ya akai Suka hwara zaman lahiyar ne ? Ai na dole ne, tunda Mai Buruji ta hwara rashin nasihwa(rashin mutunci) , ta ga bata diban komai jikin Lamishi, shi na aka zauna lahiya, Kuma indai batun suhwa ne Dan Jumma yassa ka min batun kishiya riqe suhwar ka, banni so, amma ka sani kai da ka samu kwaciyar hankali gidan ga sai na huce haushi na"
"Ga leda nan na shigo maki da ita, huce haushin ki saman ta"
Alwala ya fita waje ya yi, ya wuce masallaci, qofar gidan ba kowa dik su Lamishi sun tafi,bayan sun gama jin drama da akai a gidan, ko a gida ma labarin da sukai ta yi kenan.
Hansatu kuwa bayan ta gama dafa wake,ta soya man ba ko albasa, ta zuba ita da yaran, ta aje ma Isa na shi, da ruwan sha, a shimfidar shi da yake zama, a tare Suka ci da yaran ta, suka qoshi, kowa ya Sha ruwa, cikin hamdala, sai annashuwa da murna suke, ga wani Nan ta Dan rage da safe ta zafafa (dumama) musu su ci.
Ta na idar da sallah ta hau wankin Lamishi, bata tashi ba sai da ta gama shi tsaf.
Ta shanya, lokaci ne na iska, bata kwanta ba sai da ta ninke su ninkin guga ta daure ta ajiye, qarfe Sha d'aya saura, hamma ta ke ta dokawa, ta gaji matuqa, ga shi har wannn lokacin qirjin ta bai daina ciwo ba, ya dai rage ne kawai.
Dan kishingid'a ta yi a tsakiyar yaran ta da ke kwance a parlour , Nan da Nan kuwa bacci Mai dadi ya share ta.
Bata sani ba, shin ta jima ta na baccin ko kuwa? Kawai dai taji an take qafar ta ne, har sau biyu, tsabar mugunta, ba zai durqusa ya tashe ta ba, sai dai ya take qafar ta.
Da sauri ta janye qafar tare da miqewa ta na masa sannu da zuwa.
Amsawa ya yi ciki ciki, ya qaqalo murmushin dole, Wanda ya Sanya gaban Hansatu faduwa da qarfi, Dan ta San ma'anar shi, taba wuyan ta tayi, ta ji shi zafi rau, ta San ba komai ya ja ba sai aikin da ta Sha, ga ciwon qirji na damun ta, gashi ta yi aiki cikin iskar da ke kadawa me sanyi.
Kwallar ta ta mayar, ta raka shi waje tare da zuba masa ruwa ya wanke hannu, kamar wani qaramin yaro, abinci ya ci, ya qoshi, tare da zabga wata gyatsa me Dan banzan wari.
Kauda kai Hansatu ta Yi, Isa kuwa ko a jikin shi, ya na tashi ta tattare komai, sannan ta je ta wanke bakin ta da ruwa da dan gishiri, ta bi shi daki, (ita ta iya ta wanke bakin ta, saboda Kar a ji warin shi, Amma shi ya wuni zubur da baki bawanki, sannan ya ci abinci, ko kurkurewa bai ba, ya tafi ya kwanta a haka)
Ga Isa da Dan banzan son yin kiss, ga baki na wari, Kuma Hansatu bata Isa ta nuna hakan ba, duk wani qoqarin ta na Sanya shi ya dinga wanke bakin,abun ya gagari tunanin baya ta fara, ta gwada aje masa hodar wanke baki da suke amfani da shi, ya yi fatali da ita, qarshe sai da yajibge ta, ya ce ta raina shi, shi zata kalla ta ce bakin shi na wari?
Ta gwada Yi masa magana direct, ya jibge ta, Kuma ya mata kiss ta qarfi, ya ce in mutuwa zatai sai dai ta mutu, Amma yanzu ya fara.
Gani ta Yi tunani ba zai kai ta ba, ya na iya fizgar ta da qarfi, da kan ta ta cire kayan ta ta kwanta a saman qaton gadon nasu, Wanda ya yi matuqar bani mamaki, ace kamar Hansatu masu ci da kyar ta na da irin wanna gadon.
Addu'a kawai take a ran ta har ya gama abinda zai ya tashi, fatan ta Allah ya raba ta da daukan wani cikin, ya Kuma bashi ikon dinga wanke bakin shi, tunda ta Yi dik wani qoqari ya qi farawa, Allah ne kawai zai sauya masa ra'ayi ya fara.
Cikin daren Isa na barci,jikin Hansatu ya dau zafi Mai tsanani, ga wani irin sanyi da take ji, bargon ta ta ja ta lullube jikin ta da kyau, Amma dik da haka sanyi take ji, Isa bai ma San tana Yi ba, Kuma in ta tashe shi ta San sauran, tunda naquda ma ya yi fada da ta tashe shi ballantana zazzabi.
Haka ta kwana da mummunan zazzabi, da zafin jikin ta ya dame shi ma sauka ya yi daga gadon, ya sa pillow a qasa ya kwanta, ya na ta surutai qasa qasa.
