dawo ne ya tuna ya kira Lawwali, wanda ya ke ta gyaran gidan su dake nan unguwar.
Lawwali ya shiga rudani, da tashin hankali jin mutuwar uban gidan nashi, tunawa ya yi da cewar, kafin magariba ya wuce ta qofar gidan kafin ya isa nasu, bai ga kowa a gate ba, har ya ke tunanin yanda rayuwa ta koma, ace gidan Gwamna Halliru ne shiru a bushe ba mutane.
Bayan ya katse wayar cikin sauri ya sanya kayan shi, ya yi alwala ya yi sallahr Isha'i, ya na idarwa ya fita dan zuwa gidan, mota ya dauka dan ya na so ya yi saurin isa.
Tafe yake ya na ta tunanin rayuwa, ya na kukan baqin cikin irin rayuwar da ya kasance ya na aikatawa a baya........
*Yau ba appetite ɗin rubutu,amma a haka na cije na daure na ci gaba, sai gobe inshaa Allah kuma*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 61:
Ya na daf da isa gidan, ya ga wata mata zaune a jikin ginin da aka saka street light, da dan qunshin buhu a gaban ta, sai sandar ta da ta jingine a jikin jakar ta, ta rufu da mayafi, da alama anan take da shirin kwana,duk yanda akai ba ta san a wace unguwa take ba, domin a iya sanin shi, wannan unguwar tuni wani zai ciki da ita, a yi wani sihirin da ita, dan neman abun duniya.
Yi ya yi kamar zai tsaya, ya taimaka mata, kawai ya yi gaba, dan ya san yanayin yanda rayuwar ta koma, su kan su, sun sha haɗawa mutane trap da mabarata.
Bai tsaya a ko ina ba sai a bakin gate din gidan su Sultan,mutane ne danqam a wajen gidan, kamar da rana, da kyar ya samu shiga ciki, har da 'yan jarida, da sabon gwamna mai ci,da muqrraban shi.
Lawwali gaisuwa ya dinga miqawa mutanen da ya tarar, tare da ta'aziyya, wasu na yi mishi ta'aziyyar shi ma, kasancewar shi surukin gidan.
Sai da wajen ya d'an lafa ne, Sultan ya raka Lawwali ciki, nan ya samu Sultana a yanayin da ya kasa jurewa sai da kwalla ta taru masa a idanun shi, matan wajen na ganin haka suka firfita, aka basu waje, a hankali ya isa gefen ta ya zauna,cikin murya mai sanyi ya ce,
"Sultyna, ki yi hakuri, mu yi hakuri gaba daya, mu yi ta yi wa Daddy addu'a, dan ko ita ce kad'ai ya ke bid'a wajen mu, kuka ba zai dawo da shi ba, ki yi hankuri kin ji, jarumar mata ta"
A hankali ta ja jikin ta, ta kwantar a nashi, cikin kuka ta ce,
"Ba ina kukan rabuwa da shi bane, dan na san komai daren dad'ewa sai mun rabu,ina kuka ne akan tunanin Daddy bai samu ya furta kowacce kalma da ake saka ran Allah zai yahe masa ba,na tabbata sai ya sha azaba a lahira, saboda abinda ya kasance ya na aikatawa"
Da sauri ya sanya dogon yatsan shi a labban ta, ya ce,
"Kar ki ce haka, kin mance da me kike fadi min kullum, ba a shiga tsakanin bawa da ubangijin shi, in mutum ya yi shisshigi tsakanin bawa da ubangijin shi, shi sai Allah ya hana mishi rahamar sa, ya yi wa wanda ya ke wa zaton Allah ba zai duba da idon rahama ba rahamar "
A hankali ta fara jin wani sanyi a ran ta,
"Haka ne, yanzu ba abinda ya mana saura da ya wuce mu yi ta masa addu'a"
"Allah ya jiqan shi, ya gafarta mishi, na yahe mishi duk abinda ya yi min a rayuwa ta, ni ma ina fata ALLAH shi yahe min"
Wani irin dad'i ne ya kama Sultana, ta qara kwantawa a jikin shi ta na murmushi,
"Na gode miji na, na gode, Allah ya amsa addu'ar ka,....ina Mubaraka?"
