ya ji ta a rufe, juyawa ya yi ya ga Lawwali na kallon yatsun hannun shi, sake jan qofar ya yi, ya ji ta gam, cikin tsananin tashin hankali ya juya tare da zubewa a wajen,ya sake jakar kud'in a qasa ya na kuka, zufa da hawayen shi duk sun hade waje daya.
"Oga don Allah ka yi min rai, ka rufa min asiri ina da iyali, ka sani, ka san mahaifiya ta, ka ɗauke ta awat-taka,Oga ina da niyyar sanar da kai tsoro nika ji kar ka kashe ni, ina da qananan yara ka sani, har takwara na yi ma oga"
Har gaban Lawwali ya isa ya kama qafar shi ya na kuka ya na bashi hakuri, wani irin naushi Lawwali ya kai mishi sai da jini ya yi tsartuwa a qasa, bakin No 4 ya fashe.
Kasa ihun ma ya yi, dan ya san ya cancanci sama da haka ma, idanun Lawwali ba bu mai fatan ya gan su a wannan lokacin.
"Taheer ni zaka ci wa amana? aza ka ke bani ganewa? To na ji duk abinda kun ka ce kai da wancan qaramin dan iskan, ina kun ka kai min qauna ta?"
"Oga na san inda suke zan kai ka da kai na, Oga ka yahe min, ba da son rai na ba an ka ɗauke ta, ba ita mun ka tai dauka ba, qawar ta mun ka tai dauka, sun ruhe fuska bamu san da ita ciki ba"
"Yi min shuuu ! Munahikin banza, ka na jin har akwai wata sauran yarda a tsakanin mu? Ba bu yarda tsakani na da kai, maza ka gaggauta kai ni ga qauna ta, sai dai zai zama siri tsakanin mu, kamar yanda gwauna da wancan shegen basu son na sani, ban yarda ka sanar da kowa ba,in kuma ka sake cin amana ta a karo na biyu, zan kashe ka, zan kashe uwar ka, dan ba uwa ta ta ba, zan kashe matar ka da diyan ka,"
"Oga ko na hwarko ma tsautsayi na wallah ban koma cin amanar ka, Nagode oga na go..."
"Dalla miqe ka je ka kai ni ga qauna ta"
Jiki na rawa No 4 ya miqe, a bakin kofa ya tsaya ya na jiran Lawwali ya bude qofar shi, sai da ya dauki makullin mota, ya lodawa bindigar shi harsashi sannan suka fita suka bar gidan.
Kafin su isa magriba ta gabata sosai, bai fi awa daya a kira ba, su na zuwa No 4 ya bawa Lawwali shawara su aje mota a nesa su qarasa da qafa, haka kuwa aka yi, sun isa qofar gidan, suka tarar an kulle da kwado, No 4 ne ya zari makulli a aljihun shi zai bude qofar, bai ankara ba ya ji an dafe qeyar shi da duka,
"Dan iska, makullin ruhe qauna ta na hannun ka, amma kullum muke haduwa baka taba hwadi min ba"
Su na shiga su ka ji gidan shiru kamar ba kowa, dakin da aka ajiye yaran suka shiga, ko da suka je sai ba su ga Mubaraka ba, sai su Murjanatu, tambayar su Lawwali ya yi ina take, cikin kuka Saliha ta ce,
"Wannan d'ayan mugun ya dauke ta, kullum in ya zo sai ya dauke ta ya hita da ita, daga baya sai ya dawo da ita, ta na kuka"
Wani irin ashar Lawwali ya saki,lallai in abinda yake zargi No 1 ya yi da Barakan shi,tabbas a yau dinnan zai kashe shi.
A guje Lawwali ya kama hanya zai fita daga gidan, No 4 ya yi maza ya kulle ko ina ya bi bayan shi da mugun gudu,shan gaban shi ya yi ya na haki, wani naushi Lawwali ya kai mishi a ciki, sai da ya duqa
"Oga ka san mutanen ga basu da dad'i, na sani Gwauna da kai ya ke taqama a duniyar siyasa,amma ba a cin munahuki da yaqin gaba da gaba, shi ma ka hito mai ta inda bai zata ba, babbar nasarar da an ka samu shi na ka san wanda ya dau qanwar ka,"
Tabbas maganar No4 gaskiya ce, to ta yaya zai rama abinda gwamna ya masa?
Kan shi cike da tunani ya shige mota, ya bar No4 a wajen, No4 komawa ya yi, ya gargad'i su Murjanatu, akan kar su kuskura su sanar da zuwan su, da yayan Mubaraka, su na sanar wa za a kashe su nan take.
Tsoro ya kama su, dan haka sun yi alqawarin ba za su fad'a wa kowa ba, har ita kan ta mubaraka din.
************************
'Yabbuga bata farka daga baccin da ya kwashe ta ba sai da ta ji qarar bude qofar gidan da qarfi, a kidime ta farka ta na fadin,
"Wayyoo Allah mun shiga uku, mi ya hwaru, ake bude gambu kamar ana girgizar qasa?"
