masanin addini sosai, ya ke koyar da su addinin su, ba tare da mahaifan sun wani damu ba, su dai abinda suka fi damuwa da shi shine, yaran su su zama masu ilimin boko, ta yanda daraja da qima, tare da ajin su zai dagu a cikin sa'annin su.
Hira suka ci gaba da yi, amma ran Sultana ba bu dadi, ta so matuqa ta yi lecturing shi ne babban burin ta a rayuwa.
**********************
Me Buruji na komawa bangaren masu aiki,ta ja hannun kishiyar ta me suna Lamishi, suka koma gefe,nan ta labarta mata me ya faru a ciki, kama baki Lamishi ta yi, sannan t ce,
"Ohhh diyan ga na Gwauna ba su samu iyayen kwarai ba wallah, wadda ki ka san ba su na sun ka haihe su ba, Allah shi kyauta, mu je ki isuwa aikin ki, da kin ka tai kin ka bari, walle ban qarasa maki,Nima nawwa ya isan"
"Lamishi hoo, yanzu dan goge kici (kitchen) din shi abbaki iya isuwa mini?"
"Ke walle ban iyawa, tai dai ki isuwa, yanzu ki na gamawa mu tai gida,wancan dan mutuwar zuciyan da yaran shi na can na jiran mu samo mu kai musu su lasa, bada aniya ki isuwa (kammala,gamawa) mu ta tahiya gida"
Ba bu bata lokaci kuwa Me Buruji ta kammala aikin ta, suka yi wa sauran ma'aikatan sallama, dauke da ledojin da suka cika da abincin da aka ci aka rage, sai masu aiki su tattara su raba a tsakanin su, saboda yawan abincin da kuma kala kalan wanda ake dafawa, shi ya sa yake isar masu aikin, watarana ko sun dafa nasu, na masu aiki, se dai su tafi da shi, gidajen su.
Sai da suka tsaya a gate aka duba kayan su, sannan suka fita.
Dan sahu suka tsayar suka dauki hanyar unguwar su da ke a TUDUN FAILA.
A qofar gida suka tadda mijin su, zaune da abokan shi, suna manne da gini, sanye da wasu jemammun tufafi, mijin su na hango su ya washe baki, ya dago daga jikin katangar ya na lashe busassun labban shi.
Lamishi ce ta saki guntun tsaki ta ce,
"Kalli mijin ki,mai matacciyar zuciya, sai wani lashe baki shi kai awaw-wani baqin maye, sun bi sun wani maqale ga gina awwad-dangin qadangaru....kaiii Allah shi wadaran wanga mutuwar zucciya walle"
"Ameen ke dai"
Ko gaishe da abokan mijin nasu ba su yi ba suka fada gidan, su na jin su na gaishe su, tare da yi masu sanu amma ko kallo ba su ishe su ba, bata rai Dan Talo ya yi, ya tattare qasan rigar shi ya afka cikin gidan nasu ya na fadin.
"Ina zuwa na iskamma wadan can lalatatun, ba dan na amince ba ko titin gidan Gwauna ba ku bi wallah, dan tsabar raini, abukkai na za ku walaqantawa haka? To ba wata sheeee....."
Maganar shi ce ta maqale, ganin wata sharbebiyar kaza na maiqo, Lamishi na aje wa a farantin silver.
Kallon shi suka yi a tare cikin daure fuska, Lamishi ta ce,
"Ba wata sheee me?"
Cikin inda inda Dan Talo ya ce,
"Ba wata 'yar shimi na sauya? Zahi ni ka ji yau"
"Ahayyyeeeeee, ayyuuuriiiriiiii, Dan Talo amanar Lamishi da Me Buruji "
Tafawa suka yi, shi kuma ya hau yaqe, dan ya san sun fahimci kwana ya sha.......
Ku dakace Ni a shafi na gaba, dan jin yanda zata kaya...
Comment
Vote
Share.
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 2:
Babu zuciya haka Dan Talo ya durqusa a gaban matan shi ,yawu na qoqarin zuba masa, sai surutu ya ke zubawa, mara ma'ana.
"Koni dun Allah Yi ki sallame shi, shi ta tahiya,ya cika min kunne da d'umin banza" a cewar Mai Buruji da ta ke wurga wa Dan Talo harara.
(Ni dak dan Allah ki yi ki sallame shi ya cika ni da surutun banza)
"Wa ka d'umin banza? Walle matar ga kin rammin, (raina Ni) tauu ya yi, in ta qamar iskanci da rashin kunya kka ji, na dame ki na shanye, ke sani ko?"
