Hajiyar Hansatu rabon ta da fitowa farfajiyar gidan haka ta manta, Hansatu na ta tuna yarintar ta, zaune suke a saman kujeru na qarfe masu matuqar kyau, gaban su table ne an aje fruits da abin sha, su na ta hira a tsakanin su, wanda ya san Hansatu sati Uku da suka wuce ya gan ta yanzu ba zai gane ta ba, ta ciko ta murmure, ga wani haske da ta yi, in ta saka riga da skirt sai ta cike su famm, ban taba zaton hansatu na da shape haka ba sai yanzu.
Hajiya ce ta kalle ta ta ce,
"Gaskiya ya kamata a sauya maki waya, yanzu da yar wayar nan ta zamani ake hira da miji, sai ku yi chatting din ku kamar ku na tare, haka naga Yayan ki na yi da waccan maras kunyar da ta qi dawowa, amma fa soyayya a waya kamar Juliet,"
"Hajiya wai mi an kai mata ne haka?"
"Wannan fa baki gane alqiblar ta, dan yanzu ko an ce mi yayi mata bata hwadi, ta na can qasar waje, da alama can taka so su koma da zama, tunda can ta yi rayuwar ta, ni kuwa ba me d'auke min yaro shi tai wata uwa duniya"
"Ohhh amma ko bata kyauta ba gaskiya, ai mace hankuri aka santa da shi a gidan miji, ba irin wanga hali ba"
"Haka ne, ita kam sam bata san wannan ba, komi so takai ayi yanda taka so, ba ko shi yiwa,"
"Allah to ya shirya ta, ya sa ta dawo su ci gaba da zaman su lahiya,"
"Ameen dai"
Su na tsaka da hira Hajiya ta dauki waya, ta kira Yayan Hansatu, tace ya aiko mata da waya mai kyau, kafin Hansatu ta wuce, amsawa ya yi, da toh, sanan suka yi sallama.
Hansatu bata koma gida ba kuwa sai da dalleliyar waya mai kyau, ba ta wani murna da wayar kawai dai ta nuna ta na murna ne, domin kuwa wanda ake mata kwadayin su yi hirar da shi, tunda ya tafi sai dai taji labari wajen Hajiya sun yi waya, amma baya kiran ta, balle ta samu No shi, kuma ita ba zata iya tambayar hajiyar ta No isah ba.
Ko a mota ajiye kwalin wayar kawai ta yi a cinyar ta ta na tunani, ga dai shi ya tafi, kuma ya fadawa Hajiya kasuwancin goro yayi albarka, amma ko sisi bai masu aike ba, bata san ranar dawowar shi ba.
A qofar gidan su motar ta tsaya, fitowa suka yi ita da yaran, kowa ya gan su ya ga jikokin masu azziqi, hatta da takalmin su yanzu mai tsada suke sakawa.
Ko kallon majalisar su 'yabbuga bata yi ba, ballantana ta ga yanda suka sanya mata ido su na gulmar ta.
Sallama ta yi da driver suka shige gida.
Can majalisar su Lamishi kuwa banda gulmar su ba abinda suka ke.
"Hummmm wagga ai ni zan baki labarin Hansatu ta sauya, bari dai, ai za su koma yar gidan jiya ne, ta na zuwa roqon abu zan mata kaca-kaca, yanzu ta koyi walaqanci,ko kallo bamu ishe ta ba,dan ta hwara daura suhwa, da holan, walle ta na barin shi"
"Ohhh ke kuwa me ya sa kin ka ce haka? Ai ba kin mata hwatan komawa gidan jiya ba, indai ta sha wahala yanda kun ka ce"
'Yabbuga ce ta kalli Asshibi a sheqe ta ce,
"Na hwadi, na ce na hwadi baki ganin wani kallon walaqanci da takai wa mutane?"
"Ai kuwa ko kallon wajen ga ma bata yi ba"
"Tauuu PA din Hansatu, ko zuwa zaki ki hwadi mata mi nicce?"
Lamishi da ta zabga tagumi ta na tunanin shin duniya ina Mubaraka ta shiga ne, ta ce,
"Dan Allah ku bar yi mana hayaniyar ga, wadda ku ka yi domin ita bata san ku na yi ba, ni abinda ya ishe ni ya dameni"
"In baki so ki ji mi muka hwadi tai garkar ki, nan garka ta ta wallah"
(in bakya so ki ji me muke cewa je ki gidan ki, nan gida na ne)
Ran Lamishi ya baci, nan da nan kuwa magana ta girmama, aka hau fada, sai ga tone tonen asiri ana ta yi, akan gulmammakin da akai ta kitsawa anan ne matar Yahai taji maganar da daga ita sai 'Yabbuga suka yi ta, ya akai Lamishi da baquwar da bata fi watanni hudu da su ba ta sani?
Ai kuwa sai fad'a ya koma kan 'Yabbuga da Matar Yahai, nan fa suma suka hau nasu maganganun, abu fa ya qi ci ya qi cinyewa, har da dambe.