"Me ki ke yi a gidan nan a wanan lokacin,"
Bude baki 'yabbuga ta yi iya qarfin ta takurma ihu, marin kan ta tayi, wai ko za ta tashi, wataqila a baccin wahalar da ya dauke ta ne ta ke ganin shi a idanun ta.
Qafa ya sa ya kwashe kujerar da ta dora qafafun ta ya yi wurgi da kujerar, kafin ya qara kaiwa d'aya kujerar duka 'yabbuga ta miqe, ta taka qafafun ta biyu a qasa, ta diba waje a guje, tsantsin ledar na diban ta, kai ba ko dan kwali, gashi duk ya tuttuje haka ta isa gida.
Dan jumma na ta gyara ma'ajiyar abincin su da awaki suka shiga suka yi wa barna, gani ya yi ta afka gidan ba ko sallama, zani qanqame a hannun ta, kai ba dankwali, duk Leda a qafar ta, tsoro da tashin hankali ne suka rufe Dan Jumma, dan a tunanin shi ko masu kidnapping ne suka dauke ta ta gudo, tunda yanzu abun qara yawa yake.
"Daga ina ki ke? Wa ya biyo ki? Masu kidnapping na halan?"
"Wanga ya ci uwar masu kilnapim, ni da gidan Dan Talo har abada,tunda ba aljanna aka rabo a gidan ba,"
Wani irin tsaki Dan jumma ya saki, sannan ya kalle ta ya ce,
"Dama can ki ka tahi na shigo na tadda bisashe (awaki) sun canye min kayan abinci? Ni da na gan ki a hirgice ma aza nikai ko sace ki an kai ki ka gudo, tunda na san ki da gudun ceton rai"
Kar kacewa ta yi rai bace ta ce,
"To mi ka ka nuhi? Wanga ba gudun ceton rai na ba halan, ka ga wadda Yaron nan ya shigo? Ka ga wadda ya dinga fatali da kujeru? Da na tsaya mi ka ka tunanin ze min? Dan Jumma na kula baka san hatsarin yaron can ba ne, Allah shi gama ku watarana"
Cikin sauri Dan Jumma ya ce,
"Ba Amin ba 'yanneman me mugun hwata,"
Haka sukai ta kace nace a tsakanin su, har ya gaji da hayaniya da ita ya bar gidan.
Can gidan su Dan Talo kuwa Lawwali na can na musu ta'adin da ya saba, daki guda su Mai Buruji suka shige, su na ta bashi hakuri, amma bai kula su ba, sai da ya gama musu ta'adin da ya so, sannan ya shiga dakin Mubaraka ya kwanta a katifar ta, hawaye ne ke bin gefen fuskar shi masu dumin gaske, da a so samun shi ne yanzu ya samu ya ɗan hahharbe ko da mutum biyar ne, amma dole zai yi hakuri ya bi shawarar Taheer, zai dauki fansa ta inda gwamna bai zata ba.
Ya na nan kwance har daya na dare, can dakin kuwa sun san bai fita ba, dan basu ji motsin shi ba, ga fitsari ya matsi Lamishi, Mai buruji ce ta ce,
"Yaya kar ki yi min boli (fitsari) ga daki, ke hwa uwar shi ta, ki tai ki bolin ki ki dawo,ko ki tai dakin ki"
Wani mugun kallo Lamishi ta sakarwa Mai Buruji, bata ce komai ba, se kwafa da ta yi, tare da sake leqawa, cikin ran ta ta na fadin,
'Ya jima da yin niyyar ajali na, ina hita a wannan halin da yake ciki, sai ya cika alqwani nai wallah'
Lawwali na nan kwance wani tunani ya fado masa, kamar wanda aka mintsina haka ya miqe, ya na murmushi, cikin wata iriyar murya Lawwali ya furta,
"RAN KI SHI DADE MASOYIYA SULTANA, MASOYIN KI AUWAL NA TAHE"
*HUMMMM LAWWALI KAR KA DAU FANSA AKAN SOYAYYAR GASKIYA PLSS😭😭😭😭*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 30:
"Alhamdu lilLAAH, a qallah Yah Auwal ya san inda nike da ma shi d'ai na damuwa ta, na san shi d'ai na zai shiga matsanancin tashin hankali akan rashi na, a wajen iyaye na kamar dashen iccen juji ni ke, wanda ya fito ga jeji a kuskure, zai gama rayuwa tai ya mace ba tare da sanin kowa ba,"
Idanun ta abushe take wannan maganar babu digon hawaye cikin su, sai tsantsar quna da suya da zuciyar ta ke yi, gaskiya ta fad'i, ko ta na raye ko bata raye ta san iyayen ta ba damuwa za su yi ba, wataqiila qannen ta su Jameelu su damu da rashin ta, amma mahaifin ta da in ya fice ma ba ganin shi ake ba sai zai ci abinci, be bawa Kowa abinci ba, amma ya na tsammanin komawa shi a ciyar da shi,babban aikin shi bai wuce zaman majalisa, da bin bangon gidajen abokan da suka ci abinci qofar gidan shi, shi ma ya ci nasu ya kade riga y koma majalisa.
