ta qi samuwa, se gwadawa take.

Har aka yi azahar ta yi itama, ta kwanta Lawwali bai kira taba, ta fara hasala yanzu kam, amma ba yanda zata yi, gashi ba zata iya fushi da shi ba, saboda kalar son da take masa ma, ba zai bata damar fushi da shi ba.

Wayar ta ta sake laluba, ta shiga wajen rubuta saqo,ta hau rubutu kamar haka.

~Auwal dan Allah ka dauki kira na, zan iya rasa raina in har ban ji Muryar ka ba a yau, kai ne maganin quncin da zuciya ta ke ciki,kai ne farin ciki na,kasancewar ka tare da ni, shi ne cikar farin ciki na, pls ka kira ni, in ka ga saqo na, Ina son ka Auwal, and I really need u now, pls~

Abinci aka shigar mata da shi, ko daga kai ta kalla ma bata yi ba, ballantana su sanya ran za ta ci, duk magiya da roqo da mai aikin ta dinga yi, qarshe itama magiya da roqo, tare da kuka ta sanya wa matar, dole ta hakura ta barta.

Ita kadai ta san ya zuciyar ta take a yanzu, wani irin qunci da ciwo take mata, wace iriyar rayuwa take ciki? Ai da wannan azziqin gwanda talaucin da ba ze raba ka da imanin ka ba, akwai abubuwa da dama da suke zamewa bawa musiba, to ta tabbata wannan azziqin musiba ne a gare su, sai dai za ta yi ta addu'a Allah ya kare su daga fadawa halaka, duniya da lahira.

Abu kamar wasa, Lawwali bai kira Sultana ba, dik da cewa ya ga kiran ta, ya ga saqon ta, aiki ne ya mishi yawa, ga wajen da suke ba network sosai, yau kuwa tun cikin dare suka fita, suna ta kai takardun da aka riga aka dangwala wa yatsan zabe, mazabu kala kala.

A gajiye yake matuqa, ko ya kira ta be san me zai ce ba, ya san dole ta fuskanci gajiyar a Muryar shi, ba shi da abin kare kan shi, dan haka ya qi kiran ta, ya ci gaba da harkokin shi.

Wani sashe na zuciyar shi ya na jin ba dad'i , da bai kira ba, tunda ya san kalar yanda take son shi, ko Muryar shi taji ta na jin dadi a ran ta, kawar da tunanin ya yi, a fili ya furta,

"Gwanda ta ji zafin rashin kiran nawa ma ai, hakan ma wani punishment ne"

Kafin duhun dare ya shiga Sultana ta ji jiki,zazzaɓi mai mugun zafi ne ya kama ta, ba abinda take banda rawar sanyi, Hajiya Ikee ta shiga bangaren nasu ta tarar da Sultana kwance ta lullubu, sai rawar sanyi take, cikin tsananin damuwa ta isa gaban ta, ta na taba goshin ta, dan ture hannun ta sultana tayi, sanan ta juya baya, Hajiya Ikee, waya ta fara yi, akan a kira likita yanzun nan, cikin rawar murya sultana ta ce,

"Ko ya zo ba abinda zai iya min, ...ba na so ya zo,... ki barshi kawai, .....ki je ku ji sakamakon zaben da kuka riga kuka san ku ne ma zaku yi nasara"

Cikin washe baki, da rashin gane mai Sultana ta ce, ta miqe,

"Bari in tai, nahi son a hwadi komai a gabana gashi can ana ta hwadi, har yanzu akwai mazabun da ba su kai sakamakon su ba, da alama za mu samu nasara, mun godewa Allah, bari na tai, in likitan ya zaka sai mu taho a baki magani ke jiya? Allah shi yi miki albarka,"

A hankali ta amsa da

"Ameen"

Shin addu'ar irin su Hajiya ma na cin mutum ne? Ni Ko na ce uwa dai uwa ce, komai lalacewar ta, in ta yi addu'a inshaa Allah, Allah zai amsa, zunubin ta daban, addu'ar ta daban, da ace mummunan kalami zata yi ga dan ta zai same shi,kamar yanda Lamishi bata da burin da ya wuce ta zagi yaran ta, ta musu baki.