"Dazu da mun ka hito gaba daya, mun yi wa daji bankwana, bankwana na har abada da yardar Allah, sai nace zan kawo ta nan wajen mu ta zauna ta ce ah ah, na kai ta gida, to ban san an yi rasuwa ba sai d'azu"
"Allah Sarki, ai da ta zo mun zauna, gidan ai da girma ba laihi, "
"Ke San ta da son su Lamishi,ba ta tahowa wajen mu yanzu, ban qi ba in ta gaji da zama wajen su,amma ke san mi ya faru?"
"Sai ka hwadi,"
"Da na je gida, na ga sauyi sosai wajen Baban mu,na tarar ya na yin rumfa, ban san mi ya ka son yi ba, mun gaisa cikin wani irin yanayi da ban san ya zan kira shi ba,ba wannan rawar kan kamar zai min kwacen kuddi, ita kan ta Lamishi haka, duk sun yi wani iri, har da yi wa Barakana oyoyo"
"Alhamdu lilLAAH, Allah ya qara kawo mana zaman lafiya, da shiriya,"
"Ameen Allah ya jiqan Daddy,"
Ta ji dad'in yanda Lawwalin ke ta masa addu'a ko ba komai, hakan ya nuna ba wani riqo a tsakanin su.
"Kin ci abinci kuwa?"
"Ahh ahh, gashi can, an kawo mana ni da Hajiya, mun kasa ci,amma yanzu da ka yi magana, na ji ina jin yunwa, ba zan iya ci bane kawai, baki na ba dad'i"
"Ayyaa dear, haka zaki daure ki ci, kin jiya?"
Tashi ya yi, da kan shi ya haɗa mata tea, ya bata, ta shanye tass,ya bata abinci kadan, ta ci, ta masa godiya, sannan ya mata sallama,ya leqa dakin da Hajiya Ikee da qawayen ta ke zaune, ya musu ta'aziyya.
Abun da ya gani ya bashi takaici, ba dan ace ya shiryu ba, da in ya buga wa wata mata da ta kafe shi da ido tsawa, sai ta rasa ina zata ta buya dan tsoro.
Tsaki ya yi a daidai saitin matar da zai fita, ta na zaune kamar wadda ta zo biki, ko ina gwala-gwalai ne,ga wata arniyar shadda ta zuba sai maiqo take.
Ta kunna snap chat kamar wata yarinya, ta na zaro harshe, ta na mayarwa, ya na shiga ta kafe shi da Mayun idanun ta, inda yake a tsugunne ta miqar da qafar ta sai da ta taɓa tashi,kallon da ya mata ne ya sanya ta janye wa da sauri ta na yaqe,ita a dole ba da niyya ta yi ba.
An zo gidan rasuwa amma wasu rasuwar bata dame su ba ma, wasu kuwa sun sanya hijabi,an riqe carbi, amma ba abinda suke sai hira.
A haka ya fita ya na takaicin yanda gidan rasuwa ya ke komawa kamar na biki, a wannan zamani.
Bai sake komawa wajen Sultana ba, gaisawa suka sake yi da su Sultan, ya tafi gida.
Sai sha d'aya na dare wasu mutanen suka dinga tafiya.
Sai da Hajiya Ikee ta zo bacci hankalin ta ya sake tashi, ita kuka Sultana kuka, ba mai lallashin wani,tabbas ba su taba zaton sun shaqu da shi har haka ba sai yanzu, ko ba komai shi din uba ne mai kulawa, ko sun ci, ko basu ci ba, ko suna da wata damuwa, ko basu da ita, shin farin cikin fuskar su ya ishe shi? Ko ya na so su fi haka farin ciki?
