da zuciyar ta,amma a zahiri dauke kai kawai ta yi ta maida gilashin ta sannan ta ce,
"In kai ma ka gama kallon nawa zamu iya tahiya yanzu"
Dariya ya yi sosai, sannan ya ja motar suka bar gidan.
Labulen dakin ta saki, tare da kallon Gwamna Halliru ta ce,
"Daddyn Sultan ka ga abinda nake ta hwada maka ka qi yarda ko? In baka d'auke yaron ga daga gidan nan ba, to ina mai tabbatar maka da sai an kawo maka shi a matsayin suruki watarana"
"Ke hwa in ki ka tsani mutum ruwa in ya taka sai ki ce ya tada qura, yanzu mi na na ki ka hwadi hakan ga? Ke San dai Sultana yarinya ce mai son mutane, halin ta ne kunya da fara'a, ko dan ki na nan huska awat-ta tamacen alade ba a gane dariya ko hushin ki, shi kenan yarinya ba zata yi hwara'a ba, a waje ma yi wa wasu takai ballantana yaron da ka tuqa ta"
Har cikin ran shi ya fi aminta da Lawwali Ya kusanci Sultana sama da kowa, amma shi ya rusa amincin da Lawwali ya bashi, da martabar da yake ganin shi da ita a ran shi.
Tsaki ya ja ya bar jikin windown da tun da lawwali ya budewa Sultana mota suke tsaye su na kallon su.
Hajiya Ikee ta qulu ta kai bango, alwashi ta ci a cikin ran ta, ba wanda ya isa ya hana ta korar Lawwali a gidan nan, dan kuwa bata haifar wa driver diya ba, Sultana matar manya ce, manyan ma na qololuwa,sabon shugaban qasa da suke saka ran ya ci zabe ta ke wa tanadin Sultana, Dan haka bata ga dalilin da zai sa driver ya shiga tsakanin burin ta ba, last week ta gama tallata sultana a wajen dan takarar shugaban qasar tasu, a lokacin da suka kai masa ziyara garin su, gaba daya ahalin, shi ne ake so a mata sagegeduwa, to ba zai yu ba.
************************
A wajen aiki ma, yau sun shaida sultana na cike da farin ciki, dan haka wajen ya zama a raye da farin ciki da nishadi, ba tare da sanin Sultana ba, Lawwali ya zari jiki, ya bar wajen, bai zame ko ina ba, sai maboyar da aka kai su Mubaraka, copy din makullin gidan da Taheer ya bashi ya dauka,duk wani abu da ya kamata ya sani Taheer ya sanar da shi, a daidai wannan lokacin su na can sansanin su, sai da rana d'aya daga cikin su ke zuwa a basu abinci.
Sai kuma da dare nan ma wanin su ko su duka za su kai masu abinci, da sassafe kuma No 4 aikin shi ne zuwa ya kai masu na safe, ya kuma tabbatar da ba abinda suke buqata.
A tsakiyar parlour ya tsaya ya na jiyo karatun qur'anin Mubaraka, zuciyar shi ta yi matuqar karyewa, musamman da ya ji ta na kuka dan bai san ma'anar abinda take karantawa ba, ballantana ya san ayar ce ta sanya ta kuka, saboda kwadayin rahamar Allah.
A tunanin shi kuka take saboda ta na cikin matsala.
Takawa ya yi cikin sanda,ya leqa ta bulin key din, zaune ya hango ta saman carpet din sallah, sai qawayen ta a saman gado, su na sauraran karatun ta.
Dan kuwa ba bacci suke ba, idanun su biyu.
Hannu ya sanya zai murda qofar,sai ya tuna bai karbi key din dakin ba, saboda ba ya so su san ya na zuwa duba su, har lokacin da ya daukar wa kan shi kubutar da su, ba dan an fi qarfin shi ba, sai dan shi ma ya na son ya rama abinda aka masa.
Yanda Lawwali ke jin kan shi, ba kusa bane, ji yake duk qasar nan ba mai iya karawa da shi, ya na jin ba abinda ya ke son yi wanda ba zai iya shi ba, sai dai in be so ba.
Cikin sanda ya bar gidan ,garin ya fita ya yar da gorar ruwa, wadda aka sha aka rage, ba a rufe bakin ba sosai .
Da sauri ya qarasa fita ya bar gidan, ya kulle, inda ya aje motar shi ya nufa, ya shiga, har zai tada ta, ya ga No 1 ya tunkari gidan daga can nesa, a motar shi, kallon agogo ya yi, ya ga ai yanzu ba lokacin ba su abinci bane, me ya kawo shi? Dube dube ya ga No 1 na yi, sannan ya bude gidan ya fada.
Lawwali ne ya bude qofar cikin tsananin fushi, ya sanya hannun shi a bayan rigar shi ya zaro 'yar qaramar bindigar shi, ya riqe, idon shi ya rufe, tsabar fushi da tashin hankalin da ya ke ciki, gidan ya nufa a fusace.......................