Asshibi naso ta raba amma abu ya fi qarfin ta, cikin sa'a kuwa Matar Yahai ta samu d'aga 'yabbuga ta maka da qasa, ta haye cikin ta, ta dinga kirba,sai da ta farfashewa 'Yabbuga baki sannan Asshibi da Mai buruji suka samu d'aga ta a jikin 'Yabbuga, Lamishi ta ji dadin hakan, dan kuwa ko ba komai an koya ma 'Yabbuga hankali, ta na miqewa ta hau kade jikin ta ta na fadin,
"Baki daki banza ba, zaki gani, har gida se hukuma ta kama min ke, bari dan Jummaa ya dawo"
"Baku da wanan azziqin da alfamar a Nigeria,"
"Haka kin ka ce ko?"
"Na hwadi,"
Haka nan suka yi ta sa'in sa har aka kirayi magariba suka tafi gidajen su, Asshibi kuwa gidan su Lamishi ta nufa suka yi ta gulmar sauran.
**************************
"Excellency gamu asibiti da shi, ba shi da halin magana shi yassa"
"Mi ya same shi halan?"
"Allah shi taimake ka wasa ta an ka yi, shi na ya samu rauni"
"Allah ya bashi lahiya, ka na ji na ba, wannan ajiyar ina so a qara bata tsaro, gaf nake nai amfani da ita, ba na so Ogan ku ya san me ke faruwa, ka gane?"
"Na gane Excellency,"
"Tau ya yi, ka gaishe shi in ya hwalka"
"Zai ji ranka shi dade "
Bayan sun gama wayar ne, ya sanar da No 1 duk yadda suka yi da gwamna, cikin jin jiki ya ke d'aga kai, alamar ya ji.
Cikin ran shi kuwa ya na tunanin kalar azabar da zai ganawa Mubaraka, duk abinda ya tunano sai ya ga ya yi kadan, qarshe saboda tsananin ciwon kan da yake ji, dole sai hakura ya yi da tunanin zuwa wani lokacin.
*Hummm anya ka daku kuwa No 1???*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 35:
Satin su Sultana biyu kafin Gwamna ya bata izin fita daga gidan gwamnati, a wannan satikan kuwa duk ta rame, ta yi zuru-zuru rashin ganin Lawwali da bata yi ya fitar da ita daga hayyacin ta, ita kan ta, ta na mamakin kalar soyayyar da take masa, anya wannan soyayyar ba zata zama ajalin ta ba kuwa?
Masu tsaron lafiyar ta ta dinga kallo daya bayan daya, sanda ta fito tafiya,dukkan su kamar sabbi ne, bata taba ganin wasun su ba.
Juyawa ta yi, ta kalli Hajiya Ikee da ta ke zuba mata murmushi, ta kalli Sultan wanda ke kallon ta da tsantsar kulawa da tausaya wa, ta ce,
"Ina driver na?"
Hade fuska Hajiya Ikee ta yi, sannan ta bude baki zata yi magana, al'ajabi ya sanya ta hadiye maganar ta.
Lawwali ne cikin uniform din shi, wanda da gani ka san sabbi ne, sai dai wadannan ba fari bane, ash color ne, da ratsin baqi a jikin riga da wandon kayan, duk yanda zan fasalta maku kalar kyaun da ya yi ba zai yu ba, sai ido ya gan shi kawai.
Hawaye ne kawai ke tsartuwa daga idon Sultana, a lokaci daya kuma ta na dariyar farin ciki, da murnar ganin jarumin maza Auwal din ta.
Ita kan ta Hajiya Ikee kasa magana ta yi tsabar kwarjinin da ya yi mata, Sultan kuwa zuwa ya yi ya daki kafadar Lawwali, tare da matsa ta, ya na zuba murmushi,
"Me na fada maka game da sa min qauna kuka?"
Lawwali dan duqawa ya yi, sannan ya ce,
"A min ahuwa ran ka shi dade, an min iyaka da shigowa gidan nan ,yau ma Umarni uwar daki na tabban, ta ce na taho na maishe ta gida, in ban taho ba zata taka daga nan zuwa can gidan da qafa, shi yasa na dawo bakin aiki na, ina fatan za a karbi uziri na"
Cikin share hawaye Sultana ta ce,
"Mu je"
"Ku tai ina? Sulty baby yaushe ki ka hwara kafiya da taurin kai, akan wannan qasqantaccen drivern ne ki ka hwara rashin kunya ko? Mu na hwadi ki na hwadi?....kaiii malam ji nan, bar ganin ka na da qirar majiya qarhi, qarhin mulki ba qarya ne ba, zan iya sanyawa a batar da kai, da kai da kaff dangin ku, ba Lamishi ba ce uwar ka? Ko ba ita ta ba? To zan ci mata mutunci gaban ka, in sa a dauren ku har igiya ta yi saura,in ga uban da ya tsaya maka kafff garin Zamfara, ka rabu da diya ta, tun kana gane hanyar komawa gida,ka karya asirin da ka mata kafin na haukata ka, ka na ji na? Ke kuma wuce mota ta mu tai"
Hannu ta sanya ta fizgi Sultana da tun da ta fara zagi da ci wa Lawwali mutunci take kuka ta na bata hakuri, Lawwali kuwa tsaye yake ya na murmushi, babu mai iya karantar yanayin da yake ciki a fuskar shi.