Lamishi kuwa jin gulmar ta da zuwa aikin ta, sun fi mata komai mahimmanci, ta na iya fita daga gidan da safe ta je aiki, ta dawo ta yi baccin awa daya ta fice gulma sai magariba ta dawo, duk abinda Mubaraka ta yi mai kyau ko mara kyau a matsayin fad'a ne, har nemo laifin ta take.
Mai Buruji kuwa sama sama ne, to iyayen da suka haife ka ma sun yar da kai balle wani? Sai wanda Allah ya taimaka ne yake samun masu yi masa kara su kula da shi .
Yah Auwal, Yah Auwal shi ne rayuwar Mubaraka, shi ne ruhi da numfashin ta, tun da aka sace ta ba ranar da za ta zo ta wuce bata wuni ta kwana kuka ba sai ranar da ta samu labarin zuwan shi, kullum a cikin damuwa da tashin hankali take, ta yi zazzabin ta yi ciwon, amma a banza, bata taɓa sanin ta na da jinnu ba sai a wannan wajen, ta tada su, har sun gaji sun lafa da kan su.
Murjanatu ce ta kalli Saliha ta ce,
"Yanzu daga tahiya ta yauce (toilet) har kin hwadi mata? Sai da an kace kar mu hwadi mata, yanzu ki na ganin rage damuwar da za ta yi ba zai sa su fahimci wani abu ba? Mun rusawa Yayan ta shirin da ya ke son yi kenan hwa, ke wai mis-sa ba ki iya riqe siri ne a ga rayuwar ki? Mtwss"
Murmushi mai ciwo mubaraka ta yi, sannan ta dauke idanun ta daga kallon waje dayan da ta yi ta zuba su akan Murjanatu ta ce,
"Kwantar da hankalin ki,ni a yanda nake dinnan ba zan taba komawa gida ba, ba zan bari Yah Auwal ya maida ni gida ba, abun kunya ne na koma gida a haka, amma ku? Ku za ku iya komawa gida, ina me baku hakuri, domin na san ni ta suka son dauka sun ka haɗa da ku,amma na sani, na san yayana ba zai taba hutawa ba sai ya his-she mu daga nan, inshaa Allahu ku na barin wajen ga"
Cikin kuka Suhaila ta ce,
"Mi ki ke nuhi? Ke dai san ba mu barin wajen ga in ba ke ko? Ko yayan ki ba na jin zai yarda ya his-she mu nan wajen ba bu ke a cikin mu,"
Shiru Mubaraka ta yi bata sake magana ba, amma ta san abu d'aya dole ya faru, za su tafi ba tare da ita ba, bata ga amfanin komawa gida ba, dama can ita GANTALALLIYA ce kamar yanda MAHAIFIYAR TA ke fadi kullum ba fashi .
************************
Da misalin takwas na safiyar litinin, Auwal ne ke tsaye a jikin motar Sultana, ya gama goge ta tass, sai sheqi take, gyara hannun rigar shi ya ke yi, ya na nannade shi sama, Sultana ce ta fito sanye da gilashi a idanun ta, fuskar nan kamar hadari, ta hade ta gam gam, ba alamar walwala, ko fara'ar nan ta ta, ba wani alamar nishadi, ko farin ciki, ga rama ta yi ainun har ba ta boyuwa, hatta da doguwar rigar da ta saka sai da ta nuna alamar ta mata yawa.
Kanta a qasa ta fito, Sultan na biye da ita da mug din tea a hannu, roqon ta ya ke ta sha ko da tea din ne amma taqi, qarshe ma fad'a ta fara yi, kwata kwata hakan ba halin ta bane, Sultan bai ji zafin fad'an ta ba, sai ma tausayi, kama ta ya yi ya rungume, jin ta a jikin shi ne ya sanya ta jin wani abu a maqoshin ta mai ciwo, ya tokare ta, ta na son fidda abun, amma ta gaji da fitar da shi kullum, meye laifin ta? Meye laifi dan ka so driver din ka? Hajiya ta tsaya tsayin daka akan ba ita ba Auwal, kar ta sake ganin wani abu mai kama da soyayya a tsakanin su, daina zuwan shi ba qaramin dad'i ya wa Hajiya ba, Daddy ne kaɗai ya damu, saboda tsaron lafiyar ta, sai Sultan, jin ta take ita da watan da ke sama ba su da bam-bamci, domin kuwa shi ya na kewaye da taurari ko ta ina, amma still shi kadai ne, ita ma ta na tare da su Sultan da Daddyn ta, amma jin ta take kamar bata da kowa a duniya, mutum d'aya da ya mallaki zuciyar ta ya mata nisa.