Likita ya zo da misalin tara na dare, ya bata magunguna, tare da bata shawarwarin rage tunani,domin jinin ta ya hau kadan, murmushi kawai ta yi masa ta yi godiya, Hajiya Ikee ta raka shi, ta koma wajen ta, dan dai ta san zabe kamar sun ci shi sun gama, amma me ke damun gudan jinin ta har jinin ta ya hau?

Cike da damuwa ta koma dakin, hawaye ta gani daga idon sultana ya na gangarewa a saman pillow duk da cewa  idanun nata na rufe ne.

Zama ta yi a gefen kan ta, tare da sanya hannu ta jaye gashin ta da ke gefen fuskar ta, ta shafa kan nata cikin kulawa da soyayya, irin ta uwa, cike da tausaya wa ta ce,

"Sulty Baby mi ka damun ki? Hawan jini? Mi ya maki zahi, da uwar ki da uban ki, ga dan uwan ki masu son ki? In akwai abinda ki ka so duniyar ga ki hwadi min ki na samun shi ko menene shi kuwa"

A wahalce Sultana ta daga ido ta kalli mahaifiyar ta, wadda take bata tsoro, tsoron gaske ma kuwa, dan bata san wanne ne halayen ta boyayyu ba kuma bayan wanda ta ji ta sani, cikin qunar rai ta ce,

"Kar ki damu,Wataqila wannan ciwon shi ne ajali na, wataqila kuma a hankali Allah ya yaye min, amma ku ba za ku iya min abinda nake so ba"

Cikin tsananin damuwa Hajiya Ikee ta sake mannewa a jikin Sultana, ta na jan ta jikin ta, da sigar lallashi, tausayi, soyayya, da tsantsar qauna,

"Habaaa Baby Sulty, wace irin magana ta wagga ki ke yi? Kin San dai ba abinda ki ke nema a duniyar nan ki rasa daga wajen mu, akan su wa muke fadi tashi dan mu tara abin duniya? Duk ba dan ku muke yi ba? Ki sanar da ni abinda ki ke so, yanzun nan zan sa a kawo maki shi"

"Hajiya kar ki damu, na fara lura da kuma sanin abinda za ki iya da wanda ba zaki iya ba, amma wannan kam na san ba zan same shi ba, Dan Allah ki bar wannan maganar ki tai an kusa sanar da sakamakon zabe"

"Rayuwar ki is more important to me, than anything else in the world my dear just tell me what you want and I will get it done for you yanzun ga"

Idanun sultana zafi suke kamar an zuba mata yaji, a hankali ta ware su a fuskar Hajiya Ikee wadda ta nuna tsantsar damuwa da gaskiyar maganar ta, na bawa sultana duk abinda take so.

"Auwal....Auwal shi ne abinda zuciya ta ka so, Auwal na ke so ku aura min, indai har da gaske ki ke za ki yi min duk abinda nake so, shi ne rayuwa ta, in ku ka hana ni auren shi Hajiya zan mutu"

Miqewa tsaye Hajiya Ikee ta yi tana kallon Sultana da wani irin kallon kan ki daya kuwa?

"Wane Auwal ki ke nufi? Lawwali driver? Ki na da hankali kuwa? Na haifi yarinya kamar ki, kyakkyawa, mai ilimin arabiyya da boko sannan ta b'ige da auren jahilin driver? Ki na hauka ne?"