"Ahayyyee, Ni ko nissani,tunda ga qarshen rashin kunya, ka tsaya mata su bido su kawo, ka canye, ka sude hannu,da ka qare ka ishe mu da jininin yohi"
Miqa masa kwano Lamishi ta yi da abinci, tini ya rufe bakin shi, ya karbi kwanon ya yi waje, ya na fadin,
"Ina zuwa, bari na isuwa cin abinci za ki maimaita abinda ki ka hwada"
"Haka nan aka iya,namijin hotiho"
Lamishi da ta dawo daga ajiye abincin yaran su ne, ta dangwara kwanon nasu abincin a gaban Mai Buruji ,ta zauna, tare da fadin ,
"Ke dai ba ki gajiya da jayo mana wancan dan na gaji jininin (mita) shi zo shi aza mana cin mutunci, se rai ya yi ta ɓaci"
Dariya kawai Mai Buruji ta fara, ta na kai lomar shinkafa bakin ta, sallama aka rangada, tare da fadin,
"Mutanen gidan na nan kuwa?"
"'Yakkwadai(kwad'ayayyiya) , ke duk san muna nan daidai wanga lokaci, shigo mu ci"
"Ba ka qi ta mutum ba ai, abinci abokin kowa na wallah"
Ba Bismillah ba komai,haka matar da ake kira da 'Yabbuga ta danna hannun ta a kwano, ta fara kai lomar shinkafa bakin ta, ta na ci ta na qoqarin basu labari .
"Dan Allah dai ki bar d'umin ga, ki na maisuwa mana na baki,"
"Akwai labari"
"Ai mun san ba a rasa nono a riga"
Fatali ya yi da butar da ke saman hanyar shiga cikin gidan , cikin maye da kirari, da kuranta kan shi ya ke magana, daga qarshe ya zabga wani ihun da ya sanya 'Yabbuga kwarewa da shinkafa,tsabar tsoro, sai tari ta ke son ta maqale ya qi maqaluwa,
"Lawwali yanzu tsakanin ka da Allah hwashe min buta zakai ka tafi ka barni da sayen sabuwa? Ka..."
"Ina abinci naaa...yunwa nake ji...ciki na ba komai kamar tekun da ta qafe haka nake ji na"
"Shi na kici tai ka dauka, lalataccen banza"
Wata zabura ya yi, kamar ba shi ne ya shiga a bige ba, ya zaro wata sharbebiyar wuqa,ya goga a qasa, tare da zuba wani uban ihu, 'Yabbuga ta zabura ta runtuma dakin Lamishi a guje ta na fadin,
"Tsautsayi ya kawo ni gidan ga, Lawwali na gari, da na san ya na gari da ban zo kwadan banza ba, yau bone ya ci ni, Allah ka taimake ni na hita gidan ga lahiya,"
Jikin ta sai rawa ya ke, zufa na karyo mata, a rayuwar ta ko Allahn da ya halicce ta bata tsoro kamar yanda take tsoron Lawwali,tunda ko salloli biyar basu dame ta ta tsaida su ba, yanda take tsaida gulma da munafurci a unguwar, Lawwali ya farke mutum ya bace a neme shi sama ko qasa a rasa ba wani abu bane a wajen shi , ko da an kama shi, ba ya kwana a cell , a ranar ze fito, kuma wanda ya sa aka kama shi, ya jawa kan shi masifa.
Shi ya sa ma, mutane suka hakura da kai shi qara wajen hukuma.
Abincin shi ya dauka, ya fita zuwa dakin shi da ke zauren gidan, ya na fito,wata ajiyar zuciya 'Yabbuga ta sauke, tare da qarasa sude hannun ta da ta ci abinci, leqe ta ke ta window dan ganin shin ya tafi ko yana nan? Ta na ganin fitar shi ta yi wuf ta fito itama, takalman ta a hannu, ta bar gidan, cikin sanda kar ya fita su gamu, Lamishi na mata magana, akan ta tsaya ta fesa masu me ya faru a shiyya da basu nan, ta ce su same ta a gida.
Kwata-kwata bata son dik wani abu da zai hada ta da Lawwali, saboda Lawwali
na da daurin gindi matuqa a wajen manyan mutane sosai,saboda rashin tsoron shi, da cika masu duk wani aiki da suka saka shi.