Har safiya Sultana bata rintsa ba, ta na kan sallaya, ga yunwa ta na ji, ta kasa cin komai.
Hajiya kuwa ba zata iya tuna sanda ta saka ko da ruwa bane a bakin ta.
Tausayin Hajiyar ne ya sa ta miqe da kyar, marar ta na murdawa, ta nufi hanyar parlour, za ta hado mata tea, wani irin jiri ne ya ɗebe ta, ta kusan faduwa, daddafe jikin bango ta yi, Hajiya Ikee da sauri ta isa wajen ta,cikin kuka ta ce,
"Dan Allah samu waje ki zauna, ko me ki ke so za a miki,dan Allah kar ki sa wa kan ki damuwa ke ma na rasa ki, ba zan iya daukan rashin ku ba,"
Kuka Hajiya Ikee ke yi sosai, Sultana kasa bata hakuri ta yi, sai da wasu 'yan uwan Hajiyan suka sa baki, sannan ta rage kukan.
Zama suka koma suka yi,tace a hadowa Hajiya Tea, da kyar aka tursasa ta ta sha, jin shi ta yi kamar mad'aci, amma haka ta daure ta sha.
A haka, a haka dai har sai da akai sadakar bakwai,sannan mutane suka tattafi gidajen su, dan yanda suka saba in sun zo a ci a sha a raqashe da kaji babu, duk da ana kawo na sadaka, amma ba kamar da gwamna na da rai ba.
*******************
A kwana na goma sha biyu, Lawwali ya je gidan Gwamna,dan gaishe da Hajiya, yanzu ya na bata girma sosai, saboda tausayi take bashi.
Ya na nan duqe gaban ta, ta na ta bashi labaran yanda tsohon gwamnan yake kyautatawa iyalan shi, da yanda ya ke matuqar son su, su Lamishi suka yi sallama, amsawa Hajiya Ikee ta yi, cikin d'an sakin fuska .
Zama su Lamishi za su yi a qasa, da sauri Hajiya Ikee ta ce,
"Dan Allah ku tashi daga qasa, rayuwar ga duk labari ce watarana, dan Allah mu yahe wa juna, abubuwan da sun ka hwaru a baya,"
"Allah Sarki Hajiya komi ya wuce, ya hankuri?"
"Alhamdu lilLAAHi,"
"Allah shi jiqan gwauna, shi mai rahama, Allah shi gafarta mai"
"Ameen Allah shi bada lada"
Mai Buruji, Mubaraka, duk sai da suma su ka bada gaisuwar su wajen Hajiya,da Sultana.
Sultana ce da ta fito daga ciki, ta je yin alwala, ta ga su Lamishi, da sauri ta je ta durqusa gaban su, suka gaisa, suka mata ta'aziyya, Mubaraka ce ta zauna kusa da ita, ta na sake mata ta'aziyya,
"Ameeen na gode, amma dai nan za a bar ki ko? Sai an yi arba'in"
Kallon Lamishi ta yi, ta na neman izini, da ido,daga baya ta maida duban ta wajen oga Lawwali, ta dire shi akan Sultan,da ya kafe ta da ido ya na jiran jin amsar ta, kowa ya yi Mamakin yanda Lamishi ta yi sanyi, ta koma kamar ba ita ba,
"Ki zauna, ba ya da komi, ai duk ɗaya ne"
A tare Mubaraka da Sultana suka ce
"Na/na gode Ummaa"
Wani qayataccen murmushi ne ya bayyana a fuskar Lawwali, miqewa ya yi, ya ce in sun gama su masa magana, zai maida su gida
Duk wani motsin Mubaraka na kan idon Sultan, duk ya sa ta ta kasa sakewa, qarshe sai da suka hau sama yin Sallah, sannan ta samu ta ji kamar an zare mata wani abu da ya takura walwalar ta.
Sun kai kimanin awa guda,kafin Baraka ta raka su waje.