Hawayen baqin ciki ne suke kwaranya a idanun ta, har aka Kira asuba,ta na Nan kwance, takasa tashi.
Ba ta samu damar tashi ba kuwa sai da safiya ta fara Yi, da kyar ta iya hura wuta ta sa musu ruwan wanka, Amina da Bilkisu ne Suka shiga gidan Yabbuga duka samo ruwa, sai masifa ta ke masu, ta na fadin wata Rana ta ga alamar sai sun qafar mata da rijiya.
Ta na gama wanka ta Yi sallah, Isa ya fita tun tini, ya na can wajen Mai soya masa, ya ce a bashi ta dari biyu abin shi.
Kayan da ta daure jiya, ta kunce ta raba, ta Dora ma yaran ta ce,
"Maza ku kai wa mama Lamishi, ki ce mata Ina godiya,in ta na da ra'ayi ta na iya kawon wani wankin Nan gaba, ku Yi sauri kafin su fita, sun kusan tahiya gidan Gwauna , maza"
Da sauri kuwa Suka je, suka isar da saqon Mahaifiyar su, aiko wanki ya yi wa Lamishi kyau, ta ce zata kawo wani in ya taru,Mai Buruji ma ta ce za ta kai nata.
A hanyar su ta komawa ne Bilkisu ta ce,
"Amina mu je ta wajen Mai masa, na San baba na can,"
"Kin San dik ya kammana muna leqen shi Kashi zai liqa Muna ga banza ko?"
"Dun Allah mu tai, ni ko yawu na hadiya, mu dawo"
Da sauri ta kama hannun yayar ta da ke son guduwa gida, suka nufi rumfar me Masa.
Isa akwai jarabar wanke hannu, an zuba masa ya ja gefe shi kad'ai ya aje masar shi, ya tafi wanke hannu.
Bilkisu kuwa lallabawa ta Yi ta dauke kwanon Masa, ta ja hannun Amina Suka gudu gida.
Su na zuwa suka miqawa Maman su, Suka ce
"Gashi baba na yacce a kawo maki"
Cikin matsanancin jin dadi Hansatu ta amsa, ta sa yara a gaba Suka fara dukan waina da ci, su na ci ta na murmushin jin dadi.
A can rumfar me Masa, wasu matasa da Suka San isan da yaran shi,sun ga sanda Suka dauka, Dan haka dariya kawai Suka dinga Yi.
Isa na zuwa bega Masa ba, ya hau matasa da duka, ya na fadin sai sun biya shi masar shi, da kyar aka raba fadan, Nan suke sanar da Isa su ba su bane, diyoyin shi ne mata Suka dauke.
Wani irin ashar ya Danna, sannan ya Sanya takalmin shi guda da ya fadi wajen dambe ya nufi gida.........
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 6:
Da qafar shi ya daki qofar gidan, gaba dayan su zabura Suka Yi a tsorace, Hansatu ce ta Dan Yi murmushi da ta ga shi ne, godiya ta ke da niyyar Yi ta ji ya hada yatsun shi biyar da fuskar ta.
A kidime ta kalle shi, domin sanin laifin da ta aikata, Amina da Bilkisu ne suka shiga tsakanin su, ya ja hannun Amina ya kife ta da mari, zai qara mata Bilkisu ta riqe shi ta na kuka,
"Baba ka bar dukan su, ni ta nid-d'akko, ni zaka daka, Kuma ni nicce Kai ka bayar mu zo gida mu ci"
Wurga ta ya yi gefe, ta fadi ta dauje guiwar hannu, kuka ta Sanya Mai qarfi, tuni Hansatu ta durqusa ta na duba hannun nata, cikin sanyin murya da mamakin halin mijin nata ta ce
"Yanzu akan wainar jikka biyu ka fiddawa diyar ka jini? Ka daki matar ka ? Wadda ta sadaukar da millions saboda Kai, anya Isa Kai ne Wanda na fada son shi shekaru Sha uku da Suka wuce kuwa? Anya Isa Kai ne Wanda ka min alqawurran kyautatawa kala kala? Haqqin ka ne fa ciyar da mu, Amma ba ka Yi, da na san ba Kai ka Basu ba dakkowa suka Yi,da bamu cin ta wallah, ka Yi hankuri inshaa Allahu ba mu koma tambayar ka kuddin abinci, ko Kuma mu dau abun ka, tashi Mu je na wanke maki, sannu"
Kalaman ta Basu ratsa fatar shi ba ma, balle tsokar jikin shi, hasalima wata fassarar ya Yi ta daban.
"Auu abun gori Kuma ya koma Hansatu? To da ni da ke wa ya fara furta ya na son wani? Sannan wa ye ya kafe ya guji kowa na shi saboda masoyi? Kar ki dakko maganar baya akan haramun din da ki ka ci ke da yaran ki, duk Wanda ya sake min wannan gangacin zai ga ganganci"
Kamar ta sanar da shi ba su ci haram ba, sai ta kama bakin ta, saboda ta San dukan banza za ta sha, har ya shiga daki ba Wanda ya sake motsawa a cikin su, sai sautin shassheqar kuka kawai ke tashi.