Sun dauke shi a matsayin wata kadara tasu mai amfani da mahimmanci,da suke kula da ita da dukiya, da qarfin mulki da ikon su, dan kar wani abu ya same shi.
Lawwali shi ne babban d'an Lamishi wadda ita ce uwar gidan Dan Talo, masu bi mashi mata ne guda uku, Rakiya, Ashibi, da Lami, dikkanin su suna dakin mazan su, sai autar Lamishi mai suna Mubaraka.
Mai Buruji na da yara biyu maza, Kamilu da Jamilu.
Dik yaran gidan ba wanda ya yi makarantar islamiyya balle ta boko, in ba Mubaraka ba, ita kadai ce ta ke zuwa islamiyya da kuma boko, da kyar ta samu Lamishi ta amince, tare da sanya bakin Lawwali, dan ya na mutuwar son qanwar shi, ba ya son dik wani abu da zai taba ta.
Duk abinda ta ke so,sai ta bi ta hannun shi ta ke samu, ba dan komai ba sai dan ban-bancin ra'ayi da d'abi'a da ta ke da shi da mutanen gidan.
Shekarar ta sha shida, amma ta matsu ta yi aure itama kamar sauran yayun ta, ta bar ma su Lamishi gidan, su yi ta jahilcin su.
Kusan kowanne gida ana samun irin wannan, yaron da ya fi biyayya, ya fi sanin ya kamata, da ciwon kan shi, ya fi shan wahala, tsangwama wajen iyaye da 'yan uwa, ya fi shan aiki, da kuma rashin samun kulawa, balle a kai ga gode masa.
Haka ce ke faruwa da Mubaraka a cikin gidan su, wajen Lawwali kawai take samun yabo, da soyayya ,har ma da kyauta, lokuta da dama, har mamaki take, anya Lamishi ce mahaifiyar ta? Amma kamannin su kad'ai sun tabbatar da hakan,Mubaraka, irin yaran nan ne, baqaqe masu madaidaicin kyau, ba ta da wani shahararren kyau, amma saboda kyaun hali da d'abi'un ta, mutum ba zai gaji da zama da ita ba.
Sallama ta yi, tare da murmushi mai annuri, ta shiga gidan, ba komai ya sa ta murmushi ba, sai ganin yayan ta a gida.
Har sun gaisa, ya bata tsarabar da ya kawo mata,ta littattafai da biskit, da alawowi, ya na bata, ya rufe dakin na shi da ke soron gidan ya yi gaba, dama ita ya ke jira.
Ba tare da sun amsa sallamar ta ba, Lamishi ta kalli sabuwar ledar da ke hannun ta ta ce,
"Ke mi nana wannan ga hannun ki?"
Cikin doki da murna Mubaraka ta ce,
"Tsaraba ta ce da Yah Auwal ya kawo min"
"Kawo ta nan,Lawwali ka bata yarinyar ga wallah, bashi da aiki sai bannar kudi nai a harikar banza, ai ta siyan takardun da ba su da anhwani"
Da fari ko kadan Mubaraka ranta bai ɓaci ba da Lamishi ta ce ta kai tsarabar, dan dama ko bata ce ba, ba zata ci komai ita daya ba, amma zagar mata takardu da karatun ta, anan ake samun matsala da ita, nan da nan kuwa ta tura baki, alamar ran ta ya baci.
Amshe ledar ta yi, ta wurga mata littafan ta a qasa, ita kuma ta na bi ta na kwashe wa, cikin qunar rai, ko biskit din bata tsaya amsa ba t shige dakin su.
A nan take suka rabe har da qawayen su da suke nunawa kalar azziqin da suke da shi a unguwa, yamma kawai suke jira ta qarasa yi, kafin nan,kowacce daki ta shiga babu sallah babu salati, suka kwanta,suna jiran la'asar ta yi...........
*A GARIN MU*
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 3:
Allah ya halicci duniyar nan kusan komai guda biyu ne, misali,da ya yi duniya sai kuma ya yi lahira,mace da namiji, mutum da aljan, mai kyau da mara kyau.
Unguwar TUDUN FAILA itama ta qunshi mutane kashi-kashi, akwai mutanen kirki, akwai na banza, a kuma kwai 'yan ba ruwan mu da kowa.
Mutanen kirkin da ke unguwar TUDUN FAILA sun fi na banza yawa, amma ya na daga d'abi'ar dan Adam, bayyana mummuna, ya boye kyakkyawa, wannan dalili ne ya sanya mutanen kirkin unguwar suka ware kan su daga cikin irin su Dan Talo, da matan shi.
