ta take addu'ar,dan ko labban ta ba ta so ta motsa,
'Ya Allah ga bawan ka nan Auwal, ya dawo gare ka, ya Allah ina roqa masa gafarar ka, ina roqa masa rahamar ka, ya Allah ka tausaya mishi kai mai tausayin bayin kane, Allah duk abinda ya aikata na zunubi Allah ka yafe masa, domin kai mai yawan gafara ne,Allah ka ni'imta qabarin shi, ka yalwata masa shi, ka haskaka masa shi,ya Allah ka masa hisabi mai sauqi a ranar tsayuwa, ya Allah ka bashi ikon amsa tambayoyin kabari cikin sauqi, Allah ka mishi rahama, ka gafarta masa'
Duqawa ta yi, bakin ta na rawa saboda kukan da ke taso mata, ta sumbaci goshin shi, sannan ta shafi fuskar shi, murmushin shi mai kyau ta ke so ta gani, amma ta san har abada hakan ba zai sake samuwa ba, kalmomin shi masu cike da so da qaunar ta take so ta ji, amma ta san hakan ba zai samu ba, kifa kan ta tayi, a qirjin shi ta rungume shi, ji take kamar kar a dauke shi, kamar ya farka ya ce Barakana wasa ta ni kai miki, Sultana ce ta duqa cikin qarfin halin da ke bawa Kowa mamaki, ta daga Mubarakan, ta rungume ta, sannan ta ja ta suka shiga ciki, su Jameelu suka bude qofar aka sake rufe Lawwali yanda ya dace, aka dauke shi sai makwancin shi na gaskiya.
Tunda suka shiga dakin na Lamishi, ba mai magana, sai kuka, Lamishi ta tabbata ta yi babban rashi, rashin da ko sanda iyayen ta suka rasu bata ji zafin shi kamar haka ba, tunawa da kalaman shi take, a kullum ba shi da burin da ya wuce iyayen shi su so shi shi da qanwar shi, a basu kulawa kamar sauran yara,amma daga ita har uban shi, sun gaza.
Rafka salati ta yi, ta fashe da kuka, na kusa da ita na ta bata hakuri, kukan 'Yabbuga da salatin ta ne ya ja hankalin mutane gare ta,
"Mun yi babban rashi, mun yi babban rashi, sannun mu da hankuri Lamishi Sannun mu da hankuri,kaiiii duniyar ga ba matabbata ba ce wallah,jiya jiya mun ka rabu ina ta bawa Dan Jumma labari har magana mun yi da Lawwali asheee asheee Lawwali kau gawa ce tsaye, mai rai ba bakin komi shi ke ba wallah,sannun mu da hankuri jama'a sannun mu da hankuri"
Surutai kawai 'Yabbuga ke zubawa, wanda ke nuni da cewa tabbas mutuwar Lawwali ta daki zuciyar ta, wani dogon numfashi ta ja sannan ta ce,
"Ina can hangame da baki, ina kwanan wahala, Dan Jummaa yaddawo yatas-san,ya ce daga gidan ga shike Lawwali ya mutu,la'ilaha illallahu"
Wata mata ce ta ce,
"Boyar Allah hankuri zaki, hankuri kowa shi ke yi wajen ga da kiggane mu, mata tai da qauna tai na ciki, su ma hankurin suke"
"Keeee wagga banni, banni yanda kin ka ganni, ba ki san ya nika ji ga zucciya ta ba,....Ohh rayuwa kenan, ina Mubarakar take, boyar Allah"
Miqewa ta yi ta bazama zuwa dakin, zaune ta gan su, da su Hajiya Ikee da Sultana, sai Mubaraka da ke kwance kusa da Sultanan, ta na ta sauke numfashi da kyar,ji take iskar shaqa ta mata kadan, amma haka take daurewa, ko dan kar Sultana ta sake samun wata damuwar.
"Sassanun mu da hankuri bayin Allah, Allah shi jiqan Lawwali, Allah shi gahwarta masa, sannun mu da hankuri, Hajiya Sannun mu da hankuri"
Amsa mata suka yi, tare da yi mata godiya.
Su na nan zaune mutanen unguwa aka fara kawo abincin sadaka, ai kuwa kafin kace me, masu zaman makoki an miqe an fara warwason abinci, kowa na son ya samu abinda zai kai bakin salati.
Sai a sannan ne Hajiya Ikee ta tuna Sultana ma bata karya ba, ga ciki, waya ta yi wa Sultan, ta ce ya samu ya ɗan siyo ko da kayan shayi ne me yawa da bread a kawo, saboda su karya, ai ba a zauna ba abinci ba.
Nan da nan kuwa ya aika su Jameelu, aka kawo kayan shayin da bread,bayan sun debi wanda za su yi amfani da shi, ta sa aka fidda sauran.
Duk yanda ta so ta matsa wa su Sultana su ci abinci qi sukai, dole ta hakura, ta ci ta bar su.
Haka akai ta zaman makoki, har kwana bakwai, sannan Hajiya Ikee ta tafi ta bar Sultana a gidan, ita da Mubaraka sun zama kamar hanta da jini, a koda yaushe su na tare da junan su, kowacce su na kallon 'yar uwar ta a matsayin Lawwali, domin su din masoyan shi ne, ya na ji da su.