A cikin zuciyar shi kuwa, kawai tunanin yanda zai yagalgala naman Hajiya Ikee a dajin su yake, manyan mata masu ji da kan su ma sun nuna su na son Lawwali yaran manya da attajirai sun qaunace shi, a duk sanda Gwamna ya dauke shi suka fita babban taron manya, ya na wahala ya bar wajen bai samu wadan da suka maqale masa ba, to ita sultana daban ce da ba zata ta so shi ba? Tunda jini na tsargawa a jijiyoyin jiki da tsokar ta.
Hajiya Ikee ce ta danna Sultana a motar ta, ta zagaya zata zauna, kafin ta zauna Sultana ta fita da gudu ta nufi Lawwali,
"Sultan kar ka bari ta tabi wannan dan talakawan, ta janyo mana tsiya a zuri'a, kar ka kuskura ka bari ta tabe shi zan saba maka"
Yanayin Sultan ya nuna ba ya son riqe sultana, Amma dole ya riqe ta, dan bai saba sab'a Umarnin iyayen nasu ba, rungume ta ya yi, ita kuma ta na tirjewa ta na kuka, tare da miqawa Lawwali hannun ta, shi dai ya na nan tsaye bai motsa ba, bai kuma b'ata rai ba, hasali ma murmushin nan ne a fuskar shi, Hajiya Ikee na kewaya wa ta daga hannu zata wanke Sultana da mari taji an mata wani irin riqon da sai da ta ji fatar hannun ta na tabo qashin ta.
Sultana kuwa ta rintse idanun ta, ta qanqame Sultan, ma'aikatan wajen da dama sun riga sun san Lawwali, tini suka sha jinin jikin su, dan kuwa bacin ran da yake ta boyewa sai da ya bayyana a saman fuskar shi, wanda basu san shi ba kuma a ma'aikatan gidan sun zabura za su kai masa hari, akan me zai riqe hannun matar gwamna haka?
Shugaban masu kula da securities ne ya dakatar da su cike da tsoro, kar su ja musu bala'i, Lawwali ya huce akan su.
Yan kanzagi da 'yan maula da 'yan siyasan da ke giggilmawa ma sun tsaya ganin ikon Allah, a hankali murmushin fuskar Lawwali ya dawo, sannan ya saki hannun Hajiya Ikee, wadda ta ji kamar jijiyoyin wajen sun tsaya da aiki, wani yammmm, zummmm hannun ke mata, a hankali Lawwali ya furta .
"Ran ki shi dad'e,shiga Mota na kai ki gida,daga nan ina da wajen zuwa"
Da sauri kuwa Sultana ta bar wajen, har ta na haɗawa da gudu gudu, ta shige motar ta, ta zauna a gaba.
Shima shigewa ya yi, ya zauna, ya ja motar, Sultan ma take musu baya ya yi, cikin tsananin fushi da jin nauyin mutanen da suka zuba mata ido, Hajiya Ikee ta fada motar ta ta zauna, jan ta akai motocin da ke take ma nata baya suka bi su.
Lallai idan Gwamna ya dawo daga tafiyar da ya yi, za a yi ta ta qare, maganar Lawwali ta zo qarshe a shafin rayuwar su.
************************
A ranar da No 1 ya ji sauqi a ranar ya shirya dan zuwa maboyar da aka ajiye su Mubaraka, duk abinda yake No 4 na kai wa Oga bayani ta message, Oga ya gama shirya duk yanda za a yi, jiran zuwan No 1 kawai yake.
Agogon shi ne last abinda ya daura, sannan ya kalli No 4 ya ce,
"Mu tai, ka kai ni, da ina iya tuqa motar ma da kai na zan je, ba ni buqatar rakiya, amma ba zan iya ba saboda yanayin da nake jin kaina a ciki"
"Kar ka damu, zan iya kai ka duk inda ka ke buqata, kai dan uwa na ne"
"Na gode, mu tai ko"
"To Oga"
Sun fita daga dajin No 4 ya koma wajen No 1 dan zuwa maboyar su Mubaraka.
No 1 na gaba a mota, No 4 ya aikawa Lawwali saqon gasu nan sun bar gidan.
Shi kuwa waya ya yi ma sabbin yaran da ya horar, guda bakwai, su ma suka tabbatar masa da a shirye suke.
Cikin duhun magariba suke tafe, kafin su isa har an yi sallah, wanda su ba ta gaban su, sunan musulmai ne kawai da su, amma duk wani abu da Musulmin kirki yake su ba sa yi.
A qofar gidan su ka kashe motar, su ka fita, No 1 ne a gaba, ya na dingisa qafa, ya sanya key ya bude qofar, ya na fito.