Ya na shiga daki ya laluba ko Ina bai samu ko sisi ba, fitowa ya Yi sannan ya ce,
"Ba kuci banza ba, ki tabbata kin nemo min dari ta biyu"
Daga Kai ta yi ta na bin shi da wani irin kallon mamaki.
Tunanin baya ta fara Yi, shekara goma Sha uku da Suka wuce, shi din yaron mahaifin ta ne,mutumin kano ne shi, ita Kuma mutuniyar zamfara, ya na ma mahaifin ta tuqin mota, ta haka suka fara soyayya, mahaifin ta na da lalurar hawan jini, kafin ya rasu soyayyar su batai qarfi ba, Amma dik da haka ya fuskanta, Dan haka ya ce ya bawa Isa ita, Yan Uwan ta da dangin ta kaf aka dinga surutu, Dan me zai dauki gudan Yar shi mace tilo ya aura mata yaron shi, budar bakin ta ta ce wa Mahaifiyar ta da Yayan ta ta na son shi.
An saka ranar biki da ta gama candy, mahaifin ta a satin ya rasu, sun shiga damuwa sosai a zuri'ar baki daya, saboda shi din mutumin kirki ne, me son dangi ne da taimakon su, mutan unguwa da abokan aikin shi sun koka rashin shi, balle Kuma iyalan shi, Hansatu kuwa har ruwa sai da aka sanya mata a asibiti, saboda yawan suman da ta dinga Yi.
Bayan rasuwar mahaifin su da wata bakwai, Yan Uwan ta Suka yanke shawarar a raba gado, sannan a aura mata Dan abokin mahaifin ta, Wanda ke riqe da kampanin Baban su, Dan ya ci gaba da kula da ita, da dukiyar ta, Amma ta dage, ta nace ta ce sai Isa ,a lokacin nan Isa kan shi ji yake in aka raba su zai iya shiga mawuyacin hali.
Rashin lafiyar da ta dinga Yi bai bawa dangin ta tausayin komai ba, su dai qoqarin su su raba ta da Isa, har korar shi akai daga wajen aiki.
Wata Rana da daddare ta tattare kayan ta tsaf, ta gudu wajen shi, a dakin da ya kama, ta roqe shi da su je ko masallaci ne a Daura masu aure, in yaso sun koma a matsayin mata da miji, ba mai raba su.
A wannan daren haka suka kwana daki daya, rungume da junan su, dik da ba abinda suka aikata na masha'a amma hakan ba daidai bane.
Washegari suka samu aka aura masu junan su a masallaci ,a ranar suka koma dangin Hansatu a matsayin ma'aurata,mahaifiyar ta ta ji takaicin hakan matuqa, Yayan ta babba ya ce ba za su bata ko sisi ba, a gaban mahaifiyar ta, kuma bata sanya baki ba, Hansatu kuwa yarinta ce? Giyar soyayya ce? Ko kuma rashin tarbiyya ne ya sanya ta shigewa dakin ta dake gidan ,har sun fara murna ta ji maganar su, kawai sai suka ganta dauke da akwati, ta kama hannun Isa suka bar gidan.
Da kudin sarqoqin ta suka sayi gidan da suke ciki, aka sanya sunan Isa a takardar,gadon ta da komai na gidan duk da kudin da ta gudu da shi ne suka siya.
Lokacin da kudi suka qare ne, Isa ya fara fito wa da Hansatu asalin kalar shi, rashin mutuncin yau daban na gobe daban, da ciki ko ba ciki in ya ga damar dukan ta, zai daka, da ya ji kawai ta bata masa rai, zai mata abinda kamar bai taba furta mata kalmar so ba.
Wani irin kuka ne mai tsanani ya turniqe Hansatu, Bilkisu ce ta fada jikin ta ta na kuka, ta ce,
"Mama dan Allah ki dena kukan haka nan, lehi na na, bazan sake ba,ki yahe min,"
Dan shafa bayan yarinyar kawai ta yi, ta ya za ta budi baki ta sanar da yaran ta me ta aikata? Sakayya ce ta qin yin biyayya ga mahaifiyar ta ke bin ta? Shin a wani bangaren ba umarnin mahaifin ta ta cika ba? Tunda dama ya so a yi auren? Ta ya zata sanar da yaran ta mahaifin su azzalumi ne? Shin wadannan abubuwan da suke faruwa da ita silar waye?
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 7:
Lawwali ne da yaran shi zaune a wani tsohon kamfani na gwamnati,waje ne da ya qunshi sashe sashe, da dikkan alamu ofishin ma'aikatan wajenne, Lawwali kuwa ya maida wajen a matsayin ma'aikatar shi ta yin garkuwa da dik Wanda aka bashi umarni, ko Kuma ra'ayin kan shi ya bashi da ya Yi hakan,waje ne da ya ke a cikin wani surquqin daji, da dikkan alamu gina shi aka fara yi domin wani aikin na gwamnati kuma aka bari ba tare da an kammala ba, ko an waiwaye shi, Lawwali da yaran shi na ta qoqarin Neman network dan yin waya amma sun rasa.