Da sauri ta d'ago kan ta a lokacin da ta ji Dadyn ta da wanda ta ke tsananin kewa da son gani su na magana, kamar jiri ze debe ta, Sultan ya yi sauri ya tare ta.
Leqa bayan Sultan ta yi, dan tabbatar da abinda kunnen ta ya ke jiyo mata,
"....DPO ni ma ya kiren jiya, ya min bayanin da ya yi min dad'i, ya ce ana ta bincike, kuma su na ganin akwai alamun nasara, ana samun ta inshaa Allahu, shi na ma ya sa na ji hankali na ya ɗan kwanta"
"Da kyau, na yi ma alqawarin ana ganin ta, nan ba da jimawa ba, ka d'ai kwantar da hankalin ka"
Wani kallo ya wa Gwamna, wanda duk sa idon mutum ba zai iya fassara shi ba, murmushi ya saki mai sauti, irin wanda ya san ya na rikita sultana ,tabbas kuwa ya samu nasarar tarwatsa zuciyar ta in to thousad pieces, wasu hawayen farin cikin ganin shi ne ke gudu a kuncin ta, tabbas shi ne ba mafarki bane, ta na jingina jikin Sultan Daddyn su ya daga mata hannu, ya shige ciki, Lawwali kuwa cikin tafiyar shi mai dauke hankalin duk wani mai kallon shi,ya ke takawa zuwa inda suke,rigar Sultan sultana ta qanqame ta baya, hannun ta na rawa, wannan wanne irin so take wa Auwal?
Ko da ya isa gaban su, dan duqar da kai ya yi, ya sanya hannun shi daya a qirji, daya a bayan shi, ya ce,
"Barkan ku da swahiya ran ku shi dade"
A hankali ya d'aga idanun shi cikin salon sace zuciya ya kalli Sultana, kashe mata ido d'aya ya yi, kamar yanda ya saba, wani numfashi ta ja, sannan ta hau qiqqifta idanun ta, dariya ta sake mai sauti, tare da hawaye,hannayen ta duka biyun ta d'ora a saman bakin ta, a hankali ta zare gilashin ta ta na goge hawayen idon ta,cikin dakiya ta ce,
"Ka gama naka saura nawa, mu je ka kai ni office ina da abun yi"
Cikin murmushi mai sauti Lawwali ya ce,
"Dan Allah in za a hukunta ni a duba halin da nake ciki a min adalci, ina mai bada hakuri akan duk abinda na aikata, ni ma ba da so na bane, a duk inda na shiga ruhi na, hankali na, zuciya ta, su na tunanin ki, su na jin zogin rashin ki, amma qauna ta ban san halin da take ciki ba har yanzu, yanzu ma na kasa jure rashin ki na yas-sa na dawo gare ki Ran ki shi dade"
Gaba dayan su ya basu tausayi, Sultan ne ya taka ya isa gaban shi, cikin jimanta rashin mubaraka ya ce,
"Tabbas dole ka shiga tashin hankali da damuwa, mu kam mu hankalin mu ba a kwance yake ba da batan kamilar yarinya kamar Mubaraka, ballantana kai, Allah ya bayyana ta cikin aminci, kuma na san sultana ma ta yahe maka,"
Har zai tafi ya juya ya sanya fuskar Babban yaya, ya ce,
"Ga amanar qauna ta nan, kar na ji kar na gani, duk ta sake kuka akan ka, za ka gamu da ni"
Dan duqar da kai Lawwali ya yi cikin girmamawa ya na murmushi ya ce,
"Ran ka shi dade ba ko ka sake ganin hawaye a wannan kyakkyawan idanun mai haske kamar hasken rana idan ta hito"
Wata iriyar kunya ce ta kama sultana, ta yi matuqar kewar wadannan kyawawa kuma dad'ad'an kalaman daga wajen kyakkyawan masoyi Auwal.
A tare suke takawa wajen motar, banda murmushi ba abinda suke yi.
Bude mata motar ya yi ya ɗan duqar da kai, dan tura baki ta yi, sannan ta ce,
"Na kula da wani sabon salo ka dawo, na ce ka dai na ce min 'Ran ki shi dad'e' ka kira ni da Sultana, ka qi, yanzu kuma wani sabon salo ka zo da shi na duqawa ko?"
Cikin murmushin shi mai sauti ya ce,
"Duk inda mai girma da daraja shike dole na a bashi girma nai, duk inda kyakkyawa take dole ne a girmama kyaun ta"
'Wayyooo zuciya ta, Auwal na so ya hwashe ki da kalaman shi' abinda sultana ta fada kenan a ran ta.
A zahiri kuwa kad'a kai kawai ta yi, ta maida qafafun ta cikin motar ya rufe, bayan ya zauna ya daidaita komai, ya kunna motar, d'aga kai ya yi, ya kalle ta ta madubi, shi kawai ta zubawa ido, kamar wanda zai gudu ta dena ganin shi.