Kafin ya kunna fitilar ya ji fito a bayan shi,cikin sauri da faduwar gaba ya lalibi makunnin fitilar dan kunnawa, hasken ta bai gama haskaka ko ina ba wani daga matasan ya sa bindiga ya harbe kwan fitilar, qara da ihun 'yan matan ne ya cika gidan,tun da suke a gidan basu taba jin an yi dambe ba ma, ballantana harbin bindiga, yau tasu ta qare.
No 1 kuwa asalin matsoraci ne dama shi, makircin shi da iya hada tuggun yaqi ne ya sanya aka bashi muqamin da yake da, amma ba jarumta ba, hankalin shi in ya yi dubu ya tashi, wani irin duka aka sakar mishi a qirjin shi, da bakin bindiga, sai da ya fara jin jiri, daya daga matasan ne ya wuce su, ya bude dakin , ya fidda yan matan, sannan ya kai su mota, tayar da motar ya yi, ya shiga gari da su,sai kuka suke, su na bashi hakuri, sun fara bashi haushi, ta madubi ya ga yarinya daya ko a jikin ta, kallon waje kawai take, ta na lumshe idanu, ita bata damu ba kenan ko sace ta za ai?
"Kaiii dalla kun cika min kunne, Oga ne ya aiko mu, wace ce Mubaraka cikin ku?"
Da sauri suka nuna ta, cikin ran shi ya ce,
'Dole ki taurin rai yarinya,'
Sai da suka shiga garin sosai,ya tsaida mota ya wurgawa su Murjanatu kudi, ya ce su bace masa da gani, in sun je gida kome aka tambaye su, su ce basu sani ba, idan qaiqayin baki ya sa suka fadi wani abu, Oga da kanshi zai sa a kashe ahalin su gaba daya .
Sai kada kai suke, su na tabbatar masa sun gane, ba wanda zai ji komai, sun yi alqawari,godiya suka dinga musu, sannan suka fita daga motar a guje, yanzu tsoron yarda da mutane ma suke, tunda kusa da unguwar su ne, ko abun hawa ba su nema ba, da qafa suka nufi gidan su.
Mubaraka kuwa gidan Oga aka yi da ita, Lawwali na can ya yi order din abinci a best restaurant na cikin garin Zamfara, ya haɗa mata ruwan wanka da kan shi,ya gyara ko ina da kan shi,yaran shi na ta so su taya shi yaqi amincewa, so yake ya burge Mubarakan shi,so yake ya mata tarba ta musamman.
Ya na da qarfin kawar da duk wanda ya so, ba tsoro bane ya sa shi jinkirtawa har wannan lokacin, ba kuma gudun tashin hankali bane, kawai komai da lokacin sa, yanzu ne lokacin da ya debar wa Gwamna da iyalan shi,duk da a tsarin shi sai gwamna ya dawo, amma inaaaa ba zai iya jira ba, dan wannan karon bai neme shi ba, bai bashi wani aiki ba, ya tabbata akwai wani shiri mara kyau da yake akan shi,gashi yau Hajiya Ikee ta tsokane shi iya tsokana.
Ya na tsaka da kallon yanda ya gyara wajen, ya ji horn din mota,da sauri ya fita ya tsaya,yaran da ya debo guda uku, daya daga cikin su ne ya bude gate suka shiga.
Zuciyar Lawwali ta karye da ganin qanwar shi, idanun shi ne suka cika tafff da hawaye, cikin azama ya nufe ta ya rungume ta, sai da ya raba ta da qasa.
Jin ta a faffadan qirjin shi ne ya sanya ta sakin kukan da ya taho da wani irin qarfi da ciccira, da kuma daukewar numfashi, qoqari yake ya kwantar mata da hankali , ta nutsu ta dena kukan amma inaa, sai yi take, ta na qarawa, duk ta gigita shi, ta kidima shi,rabon shi da shiga irin tashin hankalin yau tun sanda ya tabbatar da batan ta.
Daukan ta yayi cak ya shiga da ita ciki, daga shi har ita hawaye suke, gashi yanayin yanda take kuka da ciccira yaqi tsayawa.
Zaunar da ita ya yi a saman cinyar shi ya na lallashi sun jima a haka daga baya ya ji ta yi shiru,ta na ta sauke ajiyar zuciya mai qarfi, ya na dago ta ya ga ta yi baccin wahala.
Ba datti a tattare da ita, ba yunwa a tattare da ita, hasali ma gani ya yi kamar ta yi qiba ta yi haske.
Dakin da ya tanada domin ta, ya nufa da ita, dauke a kafadar shi, ya kwantar da ita, zama ya yi a bakin gadon ya na kallon ta, cike da tausaya wa, shi ne Silar shigar ta wannan mawuyacin halin, amma daga gobe komai yazo qarshe .
Cikin fushi ya miqe, ya sanya rigar shi a saman vest din jikin shi, ya dau bindigogin shi, sannan ya dau key din motar shi, basu zame ko ina ba sai gidan da aka ajiye su Mubaraka.