Sultana bata bar gidan ba sai da aka yi arba'in a lokacin cikin ta ya shiga wata na tara, Mubaraka ke raka ta ganin likita, Sultan ya yi hakuri iya hakuri, domin ba zai iya bijiro da maganar kai masa amarya a wannan lokacin ba, amma tabbas ya na da buqatar matar shi.
Cikin Sultana har ya haura wata tara, ta wuce EDD din ta, haihuwa shiru, kuma ciki kullum aka je ganin likita zai ce lafiya qlou take.
Yau ma sun shirya tsaf dan zuwa asibiti ganin likita, Sultana ce ta ke ta yi wa Mubaraka magana akan ta hanzarta Sultan na jiran su a qofar gida.
Cikin sauri ta qarasa sanya hijabin ta ta sake yi wa Lamishi sallama suka fita, zaune yake a motar ya sha gayun shi da wata brown din shadda da baqar hula, hasken shi ya qara fita sosai, ya yi wani irin kyau,tunda suka shiga motar Suka gaishe shi, Mubaraka ta ja baki ta tsuke, lokaci zuwa lokaci ta na satar kallon shi ta madubi.
"B love ki kalle ni kan ki tsaye, ni din naki ne, ke kadai, ba sai kin yi ta satar kallo na ba kamar wani baqon saurayi a unguwa"
Kunya ce ta kama ta sosai, ta sa hannun ta ta kare fuskar ta, ta na kallon waje.
Sultana kuwa murmushi ta yi, tunawa da nata masoyin sai ya sanya kwalla taruwa a idon ta, har suka isa bata san wainar da su Sultan ke toyawa ba a motar.
Su na zaune a asibitin Mubaraka ta hango Hansatu riqe da Ahmad sai wani mutum a gefen ta, Hansatu ta yi shar da ita kamar ba Hansatun Isah da ta sani ba, ganin Ahmad ne ya sake tabbatar mata da cewa Hansatun ce dai.
Ta gaban su za ta wuce, har sun gota su ta koma baya,
"Ahhh Ahhh Mubaraka d'iyar albarka, kwana da yawa"
"Aunty Hansatu ina kwana, ya gida, ya su Ameenatu,"
"Lahiya qalou, ya bayan rabuwaaa? Ina mutanen shiyyar mu, ya su Lamishi, ya yayan ki, ina hwata kowa lahiya"
Cike da murmushi Mubaraka ta ce,
"Kowa lahiya lau Aunty Hansatu, Yayana ne dai Allah ya yi mai rasuwa har an yi arba'in ma, waccan matar shi ta, mun ka kawo ganin likita,"
Salati Hansatu ta yi, sanan ta ja Mubaraka su ka ɗan koma gefe,
"Allahu akbar, Allah ya jiqan shi, dan Allah ki gaishe min da su Lamishi, ina nan tahe, ban sani ba, ban da labari, dan tunda na tai ban koma ba da nayi aure ne ma Asshibi ta tai, dan mu na gaisawa ta waya da ita, jehi jehi, bata sanar da ni wannan babban rashi da an kai ba, Allah shi gahwarta mai"
Mubaraka na son Hansatu, saboda mace ce mai kirki, ta ji dadin yanda ta nuna kulawar ta, kallon mutumin dake mata ta'aziyya ta yi, sannan ta ce,
"Aunty Hansatu wanga na Yayan nawa?"
"Shi na Mubaraka, shi na wanda iyaye na sun ka so na aura tun kahin Isah, Allah be nufa ba sai yanzu"
"Allah Sarki, matar mutum kabarin shi,Allah shi sanya alkhairi aunty,"
"Ameeen na gode, Ahmad mun ka kawo ganin likitan yara ba shi da lahiya, bari mu tai, sai na shigo shiyyar"
"Allah shi bi da lahiya sai kin zo din, na gode"
Shafa kan Ahmad Mubaraka ta yi, ta ce ya gaida su Ameenatu, dan ya san ta sosai, Islamiyya daya suke zuwa, ita a babban aji take, murmushi ya yi, har da daga mata hannu ya tafi, Sultana ta shiga ganin likita, Sultan ya zo ya tsaya a gefen mubaraka, da ke kallon inda su Hansatu suka bi dauke da murmushi, dan dukan kafadar ta ya yi kadan, da tashi, sannan ya ce,
"Da ace za a kawon ke yau, kema nan da wata tara ko goma za ki haifa mana baby, nan da shekara bakwai ya zama kamar wancan yaron,"
Kunya ce ta bi ta lullube Mubaraka, ta rasa ina za ta sanya kan ta, su na nan tsaye suka ga an gunguro da gado, Sultana na kai, da sauri Mubaraka da Sultan suka yi kan ta, gani suka yi ta na ta yatsina fuska, kamar za ta yi kuka.
"Me ya hwaru?"
"Daga duba ta naquda ta taso, zamu kai ta dakin haihuwa, ku je ku kawo kayan haihuwa"
Cikin sauri kuwa Mubaraka ta duqa gaban Sultana ta ce,
"Sannu Aunty Sultana, Allah shi sauke ki lahiya, Allah shi kawo miki haihuwar da sauqi, bari mu tai mu doko kayan,"
Shafa kan Sultana, Sultan ya yi, Sannan suka tafi.