A bakin motar shi ya tsaya, ya na jiran su, da kan shi ya budewa Lamishi mota, ta shiga, ta na mai jin dadi, da da suke tsananin maitar mota ma ko kusa da ita ya hana su zuwa, amma yanzu gashi shi ke bude musu su zauna.
Sallama suka yi da Mubaraka, ya ce zai debo mata kayan ta, in ya kai su Lamishi, nan ta fara shagwaba, ita Umman ta ne za ta debar mata kayan, ta yi ajiya ba ta so ya gani, yafitar ta yayi, ta kai kunnen ta saitin bakin shi,
"Na hwa san mi ki ke boye min, yo ni ma mata ta ta na da su, ko d'azu a gida sai da na wanke mata su, mi na na acciki to dan na gani, ni ne fa Yah Auwal d'in ki"
Dariya take son ta yi amma dole ta daure, dan ko ba komai gidan rasuwa suke
Shi kuwa fita ya yi da mota ya na dariya,.
Lamishi kuwa cikin ran ta, ta na jin wani irin dad'i na ratsa ta, a baya haushi take ji, ta ga Lawwali na fifita Mubaraka akan su, amma yanzu sai ta gane hakan ba wata matsala bace da zata sa ta dinga jin haushi, hakan na nuna su din su na son junan su, da bawa juna kulawa.
Bayan sun Isah gidan, ya sha mamakin ganin Icce da gawayi buhu uku, a aje a rumfar da Dan Talo ke ta yi da kan shi, juyawa Lawwali ya yi bayan motar ya ce ma su Lamishi,
"Wa ka sai da ic-ce a unguwar nan?"
"Baban ku ne, ya ce yanzu in shaa Allahu ba zai sake zaman banza ba,da kuddin da ka bamu, ya samu ya siyo komai da shika bid'a, abokan shi na masa dariya, shi ko ko a jikin shi, sai da ya qare ya siyo motar icce guda an ka juye mai, ya sa gawaiyi, har da barahuni (kananzir)yaka sayarwa"
"Ikon Allah"
Daga haka bai qara magana ba, fuskar shi dauke da murmushi ya qarasa rumfar.
Sallama suka wa juna, Dan Talo ya dinga neman afuwa da gafarar Lawwali, ya ce ya nemi gafarar sauran yaran shi, ya kuma yi alqawarin zai zama uba na gari
"Allah shi bada iko baba, ni ma ka yahe ni, in shaa Allahu, sana'ar ga sai tayi albarka, yanzu mi ka ke buqata a qaro?"
"Babu komi, in ma akwai ina da kud-din siye, yafe min da ka yi ma ya ishe ni, ban san cin iyali na ba, ban san shan su ba, ban san suturar su ba, balle wajen kwanan su, ba su da lahiya, ko su na cikin b'acin rai, da quncin rayuwa duk ban sani ba, a da ji na nikai kamar wanda an ka d'ebewa tunani,amma yanzu hankali na ya dawo jiki na, na san fari na san baqi yanzu, da yardar Allah sai iyali na sun yi farin ciki da ni kamar yadda kowanne iyali ke jin dad'in mai gidan su"
Lawwali ya kasa cewa komai, sai murmushin jin dad'i kawai ya ke zubawa, nan ya zauna su ka yi ta hira da mahaifin shi, daga qarshe shi ma ya yanke shawarar Kano zai dinga zuwa ya na kasuwanci, duk qarshen wata ya na dawowa.
************************
Zaman mubaraka da su sultana ya sa sun rage kewa kadan, dan kuwa, tare suke haduwa, da Sultanan su yi ta karanta qur'ani, Hajiya Ikee ba a iya karatu ba, ita daga qulhuwallahu sai Fateeha su ma a sallah take yin su, da mutum zai saurara zai rantse da Allah Yaren mutan China take ba larabci ba, rayuwar ta kafff ta qare ta ne wajen neman duniya, amma harafin alif da baa na mata wuyar haɗawa, balle ta kai ga karanta qur'anin sukutum.