Ya fi awa uku ya na abu d'aya, cikin nasara kuwa ya samu wayar da ya ke son Yi ta shiga, da hanzari ya fara magana.
"Hello Excellency ba waku, yunwa ta addabe ni da yara na, ga shi ba ruwan sha, mu na buqatar kayan caji,...hello...hello"
Wayar ce ta sake katsewa, cikin fushi ya buga ta da qasa, ya daki jikin ginin wajen, wani dattijo ne daure a jikin ginshiqin da ke a tsakiyar faffadan wajen da suke, bakin shi ya bushe, da alama yunwa da qishirwa suna damun shi, idanun shi a rufe suke, ba ya ganin kowa, amma ya na sauraren su.
Cikin wahalalliyar murya ya ke magana,
"Yanzu Lawwali duk irin amanar ka da na dauka, na riqe, haka zaka saka min da shi? Ba irin taimakon da ban maka ba a rayuwa, amma saboda wancan dan adawar ya biya ku kudi qalilan kuke wulaqanta ni haka"
Cikin fushi Lawwali ya kalli mutumin da ya haife shi, ya shure shi da qafa, sannan ya naushe shi sau ba adadi, har sai da wani daga yaran shi ya riqe shi.
"Oga ka Yi hakuri,Kar ya mutu, in ya mutu Excellency ba ze Mana da kyau ba, ajiya kawai ya ce muyi, ba kisa ba, ya jaddada Mana hakan, sai bayan zabe mu sake shi"
Bangaje yaron nashi ya Yi ya duqa gaban bawan Allah n da ya gama duka, cikin qunci yake magana.
"Ka riqe ni amana? Wace iriyar amana ka riqe? Amanar shaye-shaye? Ko ta Neman mata da kisan kan mutane? Ko kuma amanar fyade da garkuwa da mutane Dan neman kudin fansa? Kai Bari ka ji, ka ga da ace Excellency ze sauka, Wanda ya sake Hawa ya ban irin wannan umarnin, shi ma qaddamar Masa zan, taimako d'aya ka min a duniya, shi ne Iyaye na Dake aiki a gidan gwamnati har yanzu, dik da ka sauka su na Nan suna ci gaba da Yi, da wannan aikin gidan mu suke ci su qoshi, su Yi sutura, Dan haka iyakar godiyar da zan maka kenan, in ma zan Yi maka godiya"
"Oga Lawwali ya suma fa,gashi ba ruwan yayyafa Masa"
Murmushin mugunta Lawwali ya Yi, babu bata lokaci ya kunce wandon shi ya fara tsiyaya ma wannan mutumin fitsari akai, sai kuwa gashi ya farfado.
Kula da abinda Lawwali ke Yi ne ya Sanya wannan bawan Allahn qoqarin kaucewa, Amma dake ya na a daddaure ne, sai ya kasa matsawa.
Dariya Lawwali da yaran shi Suka dinga Yi.
Har magariba ba wani bayani daga wajen gwamna, yunwa dik ta cinye su da qishirwa, ga wayoyi sun mace ba caji, sai torch lights suka kukkuna, su na Nan zaune, har isha'i ta Yi, Lawwali ne ya tada mutane uku ya ce su dau mota su shiga gari,su sama masu abinda za su ci,Dan ya na ta jiyo kukan yaran da ke killace a wasu sashen da ke gidan da ko rufin kwano babu a wasu sashen, ya kuwa tabbata yunwa ke damun su,kudi ya Basu akan su siyo Dan wani abu ko ba yawa a fara da shi, Kuma su tabbata sun samu ganin Gwamna a daren ko Kuma su Yi magana da shi ta waya, a Kai masu abinci da ruwa.
Har za su tafi Lawwali ya dakatar da su,
"Yauwa ga waya ta ku tafi da ita, a sama min caji"
"To Oga,"
Mota suka tada Suka dauki hanyar shiga gari.
Sun samu sabani da mutanen gwamna, Dan kuwa Basu jima da tafiya ba aka kawo qatuwar mota lode da abinci da dik abinda suke buqata.
Ba bata lokaci yaran Lawwali da za su Kai su goma suka dirar wa abincin suka dinga shigar wa wani daki ana lodewa, bayan sun kammala shigar da duk wani abu da ya kamata suka zauna cin biscuits da juice dan kawar da yunwa kafin matan da ke cikin wajen su dafa abincin, drivern da ya kawo saqon ne ya tsaya ya na bawa Lawwali saqon gwamna.
