kan daya kamar ya na a gidan shi, Hajiya Ikee da Gwamna Halliru suka fito a tare.
Cikin daure fuska tamau Lawwali ya miqe tsaye, ya na wasa da glass din shi, sannan ya ce,
"Ba na son jira ka hi kowa sanin haka Excellency ,me yasa ka ke bari na yin jira?"
"Lawwali har yanzu ina da tantama akan baka d'iya...."
A zafafe Lawwali ya juya ya kalli Gwamna ya ce,
"Tantama? Tantama hwa kacce, ka na da wani zabi ne da ya wuce ka aura min ita, ko ku na so ko ba ku so,na ga alama kun zaci ba zan aikata abinda na hwadi ba ko? Ka san ni, ka san wane ne ni, ka san mi zan iya da wanda ba zan iya ba, kar ka bari raina shi fi haka ɓaci, abin ba zai mana kyawu ba"
Cikin hura hanci Hajiya Ikee ta ce,
"Yaro yaro ne bai san wuta ba sai ya taka, in ka na da abinda ka ke ganin za ka yi, ka je ka yi, diya ta bata auren dan iska irin ka, lalatacce d'ebabbe"
Abu kamar sihiri, kafin ta rufe labban ta Lawwali ne a gaban ta, ya sa hannun shi guda daya ya shaqe mata wuya, ya sanya bakin bindigar shi cikin bakin ta, jijiyoyin kan shi, da hannayen shi sun fito rudu rudu, idanun nan kamar an watsa masa barkono, leban shi na qasa ya ciza sai da jini ya fito,Gwamna ne ya isa gaban shi ya fara qoqarin kwace Hajiya Ikee da ke fitar da numfashi a wahalce, idanun ta na ta tsiyayar da hawaye, sai miqawa gwamna hannu take, wata tsawa Lawwali ya daka mata, akan ta dena wannan motsi da kukan da take, diffff ta hadiye kukan nata, ido ya fito ya mata gulu gulu.
"Me ki ka ce, yaro bai san wuta ba sai ya taka? Waye yaro? Na ce waye yaro? A duniya akwai lalatattu d'ebabbu Sama da ku ne? Har ni zaki kalla ki wa zagin d'iban albarka, ke ba dan ina da burika masu yawa ba kin isa na bar ki ki kai gobe, (subhaballah kamar ran a hannun shi yake)"
Ba damar magana bindiga na baki, ga wuya ya sha shaqa,
Da qarfi ya wurga ta qasa ta fad'i, a gigice take neman iskar shaqa, tsabar azabar da take ciki, dishi dishi take gani, Gwamna ne ya duqa gaban ta, ya na taimaka mata wajen daidaita numfashin ta.
"Ku na ji na ko? Nan da sati guda nika so a yi auren mu da Sultana, in hakan bata faru ba, ku sani, har cikin dakin ta, zan shiga in dauke ta, domin babu abinda ba zan iya ba akan cikar buri na, kamar yanda kai ma ba abinda baka yi dan cikar burin ka"
"Lawwali d'iya ta ka ke son a yi wa irin wanga aure? Sati guda kamar d'iyar tallaka?"
Da sauri Hajiya Ikee ta ce,
"Kar ka ja mana magana, ka bari kawai a yi nan da sati guda din, kaga Lawwali, ka turo magabatan ka kawai a sa rana a yi komi a gama lahiya"
Murmushi mai kyau Lawwali ya saki, ya dauke qafar shi da ya dora a saman kujerar su, ya duqa gaban Hajiya, Ita kuwa ta yi baya da azama, dan ba ta so ma ya rab'e ta ko kusa, rabon da a dake ta ba zata iya tunawa ba, amma gata da girman ta, ta sha shaqa .
"Yauwa suruka ta, da kyau,bari na tai gida na sanar da iyaye na, gobe za su zo, a gobe nake so a saka rana, duk wanda ya lalata min shiri, zan lalata masa rayuwa, wanan alqawari na ne"
D'aga kai kawai Hajiya take, Gwamna kuwa kallon Lawwali kawai yake, ba komai, zai aurawa Lawwali Sultana, amma zai nuna wa Lawwali mulki gaba yake da dabanci................
*Hummmm kun amince Mulki gaba yake da dabanci?*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 41:
Zaune ya ke a kujerar da ke kallon ta a cikin office din na ta, su na fuskantar juna, hannun ta ya kama guda daya ya riqe a na shi, ya na kallon yanda gyararran farcen ta yake sheqi, cikin sassanyar murya ya ce,
"Ran ki shi dade, ki na ganin za ki iya zama da ni a duk inda na ajiye ki? Domin ba zan taba karbar gida ko wata alfarma da iyayen ki za su bani ba, ke sani Hajiyan ku da kyar ta yarda da auren mu, dan kawai ina diyan tallaka, ina so na yi komai da kuddi na, ina so ki goya min baya akan wannan, za ki iya?"