Ya na shiga ya tadda su a tsakar gida, No 1 cikin jini, No 4 na zaune a kujera, sai sauran yaran a tsaye sun yi shirin ko ta kwana.
Lawwali na shiga kowa ya miqe da kyau, direct wajen No 1 ya nufa, ya daga shi,
Showing 69001 words to 72000 words out of 150481 words
Hajiya ce ta kalle ta ta ce,
"Gaskiya ya kamata a sauya maki waya, yanzu da yar wayar nan ta zamani ake hira da miji, sai ku yi chatting din ku kamar ku na tare, haka naga Yayan ki na yi da waccan maras kunyar da ta qi dawowa, amma fa soyayya a waya kamar Juliet,"
"Hajiya wai mi an kai mata ne haka?"
"Wannan fa baki gane alqiblar ta, dan yanzu ko an ce mi yayi mata bata hwadi, ta na can qasar waje, da alama can taka so su koma da zama, tunda can ta yi rayuwar ta, ni kuwa ba me d'auke min yaro shi tai wata uwa duniya"
"Ohhh amma ko bata kyauta ba gaskiya, ai mace hankuri aka santa da shi a gidan miji, ba irin wanga hali ba"
"Haka ne, ita kam sam bata san wannan ba, komi so takai ayi yanda taka so, ba ko shi yiwa,"
"Allah to ya shirya ta, ya sa ta dawo su ci gaba da zaman su lahiya,"
"Ameen dai"
Su na tsaka da hira Hajiya ta dauki waya, ta kira Yayan Hansatu, tace ya aiko mata da waya mai kyau, kafin Hansatu ta wuce, amsawa ya yi, da toh, sanan suka yi sallama.
Hansatu bata koma gida ba kuwa sai da dalleliyar waya mai kyau, ba ta wani murna da wayar kawai dai ta nuna ta na murna ne, domin kuwa wanda ake mata kwadayin su yi hirar da shi, tunda ya tafi sai dai taji labari wajen Hajiya sun yi waya, amma baya kiran ta, balle ta samu No shi, kuma ita ba zata iya tambayar hajiyar ta No isah ba.
Ko a mota ajiye kwalin wayar kawai ta yi a cinyar ta ta na tunani, ga dai shi ya tafi, kuma ya fadawa Hajiya kasuwancin goro yayi albarka, amma ko sisi bai masu aike ba, bata san ranar dawowar shi ba.
A qofar gidan su motar ta tsaya, fitowa suka yi ita da yaran, kowa ya gan su ya ga jikokin masu azziqi, hatta da takalmin su yanzu mai tsada suke sakawa.
Ko kallon majalisar su 'yabbuga bata yi ba, ballantana ta ga yanda suka sanya mata ido su na gulmar ta.
Sallama ta yi da driver suka shige gida.
Can majalisar su Lamishi kuwa banda gulmar su ba abinda suka ke.
"Hummmm wagga ai ni zan baki labarin Hansatu ta sauya, bari dai, ai za su koma yar gidan jiya ne, ta na zuwa roqon abu zan mata kaca-kaca, yanzu ta koyi walaqanci,ko kallo bamu ishe ta ba,dan ta hwara daura suhwa, da holan, walle ta na barin shi"
"Ohhh ke kuwa me ya sa kin ka ce haka? Ai ba kin mata hwatan komawa gidan jiya ba, indai ta sha wahala yanda kun ka ce"
'Yabbuga ce ta kalli Asshibi a sheqe ta ce,
"Na hwadi, na ce na hwadi baki ganin wani kallon walaqanci da takai wa mutane?"
"Ai kuwa ko kallon wajen ga ma bata yi ba"
"Tauuu PA din Hansatu, ko zuwa zaki ki hwadi mata mi nicce?"
Lamishi da ta zabga tagumi ta na tunanin shin duniya ina Mubaraka ta shiga ne, ta ce,
"Dan Allah ku bar yi mana hayaniyar ga, wadda ku ka yi domin ita bata san ku na yi ba, ni abinda ya ishe ni ya dameni"
"In baki so ki ji mi muka hwadi tai garkar ki, nan garka ta ta wallah"
(in bakya so ki ji me muke cewa je ki gidan ki, nan gida na ne)
Ran Lamishi ya baci, nan da nan kuwa magana ta girmama, aka hau fada, sai ga tone tonen asiri ana ta yi, akan gulmammakin da akai ta kitsawa anan ne matar Yahai taji maganar da daga ita sai 'Yabbuga suka yi ta, ya akai Lamishi da baquwar da bata fi watanni hudu da su ba ta sani?
Ai kuwa sai fad'a ya koma kan 'Yabbuga da Matar Yahai, nan fa suma suka hau nasu maganganun, abu fa ya qi ci ya qi cinyewa, har da dambe.