"Oga Lawwali gwauna ya ce na hwada maka, kudin fansa da za a ce dangin Lamido su bayar ace su basuwa milliyon dari biyar, kar a rage masu ko sisi, dan ya San ya saci ya hi haka nan, da zarar sun kawo kun amshe ku qarasa shi, ya gama Yi wa qasa banna"
Daga Kai kawai Lawwali ya Yi cikin Isa, da nuna shi ne oga a wajen,dik qoqarin cin binci da kowa ya ke, shi bai je ba ya na gefe, ya na son ya ga kowa ya qoshi har da yara da
Showing 6001 words to 9000 words out of 150481 words
"Ga leda nan na shigo maki da ita, huce haushin ki saman ta"
Alwala ya fita waje ya yi, ya wuce masallaci, qofar gidan ba kowa dik su Lamishi sun tafi,bayan sun gama jin drama da akai a gidan, ko a gida ma labarin da sukai ta yi kenan.
Hansatu kuwa bayan ta gama dafa wake,ta soya man ba ko albasa, ta zuba ita da yaran, ta aje ma Isa na shi, da ruwan sha, a shimfidar shi da yake zama, a tare Suka ci da yaran ta, suka qoshi, kowa ya Sha ruwa, cikin hamdala, sai annashuwa da murna suke, ga wani Nan ta Dan rage da safe ta zafafa (dumama) musu su ci.
Ta na idar da sallah ta hau wankin Lamishi, bata tashi ba sai da ta gama shi tsaf.
Ta shanya, lokaci ne na iska, bata kwanta ba sai da ta ninke su ninkin guga ta daure ta ajiye, qarfe Sha d'aya saura, hamma ta ke ta dokawa, ta gaji matuqa, ga shi har wannn lokacin qirjin ta bai daina ciwo ba, ya dai rage ne kawai.
Dan kishingid'a ta yi a tsakiyar yaran ta da ke kwance a parlour , Nan da Nan kuwa bacci Mai dadi ya share ta.
Bata sani ba, shin ta jima ta na baccin ko kuwa? Kawai dai taji an take qafar ta ne, har sau biyu, tsabar mugunta, ba zai durqusa ya tashe ta ba, sai dai ya take qafar ta.
Da sauri ta janye qafar tare da miqewa ta na masa sannu da zuwa.
Amsawa ya yi ciki ciki, ya qaqalo murmushin dole, Wanda ya Sanya gaban Hansatu faduwa da qarfi, Dan ta San ma'anar shi, taba wuyan ta tayi, ta ji shi zafi rau, ta San ba komai ya ja ba sai aikin da ta Sha, ga ciwon qirji na damun ta, gashi ta yi aiki cikin iskar da ke kadawa me sanyi.
Kwallar ta ta mayar, ta raka shi waje tare da zuba masa ruwa ya wanke hannu, kamar wani qaramin yaro, abinci ya ci, ya qoshi, tare da zabga wata gyatsa me Dan banzan wari.
Kauda kai Hansatu ta Yi, Isa kuwa ko a jikin shi, ya na tashi ta tattare komai, sannan ta je ta wanke bakin ta da ruwa da dan gishiri, ta bi shi daki, (ita ta iya ta wanke bakin ta, saboda Kar a ji warin shi, Amma shi ya wuni zubur da baki bawanki, sannan ya ci abinci, ko kurkurewa bai ba, ya tafi ya kwanta a haka)
Ga Isa da Dan banzan son yin kiss, ga baki na wari, Kuma Hansatu bata Isa ta nuna hakan ba, duk wani qoqarin ta na Sanya shi ya dinga wanke bakin,abun ya gagari tunanin baya ta fara, ta gwada aje masa hodar wanke baki da suke amfani da shi, ya yi fatali da ita, qarshe sai da yajibge ta, ya ce ta raina shi, shi zata kalla ta ce bakin shi na wari?
Ta gwada Yi masa magana direct, ya jibge ta, Kuma ya mata kiss ta qarfi, ya ce in mutuwa zatai sai dai ta mutu, Amma yanzu ya fara.
Gani ta Yi tunani ba zai kai ta ba, ya na iya fizgar ta da qarfi, da kan ta ta cire kayan ta ta kwanta a saman qaton gadon nasu, Wanda ya yi matuqar bani mamaki, ace kamar Hansatu masu ci da kyar ta na da irin wanna gadon.
Addu'a kawai take a ran ta har ya gama abinda zai ya tashi, fatan ta Allah ya raba ta da daukan wani cikin, ya Kuma bashi ikon dinga wanke bakin shi, tunda ta Yi dik wani qoqari ya qi farawa, Allah ne kawai zai sauya masa ra'ayi ya fara.
Cikin daren Isa na barci,jikin Hansatu ya dau zafi Mai tsanani, ga wani irin sanyi da take ji, bargon ta ta ja ta lullube jikin ta da kyau, Amma dik da haka sanyi take ji, Isa bai ma San tana Yi ba, Kuma in ta tashe shi ta San sauran, tunda naquda ma ya yi fada da ta tashe shi ballantana zazzabi.
Haka ta kwana da mummunan zazzabi, da zafin jikin ta ya dame shi ma sauka ya yi daga gadon, ya sa pillow a qasa ya kwanta, ya na ta surutai qasa qasa.
Hawayen baqin ciki ne suke kwaranya a idanun ta, har aka Kira asuba,ta na Nan kwance, takasa tashi.