Tunda ya fara magana take kallon shi, ta gano gaskiyar maganar shi, ta kuma fahimce shi, ta na alfahari da kasancewar shi mijin da za ta aura, ya san yanda zai ya tsaya a matsayin shi a koda yaushe, baya manta tushen shi, sai dai ta na tsoron rayuwar wahala, amma indai da Auwal din ta ne ba komai, ba abinda ba zata iya yi domin shi ba, sai dai in abun sab'on Allah ne, dan haka ta na ji a jikin ta, za ta iya taya shi cika duk wani burin shi, indai su na tare komai zai zo da sauqi da yardar Allah.
Cikin murmushin da ke nuna gaskiyar maganar da take son furtawa, ta d'aga kai, tare da janye hannun ta daga nashi ta ce,
"Na amince, na amince Zan zauna da kai a duk inda ka ajiye ni, duk inda ka sa qafa nan zan aje tawa, ni kai nake so,ba kudin ka ba,zan amfani da tushen ka ne, ba na iyaye na ba, kai nawa ne, ni taka ce"
Godiya ya mata, suka ci gaba da hirar su sama sama, ta na tsara takardun da za a ware tallafi zuwa ga mabuqata.
Bayan ya maida ita gida, suka ga motoci masu numfashi an Parker su a harabar gidan, Sultana na gani ta gane su waye a ciki, juya ido sama ta yi, ta amshe jakar ta a hannun Lawwali da ke mata sai da safe, sallama suka yi ta shiga gida, ta samu Hajiya Ikee a parlour su na hira da qawayen ta sai zuba musu qarya take, akan shaharar Lawwali a kasuwancin qasashen waje, duk da haka bata tsira ba, sai da suka dinga yada mata da baqar magana, akan 'yar ta bata samu auren shugaban qasa ba.
Gaida su Sultana ta yi ta haye sama, ta na matuqar takaicin rayuwar qaryar da mahaifiyar ta ke gudanarwa.
A can parlour kuwa su Hajiya da qawayen ta sun gama tsare tsaren yanda bikin zai kasance, a cikin qawayen ta akwai wadan da sun taba aurar da yara mata, sun yi alqawarin kawo masu gyaran jiki na musamman har gida.
Wani party da duk abinda Hajiya Ikee ta ke da buri ya faru a bikin nan, sun kammala tsara yanda zai kasance, a bangare guda kuma Lawwali ya gama hurewa sultana kunne kar ta yarda a yi wadannan abubuwan, kuma ta yarda da hakan, bata bayyana ma Hajiya abinda suka tsara ba ita da Lawwali sai bayan tafiyar qawayen Hajiya ne Sultana ta sanya riga da skirt na bature, ta daure gashin ta a bayan ta, ta sanya takalmin ta ta sauka qasa, zama ta yi kusa da Hajiya,dauke da wayar ta a hannu, ta na dannawa ta na wa Hajiya bayanin da ya zama kamar dukan tsiya take wa Hajiyan.
"To kin ji yanda mukai da Auwal, Hajiya in ba gyaran jikin ba ni dai dan Allah ki bar zancen wasu party har kala hudu, ayi guda daya ma ya isa, ni dayan ma da za a bi nawa da ba za a yi ba, amma saboda kema ki fita kunyar qawayen ki za mu yi, yanzu yaushe Juwairah din za ta zo, na ji ana zancen gyaran jikin ta, irin na sudanis ya na da kyau" (ta na a garin Bauchi ga mai neman kwararriyar mai gyaran jiki irin na sudanis ku min magana)
"Na ji duk bayanan ki, kenan ki na nuhin shi Lawwalin ne yacce ba a yin komi?"
"Eh Hajiya, ko na kira shi ku yi magana, dan..."
"Ahhhhh ni ba na neman tashin hankali da ki ka ganni nan, magana ta qare, ai auren ku ne, in ma cewa kun kai a daura a kai ki haka nan ku kun ka sani, ni na hau sama, in Sultan ya zo ki kire min shi, ba mu da lokacin fita waje dan siyayyar kayan aure, in ma mun ce order za a yi, yanzu yaushe mun ka gama zabe zaben abubuwan da duk muke da burin saye? Ni dai wanga aure naku Allah dai shi hisshe ni kunyar abukkai na"
"Ai Hajiya ki kwantar da hankali ki, domin kuwa ya na da inda zai aje ni, ya ce ko cibi (tsokali) ba shi so a siye, ni kad'ai ya ke so a bashi, kin san hwa gidan da yake a nan shiyyar yake, kuma gida ne mai kyawu daidai misali, dama ni kin san rayuwar qarya bata gaba na"
"Hummmmm in ji me ciyon haqurra, ba ke ji komi daga baki na ba, ballantana ki hwadi mai, na hau sama, Allah dai shi gwadi mana ranar bikin"
"Ameen Hajiya ta"
Sama ta haye ta na ta maganganu qasa qasa, ita kadai ta san me take ji a zuciyar ta, na baqin cikin auren Lawwali amma ba halin bayyanawa, da ace wani na sauraron abinda mutum ke quqqullawa a zuciya, lallai da Hajiya Ikee ta shiga bala'i.