A dakin haihuwa kuwa banda kiran sunan Allah ba abinda sultana ke yi, irin azabar da take ji ba ta da misali.
Cikin ikon Allah kafin Mubaraka su je su dawo, ta samu haihuwar yaron ta namiji, sambalele, dan lukuti kamar OO.
Duk ya cika dakin da kuka, Midwife din da ta karbi haihuwar sai tsokanar shi take da kiran shi ragon maza, a ido gashi kamar namiji, amma sai kuka, Sultana kuwa kuka kawai take, zuciyar ta ta shiga wani irin yanayi wanda ba shi da misali,tun Nurses na ganin kamar kukan Murna ne, har abun ya basu mamaki,
"Boyar Allah kukan ga ya yi yawa, ke da zaki godewa Allah, sai ki zanka kuka haka?"
Mubaraka ce ta leqa kan ta dakin,riqe da kayan baby, kamar yanda aka buqata, Sultana na ganin ta, ta sake bare baki da kuka, Mubaraka ta fahimci kukan me take, kawai sai ta ji hawaye ya na gudu a nata kuncin, qarasawa ta yi, ta duqa ta rungume Sultanan, ita ma rungume ta tayi da duk wani qarfin da ya rage mata, kuka sukai ta yi, kamar ranar ne Lawwali ya tafi ya bar su.
Da kyar Nurses din wajen suka raba su, cikin kuka Mubaraka ta ce,
"Ku yi hankuri dole mu yi kuka, mahaifin yaron ya rasu,tunawa da shi ne ya sa mu kokawa, da ace shi na nan da na tabbatar sai ya maku kyautar da za ku san kun karbi haihuwar matar so, na tabbatar da ya na nan da kun tabbata kun jima baku ga uban da ke son matar shi da d'an shi ba kamar shi,da za ku yi mamakin shin waya hi so a tsakanin mu ukun nan, matar shi? Dan shi? Ko qauna tai? Zuciyar shi cike take da soyayya, wadda in ya na wa mutum,sai mutum shi zaci shi kadai ya ke so,wannan dalili ne ya sa muke kuka, mun rasa wani bangare na jikin mu, kuma a yau mun samu wani bangare na jikin mu"
Wata midwife a wajen ce ta share hawayen ta ta ce,
"Allah Sarki, ku yi hankuri, Allah ba shi barin wani dan wani shi ji dad'i, Allah shi raya,"
"Ameeen"
An gyara jariri, da mahaifiyar shi, Sultan ya yi wa yaro huduba da suna Muhammad Auwal,Sultana kuwa qin bari ta yi a aje yaro nesa da ita, in ba Mubaraka ce ta dauke shi ba, kowa ya dauke shi za ta yi ta magana a miqa shi, ba kunya ba tsoron surutun mutane.
Kwanan su biyu a asibitin aka sallame ta, ta koma gidan Hajiya Ikee, nan fa Sultana ta ga gata, Mubaraka ba tare da wani tunani ba ta tattaro kayan su, ta taho gidan Hajiya Ikee, Sultan ya ji dadin hakan matuqa.
Ranar suna mutanen Tudun faila sun samu halartar sunan, an yi suna ba laifi, ba yabo ba fallasa.
Bayan Suna Lamishi ta tattara sauran kayan Mubaraka ta aiko mata da su, tare da yi mata aiken Fatan alkhairi daga wajen Jameelu, yana ta mata dariya yake bata saqon, ya ce,
"Mama 'Yabbuga ta ce dama haka ki ka so, ki koma gidan mijin ki, tunda ba su kai ki ba to gashi ke samu dama"
"Kaiiiii ya Salam, matar ga ta iya sheri wallah,"
Sultan ne da ya shiga dakin da Mubarakan ke da zama a gidan ya ce,
"Ai Jameelu na ke hwada maka harda roqo na ta yi wai na ce su Mama 'Yabbuga su maishe ta dakin ta"
"Innalillahi Yah Sultan yaushe mun kai haka da kai"
"Rannannn, ki tuna mana, rannan"
Dariya Jameelu ya dinga yi, ya na jin dadin ganin farin ciki a fuskar yayar tashi ,sallama ya musu ya koma gida, Sultan kuwa cewa ya yi,
"Tooo amarya ta, tunda yanzu kowa ya nutsu, mu ma ya kamata mu nutse cikin dausayin soyayyar mu ko? Yaushe za ki koma dakin ki? Nan dai dakin baqi na"
"Ba rana, ba dai ka yi min sheri ba?"
Dan tura baki ta yi ita a dole ranta ya ɓaci, ba tare da ta ji takun shi ba, ta ji an sumbaci lips din ta da ta tura gaba, da sauri ta kalle shi, dariya ya mata, sannan ya mata gwalo zai gudu, take masa baya ta yi, suka fita su na gudu su na dariya, dakin shi ya fada, ya na sane ya bar qofar a bude, ta na shiga ya mayar ya rufe, ya maida ta jikin qofar ya mata rumfa, kallon ta ya ke daga saman idanun shi har zuciyar shi, ya na haddace duk wani tudu da kwari na fuskar ta,Itan ma da kallo ta bi shi, cike da wani irin yanayi da bata taba shiga kalar shi ba a rayuwar ta, murya can qasa Sultan yace,
"Gudun mi ki ke yi haka?"