"Hajiya ba fa jahili bane masanin qur'ani ne sosai, masanin qur'ani kuwa ai ba mai kira nai Jahili"

"Sai ni, ni zan kire shi jahili tunda banga alamar shi na aiki da shi ba, qur'ani ya hana neman ilimin boko ne? Namiji har namiji ace driving shikai? Ba da ni ba, kar ki bata min rai, ki nemi komai a waje na, amma banda wanga, yau ga zancen banza zancen yohi, to bari ki ji, kar ma ki kuskura ki wa mahaifin ku maganar ga, dan rai nai sai yahi nawa ɓaci, ba abinda ya tsana sama da talauci ga rayuwa tai, ba zai so ya miqa ki gidan wahala ba, na hwada maki tanadin da nake a kan ki, shi na ki ke debo min wahala? Sam ba zai yu ba,"

Ta na ta Masifa ta bar dakin, a qasan ran ta bata so suka rabu ta haka da diyar ta ta ba, musamman yanzu da bata da lafiya.

Sultana kuwa ko kukan ta kasa, tabbas sai yanzu ta fahimci me Auwal ke nufi,abinda babba ya hango dama an ce yaro ko ya hau rimi ba zai hango ba, ya riga ya fahimci ba za a bashi ita ba, ita kuma ta zaci son da iyayen ta ke mata zai taimake ta a bata wanda take so.

Ta na nan kwance ido biyu ta ji ana taken Nigeria, ana iface iface, a cikin gidan, rintse idanun ta tayi cikin qunar zuciya ta ce,

"Ban san sanda tallakan Nigeria zai bude ido nai ba, ban san sanda tallakan Nigeria zai fara addu'ar samun shugabanni wanda suka cancanta managarta ba, ba wanda suka so ba, ban san sanda tallakan Nigeria zai gyara tsakani nai da Allah ba, har Allah ya ji tausayin shi ya raba shi da shugabanni kamar su Daddy, ya Allah ka kawo mana qarshen wannan rayuwa mara aminci da muke ciki, ya Allah ka sa qasar mu Nigeria da duniya baki daya ta zama waje mai aminci ga bayin ka,"

"Ameeen Sulty Baby, ya jikin naki? Hajiya ta je ta na ta hwada, ban san akan mi take magana ba dai, amma na ji ta na akwai tanadin da ta yi akan ki, ko kin san akan mi taka magana?"

Murmushin da be kai ko ina ba ta yi wa Sultan da Ke bin ta da kallo, sannan ta ce,

"Ka manta mun je gidan dan takarar shugaban qasa?  To tun daga can ta fara ciniki na, ka shirya kaima za a yi naka kwanan nan, da ta samu wadda ta hito gidan kuddi za a saishe ka, Yah Sultan ina da wanda nika so, ta ce kar ma na bude baki na sanar da Daddy, sun gama maganar wanda za su bawa ni"

Hawaye ne suka fara tsartuwa daga idanun ta, ran Sultan ya ɓaci matuqa, zai d'auki komai akan shi, amma ba zai taba jure ganin Sultana cikin mummunan hali haka ba, nawa take har da za a ce hawan jini ya kama ta?

Cikin fushi ya bar d'akin, ta na ta kiran shi bai juya ba.

Ya na fita wayar ta na daukan ringing, da kyar ta janyo ta, ta na ganin sunan Auwal,  hannun ta ya d'au rawa, bakin ta na rawa saboda kukan da ya taso mata, ta na dauka kuwa ta fashe da kuka, Lawwali na jin kukan ta, ya ji wani abu mai qarfi ya daki zuciyar shi, ba ya son jin haka saboda ita, ba ya son jin damuwa da damuwar ta, amma ya kasa jurewa sai da ya tausasa murya ya ce,

"Ran ki shi dade ki yi min afuwa,na shiga matuqar busy ne, inda na tai ba network ,shi yasa ban dauka ba,amma ki yi hankuri, gani na dawo gida,dan Allah ki dena kukan"

Cikin shagwaba ta ce,

"In ka sake tafiya inda ba Network zan yi fushi da kai mai tsanani, ba zan sake kula ka ba"

Siririyar dariya ya yi, Sannan ya ce,

"A min ahuwa, in ki ka dena kula ni, ashe qarshen rayuwa ta ne ya zo, ba ke ba Mubaraka, lallai da zan zama kamar gunki, domin zan zam ba rayuwa a tare da ni"

Itan ma dariya ta saka, wadda ba zata iya tuna sanda ta yi dariya ba a ranar gaba daya.