Ko da Sultan ya dawo, ya ji dadi matuqa da ya ga qanwar shi cikin farin ciki, fatan alkhairi ya mata sosai sannan ya je kiran da Hajiya ke masa.
*************************
Lawwali ne ke ta Video call da Mubaraka, sai tsokanar ta yake wai ta girma, ya ga ta na fari, ko bleaching take ne?
"Haba Yah Auwal, mi zai sani bleaching, baqi na mai kyawu na wallah, tau ko ba shi da kyawu ma yanda Allah ya yi ni haka nan zan zauna, sab'a halittar Allah haramun na, ina dai gyara jiki na da abubuwan da muke da su na gida shi na yas-sa ka ga na yi haske, Aunty Fateema ke yi min gyaran jiki, in ta yi,"
"Ohhhh Mubaraka, wanga bayanin kare kai, anya ba bleaching din ki ke ba? Tau ba wannan ba, ke san kuwa maganar aure na ta tashi ni da mutuniyar ki?"
Hamdala ta dinga yi, tare da babbaka dariyar farin ciki,
"Yah Auwal yaushe ne bikin? Kuma yushe za mu taho"
Dan jimmm ya yi, kafin ya gyara zaman shi ya ci serious dan ba ya so ta masa daru,
"Ke gane ko, saboda abubuwan da suka hwaru a baya, shi ne nicce ko za ku zauna ba sai kun...."
Cikin kukan shagwaba ta katse shi,
"Ni dai gaskiya sai na zo, bikin ku ne fa"
"Baraka na ki saurare ni da kyau, zan so a ce ki na nan, rashin ki zai zama kamar bani da dangi ne a wajen, amma ba zan iya sanya rayuwar ki cikin hatsari ba, hatsarin da nake ciki a yanzu ya hi Wanda kin ka sani,ki bani goyon baya, na miki alqawari hatta da hita ta daga gida, sai an miki video kin gani, kwanciyar hankalin ki da zaman ki lahiya ya hiye min komi ga rayuwa ta, dan Allah kar ki min taurin kai"
Cikin hawaye da sanyin murya ta ce,
"Yaushe ne bikin?"
"Asabar din ga me zuwa, yau saura kwana biyu,ki yi hakuri, i am very sorry, in ji ku turawa"
Cikin kama kunnuwan shi duka biyun ya ke bata hakuri, ran ta ya ɓaci , wai a ce sauran kwana biyu bikin shi, sai yau yake fada mata, amma ba komai, za ta girmama maganar shi, wataqila hakan da ya yi shi ne daidai, fatan alkhairi ta dinga musu, ta na murnar yaqe, qasan ran ta kuwa ta na jin ba dad'i , za ai auren Yah Auwal din ta guda ba ita.
Shi kuwa wasa da dariya ya dinga mata dan dauke hankalin ta, ya samu nasara kuwa dan ba su bar video call din ba sai da ya tabbata ta saki ran ta.
Kwantawa ya yi ya na kallon sama, tunanin iyayen shi yake yi, a rayuwa shi dai ba shi da sa'a, wai ace ya na da iyaye a cikin garin Zamfara, amma kamar ba shi da kowa, ba wanda ya ke da kusanci da shi, da zuciyar shi, balle ya ji damuwar shi, ba wanda ya damu da rayuwar shi,tunawa ya yi da sanda ya kai musu maganar auren, kafin ya fita daga gidan ya na dakin shi, ya ji mata na ta shiga ana fita, ana yi wa Lamishi Barka, d'an ta zai auri diyar gwamna, wa ya je ya baza a unguwar sai Allah masani.
Gaba daya basu damu da wai bari a bincika a ga mene ne dalilin yin auren ba, farin cikin su kawai dan su zai auri yar gwamna, ba komai, Allah dai ya kai mu biki lafiya.
Tunani ya dinga yi, na me ya rage a bikin wanda yake haqqin shi ne bai ba? Domin hatta da lefe da ya yi wa Sultana maganar shi, cewa ta yi ba sai ya yi ba, Hajiya Ikee kuwa ta ce bata san zance ba, ba a ɗauke masa lefe ba, sai ya yi, duk abinda ake buqata, dan haka kudin kawai ya tura ta account din Hajiya Ikee, ya ce su sai duk abinda ya kamata, ganin mahaukatan kudin sun rudar da Hajiya Ikee, amma bata yi mamaki ba, duba da wa ya tsaya masa a garin, ba qananan kudi yake samu ba a wajen Gwamna, Hajiya ta dau alqawarin ita zata kula da lefe, to amma ya rasa dalilin da ya sa yake neman dalilin da zai kai shi gidan su Sultana, ya na so ya sanya ta a idanun shi, zuciyar shi na azalzalar shi ta na tunzira shi akan ya je ya gan ta, daya bangaren na zuciyar shi na kwabar shi, bai biye wa daya daga cikin su ba, ko da ya fita ya dauki hanya, bai tsaya a ko ina ba sai gidan su.