"Ramawa zan yi"
"Me za ki rama?"
Shiru ta yi ta maida kan ta qasa, ta na wasa da rigar ta da ta kama ta gefen dama
"Gani tau rama"
"Na yahe maka"
"Ni kuma ban yahe ba sai kin rama"
"Ni dai nace na yahe"
"Ni kuma na ce ban yahe ba"
"Allah na yahe maka, ka ga ka bari na tai aunty Sultana na can qasa ita da Hajiya su na jira na na tai na goyi Yaya"
"Ni kuma ga ni mijin ki ina so ki rama abinda na miki, ko ki bari na rama miki, sai ki koma"
Shiru ta yi ta na kallon shi, cike da so da qaunar shi,
"In rama miki ko?"
Daga kai ta yi, a hankali,tare da runtse idanun ta, babu bata lokaci kuwa Sultan ya dora lips din shi saman nata, tun Mubaraka bata mayar masa, har sai data maida hankalin ta, da nutsuwar ta wajen rama abinda yake mata.
A yammacin ranar Sultan ya samu angwancewa da amaryar shi Mubaraka.
Hajiya da Sultana tunda suka ji shiru ba su bi sahun su ba, sai bayan da magariba ta yi, ba su ga Mubaraka ba, kawai sai suka yi sallar su, suka ci abincin su, suka bar musu nasu,ita da Sultan.
Sultan ya so ya kira Sultana ta taimaka wa Mubaraka, amma ta qi sam, ta ce za ta iya kula da kan ta kar ya manta ba na farko bane ba, wanda shi ji ya yi kamar ba a taba mata wata hanya ba shi ya fara sanin ta 'ya mace (aikin d'inkin bature da cin kaji da kayan marmari kenan) , dan haka da taimakon shi ta gyara kan ta, ta gasa jikin ta da kyau da ruwan dumi, dan akwai komai da take buqata a dakin Sultan din, kayan ta ne kawai ke can dakin da baqin.
Sai da ya bari qafa ta dauke, kowa ya haye sama, ya shiga dakin baqin ya tattaro komai na Mubaraka ya mayar dakin shi.
Kafin ta gama shiryawa ya tafi debo musu abinci, ya na dumama abincin a microwave ya na murmushi, ya na nan tsaye Sultana ta fito diban ruwan zafi a flask da take sha.
Ganin shi ta yi ya nata zabga murmushi dariya ta yi, ta ce,
"Ango ka sha qamshi, ni da na ji qamshin jikin ka ma na zaci Mubaraka ce, ashe kai ne"
"Sultana baki da kunya ko?"
Dariya suka kwashe da ita sannan suka tafa,
"Bari kawai, Allah ya ma yarinyar can albarka, amma ni ina mamaki, an ce an taba mata fyade, amma ban ji wata alama da ta nuna hakan ba, ko dai dan ban san kan abun bane?"
"Wataqila dan baka san kan abun bane, and akwai matan da suke da baiwa, kamar wadda ka ke fada yanzu ba zata taba komawa da budurcin ta ba, amma fa ba za a ji ta a bude ba sosai, sannan ka san matan garin ga dai da gyara ko? Na tabbata an gyara ta sosai, musamman da sun ka san me ya hwaru da ita a baya"
Jinjina kai kawai Sultan ya yi, dan ya san me ya tarar, tabbas to iyayen ta sun masa qoqari matuqa.
Abincin ya haɗa musu, ya mata sai da safe, ya ce ta shafa masa kan Auwal.
Murmushi ta yi,ta na jin wani irin dad'i da farin cikin ganin annuri a fuskar yayan nata.
Bayan sun ci abincin su,sukai kwanciyar su, Sultan ya rungume amaryar shi kamar an ce masa ga masu kilinafin matan mutane nan.
**************************
Sai bayan wata biyu da haihuwar Sultana Hansatu ta samu zuwa can Tudun faila, dan yi musu gaisuwa, ta samu labarin an yi wa Mubaraka aure, nan ta nemi adireshin gidan aka bata, daga nan mijin ta abin son ta, ya kai ta gidan tsohon gwamna Halliru, ba ya jin nauyi ko ganin bata lokaci,in zai kai ta unguwa, ko ina ne kuwa.
Mubaraka ta ji dadin ganin ta sosai, sun sha hira matuqa kafin Hansatu ta tafi.