Mubaraka ta kula da hakan, dan haka ta qudirta a ranta, za ta taimaka wa Hajiya, dan ganin ta samu tagomashin alkhairi da ladan da ake samu, wajen karanta littafin Allah.
A hankali kuwa Hajiyan ta fuskanci me Mubarakan ke so ta yi,da sauri ta ajiye girman kan ta, ta na koya, Mubaraka ta yi amfani da koyar da Hajiya ta na rage mata kewa, da yawan tunani.
Da ta gilma ta gan ta tana kuka, ko tunani, za ta ce,
"Hajiya, in an had'a, ba'un da fataha, da mimun da fataha, me zai baki?"
Sai ta yi shiruuuu ta na nazari, can sai ta washe baki ta ce,
"Bama"
"Yeeehhh Hajiya za ta ci Bama"
"Yannema ni dai a dinga yi min kad'an kad'an, kar karatun ga shi yi min yawa, in taho banni gane komi"
"Ganewa ki kai inshaa Allahu, kahin Ramadan mai zuwa ke zaki zanka ja wa Aunty Sultana baqi, ita kau ta na fassarawa,tafsirin cikin gida za mu yi"
Dariya sosai suke yi, in Mubaraka na musu irin wannan barkwancin.
Sultan kuwa da ya gan ta zaune da su Hajiya, shi ba ta masa hira kamar ta su Hajiya, sai ya yi ta bata rai,ya na wani abu kamar qaramin yaro, ya na sane sai ya zubar da ruwa, ko tea, ko ya b'ata waje,ya kwala mata kira, Ita kuwa ta gane me yake nufi, ba ta kula shi, sai dai ta je ta gyara wajen, fuskar ta dauke da Murmushi, kallon ta zai ta yi, kamar ya samu TV, da ya ga za ta tafi, zai qara yin wata barnar,dan kawai ta tsaya.
Watarana suna can sama su na hira, Hajiya na basu labarin yanda ta hadu da Daddy, har suka yi aure.
Sultan ya zubar da tea, ya kwalawa Mubaraka kira, tare da sanar da ita ta je da abun gogewa.
Har za ta miqe Hajiya ta ce,
"Zauna, baki zuwa, ni bari na je, na goge masa, in ba ze zo ya ce Hajiya aramin ita ni ma muyi hira ba,ba ki zuwa yi mai aiki, danneman rainin wayo kai, ya zaci ban gane komi ba, tunda takkwala na ke, na hi kowa qaramar kwanya gidan ga"
(Tunda daqiqiya ce ni na fi kowa karamar ƙwaƙwalwa a gidan nan)
Da kan ta ta shiga dakin na shi, Sultan an sha wanka da wata shadda da akai wa d'inkin half jumpa, kan shi ba hula, sai qamshi yake zubawa, ya na tsaye jikin TV, ya na rage volume Hajiya ta shiga, ba tare da ya juya baya ba, ya fara magana,
"Mubaraka, ki yi hankuri da aikin da ni ke saka ki, ta haka ne kawai zan gan ki, dan na kula yanzu ke hi son su Hajiya akai na, jiya Daddy ya cika kwana arba'in da rasuwa, ina fatan nan da wasu kwanaki mu bayyana wa h......"
Maganar shi ce ta maqale da ya juya suka yi ido hudu da Hajiya, fuskar ta ba wani emotion a jiki, ji ya yi gaban shi ya yanke ya fad'i, dube dube ya fara yi, ya na neman Mubaraka, bai gan ta ba,
"Ha...haaajiya Mum, inaa Mubaraka?"
"Dama kenan ta san ka na son ta?"
Yanayin yanda ta yi maganar ya so ya bashi tsoro, cikin zuciyar shi ya fara tsoron kar dai Hajiya har yanzu ba ta dena qin jinin talaka ba? Bai san ya zai da rayuwar shi ba in ta ce ba zai auri mubaraka ba.
Juya baya ta yi, Sultan na nan tsaye ya kasa magana, saboda rashin sanin me ne ne a zuciyar Hajiya Ikee game da zabin shi..........