Bahaushe ya ce, wake d'aya ke bata gari.
Lamishi ce ta fito, cikin wata atampa, mai kyau, da hijabi kalar kayan ta, takalmin ta baqi, sai 'yar wayar ta a hannu, ta kalli qofar dakin Mai Buruji ta yi tsaki, sannan ta ce,
"Kedai akwai malalaciyar mata, komai saurin da ake sai kin bata wa mutane lokaci, Allah shi cece ki kar a tashi tahiya Makka ki makara, walle jirgi tahiyasshi zai shi barki, ba ruwa nai, dan ba ya jiran kowa"
Cikin dariya Mai Buruji ta fito sanye da ta ta shigar kamar wadan da za su biki, ko suna.
Kallon ta Lamishi ta yi, ta miqa mata hannu suka tafa, sannan suka sanya dariya kamar wasu yara.
"Mika saki dariya halan?"
"Idon mutuniyar nih-hango, dut ta walqita taga tuwahin (kaya) ga sai hankalin ta ya tashi"
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 1:
Jihar Zamfara, jiha ce mai tarin albarka, jiha ce mai cike da arziqi, na noma, na ma'adanai, da kiwo, Allah ya azurta Zamfara da mutanen kirki tun kafuwar ta, ya sanya ta zama qasa mai tarin albarka, da ruqo da addinin musulunci, jihar Zamfara na daya daga cikin jihohin Nigeria da suka yi tashe a tsaida shari'ar Musulunci shekaru masu yawa da suka gabata.
An san mutanen jihar Zamfara da son zaman lafiya, gaskiya, amana, juriya, jarumta,ilimi, kasuwanci, sana'o'i, sarauta, da dik wani abu na jin dadin rayuwa.
Zamfara gari ne na zaman lafiya a baya, gari ne da aka yanke shi daga jihar Sokoto,a zamanin General Sani Abacha, a 1st October 1996, shine shugaban qasar da ya ba ta 'yancin ta, ta zama jaha kamar sauran jahohi a qasar nan ta Nigeria.
Jihar Zamfara ta tara sarakuna, da shuwagabannin gwamnati masu adalci a baya, ta yanda qasar ta zamanto a koda yaushe cikin aminci take, kowanne dan jahar kuma kowanne yare, da addini ya ke zaune cikin kwanciyar hankali, ba fargaba, ba tashin hankali, balle tsoro.
Wannan ita ce jihar Zamfara a shekarun da suka gabata.
Garin Gusau shi ne babban birnin jihar zamfara, gari ne da ya qunshi al'umma kala kala, mabanbanta, yaruka daban_daban, da addinai daban-daban.
Gwamna Halliru Murtala Gusau, shi ne Gwamna mai ci, ya na zaune da iyalan shi a unguwar GRA, Gwamna Halliru ba shi da abin so a duniya sama da iyalin shi, dan haka komai ya ke yi a duniyar siyasa domin su ne, Hajiya Ikilima wadda aka fi kira da Hajiya Ikee, ita ce matar shi, sai yaran su biyu Sultan me shakara Ashirin da tara, da Sultana Mai shekara Ashirin da biyar,dikkan su sun yi karatu ne a University of Westminster London, in da Sultan na da BSc a Architectural Technology, Sultana Kuma na da BA a Arabic and linguistics.
Dikkanin su sun samu gata, kalar wanda in da za a hada su da sauran yaran gwamnonin Nigeria, za a yi wahala a samu ya su, kama daga dukiya,da tsaro, saboda tsaron da suke samu in Sun samu amincewar iyayen su har su ka fita, to sai mutum ya rantse Gwamna ne da kan shi ke yawo, motocin sojoji da 'yan sanda ne kawai mutum zai hango su na biye da su dik inda suka dosa.
Yau kusan sati biyu kenan, Sultana na roqar mahaifiyar ta da su bata dama ta fara aiki itama, dan kasar ta ta mori ilimin da Allah ya hore mata, yau ma kamar kullum, Hajiya Ikee shiru ta mata ta ci gaba da ɗaukan inibin ta ta na jefawa a baki, hankali kwance, qafar ta kuwa mai aikin su ce Me Buruji ke matsa mata, kan ta a qasa, saboda tsoron had'a ido da uwar gidan nata.
Cikin tausaya wa Sultana ta ce,
" Baaba je ki kitchen za mu yi magana da Hajiya"
"To ran ki shi dade"
A duqe ta miqe kamar wadda take a fadar matar sarki.