Tunda Hansatu ta je gida take bawa Hajiya Labarin Sultana, har sai da Hajiya ta ce,
"Gaskiya da za su bamu ita Musa shi aure, da mun gode musu, maganar yaro kuwa ai shi d'a na kowa ne,na tabbata Musa zai riqe shi kamar shi ya haihe shi,"
Cike da murna Hansatu ta ce,
"Kwarai kuwa, ki duba ki gani, yanda Yah Abdullah ke son su Ameenatu, yanzu hwa ba ya so na kira shi da kowanne suna sai da Baban Ahmad,diyan nan gaba daya sun mance da uban su, tunda daidai da rana guda ba na iya tuna sanda ya dauki dayan su, balle har ya musu wasa, amma shi
Showing 147001 words to 150000 words out of 150481 words
'Ya Allah ga bawan ka nan Auwal, ya dawo gare ka, ya Allah ina roqa masa gafarar ka, ina roqa masa rahamar ka, ya Allah ka tausaya mishi kai mai tausayin bayin kane, Allah duk abinda ya aikata na zunubi Allah ka yafe masa, domin kai mai yawan gafara ne,Allah ka ni'imta qabarin shi, ka yalwata masa shi, ka haskaka masa shi,ya Allah ka masa hisabi mai sauqi a ranar tsayuwa, ya Allah ka bashi ikon amsa tambayoyin kabari cikin sauqi, Allah ka mishi rahama, ka gafarta masa'
Duqawa ta yi, bakin ta na rawa saboda kukan da ke taso mata, ta sumbaci goshin shi, sannan ta shafi fuskar shi, murmushin shi mai kyau ta ke so ta gani, amma ta san har abada hakan ba zai sake samuwa ba, kalmomin shi masu cike da so da qaunar ta take so ta ji, amma ta san hakan ba zai samu ba, kifa kan ta tayi, a qirjin shi ta rungume shi, ji take kamar kar a dauke shi, kamar ya farka ya ce Barakana wasa ta ni kai miki, Sultana ce ta duqa cikin qarfin halin da ke bawa Kowa mamaki, ta daga Mubarakan, ta rungume ta, sannan ta ja ta suka shiga ciki, su Jameelu suka bude qofar aka sake rufe Lawwali yanda ya dace, aka dauke shi sai makwancin shi na gaskiya.
Tunda suka shiga dakin na Lamishi, ba mai magana, sai kuka, Lamishi ta tabbata ta yi babban rashi, rashin da ko sanda iyayen ta suka rasu bata ji zafin shi kamar haka ba, tunawa da kalaman shi take, a kullum ba shi da burin da ya wuce iyayen shi su so shi shi da qanwar shi, a basu kulawa kamar sauran yara,amma daga ita har uban shi, sun gaza.
Rafka salati ta yi, ta fashe da kuka, na kusa da ita na ta bata hakuri, kukan 'Yabbuga da salatin ta ne ya ja hankalin mutane gare ta,
"Mun yi babban rashi, mun yi babban rashi, sannun mu da hankuri Lamishi Sannun mu da hankuri,kaiiii duniyar ga ba matabbata ba ce wallah,jiya jiya mun ka rabu ina ta bawa Dan Jumma labari har magana mun yi da Lawwali asheee asheee Lawwali kau gawa ce tsaye, mai rai ba bakin komi shi ke ba wallah,sannun mu da hankuri jama'a sannun mu da hankuri"
Surutai kawai 'Yabbuga ke zubawa, wanda ke nuni da cewa tabbas mutuwar Lawwali ta daki zuciyar ta, wani dogon numfashi ta ja sannan ta ce,
"Ina can hangame da baki, ina kwanan wahala, Dan Jummaa yaddawo yatas-san,ya ce daga gidan ga shike Lawwali ya mutu,la'ilaha illallahu"
Wata mata ce ta ce,
"Boyar Allah hankuri zaki, hankuri kowa shi ke yi wajen ga da kiggane mu, mata tai da qauna tai na ciki, su ma hankurin suke"
"Keeee wagga banni, banni yanda kin ka ganni, ba ki san ya nika ji ga zucciya ta ba,....Ohh rayuwa kenan, ina Mubarakar take, boyar Allah"
Miqewa ta yi ta bazama zuwa dakin, zaune ta gan su, da su Hajiya Ikee da Sultana, sai Mubaraka da ke kwance kusa da Sultanan, ta na ta sauke numfashi da kyar,ji take iskar shaqa ta mata kadan, amma haka take daurewa, ko dan kar Sultana ta sake samun wata damuwar.
"Sassanun mu da hankuri bayin Allah, Allah shi jiqan Lawwali, Allah shi gahwarta masa, sannun mu da hankuri, Hajiya Sannun mu da hankuri"
Amsa mata suka yi, tare da yi mata godiya.
Su na nan zaune mutanen unguwa aka fara kawo abincin sadaka, ai kuwa kafin kace me, masu zaman makoki an miqe an fara warwason abinci, kowa na son ya samu abinda zai kai bakin salati.
Sai a sannan ne Hajiya Ikee ta tuna Sultana ma bata karya ba, ga ciki, waya ta yi wa Sultan, ta ce ya samu ya ɗan siyo ko da kayan shayi ne me yawa da bread a kawo, saboda su karya, ai ba a zauna ba abinci ba.
Nan da nan kuwa ya aika su Jameelu, aka kawo kayan shayin da bread,bayan sun debi wanda za su yi amfani da shi, ta sa aka fidda sauran.
Duk yanda ta so ta matsa wa su Sultana su ci abinci qi sukai, dole ta hakura, ta ci ta bar su.
Haka akai ta zaman makoki, har kwana bakwai, sannan Hajiya Ikee ta tafi ta bar Sultana a gidan, ita da Mubaraka sun zama kamar hanta da jini, a koda yaushe su na tare da junan su, kowacce su na kallon 'yar uwar ta a matsayin Lawwali, domin su din masoyan shi ne, ya na ji da su.