Ko gaishe su bai ba, ya tsaya a tsaye ya ciro kudi masu uban yawa daga aljifan jikin shi, ya ajiye wa Lamishi, ya ce gashi nan su samu inda za a musu ɗinkin gaggawa in sun sai tufafin da suke so su sa a bikin, ba ya so su je masa wajen biki a hargitse.
Godiya suka dinga yi kamar za su kwanta, makullin mota ya bawa Jameelu, ya ce ya dakko wasu manyan ledoji a bayan motar, a guje ya fita ya na tsalle, ledoji ne manya masu nauyi Jameelu ya shiga da su, Dan Talo na ta bata rai ba a bashi komai ba.
Lawwali murmushin takaici ya yi, dan duk ya fahimci komai, tura leda daya gaban Dan Talo ya yi, ya ce,
"Sai ka bar bata fuska, ka sanya ranar daurin aure, kuma ka yi wanka dan Allah, kaya duk kyawun su in ba wanka ba sa kyau, Jameelu ga naku nan,ga wannan ku tai ku sai takalma da hulla, bana so ku taho wajen nan kamar almajirrai,"
"Tau Yaya mun gode"
"Kaiii wanga yaro Allah shi qaro bud'i" in ji Dan Talo.
"Addu'ar ku kenan,bud'i dai bud'i dai, to Allah shi bud'a din, ba bu ruwan ku da ta ina bud'in zai taho"
Fatali ya yi da dan karamin kwanon man gyadan da Mai Buruji ta soya, ya bar gidan, cikin takaicin iyayen nashi.
Ko da ya koma unguwar da yake zama, har zai wuce gidan shi, kawai ya tsaya, ya kira Sultana, ta na dauka ya ce,
"Ki shirya ki hito, zamu daukan hoto, ina jiran ki, nan da awa guda"
"Daukan hoto kuma? Na ko aza bai dame ka ba irin wannan abubuwan"
"Za mu yi ne dan Hajiya, ke san wadda taka son ayi komai a bayyane, hoton zai faranta ran ta"
Ta ji dadin yanda ya duba lamarin Hajiyar ta, da gaskiyar shi, hoton zai faranta ranta matuqa.
A gaggauce ta shiga wanka,ta fara shirya wa, dan bata so ta bar shi ya zauna jiran ta.
Shima gida ya wuce, ya samu ya watsa ruwa, ya yi shirin shi tsaf cikin farar shadda mai golden din aiki, ya na daga cikin dinkunan da suka siyo ready made shi da Sultana, a qalla sun siya kaya masu kyau da tsada kusan kala goma goma, a gogon shi na gold ya daura, kuma kalar aikin kayan shi (maza ku sani haramun ne namiji ya sanya agogo gold ko zoben gold sai azurfa).
Takalmin shi ma kalar aikin rigar shi, sai hula fara mai ratsin golden, Masha Allah, ko shi kan shi sai da ya jima gaban madubi ya na kallon kan shi, a fili ya bayyana cewa,
"Lawwali kenan, dan gidan Lamishi da Dan Talo, Yayan Mubaraka, Angon Sultana"
(Aunty Asma'u😆)
Murmushi ya yi, ya dauki turarukan shi ya dinga fesawa a hankali, ta yanda qamshin su ba zai hau kai ba, ya na gamawa ya taje gemun shi da ke qarawa fuskar shi kyau da kwarjini, (Team Gemu🥰)
Sai da ya rufe gidan sannan ya shige motar shi da ya bari a waje.
Ya na zuwa qofar gidan su Sultana Kiran ta na shiga wayar shi, dauka ya yi, ya ce ta fito ya na waje.
Ya na nan zaune a mota ya ga securies guda uku sun bude mata qofar, kamar hadin baki ta fito sanye da doguwar riga golden color, ta na ta walkiya a cikin duhun daren, Lawwali sakin baki ya yi ya na kallon Sultana, anyaa ita ce kuwa?
Sultana ta ji dad'in yanda Lawwali ya shagala da kallon ta, sai yanzu ta ke godewa Hajiya da ta dage sai an kawo wadda zata shirya ta, dan kuwa in ita zata shirya ba zata fito a matsayin amarya ba, dunkunan da a ka kashe makudan kudi aka yi su, a banza za a sanya su ba su yi kyawun da ake so ba.
Da sauri ya fita ya bude mata qofa, ta shiga, ta na murmushi qasa qasa.
Bayan ya zauna kafin ya tada motar,suka kalli juna, a tare suka furta,
"Ka/kin yi kyau"
Dariya suka yi, sannan Lawwali ya tada mota, sai hadadden gidan Hoton da ke cikin garin na Gusau, tun da suka shiga wajen mutane ke kallon su, domin kusan duk amaren da angwayen da suka je wajen dan d'aukan hoto Lawwali da Sultana
Showing 87001 words to 90000 words out of 150481 words
Cikin daure fuska tamau Lawwali ya miqe tsaye, ya na wasa da glass din shi, sannan ya ce,
"Ba na son jira ka hi kowa sanin haka Excellency ,me yasa ka ke bari na yin jira?"