Ba ta samu damar tashi ba kuwa sai da safiya ta fara Yi, da kyar ta iya hura wuta ta sa musu ruwan wanka, Amina da Bilkisu ne Suka shiga gidan Yabbuga duka samo ruwa, sai masifa ta ke masu, ta na fadin wata Rana ta ga alamar sai sun qafar mata da rijiya.
Ta na gama wanka ta Yi sallah, Isa ya fita tun tini, ya na can wajen Mai soya masa, ya ce a bashi ta dari biyu abin shi.
Kayan da ta daure jiya, ta kunce ta raba, ta Dora ma yaran ta ce,
"Maza ku kai wa mama Lamishi, ki ce mata Ina godiya,in ta na da ra'ayi ta na iya kawon wani wankin Nan gaba, ku Yi sauri kafin su fita, sun kusan tahiya gidan Gwauna , maza"
Da sauri kuwa Suka je, suka isar da saqon Mahaifiyar su, aiko wanki ya yi wa Lamishi kyau, ta ce zata kawo wani in ya taru,Mai Buruji ma ta ce za ta kai nata.
A hanyar su ta komawa ne Bilkisu ta ce,
"Amina mu je ta wajen Mai masa, na San baba na can,"
"Kin San dik ya kammana muna leqen shi Kashi zai liqa Muna ga banza ko?"
"Dun Allah mu tai, ni ko yawu na hadiya, mu dawo"
Da sauri ta kama hannun yayar ta da ke son guduwa gida, suka nufi rumfar me Masa.
Isa akwai jarabar wanke hannu, an zuba masa ya ja gefe shi kad'ai ya aje masar shi, ya tafi wanke hannu.
Bilkisu kuwa lallabawa ta Yi ta dauke kwanon Masa, ta ja hannun Amina Suka gudu gida.
Su na zuwa suka miqawa Maman su, Suka ce
"Gashi baba na yacce a kawo maki"
Cikin matsanancin jin dadi Hansatu ta amsa, ta sa yara a gaba Suka fara dukan waina da ci, su na ci ta na murmushin jin dadi.
A can rumfar me Masa, wasu matasa da Suka San isan da yaran shi,sun ga sanda Suka dauka, Dan haka dariya kawai Suka dinga Yi.
Isa na zuwa bega Masa ba, ya hau matasa da duka, ya na fadin sai sun biya shi masar shi, da kyar aka raba fadan, Nan suke sanar da Isa su ba su bane, diyoyin shi ne mata Suka dauke.
Wani irin ashar ya Danna, sannan ya Sanya takalmin shi guda da ya fadi wajen dambe ya nufi gida.........
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 6:
Da qafar shi ya daki qofar gidan, gaba dayan su zabura Suka Yi a tsorace, Hansatu ce ta Dan Yi murmushi da ta ga shi ne, godiya ta ke da niyyar Yi ta ji ya hada yatsun shi biyar da fuskar ta.
A kidime ta kalle shi, domin sanin laifin da ta aikata, Amina da Bilkisu ne suka shiga tsakanin su, ya ja hannun Amina ya kife ta da mari, zai qara mata Bilkisu ta riqe shi ta na kuka,
"Baba ka bar dukan su, ni ta nid-d'akko, ni zaka daka, Kuma ni nicce Kai ka bayar mu zo gida mu ci"
Wurga ta ya yi gefe, ta fadi ta dauje guiwar hannu, kuka ta Sanya Mai qarfi, tuni Hansatu ta durqusa ta na duba hannun nata, cikin sanyin murya da mamakin halin mijin nata ta ce
"Yanzu akan wainar jikka biyu ka fiddawa diyar ka jini? Ka daki matar ka ? Wadda ta sadaukar da millions saboda Kai, anya Isa Kai ne Wanda na fada son shi shekaru Sha uku da Suka wuce kuwa? Anya Isa Kai ne Wanda ka min alqawurran kyautatawa kala kala? Haqqin ka ne fa ciyar da mu, Amma ba ka Yi, da na san ba Kai ka Basu ba dakkowa suka Yi,da bamu cin ta wallah, ka Yi hankuri inshaa Allahu ba mu koma tambayar ka kuddin abinci, ko Kuma mu dau abun ka, tashi Mu je na wanke maki, sannu"
Kalaman ta Basu ratsa fatar shi ba ma, balle tsokar jikin shi, hasalima wata fassarar ya Yi ta daban.
"Auu abun gori Kuma ya koma Hansatu? To da ni da ke wa ya fara furta ya na son wani? Sannan wa ye ya kafe ya guji kowa na shi saboda masoyi? Kar ki dakko maganar baya akan haramun din da ki ka ci ke da yaran ki, duk Wanda ya sake min wannan gangacin zai ga ganganci"
Kamar ta sanar da shi ba su ci haram ba, sai ta kama bakin ta, saboda ta San dukan banza za ta sha, har ya shiga daki ba Wanda ya sake motsawa a cikin su, sai sautin shassheqar kuka kawai ke tashi.