Sultana bata bar gidan ba sai da aka yi arba'in a lokacin cikin ta ya shiga wata na tara, Mubaraka ke raka ta ganin likita, Sultan ya yi hakuri iya hakuri, domin ba zai iya bijiro da maganar kai masa amarya a wannan lokacin ba, amma tabbas ya na da buqatar matar shi.
Cikin Sultana har ya haura wata tara, ta wuce EDD din ta, haihuwa shiru, kuma ciki kullum aka je ganin likita zai ce lafiya qlou take.
Yau ma sun shirya tsaf dan zuwa asibiti ganin likita, Sultana ce ta ke ta yi wa Mubaraka magana akan ta hanzarta Sultan na jiran su a qofar gida.
Cikin sauri ta qarasa sanya hijabin ta ta sake yi wa Lamishi sallama suka fita, zaune yake a motar ya sha gayun shi da wata brown din shadda da baqar hula, hasken shi ya qara fita sosai, ya yi wani irin kyau,tunda suka shiga motar Suka gaishe shi, Mubaraka ta ja baki ta tsuke, lokaci zuwa lokaci ta na satar kallon shi ta madubi.
"B love ki kalle ni kan ki tsaye, ni din naki ne, ke kadai, ba sai kin yi ta satar kallo na ba kamar wani baqon saurayi a unguwa"
Kunya ce ta kama ta sosai, ta sa hannun ta ta kare fuskar ta, ta na kallon waje.
Sultana kuwa murmushi ta yi, tunawa da nata masoyin sai ya sanya kwalla taruwa a idon ta, har suka isa bata san wainar da su Sultan ke toyawa ba a motar.
Su na zaune a asibitin Mubaraka ta hango Hansatu riqe da Ahmad sai wani mutum a gefen ta, Hansatu ta yi shar da ita kamar ba Hansatun Isah da ta sani ba, ganin Ahmad ne ya sake tabbatar mata da cewa Hansatun ce dai.
Ta gaban su za ta wuce, har sun gota su ta koma baya,
"Ahhh Ahhh Mubaraka d'iyar albarka, kwana da yawa"
"Aunty Hansatu ina kwana, ya gida, ya su Ameenatu,"
"Lahiya qalou, ya bayan rabuwaaa? Ina mutanen shiyyar mu, ya su Lamishi, ya yayan ki, ina hwata kowa lahiya"
Cike da murmushi Mubaraka ta ce,
"Kowa lahiya lau Aunty Hansatu, Yayana ne dai Allah ya yi mai rasuwa har an yi arba'in ma, waccan matar shi ta, mun ka kawo ganin likita,"
Salati Hansatu ta yi, sanan ta ja Mubaraka su ka ɗan koma gefe,
"Allahu akbar, Allah ya jiqan shi, dan Allah ki gaishe min da su Lamishi, ina nan tahe, ban sani ba, ban da labari, dan tunda na tai ban koma ba da nayi aure ne ma Asshibi ta tai, dan mu na gaisawa ta waya da ita, jehi jehi, bata sanar da ni wannan babban rashi da an kai ba, Allah shi gahwarta mai"
Mubaraka na son Hansatu, saboda mace ce mai kirki, ta ji dadin yanda ta nuna kulawar ta, kallon mutumin dake mata ta'aziyya ta yi, sannan ta ce,
"Aunty Hansatu wanga na Yayan nawa?"
"Shi na Mubaraka, shi na wanda iyaye na sun ka so na aura tun kahin Isah, Allah be nufa ba sai yanzu"
"Allah Sarki, matar mutum kabarin shi,Allah shi sanya alkhairi aunty,"
"Ameeen na gode, Ahmad mun ka kawo ganin likitan yara ba shi da lahiya, bari mu tai, sai na shigo shiyyar"
"Allah shi bi da lahiya sai kin zo din, na gode"
Shafa kan Ahmad Mubaraka ta yi, ta ce ya gaida su Ameenatu, dan ya san ta sosai, Islamiyya daya suke zuwa, ita a babban aji take, murmushi ya yi, har da daga mata hannu ya tafi, Sultana ta shiga ganin likita, Sultan ya zo ya tsaya a gefen mubaraka, da ke kallon inda su Hansatu suka bi dauke da murmushi, dan dukan kafadar ta ya yi kadan, da tashi, sannan ya ce,
"Da ace za a kawon ke yau, kema nan da wata tara ko goma za ki haifa mana baby, nan da shekara bakwai ya zama kamar wancan yaron,"
Kunya ce ta bi ta lullube Mubaraka, ta rasa ina za ta sanya kan ta, su na nan tsaye suka ga an gunguro da gado, Sultana na kai, da sauri Mubaraka da Sultan suka yi kan ta, gani suka yi ta na ta yatsina fuska, kamar za ta yi kuka.
"Me ya hwaru?"
"Daga duba ta naquda ta taso, zamu kai ta dakin haihuwa, ku je ku kawo kayan haihuwa"
Cikin sauri kuwa Mubaraka ta duqa gaban Sultana ta ce,
"Sannu Aunty Sultana, Allah shi sauke ki lahiya, Allah shi kawo miki haihuwar da sauqi, bari mu tai mu doko kayan,"
Shafa kan Sultana, Sultan ya yi, Sannan suka tafi.