"Na maka alqawarin sai ka mallake ni a matsayin matar ka, kuma sai mubaraka ta dawo gare mu lahiya"

Kalaman ta na qarshe ba karamin faranta ran shi suka yi ba,har ya ji sabon lamari game da ita...............

*Tambaya ta anan shi ne, Sultana da ke yi wa Lawwali alqawari, ta manta maganganun Hajiya ne?*

💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻


BY HAERMEEBRAERH



PAGE 34:


"Dakata min Sultan, kai har ka isa ka taho ka yi min titsiye? To bari ka ji, kai kan ka, ina nan na tanadar maka wadda za ka aura, lokaci nika jira, ta na kammala digirin ta ta dawo qasar ga za a daura muku aure, diya ce ga minister'n tsaro, kuma babbar diyar shi, na duba wayar ka tass na ga duk matan da ka ke mu'amala da su, duk ba ya wuce gaisuwa, Ita dai nigga ku na hira jefi jefi, tunda Allah ya sa hankalin ku ya gamu waje guda, Daddyn ku ya ma iyayen ta magana, kuma sun yi na'am, ka shirya, ana gama auren Sultana naka za a yi"

Baki Sultan ya sake kawai ya na mamaki, ya na namiji amma ana so a masa auren dole, to ba ma wannan ba, in an masa auren dole ya hakura tunda dama baida budurwar da ta kwanta masa ga rai, to ita sultana da ke son Lawwali fa?

"Hajiya na amince ku aura min duk wadda kuka so, amma fa ba zan amince ku aura wa sultana mutunin da bata qauna ba"

"To Uban mu, mun jiya, in an tashi auren sai ka hana,...dalla fita ka ban waje, yau so kuke sai kun batan duk wani farin ciki da nake ciki na ga alama"

Daddy ne ya shiga dakin bakin nan kamar gonar audiga, cikin, farin ciki ya ce ma Sultan,

"Ku shirya kai da qaunar ka gobe akwai party, around 1am, kwana za a yi ana murnar samun nasara, diyoyin gwamnoni ne suka partyn a Abuja, na san za ku buqaci kudi sosai, dan kusan kowa a wajen ya na taqama da uba nai, ga wannan, ku dauki duk nawa ya muku"

Wani dan kati ya miqa masa,wanda yake a matsayin makullin ma'ajiyar kudin Gwamnan, kallo kawai Sultan ya bisu da shi,ya kasa cewa komai, da kyar ya bude baki ya ce,

"Yaushe ku ka zama haka? Yaushe kuka dena damuwa da abinda muke so sai wanda kuke so? Yaushe za ku saki duniya, ku kama qiyama?"

Daddy bai fahimci ina Sultan ya dosa ba, ita da ta san akan me yake magana, tuni ta miqe, ta na son kawar da zancen Sultan ya sa kai ya bar dakin.

"Kwantar da hankalin ka ka jiya diyan ga in ka ce kabi nasu to fa ruwa ma sai an tauna musu an hadiye musu tsabar gata"

"Amma mi an kai mai ? Ban taba ganin Sultan ya yi hushi haka ba,mi kin kai mai? Ki hwadi min gaskiya ko inna bincika  na gano kin masa wani abu ran ki zai ɓaci, ban hada d'iya na  da kowa ba"

"Ni kuma ni na haihe su , har da ka ke hwadi min baka hada d'iyan ka da kowa ba, maganar wannan yaron driver ne taqi qarewa gidan ga, ya zo ya na wani hwadin magana yanda ya ga dama, to shi kan shi na sanar masa magana diyar Minister , shi na yake hushi "

Shiru ya yi bai ce komai ba, ya fita ya bar dakin, bai tsaya a ko ina ba sai dakin Sultana, ta na bathroom, ta na alwala, sai da ta gama ta fito taga wayar ta a hannun shi, ya na duddubawa, har ta isa gaban shi bai aje wayar ba sai da ya gama abinda yake.