*Hummmm Ni kuma anan na ji naaaaa gaji zan huuuutaaa😅😉😝😝*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 31:
A guje Lawwali ya ke bin hanyar da za ta sada shi da gidan, kafin ya isa No 1 ya rufe qofar, har zai saka key ya bude wani tinani ya zo masa, cikin ran shi ya ke fadin.
'Haba Lawwali, ai bai kamata ka kashe wannan qaramin dan iska cikin sauqi ba, ka yi mishi kisan nan dai da ka yi niyya tun da can, ka bawa zuciyar ka hankuri, komai na da lokaci nai'
Da sauri ya bar wajen, ya nufi motar shi, dan ba ya son ya ga me No 1 ze aikata a gaba, gashi lokacin tashin Sultana na ta gabatowa, wataqila ma ya na isa time ya yi, a dayan bangaren ma ba zai so rusa plan din shi ba na wajen Sultanan, dole ya na ji ya na gani ya hakura.
Ya na tafe ya na sauke wani irin numfashi,kamar wani mayunwacin zaki, duk wanda ya san wane ne asalin Lawwali, a wannan lokacin is not a good idea ka bata masa rai, dan yanzu zai ma lahira sabon baqo da mutum.
Gudun da yake zubawa har ya wuce misali, wataqila da a qasashen turawa ne da tuni an tsaida shi .
Birkin da ya ci ne ya janyo hankalin mutanen da ke wajen, cikin su har da sultana, da ke saka hannu a wata takardar da za a fitar da buhunan shinkafa domin mabuqata.
Ta na kallon idon shi ta ji wani irin yanayi da bata taba ji ba game da Lawwali, wato tsoro,sai dai ta bangaren Lawwali, su na hada ido sai ya ji bacin rai da baqin cikin shi ya ɗan ragu, har murmushi ya ɗan yi mata.
Ganin murmushin shi ne ya sanya ta sakin nata, ta kawar da tsoron da ke ran ta, amma tabbas fuskar da Lawwali ya sanya a baya, bata fatan sake ganin irin ta har gaban abada.
Kafin ta zo ya bude mata qofar,ta na shiga ya mayar ya rufe da qarfi,sai da ta ɗan razana, shi din ma da qarfi ya shiga ,ya kuma rufe da qarfin, cikin sauri ya tada motar dan ya na buqatar leqa sansanin su, ya ɗan huce haushin shin shi a can.
Ba tare da ta yi wani tunani ba ta miqa hannun ta zuwa kafadar shi, a hankali ta shafa saman rigar tashi kafin ta matsa kafadar tashi sannu a hankali, wata iriyar ajiyar zuciya lawwali ya sauke mai qarfin gaske, tare da gangarawa gefen hanyar ya tsaida motar, kifa kan shi ya yi a jikin sitiyarin motar, ya na sauke numfashi, quncin da ke cikin zuciyar shi ba shi da misali, ya na ji ya na gani qanwar shi take a wulaqance, kafin ya gano ta ya zaci ba tashin hankalin da ya fi rasa ta da ya yi, amma yanzu ji yake wannan tashin hankalin ya fi na rasa ta da ya yi, shi ba qarfin shi aka fi ba, ba komai ba, amma ya ke azabtuwa.
Bai san sanda ta zauna a gefen shi ba, sai jin hannun ta ya yi a saman qeyar shi ta na shafawa a hankali, idanun ta na zubar da hawayen tausayin masoyin nata, ta san duk damuwar shi ba ta wuce ta rashin Mubaraka ba.
A hankali ya daga kai suka kalli juna, gaban ta ne ya yi wani mummunan faduwa, Lawwali kamar ba shi ba, fuskar shi ta yi jawur, idanun shi ma haka, ga wani dagawa da komawa da qirjin shi ke yi, cikin sauri ta zame hannun ta, ta sunkuyar da kan ta qasa, ba za ta iya jurar kallon shi ba.
Muryar shi na rawa, ya ce,
"Sultana....qauna ta a duk inda take ta na buqata ta, ina ji a jiki na, ta na cikin matsala,"
Tsigar jikin ta gaba daya ta miqe, sakamakon kiran sunan ta da ya yi, bata taɓa zaton bayan iyayen ta da suka saka mata suna sultana ba, akwai wanda ya iya fadin sunan ya yi daɗin saurara kamar Lawwali ba, ga wani matsanancin tausayin shi da ke addabar zuciyar ta, cike da raunin murya ta ce,
"Allah na tare da ita ko ba ka nan, zai kula da lamarin ta, baka cutar da d'an kowa ba, kai ma ba za a cutar da taka qaunar ba"
Da sauri ya kalle ta, sannan ya ce,
"In kuma na cutar da wani fa? Sai a cutar da tawa qaunar ki ka nuhi?"
Yanayin yanda ya yi maganar ya sa ta jin kalaman ta ba su yi dadin saurara ba a kunnuwan shi, cikin sauri ta ce,
"Nooo ba haka ni ka nuhi ba, mu je gida mu sake wa Daddy magana, Ni kai na na damu da rashin Mubaraka,"
Cikin kauda maganar, dan gujewa bacin ran da ta hango kwance a fuskar shi, ita abun ma ya fara bata tsoro, ba ta taba ganin wanan Auwal din ba.