"Ran ki shi dade Lawwali ne dai ba wani ba, in ki na min irin kallon ga za ki sa mu hwada rami,"
Kashe mata ido daya ya yi, tare da murmusawa ta gefen baki, Sultana ji ta yi kamar ta narke daga cikin jiki,
Showing 57001 words to 60000 words out of 150481 words
"Oga don Allah ka yi min rai, ka rufa min asiri ina da iyali, ka sani, ka san mahaifiya ta, ka ɗauke ta awat-taka,Oga ina da niyyar sanar da kai tsoro nika ji kar ka kashe ni, ina da qananan yara ka sani, har takwara na yi ma oga"
Har gaban Lawwali ya isa ya kama qafar shi ya na kuka ya na bashi hakuri, wani irin naushi Lawwali ya kai mishi sai da jini ya yi tsartuwa a qasa, bakin No 4 ya fashe.
Kasa ihun ma ya yi, dan ya san ya cancanci sama da haka ma, idanun Lawwali ba bu mai fatan ya gan su a wannan lokacin.
"Taheer ni zaka ci wa amana? aza ka ke bani ganewa? To na ji duk abinda kun ka ce kai da wancan qaramin dan iskan, ina kun ka kai min qauna ta?"
"Oga na san inda suke zan kai ka da kai na, Oga ka yahe min, ba da son rai na ba an ka ɗauke ta, ba ita mun ka tai dauka ba, qawar ta mun ka tai dauka, sun ruhe fuska bamu san da ita ciki ba"
"Yi min shuuu ! Munahikin banza, ka na jin har akwai wata sauran yarda a tsakanin mu? Ba bu yarda tsakani na da kai, maza ka gaggauta kai ni ga qauna ta, sai dai zai zama siri tsakanin mu, kamar yanda gwauna da wancan shegen basu son na sani, ban yarda ka sanar da kowa ba,in kuma ka sake cin amana ta a karo na biyu, zan kashe ka, zan kashe uwar ka, dan ba uwa ta ta ba, zan kashe matar ka da diyan ka,"
"Oga ko na hwarko ma tsautsayi na wallah ban koma cin amanar ka, Nagode oga na go..."
"Dalla miqe ka je ka kai ni ga qauna ta"
Jiki na rawa No 4 ya miqe, a bakin kofa ya tsaya ya na jiran Lawwali ya bude qofar shi, sai da ya dauki makullin mota, ya lodawa bindigar shi harsashi sannan suka fita suka bar gidan.
Kafin su isa magriba ta gabata sosai, bai fi awa daya a kira ba, su na zuwa No 4 ya bawa Lawwali shawara su aje mota a nesa su qarasa da qafa, haka kuwa aka yi, sun isa qofar gidan, suka tarar an kulle da kwado, No 4 ne ya zari makulli a aljihun shi zai bude qofar, bai ankara ba ya ji an dafe qeyar shi da duka,
"Dan iska, makullin ruhe qauna ta na hannun ka, amma kullum muke haduwa baka taba hwadi min ba"
Su na shiga su ka ji gidan shiru kamar ba kowa, dakin da aka ajiye yaran suka shiga, ko da suka je sai ba su ga Mubaraka ba, sai su Murjanatu, tambayar su Lawwali ya yi ina take, cikin kuka Saliha ta ce,
"Wannan d'ayan mugun ya dauke ta, kullum in ya zo sai ya dauke ta ya hita da ita, daga baya sai ya dawo da ita, ta na kuka"
Wani irin ashar Lawwali ya saki,lallai in abinda yake zargi No 1 ya yi da Barakan shi,tabbas a yau dinnan zai kashe shi.
A guje Lawwali ya kama hanya zai fita daga gidan, No 4 ya yi maza ya kulle ko ina ya bi bayan shi da mugun gudu,shan gaban shi ya yi ya na haki, wani naushi Lawwali ya kai mishi a ciki, sai da ya duqa
"Oga ka san mutanen ga basu da dad'i, na sani Gwauna da kai ya ke taqama a duniyar siyasa,amma ba a cin munahuki da yaqin gaba da gaba, shi ma ka hito mai ta inda bai zata ba, babbar nasarar da an ka samu shi na ka san wanda ya dau qanwar ka,"
Tabbas maganar No4 gaskiya ce, to ta yaya zai rama abinda gwamna ya masa?
Kan shi cike da tunani ya shige mota, ya bar No4 a wajen, No4 komawa ya yi, ya gargad'i su Murjanatu, akan kar su kuskura su sanar da zuwan su, da yayan Mubaraka, su na sanar wa za a kashe su nan take.
Tsoro ya kama su, dan haka sun yi alqawarin ba za su fad'a wa kowa ba, har ita kan ta mubaraka din.
************************
'Yabbuga bata farka daga baccin da ya kwashe ta ba sai da ta ji qarar bude qofar gidan da qarfi, a kidime ta farka ta na fadin,
"Wayyoo Allah mun shiga uku, mi ya hwaru, ake bude gambu kamar ana girgizar qasa?"
