Yanzu Lawwali ba wata alfarma da zaka yi muna mu gan su?ka duba halin da Daddyn Sultan ke ciki"
Dariya Lawwali ya yi, sanda ya kalli yanda Excellency ke dalalar da yawu, ya kasa magana sai hawaye.
"Ke walle wanga aljannu ka damun shi ba kewar d'iya nai ba, in ku na neman maganin aljannu ku nema, sai an jima"(ke wannan aljanu ke damun shi ba kewar yaran shi ba, in zaku nemi maganin aljanu ku nema se an jima)
Mubaraka ce ta ce,
"Hajiya ki gafarce ni, ni qarama ce, amma ina mai baku shawara, da ku nemo mallammai na kwarai,wanda sunka san Allah, su yi addu'a aljannun su tafi, amma in kuka yi musu yanka, za su dawo su ce wani abu suke so, ko rayuwar wani a cikin ku, Allah shi kiyaye"
Ai Hajiya ikee na jin rayuwar wani a cikin su, ta tsure, kallon Gwamna Halliru ta yi, ta ce,
"Mu na zaman zaman mu da rufin asirin mu ka doko muna siyasa, gashi nan, mu na ganin ibtila'in rayuwa, ba mulkin, ba dukiyar, ba d'iyan mu, ga wani tashin hankalin yanda za mu rabu da aljanun da ka jajibo muna"
Lawwali kam dariya kawai yake kamar wani wawa, cikin surutai da sambatu suka bar Hajiya Ikee, Gwamna Halliru kuwa na kwaranyar da hawaye ta gefen ido.
Sai da suka tsaya Lawwali ya yi siyayya ta kayan kwalama, da duk wani abu da ya san Mubaraka na so, har zai fita daga wajen shopping din bai sai wa Sultana komai ba, sai ya ji ya kasa tafiya, komawa ciki ya yi, ya daukar mata best chocolate din ta, da candy din da ta fi so, sannan ya ga wani turare mai kyau na mata, daukar mata ya yi, ya na murmushi.
Sai da ya biya kudin komai, sanan ya koma mota, Mubaraka na nan zaune, ta na ta tunanin yanda za ta sanya Lawwali ya bar Su sultana Su je su ga iyayen su, Hajiya Ikee ta matuqar bata tausayi.
Ajiye mata ledojin ya yi a cinyar ta, ya koma mazaunin driver ya zauna.
"Barakana ga naki nan, wancan na Sultyna ne, ki bata amma kar ki ce ni ne na bayar a bata,"
"Yah Auwal kenan, ana soooo ana kaiwa kassuwaaa"
Dariya suka yi, sannan ya tada motar dan komawa gida.
Mubaraka ta matsu su koma, dan basu yi sallar azahar ba, ga la'asar ta Kunno Kai.
************************
Hajiyan Hansatu ce ta kira Hansatu, ta ke tambayar ta, tunda Isah ya tafi sun yi waya kuwa? Saboda yau sati d'aya da kwana uku ba labarin Isah ko ta ina, layin shi tun ya na shiga ba a dagawa, yanzu ya ma dena shiga.
Hansatu ta rasa amsar da za ta ba Hajiya, kawai sai ta ce,
"Shi na lahiya qalou Hajiya, kar ki damu, in mun kai waya zan sanar masa ki na so ku gaisa"
"Ahhh ahh basshi d'ai, dama son nikai na ji lahiya shike ko ah ah"
"Shi na lahiya lumui Hajiya, ina Yayah Musa? Shin aunty bata dawo ba har yanzu?"
"Shekaran jiya dai Yayan ki ya aika musu da takardar saki, ya ce ya gaji da iskancin ta,na so na hana shi, na kira na mata magana, ta inda take shiga ba ta nan taka hita ba, wai na bi na qanqame d'a na, na hana su sakewa, ban barin shi ya je wajen ta, ke ki ji hwa?"
"Kayyaa ban ji dad'in rabuwar su ba, Allah shi sa hakan shi ne ya hi alkhairi"
"Ameen, ina wannan me gidan da bai iya cehwane ba?"
"Shi na lahiya, ya ce zai siyo maki haqorin roba ki laqa, tunda na ki ya hwara tsuhwa"
Dariya Hajiya ta yi, suka ci gaba da hira cikin nishadi, ita da yar ta
************************
A kurkuku kuwa, Isah.............
*Sai anjima Inshaa Allahu*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 57:
Isah na can an miqa shi wajen kuliya manta sabo, ba irin bayani da Isah bai yi ba,amma abu ya ci tura, duk iya bincike da shaidu sun nuna koken ta Isah ce,dan haka nan take aka yanke masa hukuncin shekara goma a gidan maza da horo mai tsanani,dan kuwa Saudiya ba kamar Nigeria bace, ba su b'ata lokaci wajen yanke wa duk wani mai laifi hukunci, Isah ya yi kuka, ya yi kuka, ya godewa Allah, ba irin yunquri da bai ba na a bashi dama ya kira gida ba wanda ya bi ta kan shi, haka aka ingiza qeyar shi zuwa kurkuku.