Asshibi naso ta raba amma abu ya fi qarfin ta, cikin sa'a kuwa Matar Yahai ta samu d'aga 'yabbuga ta maka da qasa, ta haye cikin ta, ta dinga kirba,sai da ta farfashewa 'Yabbuga baki sannan Asshibi da Mai buruji suka samu d'aga ta a jikin 'Yabbuga, Lamishi ta ji dadin hakan, dan kuwa ko ba komai an koya ma 'Yabbuga hankali, ta na miqewa ta hau kade jikin ta ta na fadin,
"Baki daki banza ba, zaki gani, har gida se hukuma ta kama min ke, bari dan Jummaa ya dawo"
"Baku da wanan azziqin da alfamar a Nigeria,"
"Haka kin ka ce ko?"
"Na hwadi,"
Haka nan suka yi ta sa'in sa har aka kirayi magariba suka tafi gidajen su, Asshibi kuwa gidan su Lamishi ta nufa suka yi ta gulmar sauran.
**************************
"Excellency gamu asibiti da shi, ba shi da halin magana shi yassa"
"Mi ya same shi halan?"
"Allah shi taimake ka wasa ta an ka yi, shi na ya samu rauni"
"Allah ya bashi lahiya, ka na ji na ba, wannan ajiyar ina so a qara bata tsaro, gaf nake nai amfani da ita, ba na so Ogan ku ya san me ke faruwa, ka gane?"
"Na gane Excellency,"
"Tau ya yi, ka gaishe shi in ya hwalka"
"Zai ji ranka shi dade "
Bayan sun gama wayar ne, ya sanar da No 1 duk yadda suka yi da gwamna, cikin jin jiki ya ke d'aga kai, alamar ya ji.
Cikin ran shi kuwa ya na tunanin kalar azabar da zai ganawa Mubaraka, duk abinda ya tunano sai ya ga ya yi kadan, qarshe saboda tsananin ciwon kan da yake ji, dole sai hakura ya yi da tunanin zuwa wani lokacin.
*Hummm anya ka daku kuwa No 1???*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 35:
Satin su Sultana biyu kafin Gwamna ya bata izin fita daga gidan gwamnati, a wannan satikan kuwa duk ta rame, ta yi zuru-zuru rashin ganin Lawwali da bata yi ya fitar da ita daga hayyacin ta, ita kan ta, ta na mamakin kalar soyayyar da take masa, anya wannan soyayyar ba zata zama ajalin ta ba kuwa?
Masu tsaron lafiyar ta ta dinga kallo daya bayan daya, sanda ta fito tafiya,dukkan su kamar sabbi ne, bata taba ganin wasun su ba.
Juyawa ta yi, ta kalli Hajiya Ikee da ta ke zuba mata murmushi, ta kalli Sultan wanda ke kallon ta da tsantsar kulawa da tausaya wa, ta ce,
"Ina driver na?"
Hade fuska Hajiya Ikee ta yi, sannan ta bude baki zata yi magana, al'ajabi ya sanya ta hadiye maganar ta.
Lawwali ne cikin uniform din shi, wanda da gani ka san sabbi ne, sai dai wadannan ba fari bane, ash color ne, da ratsin baqi a jikin riga da wandon kayan, duk yanda zan fasalta maku kalar kyaun da ya yi ba zai yu ba, sai ido ya gan shi kawai.
Hawaye ne kawai ke tsartuwa daga idon Sultana, a lokaci daya kuma ta na dariyar farin ciki, da murnar ganin jarumin maza Auwal din ta.
Ita kan ta Hajiya Ikee kasa magana ta yi tsabar kwarjinin da ya yi mata, Sultan kuwa zuwa ya yi ya daki kafadar Lawwali, tare da matsa ta, ya na zuba murmushi,
"Me na fada maka game da sa min qauna kuka?"
Lawwali dan duqawa ya yi, sannan ya ce,
"A min ahuwa ran ka shi dade, an min iyaka da shigowa gidan nan ,yau ma Umarni uwar daki na tabban, ta ce na taho na maishe ta gida, in ban taho ba zata taka daga nan zuwa can gidan da qafa, shi yasa na dawo bakin aiki na, ina fatan za a karbi uziri na"
Cikin share hawaye Sultana ta ce,
"Mu je"
"Ku tai ina? Sulty baby yaushe ki ka hwara kafiya da taurin kai, akan wannan qasqantaccen drivern ne ki ka hwara rashin kunya ko? Mu na hwadi ki na hwadi?....kaiii malam ji nan, bar ganin ka na da qirar majiya qarhi, qarhin mulki ba qarya ne ba, zan iya sanyawa a batar da kai, da kai da kaff dangin ku, ba Lamishi ba ce uwar ka? Ko ba ita ta ba? To zan ci mata mutunci gaban ka, in sa a dauren ku har igiya ta yi saura,in ga uban da ya tsaya maka kafff garin Zamfara, ka rabu da diya ta, tun kana gane hanyar komawa gida,ka karya asirin da ka mata kafin na haukata ka, ka na ji na? Ke kuma wuce mota ta mu tai"
Hannu ta sanya ta fizgi Sultana da tun da ta fara zagi da ci wa Lawwali mutunci take kuka ta na bata hakuri, Lawwali kuwa tsaye yake ya na murmushi, babu mai iya karantar yanayin da yake ciki a fuskar shi.