Da sauri Hajiya Ikee ta kalli Sultana ta ce,
"Na hwa san mi kike yi Sultana ,wato Ina Sanya Me Buruji wahala ko? Shi na kin ka kore ta, tau ki kiyaye ni, kar ki koma yi min haka nan, and da ki ke damu na akan ki hwara aiki,Ni misshamin kai da aikin ki? Daddyn ku ya ce ba za ku yi aiki ba, kuma na goyi da bayan shi, % saboda ku ba diyan talaka kuke ba, albashin ga dai in shi ki ka bida ana baki duk wata, dangi ma aka basu albashi ba tare da sun tai aikin komi ba balle ke? Daga yau kar ke ko dan uwan ki ku sake tunkara ta da wanga batu, kin ishen da d'umin banza, haba"
Cikin fushi ta tashi za ta bar tafkeke kuma qayataccen parlourn na su, wanda tsayawa ma fadin had'uwar shi, bata lokacin mai karatu ne.
Da sauri Sultana ta rungume Mahaifiyar tata ta baya, tare da dora kan ta a saman bayan ta, cikin kalamai masu sauqi Sultana ke magana.
"Mum Dan Allah ki hakuri, indai ni ta, ban koma yin magana akan aiki, zan hakura, ba zan sake maganar ba, ki dena hushi pls"
Juyawa ta Yi ta na Dan murmishi, sannan ta zauna a kujerar da ta tashi, sannan ta ce,
"Ni wallah mamaki kuke ban diyan ga, kamar ba kuyi karatu qasar waje ba, kamar wadan da sun ka yi cudanya da talakawa, Allah ya daukaka ku, amma kullum burin ku bai wuce ku ga kun wulaqanta kanun ku ba,"
Murmushin takaici Sultana ta yi, dan ta san in tai magana, yanzu ran mahaifiyar ta zai qara ɓaci.
Amma tabbas ko a dangi ana mamakin yanayin tarbiyyar su, wadda ta sha bam_bam da ta iyayen su.
Su kuwa ba su ga abun mamaki ba, dan sun san yanda akai suka samu tarbiyyar nan, sannan sun sani Ubangiji Allah ya na yin yadda ya so, a sanda ya so ba tare da neman izinin kowa ba, sun sani da izinin shi, da ikon shi ne suka zamo yara na gari, tarbiyyar da suke da ita ta sha banban da halayyar iyayen su.
Lokacin da aka kai su Sultana makaranta a qasar waje, sun kammala primary a nan Nigeria a Abuja, makarantar hade take da islamiyya, mai matuqar tsada ce, dan haka yara suna samun ilimi na kowane fanni, sun haddace qur'ani tun su na Nigeria, wanda iyayen su ma basu wani damu da hakan ba, fatan su su samu kyakkyawan result da zai kai yaran babbar makarantar gaba da primary, dake qasar turawa.
Kuma sun samu nasarar hakan, an kai su makarantar gaba da Sakandire a London,ba su samu damar ci gaba da karatun Islama ba, sai bayan da suka shiga jami'a lokacin hankali ya shige su, Sultan ya ga haddar su na zubewa, shi ne ya sama masu wani malami Bature ne,amma Musulmi masanin addini sosai, ya ke koyar da su addinin su, ba tare da mahaifan sun wani damu ba, su dai abinda suka fi damuwa da shi shine, yaran su su zama masu ilimin boko, ta yanda daraja da qima, tare da ajin su zai dagu a cikin sa'annin su.
Hira suka ci gaba da yi, amma ran Sultana ba bu dadi, ta so matuqa ta yi lecturing shi ne babban burin ta a rayuwa.
**********************
Me Buruji na komawa bangaren masu aiki,ta ja hannun kishiyar ta me suna Lamishi, suka koma gefe,nan ta labarta mata me ya faru a ciki, kama baki Lamishi ta yi, sannan t ce,
"Ohhh diyan ga na Gwauna ba su samu iyayen kwarai ba wallah, wadda ki ka san ba su na sun ka haihe su ba, Allah shi kyauta, mu je ki isuwa aikin ki, da kin ka tai kin ka bari, walle ban qarasa maki,Nima nawwa ya isan"
"Lamishi hoo, yanzu dan goge kici (kitchen) din shi abbaki iya isuwa mini?"