Duk da cewa kurkukun su ba irin namu bane, mai cike da datti,qazanta da rashin abubuwan da mutum zai buqata, amma kurkuku kurkuku ne, Isah ya yi dana sanin zuwan shi Makka, ya yi dana sanin sanin sana'ar saida goro a rayuwar shi.
Tun ya na kuka da qarfi, ya koma yin na zuci, sai dai hawaye da ke kwaranya kamar an bude magudanar ruwa, rayuwar shi tun daga yarinta ya ke tunawa, shi dai gaba d'aya bai da sa'a a rayuwa, bai rabu da iyaye lafiya ba, ga iyalin shi ya baro su na fushi da shi, bai kyautata alaqa da su ba balle su neme shi, yanzu da ace a baya ya na kiran Hansatu da ya zo,ya san da ta ji shi shiru dole za ta neme shi,
"Kaico na, kaicon rayuwa ta ni Isah, yanzu ina zan saka rayuwa ta na ji dad'i, shekara goma ba kwana goma bane ba fa,"
(A haka Isah ya samu rangwame ne, domin kuwa wasu hukuncin kisa ake yanke musu a Saudiya, indai aka kama mutum da miyagun kwayoyi, wasu shekara biyu da bulalai, wasu goma da bulalai)
A ranar ko abinci Isah bai iya kaiwa bakin shi ba, duk ya fad'a ya yi zuru-zuru kamar ya yi shekaru a wajen.
A can gida Nigeria kuwa Hansatu ta d'auki shawarar Hajiyan ta, sun saka yaran a makarantar kud'i, driver guda Yaya Musa ya sama musu da mota, ya je ya kai su, in an tashi ya maida su gida.
Da yamma kuma Hansatu da kan ta za ta raka su Islamiyya, ta kuma gargad'e su kar su kuskura su koma gida ba tare da ta je daukan su ba, su zauna wajen Baba me gadin makarantar har ta je.
A cikin gida kuma ta kama sana'ar had'a sabulan gyaran jiki, dan kuwa ta kware sosai a haɗawa, jikin ta ya yi luwai luwai kamar matar wani hamshaqin.
Ta na yin sabulun tumeric
Sabulun water melon
Sabulun hinna
Sabulun carrot da
Sabulun cucumber.
Sai man kitso mai kyau da gyaran gashi, ta dage sosai wajen bunqasa sana'ar ta, da inganta ta, ta yanda kowa ya gani zai sha'awa, in mutum ya siya ya yi amfani da su, sai ya koma, kafin wani qanqanin lokaci Hansatu ta fara shiga gari itama,ta maida wa yaran ta da sana'ar ta hankali,lokuta da dama, in ba wani abu ne ya faru ba, mantawa take da Isah, ita kan ta ta na mamakin yanda a lokaci daya ya fita a ran ta.
(Duk Mai son man kitso Mai Sanya gashi tsaho da santsi da maganin amosalin Kai da karyewar gashi, ko Kuma Mai son sabulu Mai kyau da zai gyara wa mace fata ta yi kyau da sheqi, ko body scrub ko body oil ta nemi wannan No 09031416423...HAMIBRAH PRODUCTS sune na d'aya wajen maida TSOHUWA YARINYA )
(Haka lamarin yake, duk sanda aka samu namiji azababbe, da ya addabi iyalin shi da mugun hali da d'abi'a, to za a wayi gari duk wata soyayya, biyayya, da tsoron shi da iyalin ke ji ta kau, qiyayya mai qarfi da rashin jin qai za su maye gurbin soyayyar da aka masa a baya, haka in mace ce da bata iya magana ba, kuma bata da kyakkyawan hali da d'abi'a, a hankali take fita a ran miji, duk kauda kan da yake akan ta, kuma da ya fito mata da halayyar shi ta musguna wa shima, sai ka ji mace na fad'in mugu ne, ba shi da dad'in zama)
In sun samu lokaci da weekend sukan kai wa Hajiya ziyara, watarana kuma Hajiya da kan ta take zuwa,su gaisa.
Bayan Hansatu ta tura yaran ta makarantar boko ne, ta yi wanka, ta shirya cikin wani yadi mai kyau, da tsada, Hajiya ce ta musu anko har su Ameenatu, kulle gidan ta yi, ta fad'a na maqotan ta, wato 'Yabbuga, bakin ta dauke da sallama ta shiga.
Shiru ta ji ba wanda ya amsa,
"Shin mutanen gidan ga su na nan kuwa?"
Cikin wata iriyar murya, kamar an shaqe mutum, ko kuma mutum na cin abinci, haka ta ji an amsa mata da,
"Ko ni shigo ciki,na amsa"
Qarasawa ta yi, dan ta san masifar 'Yabbuga, ko ba abinda akai, ta na iya b'ata rai, ta na amsa wa mutum magana d'aya d'aya.
Hansatu ce ta ja ta tsaya, tare da rafka salati,
"Waggaa, mi ya faru hakan na gankin huska ta qabe (kumbura) me ya kwashe maki huska? Shin gobara ta kun ka yi ban sani ba? Ko hatsarin mota?"