"Me ki ke yi a gidan nan a wanan lokacin,"
Bude baki 'yabbuga ta yi iya qarfin ta takurma ihu, marin kan ta tayi, wai ko za ta tashi, wataqila a baccin wahalar da ya dauke ta ne ta ke ganin shi a idanun ta.
Qafa ya sa ya kwashe kujerar da ta dora qafafun ta ya yi wurgi da kujerar, kafin ya qara kaiwa d'aya kujerar duka 'yabbuga ta miqe, ta taka qafafun ta biyu a qasa, ta diba waje a guje, tsantsin ledar na diban ta, kai ba ko dan kwali, gashi duk ya tuttuje haka ta isa gida.
Dan jumma na ta gyara ma'ajiyar abincin su da awaki suka shiga suka yi wa barna, gani ya yi ta afka gidan ba ko sallama, zani qanqame a hannun ta, kai ba dankwali, duk Leda a qafar ta, tsoro da tashin hankali ne suka rufe Dan Jumma, dan a tunanin shi ko masu kidnapping ne suka dauke ta ta gudo, tunda yanzu abun qara yawa yake.
"Daga ina ki ke? Wa ya biyo ki? Masu kidnapping na halan?"
"Wanga ya ci uwar masu kilnapim, ni da gidan Dan Talo har abada,tunda ba aljanna aka rabo a gidan ba,"
Wani irin tsaki Dan jumma ya saki, sannan ya kalle ta ya ce,
"Dama can ki ka tahi na shigo na tadda bisashe (awaki) sun canye min kayan abinci? Ni da na gan ki a hirgice ma aza nikai ko sace ki an kai ki ka gudo, tunda na san ki da gudun ceton rai"
Kar kacewa ta yi rai bace ta ce,
"To mi ka ka nuhi? Wanga ba gudun ceton rai na ba halan, ka ga wadda Yaron nan ya shigo? Ka ga wadda ya dinga fatali da kujeru? Da na tsaya mi ka ka tunanin ze min? Dan Jumma na kula baka san hatsarin yaron can ba ne, Allah shi gama ku watarana"
Cikin sauri Dan Jumma ya ce,
"Ba Amin ba 'yanneman me mugun hwata,"
Haka sukai ta kace nace a tsakanin su, har ya gaji da hayaniya da ita ya bar gidan.
Can gidan su Dan Talo kuwa Lawwali na can na musu ta'adin da ya saba, daki guda su Mai Buruji suka shige, su na ta bashi hakuri, amma bai kula su ba, sai da ya gama musu ta'adin da ya so, sannan ya shiga dakin Mubaraka ya kwanta a katifar ta, hawaye ne ke bin gefen fuskar shi masu dumin gaske, da a so samun shi ne yanzu ya samu ya ɗan hahharbe ko da mutum biyar ne, amma dole zai yi hakuri ya bi shawarar Taheer, zai dauki fansa ta inda gwamna bai zata ba.
Ya na nan kwance har daya na dare, can dakin kuwa sun san bai fita ba, dan basu ji motsin shi ba, ga fitsari ya matsi Lamishi, Mai buruji ce ta ce,
"Yaya kar ki yi min boli (fitsari) ga daki, ke hwa uwar shi ta, ki tai ki bolin ki ki dawo,ko ki tai dakin ki"
Wani mugun kallo Lamishi ta sakarwa Mai Buruji, bata ce komai ba, se kwafa da ta yi, tare da sake leqawa, cikin ran ta ta na fadin,
'Ya jima da yin niyyar ajali na, ina hita a wannan halin da yake ciki, sai ya cika alqwani nai wallah'
Lawwali na nan kwance wani tunani ya fado masa, kamar wanda aka mintsina haka ya miqe, ya na murmushi, cikin wata iriyar murya Lawwali ya furta,
"RAN KI SHI DADE MASOYIYA SULTANA, MASOYIN KI AUWAL NA TAHE"
*HUMMMM LAWWALI KAR KA DAU FANSA AKAN SOYAYYAR GASKIYA PLSS😭😭😭😭*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 30:
"Alhamdu lilLAAH, a qallah Yah Auwal ya san inda nike da ma shi d'ai na damuwa ta, na san shi d'ai na zai shiga matsanancin tashin hankali akan rashi na, a wajen iyaye na kamar dashen iccen juji ni ke, wanda ya fito ga jeji a kuskure, zai gama rayuwa tai ya mace ba tare da sanin kowa ba,"
Idanun ta abushe take wannan maganar babu digon hawaye cikin su, sai tsantsar quna da suya da zuciyar ta ke yi, gaskiya ta fad'i, ko ta na raye ko bata raye ta san iyayen ta ba damuwa za su yi ba, wataqiila qannen ta su Jameelu su damu da rashin ta, amma mahaifin ta da in ya fice ma ba ganin shi ake ba sai zai ci abinci, be bawa Kowa abinci ba, amma ya na tsammanin komawa shi a ciyar da shi,babban aikin shi bai wuce zaman majalisa, da bin bangon gidajen abokan da suka ci abinci qofar gidan shi, shi ma ya ci nasu ya kade riga y koma majalisa.