"Ke walle ban iyawa, tai dai ki isuwa, yanzu ki na gamawa mu tai gida,wancan dan mutuwar zuciyan da yaran shi na can na jiran mu samo mu kai musu su lasa, bada aniya ki isuwa (kammala,gamawa) mu ta tahiya gida"
Ba bu bata lokaci kuwa Me Buruji ta kammala aikin ta, suka yi wa sauran ma'aikatan sallama, dauke da ledojin da suka cika da abincin da aka ci aka rage, sai masu aiki su tattara su raba a tsakanin su, saboda yawan abincin da kuma kala kalan wanda ake dafawa, shi ya sa yake isar masu aikin, watarana ko sun dafa nasu, na masu aiki, se dai su tafi da shi, gidajen su.
Sai da suka tsaya a gate aka duba kayan su, sannan suka fita.
Dan sahu suka tsayar suka dauki hanyar unguwar su da ke a TUDUN FAILA.
A qofar gida suka tadda mijin su, zaune da abokan shi, suna manne da gini, sanye da wasu jemammun tufafi, mijin su na hango su ya washe baki, ya dago daga jikin katangar ya na lashe busassun labban shi.
Lamishi ce ta saki guntun tsaki ta ce,
"Kalli mijin ki,mai matacciyar zuciya, sai wani lashe baki shi kai awaw-wani baqin maye, sun bi sun wani maqale ga gina awwad-dangin qadangaru....kaiii Allah shi wadaran wanga mutuwar zucciya walle"
"Ameen ke dai"
Ko gaishe da abokan mijin nasu ba su yi ba suka fada gidan, su na jin su na gaishe su, tare da yi masu sanu amma ko kallo ba su ishe su ba, bata rai Dan Talo ya yi, ya tattare qasan rigar shi ya afka cikin gidan nasu ya na fadin.
"Ina zuwa na iskamma wadan can lalatatun, ba dan na amince ba ko titin gidan Gwauna ba ku bi wallah, dan tsabar raini, abukkai na za ku walaqantawa haka? To ba wata sheeee....."
Maganar shi ce ta maqale, ganin wata sharbebiyar kaza na maiqo, Lamishi na aje wa a farantin silver.
Kallon shi suka yi a tare cikin daure fuska, Lamishi ta ce,
"Ba wata sheee me?"
Cikin inda inda Dan Talo ya ce,
"Ba wata 'yar shimi na sauya? Zahi ni ka ji yau"
"Ahayyyeeeeee, ayyuuuriiiriiiii, Dan Talo amanar Lamishi da Me Buruji "
Tafawa suka yi, shi kuma ya hau yaqe, dan ya san sun fahimci kwana ya sha.......
Ku dakace Ni a shafi na gaba, dan jin yanda zata kaya...
Comment
Vote
Share.
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 2:
Babu zuciya haka Dan Talo ya durqusa a gaban matan shi ,yawu na qoqarin zuba masa, sai surutu ya ke zubawa, mara ma'ana.
"Koni dun Allah Yi ki sallame shi, shi ta tahiya,ya cika min kunne da d'umin banza" a cewar Mai Buruji da ta ke wurga wa Dan Talo harara.
(Ni dak dan Allah ki yi ki sallame shi ya cika ni da surutun banza)
"Wa ka d'umin banza? Walle matar ga kin rammin, (raina Ni) tauu ya yi, in ta qamar iskanci da rashin kunya kka ji, na dame ki na shanye, ke sani ko?"
"Ahayyyee, Ni ko nissani,tunda ga qarshen rashin kunya, ka tsaya mata su bido su kawo, ka canye, ka sude hannu,da ka qare ka ishe mu da jininin yohi"
Miqa masa kwano Lamishi ta yi da abinci, tini ya rufe bakin shi, ya karbi kwanon ya yi waje, ya na fadin,
"Ina zuwa, bari na isuwa cin abinci za ki maimaita abinda ki ka hwada"
"Haka nan aka iya,namijin hotiho"
Lamishi da ta dawo daga ajiye abincin yaran su ne, ta dangwara kwanon nasu abincin a gaban Mai Buruji ,ta zauna, tare da fadin ,
"Ke dai ba ki gajiya da jayo mana wancan dan na gaji jininin (mita) shi zo shi aza mana cin mutunci, se rai ya yi ta ɓaci"
Dariya kawai Mai Buruji ta fara, ta na kai lomar shinkafa bakin ta, sallama aka rangada, tare da fadin,
"Mutanen gidan na nan kuwa?"