Wata harara 'Yabbuga ta samu da kyar ta wurgawa Hansatu, sannan ta lashe dan saman bakin ta da ya haye, ya yi sintim, zama Hansatu ta yi a gefen 'Yabbuga, ta nata watsawa'Yabbugan tambaya, dan ta na son sanin me ya faru da ita, ta ga guiwar ta d'aya a dauje, ga gefen fuskar ta ya dauje shima, baki ya haye, 'Yabbuga dai bata kula ta ba, sai ma wani tuquqin baqin ciki da ke taso mata a rai da take ji, wai me ma ya kawo Hansatu gidan a irin wannan yanayin?
Sallamar Dan Jumma ce ta karad'e tsakar gidan, Dan Jumma da Hansatu sun gaisa ta masa ya me jiki ya amsa, tare da fad'in,
"Jiki dai ga shi nan, mai shi na jin shi,tunda kin gane ta nan, ta dai girme ki, amma kin hita hankali, da sanin ciwon kai, ta je jidali(fad'a) , can gidan Dan Talo, sun ka liqa mata mugun kashi"
A hasale 'Yabbuga ta kalle shi da kumburarran baki, ta ce,
"Wai shin uban wa yacce kashi an ka ban? Wacce ma kashi an ka ban eyee?"
"Tau sanda kin ka yi aniyar tahiya yin hwada(fad'a) akan atanhwar (atampa) da ko dubu uku ba a siye ta ba ban hana miki zuwa ba? Nan nan na dinga baki hankuri, zaman tare ba a haka nan, kema su na kyautata maki, kin ka ce ba ki iya hankuri sai sun biya, ki ka tai, kuma ki ka dawo a haka, bani cewa liqa miki kashin wahala an ka yi?"
"Banga wahala ba, sai dai ka gan ta nan bisa kan ka, ba wadda ta isa liqa min kashin wahala duk shiyyar nan balle gidan Dan Talo, bai auri matar da zata liqan kashi ba, nace bai auri matar da zata ban kashi ba,"
"To in ba kashi sun ka baki ba mi na na ya hwaru?"
Cikin bata rai ta labarta musu duk abinda ya faru, Hansatu da Dan Jummaa kasa riqe dariyar su suka yi, sai da suka dara sosai, sannan Dan Jummaa ya ce,
"Ko da na ji, ashe ke da giinaa (gini) kin kai hwada tak-kashe ki qas, (ashe ke da gini ki kai fada ta kayar da ke qasa) kuma ke da d'an ki menene na gudu har da haure gini? Inda kin samu karaya hwa?"
"Walle gwanda na samu karaya a gini, da ace yaron nan mai baqar zucciya ya kammin, na zama abar kwatance ga shiyya,iyayen shi ma ba barin su ya yi ba balle ni"
Dariya kam ranar Hansatu ta yi ta har da hawaye, daga qarshe ta zari dubu daya ta bawa 'Yabbuga ta ce ta sai madara, dan kuwa bata ga ta inda abinci ze shiga bakin nan ba, ba tare da an ci azaba ba, Godiya ta dinga yi kuwa, ta na so ta yi murmushi ba hali.
Hansatu bakin titi ta je, ta sai musu kayan miya da naman miya, ta koma gida, dan d'ora girki, kafin yara su koma gida.
************************
Sultana na zaune a bakin qofar dakin su, ita da Sultan su na hira, ta sanar da shi abinda Lawwali ya ce, na hana su zuwa ganin Daddyn su, bai b'ata rai ba, bai kuma nuna damuwa ba, ya ce kar ta damu, duk sanda ya bar su za su je ne, hira suke sosai akan abubuwan da suka faru a baya, suka ga motar Lawwali ta nufi wajen da suke aje motoci, gaba dayan su hankalin su ya tattara ya koma kan masu fitowa daga motar, Sultan na ta kallon mubaraka, sultana kuwa idon ta na kan gwarzon mijin nata.
Lawwali na ta wani had'e fuska, shi a dole kar Sultana ta ce ya sakko daga fushin da yake da ita, gaisawa suka yi sama sama da Sultan ya shige daki, Mubaraka na qunshe dariya, cike da murmishi ta miqa wa Sultana ledar ta na kallon idanun ta, dan ganin kalar murnar da za ta yi, in ta ga me ke ciki, Sultan kuwa ita ya ke kallo, ya na murmusawa, yana yin ta ba qaramin tafiya da shi ya yi ba.
Taheer ne tafe zuwa wajen su Mubarakan, dan tunda ya ji dawowar su ya tsaya ya ɗan gaggyara shi ma a gan shi fess, tun daga nesa ya hango irin kallon da Sultan ke yi ma Mubaraka, kwafa ya yi, a ran shi ya ce,
'kaii wanga ba dan yanzu mun aje harka ba, ai da tuni na sheqe shege, ji wani kallo awa baqin maye'
Sake kwafa ya yi, sannan ya d'aga qafa dan zuwa wajen nasu.
"Mubaraka wannan fa?"