Ya na shiga daki ya laluba ko Ina bai samu ko sisi ba, fitowa ya Yi sannan ya ce,
"Ba kuci banza ba, ki tabbata kin nemo min dari ta biyu"
Daga Kai ta yi ta na bin shi da wani irin kallon mamaki.
Tunanin baya ta fara Yi, shekara goma Sha uku da Suka wuce, shi din yaron mahaifin ta ne,mutumin kano ne shi, ita Kuma mutuniyar zamfara, ya na ma mahaifin ta tuqin mota, ta haka suka fara soyayya, mahaifin ta na da lalurar hawan jini, kafin ya rasu soyayyar su batai qarfi ba, Amma dik da haka ya fuskanta, Dan haka ya ce ya bawa Isa ita, Yan Uwan ta da dangin ta kaf aka dinga surutu, Dan me zai dauki gudan Yar shi mace tilo ya aura mata yaron shi, budar bakin ta ta ce wa Mahaifiyar ta da Yayan ta ta na son shi.
An saka ranar biki da ta gama candy, mahaifin ta a satin ya rasu, sun shiga damuwa sosai a zuri'ar baki daya, saboda shi din mutumin kirki ne, me son dangi ne da taimakon su, mutan unguwa da abokan aikin shi sun koka rashin shi, balle Kuma iyalan shi, Hansatu kuwa har ruwa sai da aka sanya mata a asibiti, saboda yawan suman da ta dinga Yi.
Bayan rasuwar mahaifin su da wata bakwai, Yan Uwan ta Suka yanke shawarar a raba gado, sannan a aura mata Dan abokin mahaifin ta, Wanda ke riqe da kampanin Baban su, Dan ya ci gaba da kula da ita, da dukiyar ta, Amma ta dage, ta nace ta ce sai Isa ,a lokacin nan Isa kan shi ji yake in aka raba su zai iya shiga mawuyacin hali.
Rashin lafiyar da ta dinga Yi bai bawa dangin ta tausayin komai ba, su dai qoqarin su su raba ta da Isa, har korar shi akai daga wajen aiki.
Wata Rana da daddare ta tattare kayan ta tsaf, ta gudu wajen shi, a dakin da ya kama, ta roqe shi da su je ko masallaci ne a Daura masu aure, in yaso sun koma a matsayin mata da miji, ba mai raba su.
A wannan daren haka suka kwana daki daya, rungume da junan su, dik da ba abinda suka aikata na masha'a amma hakan ba daidai bane.
Washegari suka samu aka aura masu junan su a masallaci ,a ranar suka koma dangin Hansatu a matsayin ma'aurata,mahaifiyar ta ta ji takaicin hakan matuqa, Yayan ta babba ya ce ba za su bata ko sisi ba, a gaban mahaifiyar ta, kuma bata sanya baki ba, Hansatu kuwa yarinta ce? Giyar soyayya ce? Ko kuma rashin tarbiyya ne ya sanya ta shigewa dakin ta dake gidan ,har sun fara murna ta ji maganar su, kawai sai suka ganta dauke da akwati, ta kama hannun Isa suka bar gidan.
Da kudin sarqoqin ta suka sayi gidan da suke ciki, aka sanya sunan Isa a takardar,gadon ta da komai na gidan duk da kudin da ta gudu da shi ne suka siya.
Lokacin da kudi suka qare ne, Isa ya fara fito wa da Hansatu asalin kalar shi, rashin mutuncin yau daban na gobe daban, da ciki ko ba ciki in ya ga damar dukan ta, zai daka, da ya ji kawai ta bata masa rai, zai mata abinda kamar bai taba furta mata kalmar so ba.
Wani irin kuka ne mai tsanani ya turniqe Hansatu, Bilkisu ce ta fada jikin ta ta na kuka, ta ce,
"Mama dan Allah ki dena kukan haka nan, lehi na na, bazan sake ba,ki yahe min,"
Dan shafa bayan yarinyar kawai ta yi, ta ya za ta budi baki ta sanar da yaran ta me ta aikata? Sakayya ce ta qin yin biyayya ga mahaifiyar ta ke bin ta? Shin a wani bangaren ba umarnin mahaifin ta ta cika ba? Tunda dama ya so a yi auren? Ta ya zata sanar da yaran ta mahaifin su azzalumi ne? Shin wadannan abubuwan da suke faruwa da ita silar waye?
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 7:
Lawwali ne da yaran shi zaune a wani tsohon kamfani na gwamnati,waje ne da ya qunshi sashe sashe, da dikkan alamu ofishin ma'aikatan wajenne, Lawwali kuwa ya maida wajen a matsayin ma'aikatar shi ta yin garkuwa da dik Wanda aka bashi umarni, ko Kuma ra'ayin kan shi ya bashi da ya Yi hakan,waje ne da ya ke a cikin wani surquqin daji, da dikkan alamu gina shi aka fara yi domin wani aikin na gwamnati kuma aka bari ba tare da an kammala ba, ko an waiwaye shi, Lawwali da yaran shi na ta qoqarin Neman network dan yin waya amma sun rasa.