"'Yakkwadai(kwad'ayayyiya) , ke duk san muna nan daidai wanga lokaci, shigo mu ci"
"Ba ka qi ta mutum ba ai, abinci abokin kowa na wallah"
Ba Bismillah ba komai,haka matar da ake kira da 'Yabbuga ta danna hannun ta a kwano, ta fara kai lomar shinkafa bakin ta, ta na ci ta na qoqarin basu labari .
"Dan Allah dai ki bar d'umin ga, ki na maisuwa mana na baki,"
"Akwai labari"
"Ai mun san ba a rasa nono a riga"
Fatali ya yi da butar da ke saman hanyar shiga cikin gidan , cikin maye da kirari, da kuranta kan shi ya ke magana, daga qarshe ya zabga wani ihun da ya sanya 'Yabbuga kwarewa da shinkafa,tsabar tsoro, sai tari ta ke son ta maqale ya qi maqaluwa,
"Lawwali yanzu tsakanin ka da Allah hwashe min buta zakai ka tafi ka barni da sayen sabuwa? Ka..."
"Ina abinci naaa...yunwa nake ji...ciki na ba komai kamar tekun da ta qafe haka nake ji na"
"Shi na kici tai ka dauka, lalataccen banza"
Wata zabura ya yi, kamar ba shi ne ya shiga a bige ba, ya zaro wata sharbebiyar wuqa,ya goga a qasa, tare da zuba wani uban ihu, 'Yabbuga ta zabura ta runtuma dakin Lamishi a guje ta na fadin,
"Tsautsayi ya kawo ni gidan ga, Lawwali na gari, da na san ya na gari da ban zo kwadan banza ba, yau bone ya ci ni, Allah ka taimake ni na hita gidan ga lahiya,"
Jikin ta sai rawa ya ke, zufa na karyo mata, a rayuwar ta ko Allahn da ya halicce ta bata tsoro kamar yanda take tsoron Lawwali,tunda ko salloli biyar basu dame ta ta tsaida su ba, yanda take tsaida gulma da munafurci a unguwar, Lawwali ya farke mutum ya bace a neme shi sama ko qasa a rasa ba wani abu bane a wajen shi , ko da an kama shi, ba ya kwana a cell , a ranar ze fito, kuma wanda ya sa aka kama shi, ya jawa kan shi masifa.
Shi ya sa ma, mutane suka hakura da kai shi qara wajen hukuma.
Abincin shi ya dauka, ya fita zuwa dakin shi da ke zauren gidan, ya na fito,wata ajiyar zuciya 'Yabbuga ta sauke, tare da qarasa sude hannun ta da ta ci abinci, leqe ta ke ta window dan ganin shin ya tafi ko yana nan? Ta na ganin fitar shi ta yi wuf ta fito itama, takalman ta a hannu, ta bar gidan, cikin sanda kar ya fita su gamu, Lamishi na mata magana, akan ta tsaya ta fesa masu me ya faru a shiyya da basu nan, ta ce su same ta a gida.
Kwata-kwata bata son dik wani abu da zai hada ta da Lawwali, saboda Lawwali
na da daurin gindi matuqa a wajen manyan mutane sosai,saboda rashin tsoron shi, da cika masu duk wani aiki da suka saka shi.
Sun dauke shi a matsayin wata kadara tasu mai amfani da mahimmanci,da suke kula da ita da dukiya, da qarfin mulki da ikon su, dan kar wani abu ya same shi.
Lawwali shi ne babban d'an Lamishi wadda ita ce uwar gidan Dan Talo, masu bi mashi mata ne guda uku, Rakiya, Ashibi, da Lami, dikkanin su suna dakin mazan su, sai autar Lamishi mai suna Mubaraka.
Mai Buruji na da yara biyu maza, Kamilu da Jamilu.
Dik yaran gidan ba wanda ya yi makarantar islamiyya balle ta boko, in ba Mubaraka ba, ita kadai ce ta ke zuwa islamiyya da kuma boko, da kyar ta samu Lamishi ta amince, tare da sanya bakin Lawwali, dan ya na mutuwar son qanwar shi, ba ya son dik wani abu da zai taba ta.
Duk abinda ta ke so,sai ta bi ta hannun shi ta ke samu, ba dan komai ba sai dan ban-bancin ra'ayi da d'abi'a da ta ke da shi da mutanen gidan.
Shekarar ta sha shida, amma ta matsu ta yi aure itama kamar sauran yayun ta, ta bar ma su Lamishi gidan, su yi ta jahilcin su.