Dan duqawa Mubarakan ta yi saitin kunnen Sultana, ta mata rad'a, ita kuwa wani irin annuri ke fita daga fuskar ta, ta na fitar da siririyar dariya,mai dad'in sauti,
"Mi na na kuke fadi ba a so na ji? Mubaraka ba kyau fa abinda kin ka yi yanzu, mu na tare ki ware ta ku yi magana a gabana ban ji ba"
Dariya ta yi, sannan tai qasa da murya ta ce,
"Ba na so yaya ya ji mi na ce, matso ka jiya"
Matsawa ya yi, sannan ta kai bakin ta kunnen shi za ta masa rad'a Taheer ya katse su da fadin,
"Mi na na haka? Ke Mubaraka me ke nan?"
Ba tare da ta kula da yanda ya b'ata rai ba, ta ce,
"Wata magana zan fada masa, bana so yaya ya ji"
"To muje ta can ki fada masa, amma me ye na masa rad'a ga kunne?"
Sultan kuwa ba abinda yake banda dariya, shi gaba daya Taheer dariya yake bashi, ko ta ina Sultan ya masa zarra, amma ba laifi wajen gwadawa, wataqila ta zabi Taheer din shi ta bar shi.
"Basshi kawai Sulty Baby za ta hwada min, ba dai ke sanar da ita abinda za ki fadan ba?"
Daga kai Mubaraka ta yi, ta na dariya,
"Tau ya yi, sai an jiman ku"
Sallama ya miqa wa Taheer hannu su yi, kamar kar ya miqa hannun, amma ya miqa, ya kuwa matse hannun Sultan din da qarfi,Sultan ya ji matsar da aka masa, amma sai ya yi kamar bai ji ba, sai da Taheer ya gaji dan kan shi, sannan ya sake masa hannu, Sultan ya wuce ya bar Taheer da Mubaraka a wajen, anan ne Mubarakan ke bashi labarin zuwan su wajen No 1.
Sultana kuwa ta shiga d'aki ta tarar da Lawwali na ta kaiwa da kawowa, daga shi sai dogon wandon kayan da ya sanya, jikin shi babu ko vest, ajiye ledar ta yi, ta zagaya ta bayan shi, ta zira hannayen ta ta rungume shi, idanun shi ya kulle, dan jin yanda take taba shi a hankali, kan ta ta kwantar a bayan nashi, cikin murya mai sanyi da sace zuciyar mai sauraro Sultana ta ce,
"Auwal ka yi hankuri, ka yahe min duk abinda ka ke tunanin na yi maka shi, ba haka bane a raina,ka sani a duk duniyar nan ban taba son kowa ba, bayan kai, kai ne namiji me matuqar mahimmanci ga rayuwa ta, kai ne dalilin da ya sa na aikata komai,ban yi dan Daddy ba, dan Allah ka min murmushin ka mai kyawun nan ko zan ji sanyi ga rayuwa ta,bana so na wayi gari ban ga hwarin ciki ga huskar ka ba, ina so ka ci gaba da kasancewa cikin walwala da annashuwa, da annuri,ina yi wa Allah godiya da ya bani kai a matsayin miji na,kai ne rayuwa ta, kai ne komai nawa,kai ke bawa rayuwa ta farin ciki, jin dad'i da nishad'i, ina murmushi ne kawai in ka na murmushi, zan shiga damuwa da tashin hankali in ka dena fara'a,soyayyar ka da kulawar ka, su ne kawai abinda suke riqe da ni a yanzu, inna rasa su, zan rasa rayuwa ta ne gaba daya"
Hawaye ke zuba a idanun ta, kalaman ta sun yi gini mai qarko a zuciyar Lawwali, cikin sanyi ya juya, ya daga fuskar ta, ya sanya hannun shi duka biyun ya na share mata hawaye, bude idon ta tayi, ta kalle shi, gani ta yi ya na murmushi, nan da nan kuwa ta saki na ta, daukan ta ya yi cak, ya nufi gadon su da ita ya ajiye ta a bakin gadon ya durqusa a gaban ta, ya na wasa da hannun ta.
"Sultyna na fahimce ki, amma abinda na ke so ki gane shi ne, na yi wa qasa barna,ni babban mai lehi ne,ki na sane da cewa gwamnatin tarayya na nan ta baza jami'an tsaro a nemo mu duk inda muke, da ba dan mahaifin ki na da hannu a lamarin ga ba, kuma ba wanda ya sanni sai amintattun jami'an tsaro, tabbas da tuni an kama mu, to su ma su na so asirin su ya ruhu, shi ya sa ba su hwadi ba, amma tunda ni Allah ya sa na fahimci gaskiya yanzu ba ki ganin ya dace ace na kai kai na ga hukuma?"
"Auwal ka hini sanin halayen shugabannin nan namu, su kan su ba gaskiya ne da su ba, da ace qasa ce da ake tsaida Shari'a irin ta addinin Musulunci, tabbas da ni da kai na zan raka ka dan ka wanke kan ka, duniya da lahira, amma a irin wannan qasa , wannan yanayi, indai ka san ka yi lehi, to ka nemi yahiya wajen Allah, ka tuba iyakar tuba shi kenan, in Allah ya yahe maka shi kenan"
Dora kan shi ya yi a cinyar ta, ya zauna sosai a wajen, ya yi shuru ya na nazarin maganganun ta.