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 62:
"Dan Allah Hajiya kar ki qi wannan auren, Mubaraka alkhairi ce a gare mu baki d'aya in shaa Allahu, ban ga wata mace da zan iya aura na ji dad'in rayuwa ta ba sama da ita,Kuma na ga yanzu ki na son ta, ko?"
A hankali Hajiya Ikee ta samu waje ta zauna, idanun ta sun sauya kala, daga farare tass zuwa jajaye, saboda hawayen da ke barazanar sauka mata, hancin ta ta ja, sannan ta dora idanun ga a saman fuskar Sultan, da ke a tsugunne a gaban ta, kamar me neman gafara, ya na jiran ya jin kalar hukuncin da za ta yanke.
"Wato Sultan na koyi darrussan rayuwa a qarshen shekarar ga, ba kadan ba, na koyi abubuwa kala kala, ciki ko har da sanin darajar Dan Adam, a
Showing 135001 words to 138000 words out of 150481 words
Lawwali ya shiga rudani, da tashin hankali jin mutuwar uban gidan nashi, tunawa ya yi da cewar, kafin magariba ya wuce ta qofar gidan kafin ya isa nasu, bai ga kowa a gate ba, har ya ke tunanin yanda rayuwa ta koma, ace gidan Gwamna Halliru ne shiru a bushe ba mutane.
Bayan ya katse wayar cikin sauri ya sanya kayan shi, ya yi alwala ya yi sallahr Isha'i, ya na idarwa ya fita dan zuwa gidan, mota ya dauka dan ya na so ya yi saurin isa.
Tafe yake ya na ta tunanin rayuwa, ya na kukan baqin cikin irin rayuwar da ya kasance ya na aikatawa a baya........
*Yau ba appetite ɗin rubutu,amma a haka na cije na daure na ci gaba, sai gobe inshaa Allah kuma*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 61:
Ya na daf da isa gidan, ya ga wata mata zaune a jikin ginin da aka saka street light, da dan qunshin buhu a gaban ta, sai sandar ta da ta jingine a jikin jakar ta, ta rufu da mayafi, da alama anan take da shirin kwana,duk yanda akai ba ta san a wace unguwa take ba, domin a iya sanin shi, wannan unguwar tuni wani zai ciki da ita, a yi wani sihirin da ita, dan neman abun duniya.
Yi ya yi kamar zai tsaya, ya taimaka mata, kawai ya yi gaba, dan ya san yanayin yanda rayuwar ta koma, su kan su, sun sha haɗawa mutane trap da mabarata.
Bai tsaya a ko ina ba sai a bakin gate din gidan su Sultan,mutane ne danqam a wajen gidan, kamar da rana, da kyar ya samu shiga ciki, har da 'yan jarida, da sabon gwamna mai ci,da muqrraban shi.
Lawwali gaisuwa ya dinga miqawa mutanen da ya tarar, tare da ta'aziyya, wasu na yi mishi ta'aziyyar shi ma, kasancewar shi surukin gidan.