Ya fi awa uku ya na abu d'aya, cikin nasara kuwa ya samu wayar da ya ke son Yi ta shiga, da hanzari ya fara magana.
"Hello Excellency ba waku, yunwa ta addabe ni da yara na, ga shi ba ruwan sha, mu na buqatar kayan caji,...hello...hello"
Wayar ce ta sake katsewa, cikin fushi ya buga ta da qasa, ya daki jikin ginin wajen, wani dattijo ne daure a jikin ginshiqin da ke a tsakiyar faffadan wajen da suke, bakin shi ya bushe, da alama yunwa da qishirwa suna damun shi, idanun shi a rufe suke, ba ya ganin kowa, amma ya na sauraren su.
Cikin wahalalliyar murya ya ke magana,
"Yanzu Lawwali duk irin amanar ka da na dauka, na riqe, haka zaka saka min da shi? Ba irin taimakon da ban maka ba a rayuwa, amma saboda wancan dan adawar ya biya ku kudi qalilan kuke wulaqanta ni haka"
Cikin fushi Lawwali ya kalli mutumin da ya haife shi, ya shure shi da qafa, sannan ya naushe shi sau ba adadi, har sai da wani daga yaran shi ya riqe shi.
"Oga ka Yi hakuri,Kar ya mutu, in ya mutu Excellency ba ze Mana da kyau ba, ajiya kawai ya ce muyi, ba kisa ba, ya jaddada Mana hakan, sai bayan zabe mu sake shi"
Bangaje yaron nashi ya Yi ya duqa gaban bawan Allah n da ya gama duka, cikin qunci yake magana.
"Ka riqe ni amana? Wace iriyar amana ka riqe? Amanar shaye-shaye? Ko ta Neman mata da kisan kan mutane? Ko kuma amanar fyade da garkuwa da mutane Dan neman kudin fansa? Kai Bari ka ji, ka ga da ace Excellency ze sauka, Wanda ya sake Hawa ya ban irin wannan umarnin, shi ma qaddamar Masa zan, taimako d'aya ka min a duniya, shi ne Iyaye na Dake aiki a gidan gwamnati har yanzu, dik da ka sauka su na Nan suna ci gaba da Yi, da wannan aikin gidan mu suke ci su qoshi, su Yi sutura, Dan haka iyakar godiyar da zan maka kenan, in ma zan Yi maka godiya"
"Oga Lawwali ya suma fa,gashi ba ruwan yayyafa Masa"
Murmushin mugunta Lawwali ya Yi, babu bata lokaci ya kunce wandon shi ya fara tsiyaya ma wannan mutumin fitsari akai, sai kuwa gashi ya farfado.
Kula da abinda Lawwali ke Yi ne ya Sanya wannan bawan Allahn qoqarin kaucewa, Amma dake ya na a daddaure ne, sai ya kasa matsawa.
Dariya Lawwali da yaran shi Suka dinga Yi.
Har magariba ba wani bayani daga wajen gwamna, yunwa dik ta cinye su da qishirwa, ga wayoyi sun mace ba caji, sai torch lights suka kukkuna, su na Nan zaune, har isha'i ta Yi, Lawwali ne ya tada mutane uku ya ce su dau mota su shiga gari,su sama masu abinda za su ci,Dan ya na ta jiyo kukan yaran da ke killace a wasu sashen da ke gidan da ko rufin kwano babu a wasu sashen, ya kuwa tabbata yunwa ke damun su,kudi ya Basu akan su siyo Dan wani abu ko ba yawa a fara da shi, Kuma su tabbata sun samu ganin Gwamna a daren ko Kuma su Yi magana da shi ta waya, a Kai masu abinci da ruwa.
Har za su tafi Lawwali ya dakatar da su,
"Yauwa ga waya ta ku tafi da ita, a sama min caji"
"To Oga,"
Mota suka tada Suka dauki hanyar shiga gari.
Sun samu sabani da mutanen gwamna, Dan kuwa Basu jima da tafiya ba aka kawo qatuwar mota lode da abinci da dik abinda suke buqata.
Ba bata lokaci yaran Lawwali da za su Kai su goma suka dirar wa abincin suka dinga shigar wa wani daki ana lodewa, bayan sun kammala shigar da duk wani abu da ya kamata suka zauna cin biscuits da juice dan kawar da yunwa kafin matan da ke cikin wajen su dafa abincin, drivern da ya kawo saqon ne ya tsaya ya na bawa Lawwali saqon gwamna.
"Oga Lawwali gwauna ya ce na hwada maka, kudin fansa da za a ce dangin Lamido su bayar ace su basuwa milliyon dari biyar, kar a rage masu ko sisi, dan ya San ya saci ya hi haka nan, da zarar sun kawo kun amshe ku qarasa shi, ya gama Yi wa qasa banna"
Daga Kai kawai Lawwali ya Yi cikin Isa, da nuna shi ne oga a wajen,dik qoqarin cin binci da kowa ya ke, shi bai je ba ya na gefe, ya na son ya ga kowa ya qoshi har da yara da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3 Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51