Fata take ta
Showing 123001 words to 126000 words out of 150481 words
Dariya Lawwali ya yi, sanda ya kalli yanda Excellency ke dalalar da yawu, ya kasa magana sai hawaye.
"Ke walle wanga aljannu ka damun shi ba kewar d'iya nai ba, in ku na neman maganin aljannu ku nema, sai an jima"(ke wannan aljanu ke damun shi ba kewar yaran shi ba, in zaku nemi maganin aljanu ku nema se an jima)
Mubaraka ce ta ce,
"Hajiya ki gafarce ni, ni qarama ce, amma ina mai baku shawara, da ku nemo mallammai na kwarai,wanda sunka san Allah, su yi addu'a aljannun su tafi, amma in kuka yi musu yanka, za su dawo su ce wani abu suke so, ko rayuwar wani a cikin ku, Allah shi kiyaye"
Ai Hajiya ikee na jin rayuwar wani a cikin su, ta tsure, kallon Gwamna Halliru ta yi, ta ce,
"Mu na zaman zaman mu da rufin asirin mu ka doko muna siyasa, gashi nan, mu na ganin ibtila'in rayuwa, ba mulkin, ba dukiyar, ba d'iyan mu, ga wani tashin hankalin yanda za mu rabu da aljanun da ka jajibo muna"
Lawwali kam dariya kawai yake kamar wani wawa, cikin surutai da sambatu suka bar Hajiya Ikee, Gwamna Halliru kuwa na kwaranyar da hawaye ta gefen ido.
Sai da suka tsaya Lawwali ya yi siyayya ta kayan kwalama, da duk wani abu da ya san Mubaraka na so, har zai fita daga wajen shopping din bai sai wa Sultana komai ba, sai ya ji ya kasa tafiya, komawa ciki ya yi, ya daukar mata best chocolate din ta, da candy din da ta fi so, sannan ya ga wani turare mai kyau na mata, daukar mata ya yi, ya na murmushi.
Sai da ya biya kudin komai, sanan ya koma mota, Mubaraka na nan zaune, ta na ta tunanin yanda za ta sanya Lawwali ya bar Su sultana Su je su ga iyayen su, Hajiya Ikee ta matuqar bata tausayi.
Ajiye mata ledojin ya yi a cinyar ta, ya koma mazaunin driver ya zauna.
"Barakana ga naki nan, wancan na Sultyna ne, ki bata amma kar ki ce ni ne na bayar a bata,"
"Yah Auwal kenan, ana soooo ana kaiwa kassuwaaa"
Dariya suka yi, sannan ya tada motar dan komawa gida.
Mubaraka ta matsu su koma, dan basu yi sallar azahar ba, ga la'asar ta Kunno Kai.
************************
Hajiyan Hansatu ce ta kira Hansatu, ta ke tambayar ta, tunda Isah ya tafi sun yi waya kuwa? Saboda yau sati d'aya da kwana uku ba labarin Isah ko ta ina, layin shi tun ya na shiga ba a dagawa, yanzu ya ma dena shiga.
Hansatu ta rasa amsar da za ta ba Hajiya, kawai sai ta ce,
"Shi na lahiya qalou Hajiya, kar ki damu, in mun kai waya zan sanar masa ki na so ku gaisa"
"Ahhh ahh basshi d'ai, dama son nikai na ji lahiya shike ko ah ah"
"Shi na lahiya lumui Hajiya, ina Yayah Musa? Shin aunty bata dawo ba har yanzu?"
"Shekaran jiya dai Yayan ki ya aika musu da takardar saki, ya ce ya gaji da iskancin ta,na so na hana shi, na kira na mata magana, ta inda take shiga ba ta nan taka hita ba, wai na bi na qanqame d'a na, na hana su sakewa, ban barin shi ya je wajen ta, ke ki ji hwa?"
"Kayyaa ban ji dad'in rabuwar su ba, Allah shi sa hakan shi ne ya hi alkhairi"
"Ameen, ina wannan me gidan da bai iya cehwane ba?"
"Shi na lahiya, ya ce zai siyo maki haqorin roba ki laqa, tunda na ki ya hwara tsuhwa"
Dariya Hajiya ta yi, suka ci gaba da hira cikin nishadi, ita da yar ta
************************
A kurkuku kuwa, Isah.............
*Sai anjima Inshaa Allahu*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 57:
Isah na can an miqa shi wajen kuliya manta sabo, ba irin bayani da Isah bai yi ba,amma abu ya ci tura, duk iya bincike da shaidu sun nuna koken ta Isah ce,dan haka nan take aka yanke masa hukuncin shekara goma a gidan maza da horo mai tsanani,dan kuwa Saudiya ba kamar Nigeria bace, ba su b'ata lokaci wajen yanke wa duk wani mai laifi hukunci, Isah ya yi kuka, ya yi kuka, ya godewa Allah, ba irin yunquri da bai ba na a bashi dama ya kira gida ba wanda ya bi ta kan shi, haka aka ingiza qeyar shi zuwa kurkuku.