"Lawwali har yanzu ina da tantama akan baka d'iya...."
A zafafe Lawwali ya juya ya kalli Gwamna ya ce,
"Tantama? Tantama hwa kacce, ka na da wani zabi ne da ya wuce ka aura min ita, ko ku na so ko ba ku so,na ga alama kun zaci ba zan aikata abinda na hwadi ba ko? Ka san ni, ka san wane ne ni, ka san mi zan iya da wanda ba zan iya ba, kar ka bari raina shi fi haka ɓaci, abin ba zai mana kyawu ba"
Cikin hura hanci Hajiya Ikee ta ce,
"Yaro yaro ne bai san wuta ba sai ya taka, in ka na da abinda ka ke ganin za ka yi, ka je ka yi, diya ta bata auren dan iska irin ka, lalatacce d'ebabbe"
Abu kamar sihiri, kafin ta rufe labban ta Lawwali ne a gaban ta, ya sa hannun shi guda daya ya shaqe mata wuya, ya sanya bakin bindigar shi cikin bakin ta, jijiyoyin kan shi, da hannayen shi sun fito rudu rudu, idanun nan kamar an watsa masa barkono, leban shi na qasa ya ciza sai da jini ya fito,Gwamna ne ya isa gaban shi ya fara qoqarin kwace Hajiya Ikee da ke fitar da numfashi a wahalce, idanun ta na ta tsiyayar da hawaye, sai miqawa gwamna hannu take, wata tsawa Lawwali ya daka mata, akan ta dena wannan motsi da kukan da take, diffff ta hadiye kukan nata, ido ya fito ya mata gulu gulu.
"Me ki ka ce, yaro bai san wuta ba sai ya taka? Waye yaro? Na ce waye yaro? A duniya akwai lalatattu d'ebabbu Sama da ku ne? Har ni zaki kalla ki wa zagin d'iban albarka, ke ba dan ina da burika masu yawa ba kin isa na bar ki ki kai gobe, (subhaballah kamar ran a hannun shi yake)"
Ba damar magana bindiga na baki, ga wuya ya sha shaqa,
Da qarfi ya wurga ta qasa ta fad'i, a gigice take neman iskar shaqa, tsabar azabar da take ciki, dishi dishi take gani, Gwamna ne ya duqa gaban ta, ya na taimaka mata wajen daidaita numfashin ta.
"Ku na ji na ko? Nan da sati guda nika so a yi auren mu da Sultana, in hakan bata faru ba, ku sani, har cikin dakin ta, zan shiga in dauke ta, domin babu abinda ba zan iya ba akan cikar buri na, kamar yanda kai ma ba abinda baka yi dan cikar burin ka"
"Lawwali d'iya ta ka ke son a yi wa irin wanga aure? Sati guda kamar d'iyar tallaka?"
Da sauri Hajiya Ikee ta ce,
"Kar ka ja mana magana, ka bari kawai a yi nan da sati guda din, kaga Lawwali, ka turo magabatan ka kawai a sa rana a yi komi a gama lahiya"
Murmushi mai kyau Lawwali ya saki, ya dauke qafar shi da ya dora a saman kujerar su, ya duqa gaban Hajiya, Ita kuwa ta yi baya da azama, dan ba ta so ma ya rab'e ta ko kusa, rabon da a dake ta ba zata iya tunawa ba, amma gata da girman ta, ta sha shaqa .
"Yauwa suruka ta, da kyau,bari na tai gida na sanar da iyaye na, gobe za su zo, a gobe nake so a saka rana, duk wanda ya lalata min shiri, zan lalata masa rayuwa, wanan alqawari na ne"
D'aga kai kawai Hajiya take, Gwamna kuwa kallon Lawwali kawai yake, ba komai, zai aurawa Lawwali Sultana, amma zai nuna wa Lawwali mulki gaba yake da dabanci................
*Hummmm kun amince Mulki gaba yake da dabanci?*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 41:
Zaune ya ke a kujerar da ke kallon ta a cikin office din na ta, su na fuskantar juna, hannun ta ya kama guda daya ya riqe a na shi, ya na kallon yanda gyararran farcen ta yake sheqi, cikin sassanyar murya ya ce,
"Ran ki shi dade, ki na ganin za ki iya zama da ni a duk inda na ajiye ki? Domin ba zan taba karbar gida ko wata alfarma da iyayen ki za su bani ba, ke sani Hajiyan ku da kyar ta yarda da auren mu, dan kawai ina diyan tallaka, ina so na yi komai da kuddi na, ina so ki goya min baya akan wannan, za ki iya?"