A dakin haihuwa kuwa banda kiran sunan Allah ba abinda sultana ke yi, irin azabar da take ji ba ta da misali.
Cikin ikon Allah kafin Mubaraka su je su dawo, ta samu haihuwar yaron ta namiji, sambalele, dan lukuti kamar OO.
Duk ya cika dakin da kuka, Midwife din da ta karbi haihuwar sai tsokanar shi take da kiran shi ragon maza, a ido gashi kamar namiji, amma sai kuka, Sultana kuwa kuka kawai take, zuciyar ta ta shiga wani irin yanayi wanda ba shi da misali,tun Nurses na ganin kamar kukan Murna ne, har abun ya basu mamaki,
"Boyar Allah kukan ga ya yi yawa, ke da zaki godewa Allah, sai ki zanka kuka haka?"
Mubaraka ce ta leqa kan ta dakin,riqe da kayan baby, kamar yanda aka buqata, Sultana na ganin ta, ta sake bare baki da kuka, Mubaraka ta fahimci kukan me take, kawai sai ta ji hawaye ya na gudu a nata kuncin, qarasawa ta yi, ta duqa ta rungume Sultanan, ita ma rungume ta tayi da duk wani qarfin da ya rage mata, kuka sukai ta yi, kamar ranar ne Lawwali ya tafi ya bar su.
Da kyar Nurses din wajen suka raba su, cikin kuka Mubaraka ta ce,
"Ku yi hankuri dole mu yi kuka, mahaifin yaron ya rasu,tunawa da shi ne ya sa mu kokawa, da ace shi na nan da na tabbatar sai ya maku kyautar da za ku san kun karbi haihuwar matar so, na tabbatar da ya na nan da kun tabbata kun jima baku ga uban da ke son matar shi da d'an shi ba kamar shi,da za ku yi mamakin shin waya hi so a tsakanin mu ukun nan, matar shi? Dan shi? Ko qauna tai? Zuciyar shi cike take da soyayya, wadda in ya na wa mutum,sai mutum shi zaci shi kadai ya ke so,wannan dalili ne ya sa muke kuka, mun rasa wani bangare na jikin mu, kuma a yau mun samu wani bangare na jikin mu"
Wata midwife a wajen ce ta share hawayen ta ta ce,
"Allah Sarki, ku yi hankuri, Allah ba shi barin wani dan wani shi ji dad'i, Allah shi raya,"
"Ameeen"
An gyara jariri, da mahaifiyar shi, Sultan ya yi wa yaro huduba da suna Muhammad Auwal,Sultana kuwa qin bari ta yi a aje yaro nesa da ita, in ba Mubaraka ce ta dauke shi ba, kowa ya dauke shi za ta yi ta magana a miqa shi, ba kunya ba tsoron surutun mutane.
Kwanan su biyu a asibitin aka sallame ta, ta koma gidan Hajiya Ikee, nan fa Sultana ta ga gata, Mubaraka ba tare da wani tunani ba ta tattaro kayan su, ta taho gidan Hajiya Ikee, Sultan ya ji dadin hakan matuqa.
Ranar suna mutanen Tudun faila sun samu halartar sunan, an yi suna ba laifi, ba yabo ba fallasa.
Bayan Suna Lamishi ta tattara sauran kayan Mubaraka ta aiko mata da su, tare da yi mata aiken Fatan alkhairi daga wajen Jameelu, yana ta mata dariya yake bata saqon, ya ce,
"Mama 'Yabbuga ta ce dama haka ki ka so, ki koma gidan mijin ki, tunda ba su kai ki ba to gashi ke samu dama"
"Kaiiiii ya Salam, matar ga ta iya sheri wallah,"
Sultan ne da ya shiga dakin da Mubarakan ke da zama a gidan ya ce,
"Ai Jameelu na ke hwada maka harda roqo na ta yi wai na ce su Mama 'Yabbuga su maishe ta dakin ta"
"Innalillahi Yah Sultan yaushe mun kai haka da kai"
"Rannannn, ki tuna mana, rannan"
Dariya Jameelu ya dinga yi, ya na jin dadin ganin farin ciki a fuskar yayar tashi ,sallama ya musu ya koma gida, Sultan kuwa cewa ya yi,
"Tooo amarya ta, tunda yanzu kowa ya nutsu, mu ma ya kamata mu nutse cikin dausayin soyayyar mu ko? Yaushe za ki koma dakin ki? Nan dai dakin baqi na"
"Ba rana, ba dai ka yi min sheri ba?"
Dan tura baki ta yi ita a dole ranta ya ɓaci, ba tare da ta ji takun shi ba, ta ji an sumbaci lips din ta da ta tura gaba, da sauri ta kalle shi, dariya ya mata, sannan ya mata gwalo zai gudu, take masa baya ta yi, suka fita su na gudu su na dariya, dakin shi ya fada, ya na sane ya bar qofar a bude, ta na shiga ya mayar ya rufe, ya maida ta jikin qofar ya mata rumfa, kallon ta ya ke daga saman idanun shi har zuciyar shi, ya na haddace duk wani tudu da kwari na fuskar ta,Itan ma da kallo ta bi shi, cike da wani irin yanayi da bata taba shiga kalar shi ba a rayuwar ta, murya can qasa Sultan yace,
"Gudun mi ki ke yi haka?"