"Sultana da dukkan alamu ki na son Lawwali, amma Sultana ki sani, ke baki san waye Lawwali ba, ni na san waye shi, ina mai baki shawara da ki hakura da shi, tun da wuri, tun lokaci bai qure miki ba"

"Daddy kenan, indai Hajiya ta ji ta gani, ta ke zaune da kai, banga dalilin da zai sa ni na kasa auren driver na ba"

Cikin rashin fahimta ya ce,

"Me ki ke nufi? Sultana yaushe kin ka hwara magana irin wannan? Me ki ke nufi da abinda kin ka hwadi yanzu?"

"Never mind Daddy, ina so nayi sallah, pls"

"Sultana ina son sanin damuwar ki, talk to ur Daddy Sulty Baby, ki sanar da ni mi ki ka so"

Cikin kuka ta ce,

"Daddy ka tambayi Hajiya, ta san komai, dan Allah ka barni na gana da Ubangiji na, shi ne kaɗai zai min maganin damuwa ta, Hajiya ta tabbatar min da ba zan samu me nake so wajen ku ba, yanzu ka tabbatar min da na hakura da farin ciki na, saboda bai muku ba, bai yi daidai da abinda kuke so ba, ni Auwal nike so, ba wani shugaban qasa ba,"

Daddyn su ne ya ja ta jikin shi ya na lallashi, a zuciyar shi kuwa ya na mamakin sanda ya yi sake Lawwali ya yi nasarar dasa soyayyar shi a zuciyar sultana haka, sai yanzu yake tunawa da alamomin da Hajiya ke sanar da shi, lallai ya yi sake, Lawwali na shirin yi masa babbar illa, indai har ta nan ya biyo.

"Ya isa kukan haka nan, zan yi tunani akan maganar, ki daina kuka"

Da sauri ta kalle shi, ta na son tabbtar da gaskiyar maganar shi, dan yanzu gaba daya ta cire yarda a tsakanin su, gani take komai nasu qarya ne.

Sai da ya ga ta daina kukan ya bar dakin, wajen Hajiya Ikee ya koma, ta na zaune ta zabga uban tagumi ta na tunanin yanda za ta raba tsakanin Lawwali da sultana.

"Ki na da gaskiya ashe da kin ka ce  na kori yaron nan daga gidan nan naqi ji, ashe ya min babbar illa ina zaune ba tare da na sani ba?"

Kamar an sosa mata inda ke mata qaiqayi haka ta miqe, kallon lokaci ta yi, ta ga ya tafi sosai, ta gaji tilis, kuma maganar nan na buqatar dogon nazari, ko kadan ba ta son batawa Sultana, amma dole ne ta raba tsakanin su da Lawwali.

"Wannan magana ta riga ta wuce, yanzu mafita za ka nemo mana, dan kuwa ba zan taba yarda diyar ciki na ta auri driver ba, yau ko min muqamin da za ka damqa masa a gwamnati walle ba ya hanawa a kire shi da driver, ba zan zama abin dariya cikin abukkai ba,dole ka dau mataki"

"Ba zaki gane ba, yanzu raba tsakanin sultana da Lawwali babbar musiba ce wallah, duk yanda zan miki bayanin yaron nan ba zaki gane ba, ni na san wane ne Lawwali,"

"Driver din? Me ye ba zan gane ba? Yau muke tare, ka kore shi kawai, shi bar gidan"

Bai ce mata komai ba ya fada bathroom.

Mita ta dunga yi tare da fadin ya sa yaron shi din nan da ke masa aiki, a sace Lawwalin ya bar doron qasa baki daya, Indai ze zame musu fitina akan dukkan tsarin su.

*************************

Sai guje guje suke abin su a katafaren tsakar gidan kakannin nasu, cike da nishad'i da jin dadi, ita kan ta
Showing 66001 words to 69000 words out of 150481 words