A cikin zuciyar shi kuwa, kawai tunanin yanda zai yagalgala naman Hajiya Ikee a dajin su yake, manyan mata masu ji da kan su ma sun nuna su na son Lawwali yaran manya da attajirai sun qaunace shi, a duk sanda Gwamna ya dauke shi suka fita babban taron manya, ya na wahala ya bar wajen bai samu wadan da suka maqale masa ba, to ita sultana daban ce da ba zata ta so shi ba? Tunda jini na tsargawa a jijiyoyin jiki da tsokar ta.
Hajiya Ikee ce ta danna Sultana a motar ta, ta zagaya zata zauna, kafin ta zauna Sultana ta fita da gudu ta nufi Lawwali,
"Sultan kar ka bari ta tabi wannan dan talakawan, ta janyo mana tsiya a zuri'a, kar ka kuskura ka bari ta tabe shi zan saba maka"
Yanayin Sultan ya nuna ba ya son riqe sultana, Amma dole ya riqe ta, dan bai saba sab'a Umarnin iyayen nasu ba, rungume ta ya yi, ita kuma ta na tirjewa ta na kuka, tare da miqawa Lawwali hannun ta, shi dai ya na nan tsaye bai motsa ba, bai kuma b'ata rai ba, hasali ma murmushin nan ne a fuskar shi, Hajiya Ikee na kewaya wa ta daga hannu zata wanke Sultana da mari taji an mata wani irin riqon da sai da ta ji fatar hannun ta na tabo qashin ta.
Sultana kuwa ta rintse idanun ta, ta qanqame Sultan, ma'aikatan wajen da dama sun riga sun san Lawwali, tini suka sha jinin jikin su, dan kuwa bacin ran da yake ta boyewa sai da ya bayyana a saman fuskar shi, wanda basu san shi ba kuma a ma'aikatan gidan sun zabura za su kai masa hari, akan me zai riqe hannun matar gwamna haka?
Shugaban masu kula da securities ne ya dakatar da su cike da tsoro, kar su ja musu bala'i, Lawwali ya huce akan su.
Yan kanzagi da 'yan maula da 'yan siyasan da ke giggilmawa ma sun tsaya ganin ikon Allah, a hankali murmushin fuskar Lawwali ya dawo, sannan ya saki hannun Hajiya Ikee, wadda ta ji kamar jijiyoyin wajen sun tsaya da aiki, wani yammmm, zummmm hannun ke mata, a hankali Lawwali ya furta .
"Ran ki shi dad'e,shiga Mota na kai ki gida,daga nan ina da wajen zuwa"
Da sauri kuwa Sultana ta bar wajen, har ta na haɗawa da gudu gudu, ta shige motar ta, ta zauna a gaba.
Shima shigewa ya yi, ya zauna, ya ja motar, Sultan ma take musu baya ya yi, cikin tsananin fushi da jin nauyin mutanen da suka zuba mata ido, Hajiya Ikee ta fada motar ta ta zauna, jan ta akai motocin da ke take ma nata baya suka bi su.
Lallai idan Gwamna ya dawo daga tafiyar da ya yi, za a yi ta ta qare, maganar Lawwali ta zo qarshe a shafin rayuwar su.
************************
A ranar da No 1 ya ji sauqi a ranar ya shirya dan zuwa maboyar da aka ajiye su Mubaraka, duk abinda yake No 4 na kai wa Oga bayani ta message, Oga ya gama shirya duk yanda za a yi, jiran zuwan No 1 kawai yake.
Agogon shi ne last abinda ya daura, sannan ya kalli No 4 ya ce,
"Mu tai, ka kai ni, da ina iya tuqa motar ma da kai na zan je, ba ni buqatar rakiya, amma ba zan iya ba saboda yanayin da nake jin kaina a ciki"
"Kar ka damu, zan iya kai ka duk inda ka ke buqata, kai dan uwa na ne"
"Na gode, mu tai ko"
"To Oga"
Sun fita daga dajin No 4 ya koma wajen No 1 dan zuwa maboyar su Mubaraka.
No 1 na gaba a mota, No 4 ya aikawa Lawwali saqon gasu nan sun bar gidan.
Shi kuwa waya ya yi ma sabbin yaran da ya horar, guda bakwai, su ma suka tabbatar masa da a shirye suke.
Cikin duhun magariba suke tafe, kafin su isa har an yi sallah, wanda su ba ta gaban su, sunan musulmai ne kawai da su, amma duk wani abu da Musulmin kirki yake su ba sa yi.
A qofar gidan su ka kashe motar, su ka fita, No 1 ne a gaba, ya na dingisa qafa, ya sanya key ya bude qofar, ya na fito.
Kafin ya kunna fitilar ya ji fito a bayan shi,cikin sauri da faduwar gaba ya lalibi makunnin fitilar dan kunnawa, hasken ta bai gama haskaka ko ina ba wani daga matasan ya sa bindiga ya harbe kwan fitilar, qara da ihun 'yan matan ne ya cika gidan,tun da suke a gidan basu taba jin an yi dambe ba ma, ballantana harbin bindiga, yau tasu ta qare.