Duk da cewa kurkukun su ba irin namu bane, mai cike da datti,qazanta da rashin abubuwan da mutum zai buqata, amma kurkuku kurkuku ne, Isah ya yi dana sanin zuwan shi Makka, ya yi dana sanin sanin sana'ar saida goro a rayuwar shi.
Tun ya na kuka da qarfi, ya koma yin na zuci, sai dai hawaye da ke kwaranya kamar an bude magudanar ruwa, rayuwar shi tun daga yarinta ya ke tunawa, shi dai gaba d'aya bai da sa'a a rayuwa, bai rabu da iyaye lafiya ba, ga iyalin shi ya baro su na fushi da shi, bai kyautata alaqa da su ba balle su neme shi, yanzu da ace a baya ya na kiran Hansatu da ya zo,ya san da ta ji shi shiru dole za ta neme shi,
"Kaico na, kaicon rayuwa ta ni Isah, yanzu ina zan saka rayuwa ta na ji dad'i, shekara goma ba kwana goma bane ba fa,"
(A haka Isah ya samu rangwame ne, domin kuwa wasu hukuncin kisa ake yanke musu a Saudiya, indai aka kama mutum da miyagun kwayoyi, wasu shekara biyu da bulalai, wasu goma da bulalai)
A ranar ko abinci Isah bai iya kaiwa bakin shi ba, duk ya fad'a ya yi zuru-zuru kamar ya yi shekaru a wajen.
A can gida Nigeria kuwa Hansatu ta d'auki shawarar Hajiyan ta, sun saka yaran a makarantar kud'i, driver guda Yaya Musa ya sama musu da mota, ya je ya kai su, in an tashi ya maida su gida.
Da yamma kuma Hansatu da kan ta za ta raka su Islamiyya, ta kuma gargad'e su kar su kuskura su koma gida ba tare da ta je daukan su ba, su zauna wajen Baba me gadin makarantar har ta je.
A cikin gida kuma ta kama sana'ar had'a sabulan gyaran jiki, dan kuwa ta kware sosai a haɗawa, jikin ta ya yi luwai luwai kamar matar wani hamshaqin.
Ta na yin sabulun tumeric
Sabulun water melon
Sabulun hinna
Sabulun carrot da
Sabulun cucumber.
Sai man kitso mai kyau da gyaran gashi, ta dage sosai wajen bunqasa sana'ar ta, da inganta ta, ta yanda kowa ya gani zai sha'awa, in mutum ya siya ya yi amfani da su, sai ya koma, kafin wani qanqanin lokaci Hansatu ta fara shiga gari itama,ta maida wa yaran ta da sana'ar ta hankali,lokuta da dama, in ba wani abu ne ya faru ba, mantawa take da Isah, ita kan ta ta na mamakin yanda a lokaci daya ya fita a ran ta.
(Duk Mai son man kitso Mai Sanya gashi tsaho da santsi da maganin amosalin Kai da karyewar gashi, ko Kuma Mai son sabulu Mai kyau da zai gyara wa mace fata ta yi kyau da sheqi, ko body scrub ko body oil ta nemi wannan No 09031416423...HAMIBRAH PRODUCTS sune na d'aya wajen maida TSOHUWA YARINYA )
(Haka lamarin yake, duk sanda aka samu namiji azababbe, da ya addabi iyalin shi da mugun hali da d'abi'a, to za a wayi gari duk wata soyayya, biyayya, da tsoron shi da iyalin ke ji ta kau, qiyayya mai qarfi da rashin jin qai za su maye gurbin soyayyar da aka masa a baya, haka in mace ce da bata iya magana ba, kuma bata da kyakkyawan hali da d'abi'a, a hankali take fita a ran miji, duk kauda kan da yake akan ta, kuma da ya fito mata da halayyar shi ta musguna wa shima, sai ka ji mace na fad'in mugu ne, ba shi da dad'in zama)
In sun samu lokaci da weekend sukan kai wa Hajiya ziyara, watarana kuma Hajiya da kan ta take zuwa,su gaisa.
Bayan Hansatu ta tura yaran ta makarantar boko ne, ta yi wanka, ta shirya cikin wani yadi mai kyau, da tsada, Hajiya ce ta musu anko har su Ameenatu, kulle gidan ta yi, ta fad'a na maqotan ta, wato 'Yabbuga, bakin ta dauke da sallama ta shiga.
Shiru ta ji ba wanda ya amsa,
"Shin mutanen gidan ga su na nan kuwa?"
Cikin wata iriyar murya, kamar an shaqe mutum, ko kuma mutum na cin abinci, haka ta ji an amsa mata da,
"Ko ni shigo ciki,na amsa"
Qarasawa ta yi, dan ta san masifar 'Yabbuga, ko ba abinda akai, ta na iya b'ata rai, ta na amsa wa mutum magana d'aya d'aya.
Hansatu ce ta ja ta tsaya, tare da rafka salati,
"Waggaa, mi ya faru hakan na gankin huska ta qabe (kumbura) me ya kwashe maki huska? Shin gobara ta kun ka yi ban sani ba? Ko hatsarin mota?"