Ba tare da ta koma baya ba suka tafi, har suka isa ba wanda ya sake magana, ta so kunna ko da rediyo ne dan kawar da shirun amma gaba daya bata ga fuska ba, ita da motar ta, ta najin tsoron driver,zuciyar ta ce ta mata tuni da cewar,
'Shi din ba wai drivern ki bane kadai,ya riqi babban matsayi a zuciyar ki Sultana, matsayin da babu wani mahaluki da ya taba riqe irin shi, a kaff tarihin rayuwar ki, shi ne namiji na farko da ki ka fara yi wa so irin na soyayya, kuma shi ne namijin da ki ke ganin za ki qarasa rayuwar ki da shi, har abada'
Ji ta yi motar ta daina tafiya, ko da ta dawo daga duniyar tunanin da ta shiga sai ta gan su a cikin gidan su, baya ta leqa dan ta tabbata ma'aikatan gidan na ta gaishe ta ma bata kula ba.
A tsaye yake a jikin qofar ya bude mata, ita kawai yake jira ta fita ya kama gaban shi, da yau har ita din ma haushi take bashi,in ba ganin shi ya yi a daji ya na ragargazar mutane ba ba zai ji dadi ba.
"Ran ki shi dade, mun iso"
Cikin yanayi na jin kunyar ya kama ta ta na kallon shi, ta fita, ya rufe, baya ta bude ta dau jakar ta, da wayar ta, duk ya na tsaye,
"Dan Allah ka kwantar da hankalin ka, duk da na san abu ne mai wahala, amma ka jaraba karanta hasbunallahu, wa ni'imal wakeel, inshaa Allahu komai zai yi daidai, za a gan ta,"
Daga mata kai kawai ya yi da fake murmushi, Wanda ta san fake ne, amma ita sai ta mayar masa da kyakkyawa kuma mai kwantar da hankalin,amma ba irin hankalin Lawwali ba, dan kuwa ya dai ji dad'in ganin murmushin nata, amma bai rage masa rad'ad'in da yake ji ba a ran shi.
Ya na qoqarin tafiya Mai Buruji na qoqarin fita itama, su na hada ido ta gigice ta yi baya a guje, ta koma bangaren masu aiki,ba ita ta bar gidan ba sai ana kiran la'asar.
************************
Gidan ya yi wa Lamishi shiru yau, ba wanda ya je mata jajen ma da ake dan yi, ga qawar ta tun jiya da ta keta da gudu, har yau bata dawo ba, ga Mai Buruji bata koma ba, shi kuma wannan lalataccen mijin nasu dan wahala sai zarya da sintiri yake kamar dan agaji, da aikin agajin ma yake da al'umma ta amfana da shi.
Shigowar shi ta biyar kenan, cikin dan had'e fuska ya ce,
"Ke ga wannan lalatacciyar bata dawo ba ko? Tunda kin ka bar zuwa ta samu wajen tafiya yawon shashancin ta, sai ta ga dama ta ka dawowa gidan ga"
"Kar ka kuskura ka zage ta, yo akwai lalatacce da ya wuce ka? Baka nema ba, ba ka bada jallin nema ba, amma ka ishi mutane da dumin banza, kai ba ka damu da jimawar da tayyi ba, amma ka damu da rashin dawowar ta dan ka ci abinci kai da lalatattun abukkan ka, Ni ka ga tahiya ta ma gidan 'Yabbuga, in ta zaka kace ina can"
Yaqe baki ya fara ya na mata kirari na uwar gida, ita kuma ta tsuke fuska gam, ta yafa mayafi ta bar gidan.
Zaune ta tarar da 'Yabbuga a saman turmi, ta kasa kunnuwan ta gidan Isah ta ji me suke ciki, Lamishi na ganin haka, ta kwashe da dariya ta rafka gud'a, sannan ta ce,
"Ahayyyeeee, Allah gani, in ji gurmuwa (gurguwa) gulma ajali, in ba ai ba a mutu,ki na nan zaune ke d'ai ga gida ba ki hitowa a sha hira? Ke tsaya kasa kunne shigifar (katanga) maqota,"
Hannu 'Yabbuga ta sa a baki ta na ma Lamishi nuni da ta yi shiru, jan hannun ta tayi, suka bar wajen, suka zauna a bakin qofar parlourn 'Yabbugan, Lamishi ce ta kalli 'Yabbuga hannu da qafa, ta ga bata ga komai ba, cikin rashin fahimta ta ce,
"Shin ina lallen da nis-sa miki jiya?"
Tsaki 'Yabbuga ta ja mai qarfi, sannan ta tura dankwalin ta gaban goshi ta na sosa cinyayyar qeyar ta,
"Ina ko kigganai? Lalle dai ba lalle na ba, miyak-kad'i ta wallah (kuka)"
(Lalle dai ba lalle bane kuka ce wallah)
"Miiii? Wanne irin miyak-kad'i?"