No 1 kuwa asalin matsoraci ne dama shi, makircin shi da iya hada tuggun yaqi ne ya sanya aka bashi muqamin da yake da, amma ba jarumta ba, hankalin shi in ya yi dubu ya tashi, wani irin duka aka sakar mishi a qirjin shi, da bakin bindiga, sai da ya fara jin jiri, daya daga matasan ne ya wuce su, ya bude dakin , ya fidda yan matan, sannan ya kai su mota, tayar da motar ya yi, ya shiga gari da su,sai kuka suke, su na bashi hakuri, sun fara bashi haushi, ta madubi ya ga yarinya daya ko a jikin ta, kallon waje kawai take, ta na lumshe idanu, ita bata damu ba kenan ko sace ta za ai?
"Kaiii dalla kun cika min kunne, Oga ne ya aiko mu, wace ce Mubaraka cikin ku?"
Da sauri suka nuna ta, cikin ran shi ya ce,
'Dole ki taurin rai yarinya,'
Sai da suka shiga garin sosai,ya tsaida mota ya wurgawa su Murjanatu kudi, ya ce su bace masa da gani, in sun je gida kome aka tambaye su, su ce basu sani ba, idan qaiqayin baki ya sa suka fadi wani abu, Oga da kanshi zai sa a kashe ahalin su gaba daya .
Sai kada kai suke, su na tabbatar masa sun gane, ba wanda zai ji komai, sun yi alqawari,godiya suka dinga musu, sannan suka fita daga motar a guje, yanzu tsoron yarda da mutane ma suke, tunda kusa da unguwar su ne, ko abun hawa ba su nema ba, da qafa suka nufi gidan su.
Mubaraka kuwa gidan Oga aka yi da ita, Lawwali na can ya yi order din abinci a best restaurant na cikin garin Zamfara, ya haɗa mata ruwan wanka da kan shi,ya gyara ko ina da kan shi,yaran shi na ta so su taya shi yaqi amincewa, so yake ya burge Mubarakan shi,so yake ya mata tarba ta musamman.
Ya na da qarfin kawar da duk wanda ya so, ba tsoro bane ya sa shi jinkirtawa har wannan lokacin, ba kuma gudun tashin hankali bane, kawai komai da lokacin sa, yanzu ne lokacin da ya debar wa Gwamna da iyalan shi,duk da a tsarin shi sai gwamna ya dawo, amma inaaaa ba zai iya jira ba, dan wannan karon bai neme shi ba, bai bashi wani aiki ba, ya tabbata akwai wani shiri mara kyau da yake akan shi,gashi yau Hajiya Ikee ta tsokane shi iya tsokana.
Ya na tsaka da kallon yanda ya gyara wajen, ya ji horn din mota,da sauri ya fita ya tsaya,yaran da ya debo guda uku, daya daga cikin su ne ya bude gate suka shiga.
Zuciyar Lawwali ta karye da ganin qanwar shi, idanun shi ne suka cika tafff da hawaye, cikin azama ya nufe ta ya rungume ta, sai da ya raba ta da qasa.
Jin ta a faffadan qirjin shi ne ya sanya ta sakin kukan da ya taho da wani irin qarfi da ciccira, da kuma daukewar numfashi, qoqari yake ya kwantar mata da hankali , ta nutsu ta dena kukan amma inaa, sai yi take, ta na qarawa, duk ta gigita shi, ta kidima shi,rabon shi da shiga irin tashin hankalin yau tun sanda ya tabbatar da batan ta.
Daukan ta yayi cak ya shiga da ita ciki, daga shi har ita hawaye suke, gashi yanayin yanda take kuka da ciccira yaqi tsayawa.
Zaunar da ita ya yi a saman cinyar shi ya na lallashi sun jima a haka daga baya ya ji ta yi shiru,ta na ta sauke ajiyar zuciya mai qarfi, ya na dago ta ya ga ta yi baccin wahala.
Ba datti a tattare da ita, ba yunwa a tattare da ita, hasali ma gani ya yi kamar ta yi qiba ta yi haske.
Dakin da ya tanada domin ta, ya nufa da ita, dauke a kafadar shi, ya kwantar da ita, zama ya yi a bakin gadon ya na kallon ta, cike da tausaya wa, shi ne Silar shigar ta wannan mawuyacin halin, amma daga gobe komai yazo qarshe .
Cikin fushi ya miqe, ya sanya rigar shi a saman vest din jikin shi, ya dau bindigogin shi, sannan ya dau key din motar shi, basu zame ko ina ba sai gidan da aka ajiye su Mubaraka.
Ya na shiga ya tadda su a tsakar gida, No 1 cikin jini, No 4 na zaune a kujera, sai sauran yaran a tsaye sun yi shirin ko ta kwana.
Lawwali na shiga kowa ya miqe da kyau, direct wajen No 1 ya nufa, ya daga shi,
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24 Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51