Wata harara 'Yabbuga ta samu da kyar ta wurgawa Hansatu, sannan ta lashe dan saman bakin ta da ya haye, ya yi sintim, zama Hansatu ta yi a gefen 'Yabbuga, ta nata watsawa'Yabbugan tambaya, dan ta na son sanin me ya faru da ita, ta ga guiwar ta d'aya a dauje, ga gefen fuskar ta ya dauje shima, baki ya haye, 'Yabbuga dai bata kula ta ba, sai ma wani tuquqin baqin ciki da ke taso mata a rai da take ji, wai me ma ya kawo Hansatu gidan a irin wannan yanayin?
Sallamar Dan Jumma ce ta karad'e tsakar gidan, Dan Jumma da Hansatu sun gaisa ta masa ya me jiki ya amsa, tare da fad'in,
"Jiki dai ga shi nan, mai shi na jin shi,tunda kin gane ta nan, ta dai girme ki, amma kin hita hankali, da sanin ciwon kai, ta je jidali(fad'a) , can gidan Dan Talo, sun ka liqa mata mugun kashi"
A hasale 'Yabbuga ta kalle shi da kumburarran baki, ta ce,
"Wai shin uban wa yacce kashi an ka ban? Wacce ma kashi an ka ban eyee?"
"Tau sanda kin ka yi aniyar tahiya yin hwada(fad'a) akan atanhwar (atampa) da ko dubu uku ba a siye ta ba ban hana miki zuwa ba? Nan nan na dinga baki hankuri, zaman tare ba a haka nan, kema su na kyautata maki, kin ka ce ba ki iya hankuri sai sun biya, ki ka tai, kuma ki ka dawo a haka, bani cewa liqa miki kashin wahala an ka yi?"
"Banga wahala ba, sai dai ka gan ta nan bisa kan ka, ba wadda ta isa liqa min kashin wahala duk shiyyar nan balle gidan Dan Talo, bai auri matar da zata liqan kashi ba, nace bai auri matar da zata ban kashi ba,"
"To in ba kashi sun ka baki ba mi na na ya hwaru?"
Cikin bata rai ta labarta musu duk abinda ya faru, Hansatu da Dan Jummaa kasa riqe dariyar su suka yi, sai da suka dara sosai, sannan Dan Jummaa ya ce,
"Ko da na ji, ashe ke da giinaa (gini) kin kai hwada tak-kashe ki qas, (ashe ke da gini ki kai fada ta kayar da ke qasa) kuma ke da d'an ki menene na gudu har da haure gini? Inda kin samu karaya hwa?"
"Walle gwanda na samu karaya a gini, da ace yaron nan mai baqar zucciya ya kammin, na zama abar kwatance ga shiyya,iyayen shi ma ba barin su ya yi ba balle ni"
Dariya kam ranar Hansatu ta yi ta har da hawaye, daga qarshe ta zari dubu daya ta bawa 'Yabbuga ta ce ta sai madara, dan kuwa bata ga ta inda abinci ze shiga bakin nan ba, ba tare da an ci azaba ba, Godiya ta dinga yi kuwa, ta na so ta yi murmushi ba hali.
Hansatu bakin titi ta je, ta sai musu kayan miya da naman miya, ta koma gida, dan d'ora girki, kafin yara su koma gida.
************************
Sultana na zaune a bakin qofar dakin su, ita da Sultan su na hira, ta sanar da shi abinda Lawwali ya ce, na hana su zuwa ganin Daddyn su, bai b'ata rai ba, bai kuma nuna damuwa ba, ya ce kar ta damu, duk sanda ya bar su za su je ne, hira suke sosai akan abubuwan da suka faru a baya, suka ga motar Lawwali ta nufi wajen da suke aje motoci, gaba dayan su hankalin su ya tattara ya koma kan masu fitowa daga motar, Sultan na ta kallon mubaraka, sultana kuwa idon ta na kan gwarzon mijin nata.
Lawwali na ta wani had'e fuska, shi a dole kar Sultana ta ce ya sakko daga fushin da yake da ita, gaisawa suka yi sama sama da Sultan ya shige daki, Mubaraka na qunshe dariya, cike da murmishi ta miqa wa Sultana ledar ta na kallon idanun ta, dan ganin kalar murnar da za ta yi, in ta ga me ke ciki, Sultan kuwa ita ya ke kallo, ya na murmusawa, yana yin ta ba qaramin tafiya da shi ya yi ba.
Taheer ne tafe zuwa wajen su Mubarakan, dan tunda ya ji dawowar su ya tsaya ya ɗan gaggyara shi ma a gan shi fess, tun daga nesa ya hango irin kallon da Sultan ke yi ma Mubaraka, kwafa ya yi, a ran shi ya ce,
'kaii wanga ba dan yanzu mun aje harka ba, ai da tuni na sheqe shege, ji wani kallo awa baqin maye'
Sake kwafa ya yi, sannan ya d'aga qafa dan zuwa wajen nasu.
"Mubaraka wannan fa?"