Fari 'Yabbuga ta yi, kamar wata 'yar daudu ta ce,
"Miyak-kadi dai da kis-sani, ita mun ka kwaba, mun ka daura, niyyi awa da wanni zaune ina sharar bacci wahala, nic-ci gudun wahalar banza akan lallen ga na banza, dan da ban kai wannan lokacin gidan ku ba da ban hadu da qanin shedan din can ba, ya hirgita ni, duba, duba, nace duba nan ki gani"
Wani shafcecen yanka ne a sharabar ta, kamar ta ji shi da icce ko langa langa,
"Ke ga yanda na here qahwa, ban ci lalle ba na ci gudu, dake jikin tallaka na ko jin yankan ban ba sai dazu da zan wanka da rana nijji zahi, nicce too Allah gani gare ka missamen? Ina dibawa nigga qahwa ta here,"
Lamishi na son yin dariya ba hali, dan yanzu sai su raba hali, ga dariya ta mata yawa,
"Yi dariyar ki, yanzu wannan dan rainin hankalin ya hita shi na yi min dariya,"
Ai kuwa kafin 'Yabbuga ta rufe baki,Lamishi ta fara keta dariya, tunano irin zaman da 'Yabbugan ta ci akan lallen da irin gudun da ta sha kawai take.
Tun 'yabbuga na bata rai, har ita ma ta sake sukai ta dariya.
Daga baya suka jajantawa juna rashin mubaraka, wanda har a wannan lokacin abun ba wai ya shiga jikin Lamishi bane, kamar yanda kowacce uwar kirki ya kamata ya shige ta ba.
************************
Lawwali na isa sansanin nasu, ya kira No 2 da No 3 suka tara masa mutanen da suka kama last 2days ,aka fitar masa da su tsakiyar daji, No 4 na ganin haka ya san tabbas Lawwali ya ga wani abun da bai ganshe shi ba, ya na son zuwa ya bada hakuri ya na tsoro, kar laifin ya koma kan shi,dan ya tabbatar wadannan mutane goma da aka fidda ba daya da zai dawo a raye...........
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 32:
Kukan bayin Allah kawai ke tashi a dokar daji, ba gida gaba ba gida baya, daga su sai Lawwali da yaran shi, kowannen su dauke da bindigogi, an gama loda wa Lawwali alburushi a bindigar shi, ya na tsaye cikin qunar rai da baqin ciki, ya na karba ya saki alburushi a kan mutum na farko da ke a gaban shi, haka ma ya yi wa na biyun shi, ya saita bindigar akan mutum na uku da ke gaban shi, kalaman Sultana suka bijiro a ƙwaƙwalwa da zuciyar shi,
'Allah na tare da ita, ko ba ka nan, zai kula da lamarin ta, baka cutar da d'an kowa ba, kai ma ba za a cutar da taka qaunar ba'
Hannun shi na rawa, kamar zai ajiye bindigar,amma dake zuciyar shi ta riga ta bushe, bai samu sauqin baqin cikin da yake ciki ba sai da ya kashe mutum biyar a cikin su, ya sa aka maida saura, a wajen aka haqa rami, ba sallah, ba addu'a aka binne bayin Allah.
Ko da suka koma sansanin su No 1 ya hango cikin 'yanmatan da ke wajen, ya na hira da su,ya na wani karairaya kamar tsohuwar karuwa, wani malolon baqin ciki ne ya taso masa, kujera ya bada umarni a saka masa a filin wajen, kamar qiftawar ido kuwa aka ajiye masa kujerar shi, ya zauna cikin isa da mulkin da yake ji kamar an bashi mulkin qasar baki d'aya ya kalli mutanen dake wajen,wanda gaba d'aya a qarqashin shi suke, matasa ne da magidanta, wanda adadin su ba zai wuce sha uku zuwa sha biyar ba, mata da maza,dattijai da matasa, sai yara wanda shekarun su na haihuwa ba zasu wuce sha uku zuwa sha biyar ba, akan yaudari mutane da su, dan a yi garkuwa da mutanen.
Kiran su ya yi gaba d'aya, nan da nan kuwa suka isa kowa ya riqe bindigar shi, suka tsaitsaya kamar wasu horarrun sojoji,hakan ya yi matuqar birge shi, ya kuma sanya ya ji ya na da ikon da a yanzu in ya ce a kama masa No 1 a harbe wata kafa a jikin shi ba zata yi saura ba, ba tare da alburushi ya huda ta ba, amma bari ya yi playing game d'in su na cin amana shima.
Murmushi kawai ya musu, saboda duk a tsorace suke, sun san labarin batan qanwar shi, sun san shi ne dalilin fushin shi, wasun su har fata suke ya gan ta da wuri saboda Ogan su ya dawo kamar da, mai fara'a, walwala, da basu nishadi.