Tunda ya fara magana take kallon shi, ta gano gaskiyar maganar shi, ta kuma fahimce shi, ta na alfahari da kasancewar shi mijin da za ta aura, ya san yanda zai ya tsaya a matsayin shi a koda yaushe, baya manta tushen shi, sai dai ta na tsoron rayuwar wahala, amma indai da Auwal din ta ne ba komai, ba abinda ba zata iya yi domin shi ba, sai dai in abun sab'on Allah ne, dan haka ta na ji a jikin ta, za ta iya taya shi cika duk wani burin shi, indai su na tare komai zai zo da sauqi da yardar Allah.
Cikin murmushin da ke nuna gaskiyar maganar da take son furtawa, ta d'aga kai, tare da janye hannun ta daga nashi ta ce,
"Na amince, na amince Zan zauna da kai a duk inda ka ajiye ni, duk inda ka sa qafa nan zan aje tawa, ni kai nake so,ba kudin ka ba,zan amfani da tushen ka ne, ba na iyaye na ba, kai nawa ne, ni taka ce"
Godiya ya mata, suka ci gaba da hirar su sama sama, ta na tsara takardun da za a ware tallafi zuwa ga mabuqata.
Bayan ya maida ita gida, suka ga motoci masu numfashi an Parker su a harabar gidan, Sultana na gani ta gane su waye a ciki, juya ido sama ta yi, ta amshe jakar ta a hannun Lawwali da ke mata sai da safe, sallama suka yi ta shiga gida, ta samu Hajiya Ikee a parlour su na hira da qawayen ta sai zuba musu qarya take, akan shaharar Lawwali a kasuwancin qasashen waje, duk da haka bata tsira ba, sai da suka dinga yada mata da baqar magana, akan 'yar ta bata samu auren shugaban qasa ba.
Gaida su Sultana ta yi ta haye sama, ta na matuqar takaicin rayuwar qaryar da mahaifiyar ta ke gudanarwa.
A can parlour kuwa su Hajiya da qawayen ta sun gama tsare tsaren yanda bikin zai kasance, a cikin qawayen ta akwai wadan da sun taba aurar da yara mata, sun yi alqawarin kawo masu gyaran jiki na musamman har gida.
Wani party da duk abinda Hajiya Ikee ta ke da buri ya faru a bikin nan, sun kammala tsara yanda zai kasance, a bangare guda kuma Lawwali ya gama hurewa sultana kunne kar ta yarda a yi wadannan abubuwan, kuma ta yarda da hakan, bata bayyana ma Hajiya abinda suka tsara ba ita da Lawwali sai bayan tafiyar qawayen Hajiya ne Sultana ta sanya riga da skirt na bature, ta daure gashin ta a bayan ta, ta sanya takalmin ta ta sauka qasa, zama ta yi kusa da Hajiya,dauke da wayar ta a hannu, ta na dannawa ta na wa Hajiya bayanin da ya zama kamar dukan tsiya take wa Hajiyan.
"To kin ji yanda mukai da Auwal, Hajiya in ba gyaran jikin ba ni dai dan Allah ki bar zancen wasu party har kala hudu, ayi guda daya ma ya isa, ni dayan ma da za a bi nawa da ba za a yi ba, amma saboda kema ki fita kunyar qawayen ki za mu yi, yanzu yaushe Juwairah din za ta zo, na ji ana zancen gyaran jikin ta, irin na sudanis ya na da kyau" (ta na a garin Bauchi ga mai neman kwararriyar mai gyaran jiki irin na sudanis ku min magana)
"Na ji duk bayanan ki, kenan ki na nuhin shi Lawwalin ne yacce ba a yin komi?"
"Eh Hajiya, ko na kira shi ku yi magana, dan..."
"Ahhhhh ni ba na neman tashin hankali da ki ka ganni nan, magana ta qare, ai auren ku ne, in ma cewa kun kai a daura a kai ki haka nan ku kun ka sani, ni na hau sama, in Sultan ya zo ki kire min shi, ba mu da lokacin fita waje dan siyayyar kayan aure, in ma mun ce order za a yi, yanzu yaushe mun ka gama zabe zaben abubuwan da duk muke da burin saye? Ni dai wanga aure naku Allah dai shi hisshe ni kunyar abukkai na"
"Ai Hajiya ki kwantar da hankali ki, domin kuwa ya na da inda zai aje ni, ya ce ko cibi (tsokali) ba shi so a siye, ni kad'ai ya ke so a bashi, kin san hwa gidan da yake a nan shiyyar yake, kuma gida ne mai kyawu daidai misali, dama ni kin san rayuwar qarya bata gaba na"
"Hummmmm in ji me ciyon haqurra, ba ke ji komi daga baki na ba, ballantana ki hwadi mai, na hau sama, Allah dai shi gwadi mana ranar bikin"
"Ameen Hajiya ta"
Sama ta haye ta na ta maganganu qasa qasa, ita kadai ta san me take ji a zuciyar ta, na baqin cikin auren Lawwali amma ba halin bayyanawa, da ace wani na sauraron abinda mutum ke quqqullawa a zuciya, lallai da Hajiya Ikee ta shiga bala'i.