Dan duqawa Mubarakan ta yi saitin kunnen Sultana, ta mata rad'a, ita kuwa wani irin annuri ke fita daga fuskar ta, ta na fitar da siririyar dariya,mai dad'in sauti,
"Mi na na kuke fadi ba a so na ji? Mubaraka ba kyau fa abinda kin ka yi yanzu, mu na tare ki ware ta ku yi magana a gabana ban ji ba"
Dariya ta yi, sannan tai qasa da murya ta ce,
"Ba na so yaya ya ji mi na ce, matso ka jiya"
Matsawa ya yi, sannan ta kai bakin ta kunnen shi za ta masa rad'a Taheer ya katse su da fadin,
"Mi na na haka? Ke Mubaraka me ke nan?"
Ba tare da ta kula da yanda ya b'ata rai ba, ta ce,
"Wata magana zan fada masa, bana so yaya ya ji"
"To muje ta can ki fada masa, amma me ye na masa rad'a ga kunne?"
Sultan kuwa ba abinda yake banda dariya, shi gaba daya Taheer dariya yake bashi, ko ta ina Sultan ya masa zarra, amma ba laifi wajen gwadawa, wataqila ta zabi Taheer din shi ta bar shi.
"Basshi kawai Sulty Baby za ta hwada min, ba dai ke sanar da ita abinda za ki fadan ba?"
Daga kai Mubaraka ta yi, ta na dariya,
"Tau ya yi, sai an jiman ku"
Sallama ya miqa wa Taheer hannu su yi, kamar kar ya miqa hannun, amma ya miqa, ya kuwa matse hannun Sultan din da qarfi,Sultan ya ji matsar da aka masa, amma sai ya yi kamar bai ji ba, sai da Taheer ya gaji dan kan shi, sannan ya sake masa hannu, Sultan ya wuce ya bar Taheer da Mubaraka a wajen, anan ne Mubarakan ke bashi labarin zuwan su wajen No 1.
Sultana kuwa ta shiga d'aki ta tarar da Lawwali na ta kaiwa da kawowa, daga shi sai dogon wandon kayan da ya sanya, jikin shi babu ko vest, ajiye ledar ta yi, ta zagaya ta bayan shi, ta zira hannayen ta ta rungume shi, idanun shi ya kulle, dan jin yanda take taba shi a hankali, kan ta ta kwantar a bayan nashi, cikin murya mai sanyi da sace zuciyar mai sauraro Sultana ta ce,
"Auwal ka yi hankuri, ka yahe min duk abinda ka ke tunanin na yi maka shi, ba haka bane a raina,ka sani a duk duniyar nan ban taba son kowa ba, bayan kai, kai ne namiji me matuqar mahimmanci ga rayuwa ta, kai ne dalilin da ya sa na aikata komai,ban yi dan Daddy ba, dan Allah ka min murmushin ka mai kyawun nan ko zan ji sanyi ga rayuwa ta,bana so na wayi gari ban ga hwarin ciki ga huskar ka ba, ina so ka ci gaba da kasancewa cikin walwala da annashuwa, da annuri,ina yi wa Allah godiya da ya bani kai a matsayin miji na,kai ne rayuwa ta, kai ne komai nawa,kai ke bawa rayuwa ta farin ciki, jin dad'i da nishad'i, ina murmushi ne kawai in ka na murmushi, zan shiga damuwa da tashin hankali in ka dena fara'a,soyayyar ka da kulawar ka, su ne kawai abinda suke riqe da ni a yanzu, inna rasa su, zan rasa rayuwa ta ne gaba daya"
Hawaye ke zuba a idanun ta, kalaman ta sun yi gini mai qarko a zuciyar Lawwali, cikin sanyi ya juya, ya daga fuskar ta, ya sanya hannun shi duka biyun ya na share mata hawaye, bude idon ta tayi, ta kalle shi, gani ta yi ya na murmushi, nan da nan kuwa ta saki na ta, daukan ta ya yi cak, ya nufi gadon su da ita ya ajiye ta a bakin gadon ya durqusa a gaban ta, ya na wasa da hannun ta.
"Sultyna na fahimce ki, amma abinda na ke so ki gane shi ne, na yi wa qasa barna,ni babban mai lehi ne,ki na sane da cewa gwamnatin tarayya na nan ta baza jami'an tsaro a nemo mu duk inda muke, da ba dan mahaifin ki na da hannu a lamarin ga ba, kuma ba wanda ya sanni sai amintattun jami'an tsaro, tabbas da tuni an kama mu, to su ma su na so asirin su ya ruhu, shi ya sa ba su hwadi ba, amma tunda ni Allah ya sa na fahimci gaskiya yanzu ba ki ganin ya dace ace na kai kai na ga hukuma?"
"Auwal ka hini sanin halayen shugabannin nan namu, su kan su ba gaskiya ne da su ba, da ace qasa ce da ake tsaida Shari'a irin ta addinin Musulunci, tabbas da ni da kai na zan raka ka dan ka wanke kan ka, duniya da lahira, amma a irin wannan qasa , wannan yanayi, indai ka san ka yi lehi, to ka nemi yahiya wajen Allah, ka tuba iyakar tuba shi kenan, in Allah ya yahe maka shi kenan"
Dora kan shi ya yi a cinyar ta, ya zauna sosai a wajen, ya yi shuru ya na nazarin maganganun ta.
Fata take ta
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42 Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51