Lamishi kuwa jin gulmar ta da zuwa aikin ta, sun fi mata komai mahimmanci, ta na iya fita daga gidan da safe ta je aiki, ta dawo ta yi baccin awa daya ta fice gulma sai magariba ta dawo, duk abinda Mubaraka ta yi mai kyau ko mara kyau a matsayin fad'a ne, har nemo laifin ta take.
Mai Buruji kuwa sama sama ne, to iyayen da suka haife ka ma sun yar da kai balle wani? Sai wanda Allah ya taimaka ne yake samun masu yi masa kara su kula da shi .
Yah Auwal, Yah Auwal shi ne rayuwar Mubaraka, shi ne ruhi da numfashin ta, tun da aka sace ta ba ranar da za ta zo ta wuce bata wuni ta kwana kuka ba sai ranar da ta samu labarin zuwan shi, kullum a cikin damuwa da tashin hankali take, ta yi zazzabin ta yi ciwon, amma a banza, bata taɓa sanin ta na da jinnu ba sai a wannan wajen, ta tada su, har sun gaji sun lafa da kan su.
Murjanatu ce ta kalli Saliha ta ce,
"Yanzu daga tahiya ta yauce (toilet) har kin hwadi mata? Sai da an kace kar mu hwadi mata, yanzu ki na ganin rage damuwar da za ta yi ba zai sa su fahimci wani abu ba? Mun rusawa Yayan ta shirin da ya ke son yi kenan hwa, ke wai mis-sa ba ki iya riqe siri ne a ga rayuwar ki? Mtwss"
Murmushi mai ciwo mubaraka ta yi, sannan ta dauke idanun ta daga kallon waje dayan da ta yi ta zuba su akan Murjanatu ta ce,
"Kwantar da hankalin ki,ni a yanda nake dinnan ba zan taba komawa gida ba, ba zan bari Yah Auwal ya maida ni gida ba, abun kunya ne na koma gida a haka, amma ku? Ku za ku iya komawa gida, ina me baku hakuri, domin na san ni ta suka son dauka sun ka haɗa da ku,amma na sani, na san yayana ba zai taba hutawa ba sai ya his-she mu daga nan, inshaa Allahu ku na barin wajen ga"
Cikin kuka Suhaila ta ce,
"Mi ki ke nuhi? Ke dai san ba mu barin wajen ga in ba ke ko? Ko yayan ki ba na jin zai yarda ya his-she mu nan wajen ba bu ke a cikin mu,"
Shiru Mubaraka ta yi bata sake magana ba, amma ta san abu d'aya dole ya faru, za su tafi ba tare da ita ba, bata ga amfanin komawa gida ba, dama can ita GANTALALLIYA ce kamar yanda MAHAIFIYAR TA ke fadi kullum ba fashi .
************************
Da misalin takwas na safiyar litinin, Auwal ne ke tsaye a jikin motar Sultana, ya gama goge ta tass, sai sheqi take, gyara hannun rigar shi ya ke yi, ya na nannade shi sama, Sultana ce ta fito sanye da gilashi a idanun ta, fuskar nan kamar hadari, ta hade ta gam gam, ba alamar walwala, ko fara'ar nan ta ta, ba wani alamar nishadi, ko farin ciki, ga rama ta yi ainun har ba ta boyuwa, hatta da doguwar rigar da ta saka sai da ta nuna alamar ta mata yawa.
Kanta a qasa ta fito, Sultan na biye da ita da mug din tea a hannu, roqon ta ya ke ta sha ko da tea din ne amma taqi, qarshe ma fad'a ta fara yi, kwata kwata hakan ba halin ta bane, Sultan bai ji zafin fad'an ta ba, sai ma tausayi, kama ta ya yi ya rungume, jin ta a jikin shi ne ya sanya ta jin wani abu a maqoshin ta mai ciwo, ya tokare ta, ta na son fidda abun, amma ta gaji da fitar da shi kullum, meye laifin ta? Meye laifi dan ka so driver din ka? Hajiya ta tsaya tsayin daka akan ba ita ba Auwal, kar ta sake ganin wani abu mai kama da soyayya a tsakanin su, daina zuwan shi ba qaramin dad'i ya wa Hajiya ba, Daddy ne kaɗai ya damu, saboda tsaron lafiyar ta, sai Sultan, jin ta take ita da watan da ke sama ba su da bam-bamci, domin kuwa shi ya na kewaye da taurari ko ta ina, amma still shi kadai ne, ita ma ta na tare da su Sultan da Daddyn ta, amma jin ta take kamar bata da kowa a duniya, mutum d'aya da ya mallaki zuciyar ta ya mata nisa.
Da sauri ta d'ago kan ta a lokacin da ta ji Dadyn ta da wanda ta ke tsananin kewa da son gani su na magana, kamar jiri ze debe ta, Sultan ya yi sauri ya tare ta.