Ko da Sultan ya dawo, ya ji dadi matuqa da ya ga qanwar shi cikin farin ciki, fatan alkhairi ya mata sosai sannan ya je kiran da Hajiya ke masa.
*************************
Lawwali ne ke ta Video call da Mubaraka, sai tsokanar ta yake wai ta girma, ya ga ta na fari, ko bleaching take ne?
"Haba Yah Auwal, mi zai sani bleaching, baqi na mai kyawu na wallah, tau ko ba shi da kyawu ma yanda Allah ya yi ni haka nan zan zauna, sab'a halittar Allah haramun na, ina dai gyara jiki na da abubuwan da muke da su na gida shi na yas-sa ka ga na yi haske, Aunty Fateema ke yi min gyaran jiki, in ta yi,"
"Ohhhh Mubaraka, wanga bayanin kare kai, anya ba bleaching din ki ke ba? Tau ba wannan ba, ke san kuwa maganar aure na ta tashi ni da mutuniyar ki?"
Hamdala ta dinga yi, tare da babbaka dariyar farin ciki,
"Yah Auwal yaushe ne bikin? Kuma yushe za mu taho"
Dan jimmm ya yi, kafin ya gyara zaman shi ya ci serious dan ba ya so ta masa daru,
"Ke gane ko, saboda abubuwan da suka hwaru a baya, shi ne nicce ko za ku zauna ba sai kun...."
Cikin kukan shagwaba ta katse shi,
"Ni dai gaskiya sai na zo, bikin ku ne fa"
"Baraka na ki saurare ni da kyau, zan so a ce ki na nan, rashin ki zai zama kamar bani da dangi ne a wajen, amma ba zan iya sanya rayuwar ki cikin hatsari ba, hatsarin da nake ciki a yanzu ya hi Wanda kin ka sani,ki bani goyon baya, na miki alqawari hatta da hita ta daga gida, sai an miki video kin gani, kwanciyar hankalin ki da zaman ki lahiya ya hiye min komi ga rayuwa ta, dan Allah kar ki min taurin kai"
Cikin hawaye da sanyin murya ta ce,
"Yaushe ne bikin?"
"Asabar din ga me zuwa, yau saura kwana biyu,ki yi hakuri, i am very sorry, in ji ku turawa"
Cikin kama kunnuwan shi duka biyun ya ke bata hakuri, ran ta ya ɓaci , wai a ce sauran kwana biyu bikin shi, sai yau yake fada mata, amma ba komai, za ta girmama maganar shi, wataqila hakan da ya yi shi ne daidai, fatan alkhairi ta dinga musu, ta na murnar yaqe, qasan ran ta kuwa ta na jin ba dad'i , za ai auren Yah Auwal din ta guda ba ita.
Shi kuwa wasa da dariya ya dinga mata dan dauke hankalin ta, ya samu nasara kuwa dan ba su bar video call din ba sai da ya tabbata ta saki ran ta.
Kwantawa ya yi ya na kallon sama, tunanin iyayen shi yake yi, a rayuwa shi dai ba shi da sa'a, wai ace ya na da iyaye a cikin garin Zamfara, amma kamar ba shi da kowa, ba wanda ya ke da kusanci da shi, da zuciyar shi, balle ya ji damuwar shi, ba wanda ya damu da rayuwar shi,tunawa ya yi da sanda ya kai musu maganar auren, kafin ya fita daga gidan ya na dakin shi, ya ji mata na ta shiga ana fita, ana yi wa Lamishi Barka, d'an ta zai auri diyar gwamna, wa ya je ya baza a unguwar sai Allah masani.
Gaba daya basu damu da wai bari a bincika a ga mene ne dalilin yin auren ba, farin cikin su kawai dan su zai auri yar gwamna, ba komai, Allah dai ya kai mu biki lafiya.
Tunani ya dinga yi, na me ya rage a bikin wanda yake haqqin shi ne bai ba? Domin hatta da lefe da ya yi wa Sultana maganar shi, cewa ta yi ba sai ya yi ba, Hajiya Ikee kuwa ta ce bata san zance ba, ba a ɗauke masa lefe ba, sai ya yi, duk abinda ake buqata, dan haka kudin kawai ya tura ta account din Hajiya Ikee, ya ce su sai duk abinda ya kamata, ganin mahaukatan kudin sun rudar da Hajiya Ikee, amma bata yi mamaki ba, duba da wa ya tsaya masa a garin, ba qananan kudi yake samu ba a wajen Gwamna, Hajiya ta dau alqawarin ita zata kula da lefe, to amma ya rasa dalilin da ya sa yake neman dalilin da zai kai shi gidan su Sultana, ya na so ya sanya ta a idanun shi, zuciyar shi na azalzalar shi ta na tunzira shi akan ya je ya gan ta, daya bangaren na zuciyar shi na kwabar shi, bai biye wa daya daga cikin su ba, ko da ya fita ya dauki hanya, bai tsaya a ko ina ba sai gidan su.