"Mun jima ba mu yi wasanni ba a wajen nan, yau
Showing 60001 words to 63000 words out of 150481 words
"In kai ma ka gama kallon nawa zamu iya tahiya yanzu"
Dariya ya yi sosai, sannan ya ja motar suka bar gidan.
Labulen dakin ta saki, tare da kallon Gwamna Halliru ta ce,
"Daddyn Sultan ka ga abinda nake ta hwada maka ka qi yarda ko? In baka d'auke yaron ga daga gidan nan ba, to ina mai tabbatar maka da sai an kawo maka shi a matsayin suruki watarana"
"Ke hwa in ki ka tsani mutum ruwa in ya taka sai ki ce ya tada qura, yanzu mi na na ki ka hwadi hakan ga? Ke San dai Sultana yarinya ce mai son mutane, halin ta ne kunya da fara'a, ko dan ki na nan huska awat-ta tamacen alade ba a gane dariya ko hushin ki, shi kenan yarinya ba zata yi hwara'a ba, a waje ma yi wa wasu takai ballantana yaron da ka tuqa ta"
Har cikin ran shi ya fi aminta da Lawwali Ya kusanci Sultana sama da kowa, amma shi ya rusa amincin da Lawwali ya bashi, da martabar da yake ganin shi da ita a ran shi.
Tsaki ya ja ya bar jikin windown da tun da lawwali ya budewa Sultana mota suke tsaye su na kallon su.
Hajiya Ikee ta qulu ta kai bango, alwashi ta ci a cikin ran ta, ba wanda ya isa ya hana ta korar Lawwali a gidan nan, dan kuwa bata haifar wa driver diya ba, Sultana matar manya ce, manyan ma na qololuwa,sabon shugaban qasa da suke saka ran ya ci zabe ta ke wa tanadin Sultana, Dan haka bata ga dalilin da zai sa driver ya shiga tsakanin burin ta ba, last week ta gama tallata sultana a wajen dan takarar shugaban qasar tasu, a lokacin da suka kai masa ziyara garin su, gaba daya ahalin, shi ne ake so a mata sagegeduwa, to ba zai yu ba.
************************
A wajen aiki ma, yau sun shaida sultana na cike da farin ciki, dan haka wajen ya zama a raye da farin ciki da nishadi, ba tare da sanin Sultana ba, Lawwali ya zari jiki, ya bar wajen, bai zame ko ina ba, sai maboyar da aka kai su Mubaraka, copy din makullin gidan da Taheer ya bashi ya dauka,duk wani abu da ya kamata ya sani Taheer ya sanar da shi, a daidai wannan lokacin su na can sansanin su, sai da rana d'aya daga cikin su ke zuwa a basu abinci.
Sai kuma da dare nan ma wanin su ko su duka za su kai masu abinci, da sassafe kuma No 4 aikin shi ne zuwa ya kai masu na safe, ya kuma tabbatar da ba abinda suke buqata.
A tsakiyar parlour ya tsaya ya na jiyo karatun qur'anin Mubaraka, zuciyar shi ta yi matuqar karyewa, musamman da ya ji ta na kuka dan bai san ma'anar abinda take karantawa ba, ballantana ya san ayar ce ta sanya ta kuka, saboda kwadayin rahamar Allah.
A tunanin shi kuka take saboda ta na cikin matsala.
Takawa ya yi cikin sanda,ya leqa ta bulin key din, zaune ya hango ta saman carpet din sallah, sai qawayen ta a saman gado, su na sauraran karatun ta.
Dan kuwa ba bacci suke ba, idanun su biyu.
Hannu ya sanya zai murda qofar,sai ya tuna bai karbi key din dakin ba, saboda ba ya so su san ya na zuwa duba su, har lokacin da ya daukar wa kan shi kubutar da su, ba dan an fi qarfin shi ba, sai dan shi ma ya na son ya rama abinda aka masa.
Yanda Lawwali ke jin kan shi, ba kusa bane, ji yake duk qasar nan ba mai iya karawa da shi, ya na jin ba abinda ya ke son yi wanda ba zai iya shi ba, sai dai in be so ba.
Cikin sanda ya bar gidan ,garin ya fita ya yar da gorar ruwa, wadda aka sha aka rage, ba a rufe bakin ba sosai .
Da sauri ya qarasa fita ya bar gidan, ya kulle, inda ya aje motar shi ya nufa, ya shiga, har zai tada ta, ya ga No 1 ya tunkari gidan daga can nesa, a motar shi, kallon agogo ya yi, ya ga ai yanzu ba lokacin ba su abinci bane, me ya kawo shi? Dube dube ya ga No 1 na yi, sannan ya bude gidan ya fada.
Lawwali ne ya bude qofar cikin tsananin fushi, ya sanya hannun shi a bayan rigar shi ya zaro 'yar qaramar bindigar shi, ya riqe, idon shi ya rufe, tsabar fushi da tashin hankalin da ya ke ciki, gidan ya nufa a fusace.......................