Leqa bayan Sultan ta yi, dan tabbatar da abinda kunnen ta ya ke jiyo mata,
"....DPO ni ma ya kiren jiya, ya min bayanin da ya yi min dad'i, ya ce ana ta bincike, kuma su na ganin akwai alamun nasara, ana samun ta inshaa Allahu, shi na ma ya sa na ji hankali na ya ɗan kwanta"
"Da kyau, na yi ma alqawarin ana ganin ta, nan ba da jimawa ba, ka d'ai kwantar da hankalin ka"
Wani kallo ya wa Gwamna, wanda duk sa idon mutum ba zai iya fassara shi ba, murmushi ya saki mai sauti, irin wanda ya san ya na rikita sultana ,tabbas kuwa ya samu nasarar tarwatsa zuciyar ta in to thousad pieces, wasu hawayen farin cikin ganin shi ne ke gudu a kuncin ta, tabbas shi ne ba mafarki bane, ta na jingina jikin Sultan Daddyn su ya daga mata hannu, ya shige ciki, Lawwali kuwa cikin tafiyar shi mai dauke hankalin duk wani mai kallon shi,ya ke takawa zuwa inda suke,rigar Sultan sultana ta qanqame ta baya, hannun ta na rawa, wannan wanne irin so take wa Auwal?
Ko da ya isa gaban su, dan duqar da kai ya yi, ya sanya hannun shi daya a qirji, daya a bayan shi, ya ce,
"Barkan ku da swahiya ran ku shi dade"
A hankali ya d'aga idanun shi cikin salon sace zuciya ya kalli Sultana, kashe mata ido d'aya ya yi, kamar yanda ya saba, wani numfashi ta ja, sannan ta hau qiqqifta idanun ta, dariya ta sake mai sauti, tare da hawaye,hannayen ta duka biyun ta d'ora a saman bakin ta, a hankali ta zare gilashin ta ta na goge hawayen idon ta,cikin dakiya ta ce,
"Ka gama naka saura nawa, mu je ka kai ni office ina da abun yi"
Cikin murmushi mai sauti Lawwali ya ce,
"Dan Allah in za a hukunta ni a duba halin da nake ciki a min adalci, ina mai bada hakuri akan duk abinda na aikata, ni ma ba da so na bane, a duk inda na shiga ruhi na, hankali na, zuciya ta, su na tunanin ki, su na jin zogin rashin ki, amma qauna ta ban san halin da take ciki ba har yanzu, yanzu ma na kasa jure rashin ki na yas-sa na dawo gare ki Ran ki shi dade"
Gaba dayan su ya basu tausayi, Sultan ne ya taka ya isa gaban shi, cikin jimanta rashin mubaraka ya ce,
"Tabbas dole ka shiga tashin hankali da damuwa, mu kam mu hankalin mu ba a kwance yake ba da batan kamilar yarinya kamar Mubaraka, ballantana kai, Allah ya bayyana ta cikin aminci, kuma na san sultana ma ta yahe maka,"
Har zai tafi ya juya ya sanya fuskar Babban yaya, ya ce,
"Ga amanar qauna ta nan, kar na ji kar na gani, duk ta sake kuka akan ka, za ka gamu da ni"
Dan duqar da kai Lawwali ya yi cikin girmamawa ya na murmushi ya ce,
"Ran ka shi dade ba ko ka sake ganin hawaye a wannan kyakkyawan idanun mai haske kamar hasken rana idan ta hito"
Wata iriyar kunya ce ta kama sultana, ta yi matuqar kewar wadannan kyawawa kuma dad'ad'an kalaman daga wajen kyakkyawan masoyi Auwal.
A tare suke takawa wajen motar, banda murmushi ba abinda suke yi.
Bude mata motar ya yi ya ɗan duqar da kai, dan tura baki ta yi, sannan ta ce,
"Na kula da wani sabon salo ka dawo, na ce ka dai na ce min 'Ran ki shi dad'e' ka kira ni da Sultana, ka qi, yanzu kuma wani sabon salo ka zo da shi na duqawa ko?"
Cikin murmushin shi mai sauti ya ce,
"Duk inda mai girma da daraja shike dole na a bashi girma nai, duk inda kyakkyawa take dole ne a girmama kyaun ta"
'Wayyooo zuciya ta, Auwal na so ya hwashe ki da kalaman shi' abinda sultana ta fada kenan a ran ta.
A zahiri kuwa kad'a kai kawai ta yi, ta maida qafafun ta cikin motar ya rufe, bayan ya zauna ya daidaita komai, ya kunna motar, d'aga kai ya yi, ya kalle ta ta madubi, shi kawai ta zubawa ido, kamar wanda zai gudu ta dena ganin shi.
"Ran ki shi dade Lawwali ne dai ba wani ba, in ki na min irin kallon ga za ki sa mu hwada rami,"
Kashe mata ido daya ya yi, tare da murmusawa ta gefen baki, Sultana ji ta yi kamar ta narke daga cikin jiki,
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20 Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51