Kusan kowanne gida ana samun irin wannan, yaron da ya fi biyayya, ya fi sanin ya kamata, da ciwon kan shi, ya fi shan wahala, tsangwama wajen iyaye da 'yan uwa, ya fi shan aiki, da kuma rashin samun kulawa, balle a kai ga gode masa.
Haka ce ke faruwa da Mubaraka a cikin gidan su, wajen Lawwali kawai take samun yabo, da soyayya ,har ma da kyauta, lokuta da dama, har mamaki take, anya Lamishi ce mahaifiyar ta? Amma kamannin su kad'ai sun tabbatar da hakan,Mubaraka, irin yaran nan ne, baqaqe masu madaidaicin kyau, ba ta da wani shahararren kyau, amma saboda kyaun hali da d'abi'un ta, mutum ba zai gaji da zama da ita ba.
Sallama ta yi, tare da murmushi mai annuri, ta shiga gidan, ba komai ya sa ta murmushi ba, sai ganin yayan ta a gida.
Har sun gaisa, ya bata tsarabar da ya kawo mata,ta littattafai da biskit, da alawowi, ya na bata, ya rufe dakin na shi da ke soron gidan ya yi gaba, dama ita ya ke jira.
Ba tare da sun amsa sallamar ta ba, Lamishi ta kalli sabuwar ledar da ke hannun ta ta ce,
"Ke mi nana wannan ga hannun ki?"
Cikin doki da murna Mubaraka ta ce,
"Tsaraba ta ce da Yah Auwal ya kawo min"
"Kawo ta nan,Lawwali ka bata yarinyar ga wallah, bashi da aiki sai bannar kudi nai a harikar banza, ai ta siyan takardun da ba su da anhwani"
Da fari ko kadan Mubaraka ranta bai ɓaci ba da Lamishi ta ce ta kai tsarabar, dan dama ko bata ce ba, ba zata ci komai ita daya ba, amma zagar mata takardu da karatun ta, anan ake samun matsala da ita, nan da nan kuwa ta tura baki, alamar ran ta ya baci.
"Kina barin turo shegen goshi awad-diyar jakka, bani nan"
Amshe ledar ta yi, ta wurga mata littafan ta a qasa, ita kuma ta na bi ta na kwashe wa, cikin qunar rai, ko biskit din bata tsaya amsa ba t shige dakin su.
A nan take suka rabe har da qawayen su da suke nunawa kalar azziqin da suke da shi a unguwa, yamma kawai suke jira ta qarasa yi, kafin nan,kowacce daki ta shiga babu sallah babu salati, suka kwanta,suna jiran la'asar ta yi...........
*A GARIN MU*
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 3:
Allah ya halicci duniyar nan kusan komai guda biyu ne, misali,da ya yi duniya sai kuma ya yi lahira,mace da namiji, mutum da aljan, mai kyau da mara kyau.
Unguwar TUDUN FAILA itama ta qunshi mutane kashi-kashi, akwai mutanen kirki, akwai na banza, a kuma kwai 'yan ba ruwan mu da kowa.
Mutanen kirkin da ke unguwar TUDUN FAILA sun fi na banza yawa, amma ya na daga d'abi'ar dan Adam, bayyana mummuna, ya boye kyakkyawa, wannan dalili ne ya sanya mutanen kirkin unguwar suka ware kan su daga cikin irin su Dan Talo, da matan shi.
Bahaushe ya ce, wake d'aya ke bata gari.
Lamishi ce ta fito, cikin wata atampa, mai kyau, da hijabi kalar kayan ta, takalmin ta baqi, sai 'yar wayar ta a hannu, ta kalli qofar dakin Mai Buruji ta yi tsaki, sannan ta ce,
"Kedai akwai malalaciyar mata, komai saurin da ake sai kin bata wa mutane lokaci, Allah shi cece ki kar a tashi tahiya Makka ki makara, walle jirgi tahiyasshi zai shi barki, ba ruwa nai, dan ba ya jiran kowa"
Cikin dariya Mai Buruji ta fito sanye da ta ta shigar kamar wadan da za su biki, ko suna.
Kallon ta Lamishi ta yi, ta miqa mata hannu suka tafa, sannan suka sanya dariya kamar wasu yara.
"Mika saki dariya halan?"
"Idon mutuniyar nih-hango, dut ta walqita taga tuwahin (kaya) ga sai hankalin ta ya tashi"
Sake sanya dariya suka yi, suka sa
Book Chapters
Chapter 1 Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51