*Hummmm Ni kuma anan na ji naaaaa gaji zan huuuutaaa😅😉😝😝*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 31:
A guje Lawwali ya ke bin hanyar da za ta sada shi da gidan, kafin ya isa No 1 ya rufe qofar, har zai saka key ya bude wani tinani ya zo masa, cikin ran shi ya ke fadin.
'Haba Lawwali, ai bai kamata ka kashe wannan qaramin dan iska cikin sauqi ba, ka yi mishi kisan nan dai da ka yi niyya tun da can, ka bawa zuciyar ka hankuri, komai na da lokaci nai'
Da sauri ya bar wajen, ya nufi motar shi, dan ba ya son ya ga me No 1 ze aikata a gaba, gashi lokacin tashin Sultana na ta gabatowa, wataqila ma ya na isa time ya yi, a dayan bangaren ma ba zai so rusa plan din shi ba na wajen Sultanan, dole ya na ji ya na gani ya hakura.
Ya na tafe ya na sauke wani irin numfashi,kamar wani mayunwacin zaki, duk wanda ya san wane ne asalin Lawwali, a wannan lokacin is not a good idea ka bata masa rai, dan yanzu zai ma lahira sabon baqo da mutum.
Gudun da yake zubawa har ya wuce misali, wataqila da a qasashen turawa ne da tuni an tsaida shi .
Birkin da ya ci ne ya janyo hankalin mutanen da ke wajen, cikin su har da sultana, da ke saka hannu a wata takardar da za a fitar da buhunan shinkafa domin mabuqata.
Ta na kallon idon shi ta ji wani irin yanayi da bata taba ji ba game da Lawwali, wato tsoro,sai dai ta bangaren Lawwali, su na hada ido sai ya ji bacin rai da baqin cikin shi ya ɗan ragu, har murmushi ya ɗan yi mata.
Ganin murmushin shi ne ya sanya ta sakin nata, ta kawar da tsoron da ke ran ta, amma tabbas fuskar da Lawwali ya sanya a baya, bata fatan sake ganin irin ta har gaban abada.
Kafin ta zo ya bude mata qofar,ta na shiga ya mayar ya rufe da qarfi,sai da ta ɗan razana, shi din ma da qarfi ya shiga ,ya kuma rufe da qarfin, cikin sauri ya tada motar dan ya na buqatar leqa sansanin su, ya ɗan huce haushin shin shi a can.
Ba tare da ta yi wani tunani ba ta miqa hannun ta zuwa kafadar shi, a hankali ta shafa saman rigar tashi kafin ta matsa kafadar tashi sannu a hankali, wata iriyar ajiyar zuciya lawwali ya sauke mai qarfin gaske, tare da gangarawa gefen hanyar ya tsaida motar, kifa kan shi ya yi a jikin sitiyarin motar, ya na sauke numfashi, quncin da ke cikin zuciyar shi ba shi da misali, ya na ji ya na gani qanwar shi take a wulaqance, kafin ya gano ta ya zaci ba tashin hankalin da ya fi rasa ta da ya yi, amma yanzu ji yake wannan tashin hankalin ya fi na rasa ta da ya yi, shi ba qarfin shi aka fi ba, ba komai ba, amma ya ke azabtuwa.
Bai san sanda ta zauna a gefen shi ba, sai jin hannun ta ya yi a saman qeyar shi ta na shafawa a hankali, idanun ta na zubar da hawayen tausayin masoyin nata, ta san duk damuwar shi ba ta wuce ta rashin Mubaraka ba.
A hankali ya daga kai suka kalli juna, gaban ta ne ya yi wani mummunan faduwa, Lawwali kamar ba shi ba, fuskar shi ta yi jawur, idanun shi ma haka, ga wani dagawa da komawa da qirjin shi ke yi, cikin sauri ta zame hannun ta, ta sunkuyar da kan ta qasa, ba za ta iya jurar kallon shi ba.
Muryar shi na rawa, ya ce,
"Sultana....qauna ta a duk inda take ta na buqata ta, ina ji a jiki na, ta na cikin matsala,"
Tsigar jikin ta gaba daya ta miqe, sakamakon kiran sunan ta da ya yi, bata taɓa zaton bayan iyayen ta da suka saka mata suna sultana ba, akwai wanda ya iya fadin sunan ya yi daɗin saurara kamar Lawwali ba, ga wani matsanancin tausayin shi da ke addabar zuciyar ta, cike da raunin murya ta ce,
"Allah na tare da ita ko ba ka nan, zai kula da lamarin ta, baka cutar da d'an kowa ba, kai ma ba za a cutar da taka qaunar ba"
Da sauri ya kalle ta, sannan ya ce,
"In kuma na cutar da wani fa? Sai a cutar da tawa qaunar ki ka nuhi?"
Yanayin yanda ya yi maganar ya sa ta jin kalaman ta ba su yi dadin saurara ba a kunnuwan shi, cikin sauri ta ce,
"Nooo ba haka ni ka nuhi ba, mu je gida mu sake wa Daddy magana, Ni kai na na damu da rashin Mubaraka,"
Cikin kauda maganar, dan gujewa bacin ran da ta hango kwance a fuskar shi, ita abun ma ya fara bata tsoro, ba ta taba ganin wanan Auwal din ba.