"Ramawa zan yi"
"Me za ki rama?"
Shiru ta yi ta maida kan ta qasa, ta na wasa da rigar ta da ta kama ta gefen dama
"Gani tau rama"
"Na yahe maka"
"Ni kuma ban yahe ba sai kin rama"
"Ni dai nace na yahe"
"Ni kuma na ce ban yahe ba"
"Allah na yahe maka, ka ga ka bari na tai aunty Sultana na can qasa ita da Hajiya su na jira na na tai na goyi Yaya"
"Ni kuma ga ni mijin ki ina so ki rama abinda na miki, ko ki bari na rama miki, sai ki koma"
Shiru ta yi ta na kallon shi, cike da so da qaunar shi,
"In rama miki ko?"
Daga kai ta yi, a hankali,tare da runtse idanun ta, babu bata lokaci kuwa Sultan ya dora lips din shi saman nata, tun Mubaraka bata mayar masa, har sai data maida hankalin ta, da nutsuwar ta wajen rama abinda yake mata.
A yammacin ranar Sultan ya samu angwancewa da amaryar shi Mubaraka.
Hajiya da Sultana tunda suka ji shiru ba su bi sahun su ba, sai bayan da magariba ta yi, ba su ga Mubaraka ba, kawai sai suka yi sallar su, suka ci abincin su, suka bar musu nasu,ita da Sultan.
Sultan ya so ya kira Sultana ta taimaka wa Mubaraka, amma ta qi sam, ta ce za ta iya kula da kan ta kar ya manta ba na farko bane ba, wanda shi ji ya yi kamar ba a taba mata wata hanya ba shi ya fara sanin ta 'ya mace (aikin d'inkin bature da cin kaji da kayan marmari kenan) , dan haka da taimakon shi ta gyara kan ta, ta gasa jikin ta da kyau da ruwan dumi, dan akwai komai da take buqata a dakin Sultan din, kayan ta ne kawai ke can dakin da baqin.
Sai da ya bari qafa ta dauke, kowa ya haye sama, ya shiga dakin baqin ya tattaro komai na Mubaraka ya mayar dakin shi.
Kafin ta gama shiryawa ya tafi debo musu abinci, ya na dumama abincin a microwave ya na murmushi, ya na nan tsaye Sultana ta fito diban ruwan zafi a flask da take sha.
Ganin shi ta yi ya nata zabga murmushi dariya ta yi, ta ce,
"Ango ka sha qamshi, ni da na ji qamshin jikin ka ma na zaci Mubaraka ce, ashe kai ne"
"Sultana baki da kunya ko?"
Dariya suka kwashe da ita sannan suka tafa,
"Bari kawai, Allah ya ma yarinyar can albarka, amma ni ina mamaki, an ce an taba mata fyade, amma ban ji wata alama da ta nuna hakan ba, ko dai dan ban san kan abun bane?"
"Wataqila dan baka san kan abun bane, and akwai matan da suke da baiwa, kamar wadda ka ke fada yanzu ba zata taba komawa da budurcin ta ba, amma fa ba za a ji ta a bude ba sosai, sannan ka san matan garin ga dai da gyara ko? Na tabbata an gyara ta sosai, musamman da sun ka san me ya hwaru da ita a baya"
Jinjina kai kawai Sultan ya yi, dan ya san me ya tarar, tabbas to iyayen ta sun masa qoqari matuqa.
Abincin ya haɗa musu, ya mata sai da safe, ya ce ta shafa masa kan Auwal.
Murmushi ta yi,ta na jin wani irin dad'i da farin cikin ganin annuri a fuskar yayan nata.
Bayan sun ci abincin su,sukai kwanciyar su, Sultan ya rungume amaryar shi kamar an ce masa ga masu kilinafin matan mutane nan.
**************************
Sai bayan wata biyu da haihuwar Sultana Hansatu ta samu zuwa can Tudun faila, dan yi musu gaisuwa, ta samu labarin an yi wa Mubaraka aure, nan ta nemi adireshin gidan aka bata, daga nan mijin ta abin son ta, ya kai ta gidan tsohon gwamna Halliru, ba ya jin nauyi ko ganin bata lokaci,in zai kai ta unguwa, ko ina ne kuwa.
Mubaraka ta ji dadin ganin ta sosai, sun sha hira matuqa kafin Hansatu ta tafi.
Tunda Hansatu ta je gida take bawa Hajiya Labarin Sultana, har sai da Hajiya ta ce,
"Gaskiya da za su bamu ita Musa shi aure, da mun gode musu, maganar yaro kuwa ai shi d'a na kowa ne,na tabbata Musa zai riqe shi kamar shi ya haihe shi,"
Cike da murna Hansatu ta ce,
"Kwarai kuwa, ki duba ki gani, yanda Yah Abdullah ke son su Ameenatu, yanzu hwa ba ya so na kira shi da kowanne suna sai da Baban Ahmad,diyan nan gaba daya sun mance da uban su, tunda daidai da rana guda ba na iya tuna sanda ya dauki dayan su, balle har ya musu wasa, amma shi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50 Chapter 51