Ko gaishe su bai ba, ya tsaya a tsaye ya ciro kudi masu uban yawa daga aljifan jikin shi, ya ajiye wa Lamishi, ya ce gashi nan su samu inda za a musu ɗinkin gaggawa in sun sai tufafin da suke so su sa a bikin, ba ya so su je masa wajen biki a hargitse.
Godiya suka dinga yi kamar za su kwanta, makullin mota ya bawa Jameelu, ya ce ya dakko wasu manyan ledoji a bayan motar, a guje ya fita ya na tsalle, ledoji ne manya masu nauyi Jameelu ya shiga da su, Dan Talo na ta bata rai ba a bashi komai ba.
Lawwali murmushin takaici ya yi, dan duk ya fahimci komai, tura leda daya gaban Dan Talo ya yi, ya ce,
"Sai ka bar bata fuska, ka sanya ranar daurin aure, kuma ka yi wanka dan Allah, kaya duk kyawun su in ba wanka ba sa kyau, Jameelu ga naku nan,ga wannan ku tai ku sai takalma da hulla, bana so ku taho wajen nan kamar almajirrai,"
"Tau Yaya mun gode"
"Kaiii wanga yaro Allah shi qaro bud'i" in ji Dan Talo.
"Addu'ar ku kenan,bud'i dai bud'i dai, to Allah shi bud'a din, ba bu ruwan ku da ta ina bud'in zai taho"
Fatali ya yi da dan karamin kwanon man gyadan da Mai Buruji ta soya, ya bar gidan, cikin takaicin iyayen nashi.
Ko da ya koma unguwar da yake zama, har zai wuce gidan shi, kawai ya tsaya, ya kira Sultana, ta na dauka ya ce,
"Ki shirya ki hito, zamu daukan hoto, ina jiran ki, nan da awa guda"
"Daukan hoto kuma? Na ko aza bai dame ka ba irin wannan abubuwan"
"Za mu yi ne dan Hajiya, ke san wadda taka son ayi komai a bayyane, hoton zai faranta ran ta"
Ta ji dadin yanda ya duba lamarin Hajiyar ta, da gaskiyar shi, hoton zai faranta ranta matuqa.
A gaggauce ta shiga wanka,ta fara shirya wa, dan bata so ta bar shi ya zauna jiran ta.
Shima gida ya wuce, ya samu ya watsa ruwa, ya yi shirin shi tsaf cikin farar shadda mai golden din aiki, ya na daga cikin dinkunan da suka siyo ready made shi da Sultana, a qalla sun siya kaya masu kyau da tsada kusan kala goma goma, a gogon shi na gold ya daura, kuma kalar aikin kayan shi (maza ku sani haramun ne namiji ya sanya agogo gold ko zoben gold sai azurfa).
Takalmin shi ma kalar aikin rigar shi, sai hula fara mai ratsin golden, Masha Allah, ko shi kan shi sai da ya jima gaban madubi ya na kallon kan shi, a fili ya bayyana cewa,
"Lawwali kenan, dan gidan Lamishi da Dan Talo, Yayan Mubaraka, Angon Sultana"
(Aunty Asma'u😆)
Murmushi ya yi, ya dauki turarukan shi ya dinga fesawa a hankali, ta yanda qamshin su ba zai hau kai ba, ya na gamawa ya taje gemun shi da ke qarawa fuskar shi kyau da kwarjini, (Team Gemu🥰)
Sai da ya rufe gidan sannan ya shige motar shi da ya bari a waje.
Ya na zuwa qofar gidan su Sultana Kiran ta na shiga wayar shi, dauka ya yi, ya ce ta fito ya na waje.
Ya na nan zaune a mota ya ga securies guda uku sun bude mata qofar, kamar hadin baki ta fito sanye da doguwar riga golden color, ta na ta walkiya a cikin duhun daren, Lawwali sakin baki ya yi ya na kallon Sultana, anyaa ita ce kuwa?
Sultana ta ji dad'in yanda Lawwali ya shagala da kallon ta, sai yanzu ta ke godewa Hajiya da ta dage sai an kawo wadda zata shirya ta, dan kuwa in ita zata shirya ba zata fito a matsayin amarya ba, dunkunan da a ka kashe makudan kudi aka yi su, a banza za a sanya su ba su yi kyawun da ake so ba.
Da sauri ya fita ya bude mata qofa, ta shiga, ta na murmushi qasa qasa.
Bayan ya zauna kafin ya tada motar,suka kalli juna, a tare suka furta,
"Ka/kin yi kyau"
Dariya suka yi, sannan Lawwali ya tada mota, sai hadadden gidan Hoton da ke cikin garin na Gusau, tun da suka shiga wajen mutane ke kallon su, domin kusan duk amaren da angwayen da suka je wajen dan d'aukan hoto Lawwali da Sultana
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30 Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51