Ba tare da ta koma baya ba suka tafi, har suka isa ba wanda ya sake magana, ta so kunna ko da rediyo ne dan kawar da shirun amma gaba daya bata ga fuska ba, ita da motar ta, ta najin tsoron driver,zuciyar ta ce ta mata tuni da cewar,
'Shi din ba wai drivern ki bane kadai,ya riqi babban matsayi a zuciyar ki Sultana, matsayin da babu wani mahaluki da ya taba riqe irin shi, a kaff tarihin rayuwar ki, shi ne namiji na farko da ki ka fara yi wa so irin na soyayya, kuma shi ne namijin da ki ke ganin za ki qarasa rayuwar ki da shi, har abada'
Ji ta yi motar ta daina tafiya, ko da ta dawo daga duniyar tunanin da ta shiga sai ta gan su a cikin gidan su, baya ta leqa dan ta tabbata ma'aikatan gidan na ta gaishe ta ma bata kula ba.
A tsaye yake a jikin qofar ya bude mata, ita kawai yake jira ta fita ya kama gaban shi, da yau har ita din ma haushi take bashi,in ba ganin shi ya yi a daji ya na ragargazar mutane ba ba zai ji dadi ba.
"Ran ki shi dade, mun iso"
Cikin yanayi na jin kunyar ya kama ta ta na kallon shi, ta fita, ya rufe, baya ta bude ta dau jakar ta, da wayar ta, duk ya na tsaye,
"Dan Allah ka kwantar da hankalin ka, duk da na san abu ne mai wahala, amma ka jaraba karanta hasbunallahu, wa ni'imal wakeel, inshaa Allahu komai zai yi daidai, za a gan ta,"
Daga mata kai kawai ya yi da fake murmushi, Wanda ta san fake ne, amma ita sai ta mayar masa da kyakkyawa kuma mai kwantar da hankalin,amma ba irin hankalin Lawwali ba, dan kuwa ya dai ji dad'in ganin murmushin nata, amma bai rage masa rad'ad'in da yake ji ba a ran shi.
Ya na qoqarin tafiya Mai Buruji na qoqarin fita itama, su na hada ido ta gigice ta yi baya a guje, ta koma bangaren masu aiki,ba ita ta bar gidan ba sai ana kiran la'asar.
************************
Gidan ya yi wa Lamishi shiru yau, ba wanda ya je mata jajen ma da ake dan yi, ga qawar ta tun jiya da ta keta da gudu, har yau bata dawo ba, ga Mai Buruji bata koma ba, shi kuma wannan lalataccen mijin nasu dan wahala sai zarya da sintiri yake kamar dan agaji, da aikin agajin ma yake da al'umma ta amfana da shi.
Shigowar shi ta biyar kenan, cikin dan had'e fuska ya ce,
"Ke ga wannan lalatacciyar bata dawo ba ko? Tunda kin ka bar zuwa ta samu wajen tafiya yawon shashancin ta, sai ta ga dama ta ka dawowa gidan ga"
"Kar ka kuskura ka zage ta, yo akwai lalatacce da ya wuce ka? Baka nema ba, ba ka bada jallin nema ba, amma ka ishi mutane da dumin banza, kai ba ka damu da jimawar da tayyi ba, amma ka damu da rashin dawowar ta dan ka ci abinci kai da lalatattun abukkan ka, Ni ka ga tahiya ta ma gidan 'Yabbuga, in ta zaka kace ina can"
Yaqe baki ya fara ya na mata kirari na uwar gida, ita kuma ta tsuke fuska gam, ta yafa mayafi ta bar gidan.
Zaune ta tarar da 'Yabbuga a saman turmi, ta kasa kunnuwan ta gidan Isah ta ji me suke ciki, Lamishi na ganin haka, ta kwashe da dariya ta rafka gud'a, sannan ta ce,
"Ahayyyeeee, Allah gani, in ji gurmuwa (gurguwa) gulma ajali, in ba ai ba a mutu,ki na nan zaune ke d'ai ga gida ba ki hitowa a sha hira? Ke tsaya kasa kunne shigifar (katanga) maqota,"
Hannu 'Yabbuga ta sa a baki ta na ma Lamishi nuni da ta yi shiru, jan hannun ta tayi, suka bar wajen, suka zauna a bakin qofar parlourn 'Yabbugan, Lamishi ce ta kalli 'Yabbuga hannu da qafa, ta ga bata ga komai ba, cikin rashin fahimta ta ce,
"Shin ina lallen da nis-sa miki jiya?"
Tsaki 'Yabbuga ta ja mai qarfi, sannan ta tura dankwalin ta gaban goshi ta na sosa cinyayyar qeyar ta,
"Ina ko kigganai? Lalle dai ba lalle na ba, miyak-kad'i ta wallah (kuka)"
(Lalle dai ba lalle bane kuka ce wallah)
"Miiii? Wanne irin miyak-kad'i?"
Fari 'Yabbuga ta yi, kamar wata 'yar daudu ta ce,
"Miyak-kadi dai da kis-sani, ita mun ka kwaba, mun ka daura, niyyi awa da wanni zaune ina sharar bacci wahala, nic-ci gudun wahalar banza akan lallen ga na banza, dan da ban kai wannan lokacin gidan ku ba da ban hadu da qanin shedan din can ba, ya hirgita ni, duba, duba, nace duba nan ki gani"
Wani shafcecen yanka ne a sharabar ta, kamar ta ji shi da icce ko langa langa,
"Ke ga yanda na here qahwa, ban ci lalle ba na ci gudu, dake jikin tallaka na ko jin yankan ban ba sai dazu da zan wanka da rana nijji zahi, nicce too Allah gani gare ka missamen? Ina dibawa nigga qahwa ta here,"
Lamishi na son yin dariya ba hali, dan yanzu sai su raba hali, ga dariya ta mata yawa,
"Yi dariyar ki, yanzu wannan dan rainin hankalin ya hita shi na yi min dariya,"
Ai kuwa kafin 'Yabbuga ta rufe baki,Lamishi ta fara keta dariya, tunano irin zaman da 'Yabbugan ta ci akan lallen da irin gudun da ta sha kawai take.
Tun 'yabbuga na bata rai, har ita ma ta sake sukai ta dariya.
Daga baya suka jajantawa juna rashin mubaraka, wanda har a wannan lokacin abun ba wai ya shiga jikin Lamishi bane, kamar yanda kowacce uwar kirki ya kamata ya shige ta ba.
************************
Lawwali na isa sansanin nasu, ya kira No 2 da No 3 suka tara masa mutanen da suka kama last 2days ,aka fitar masa da su tsakiyar daji, No 4 na ganin haka ya san tabbas Lawwali ya ga wani abun da bai ganshe shi ba, ya na son zuwa ya bada hakuri ya na tsoro, kar laifin ya koma kan shi,dan ya tabbatar wadannan mutane goma da aka fidda ba daya da zai dawo a raye...........
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 32:
Kukan bayin Allah kawai ke tashi a dokar daji, ba gida gaba ba gida baya, daga su sai Lawwali da yaran shi, kowannen su dauke da bindigogi, an gama loda wa Lawwali alburushi a bindigar shi, ya na tsaye cikin qunar rai da baqin ciki, ya na karba ya saki alburushi a kan mutum na farko da ke a gaban shi, haka ma ya yi wa na biyun shi, ya saita bindigar akan mutum na uku da ke gaban shi, kalaman Sultana suka bijiro a ƙwaƙwalwa da zuciyar shi,
'Allah na tare da ita, ko ba ka nan, zai kula da lamarin ta, baka cutar da d'an kowa ba, kai ma ba za a cutar da taka qaunar ba'
Hannun shi na rawa, kamar zai ajiye bindigar,amma dake zuciyar shi ta riga ta bushe, bai samu sauqin baqin cikin da yake ciki ba sai da ya kashe mutum biyar a cikin su, ya sa aka maida saura, a wajen aka haqa rami, ba sallah, ba addu'a aka binne bayin Allah.
Ko da suka koma sansanin su No 1 ya hango cikin 'yanmatan da ke wajen, ya na hira da su,ya na wani karairaya kamar tsohuwar karuwa, wani malolon baqin ciki ne ya taso masa, kujera ya bada umarni a saka masa a filin wajen, kamar qiftawar ido kuwa aka ajiye masa kujerar shi, ya zauna cikin isa da mulkin da yake ji kamar an bashi mulkin qasar baki d'aya ya kalli mutanen dake wajen,wanda gaba d'aya a qarqashin shi suke, matasa ne da magidanta, wanda adadin su ba zai wuce sha uku zuwa sha biyar ba, mata da maza,dattijai da matasa, sai yara wanda shekarun su na haihuwa ba zasu wuce sha uku zuwa sha biyar ba, akan yaudari mutane da su, dan a yi garkuwa da mutanen.
Kiran su ya yi gaba d'aya, nan da nan kuwa suka isa kowa ya riqe bindigar shi, suka tsaitsaya kamar wasu horarrun sojoji,hakan ya yi matuqar birge shi, ya kuma sanya ya ji ya na da ikon da a yanzu in ya ce a kama masa No 1 a harbe wata kafa a jikin shi ba zata yi saura ba, ba tare da alburushi ya huda ta ba, amma bari ya yi playing game d'in su na cin amana shima.
Murmushi kawai ya musu, saboda duk a tsorace suke, sun san labarin batan qanwar shi, sun san shi ne dalilin fushin shi, wasun su har fata suke ya gan ta da wuri saboda Ogan su ya dawo kamar da, mai fara'a, walwala, da basu nishadi.
"Mun jima ba mu yi wasanni ba a wajen nan, yau
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21 Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51