Sai da wajen ya d'an lafa ne, Sultan ya raka Lawwali ciki, nan ya samu Sultana a yanayin da ya kasa jurewa sai da kwalla ta taru masa a idanun shi, matan wajen na ganin haka suka firfita, aka basu waje, a hankali ya isa gefen ta ya zauna,cikin murya mai sanyi ya ce,
"Sultyna, ki yi hakuri, mu yi hakuri gaba daya, mu yi ta yi wa Daddy addu'a, dan ko ita ce kad'ai ya ke bid'a wajen mu, kuka ba zai dawo da shi ba, ki yi hankuri kin ji, jarumar mata ta"
A hankali ta ja jikin ta, ta kwantar a nashi, cikin kuka ta ce,
"Ba ina kukan rabuwa da shi bane, dan na san komai daren dad'ewa sai mun rabu,ina kuka ne akan tunanin Daddy bai samu ya furta kowacce kalma da ake saka ran Allah zai yahe masa ba,na tabbata sai ya sha azaba a lahira, saboda abinda ya kasance ya na aikatawa"
Da sauri ya sanya dogon yatsan shi a labban ta, ya ce,
"Kar ki ce haka, kin mance da me kike fadi min kullum, ba a shiga tsakanin bawa da ubangijin shi, in mutum ya yi shisshigi tsakanin bawa da ubangijin shi, shi sai Allah ya hana mishi rahamar sa, ya yi wa wanda ya ke wa zaton Allah ba zai duba da idon rahama ba rahamar "
A hankali ta fara jin wani sanyi a ran ta,
"Haka ne, yanzu ba abinda ya mana saura da ya wuce mu yi ta masa addu'a"
"Allah ya jiqan shi, ya gafarta mishi, na yahe mishi duk abinda ya yi min a rayuwa ta, ni ma ina fata ALLAH shi yahe min"
Wani irin dad'i ne ya kama Sultana, ta qara kwantawa a jikin shi ta na murmushi,
"Na gode miji na, na gode, Allah ya amsa addu'ar ka,....ina Mubaraka?"
"Dazu da mun ka hito gaba daya, mun yi wa daji bankwana, bankwana na har abada da yardar Allah, sai nace zan kawo ta nan wajen mu ta zauna ta ce ah ah, na kai ta gida, to ban san an yi rasuwa ba sai d'azu"
"Allah Sarki, ai da ta zo mun zauna, gidan ai da girma ba laihi, "
"Ke San ta da son su Lamishi,ba ta tahowa wajen mu yanzu, ban qi ba in ta gaji da zama wajen su,amma ke san mi ya faru?"
"Sai ka hwadi,"
"Da na je gida, na ga sauyi sosai wajen Baban mu,na tarar ya na yin rumfa, ban san mi ya ka son yi ba, mun gaisa cikin wani irin yanayi da ban san ya zan kira shi ba,ba wannan rawar kan kamar zai min kwacen kuddi, ita kan ta Lamishi haka, duk sun yi wani iri, har da yi wa Barakana oyoyo"
"Alhamdu lilLAAH, Allah ya qara kawo mana zaman lafiya, da shiriya,"
"Ameen Allah ya jiqan Daddy,"
Ta ji dad'in yanda Lawwalin ke ta masa addu'a ko ba komai, hakan ya nuna ba wani riqo a tsakanin su.
"Kin ci abinci kuwa?"
"Ahh ahh, gashi can, an kawo mana ni da Hajiya, mun kasa ci,amma yanzu da ka yi magana, na ji ina jin yunwa, ba zan iya ci bane kawai, baki na ba dad'i"
"Ayyaa dear, haka zaki daure ki ci, kin jiya?"
Tashi ya yi, da kan shi ya haɗa mata tea, ya bata, ta shanye tass,ya bata abinci kadan, ta ci, ta masa godiya, sannan ya mata sallama,ya leqa dakin da Hajiya Ikee da qawayen ta ke zaune, ya musu ta'aziyya.
Abun da ya gani ya bashi takaici, ba dan ace ya shiryu ba, da in ya buga wa wata mata da ta kafe shi da ido tsawa, sai ta rasa ina zata ta buya dan tsoro.
Tsaki ya yi a daidai saitin matar da zai fita, ta na zaune kamar wadda ta zo biki, ko ina gwala-gwalai ne,ga wata arniyar shadda ta zuba sai maiqo take.
Ta kunna snap chat kamar wata yarinya, ta na zaro harshe, ta na mayarwa, ya na shiga ta kafe shi da Mayun idanun ta, inda yake a tsugunne ta miqar da qafar ta sai da ta taɓa tashi,kallon da ya mata ne ya sanya ta janye wa da sauri ta na yaqe,ita a dole ba da niyya ta yi ba.
An zo gidan rasuwa amma wasu rasuwar bata dame su ba ma, wasu kuwa sun sanya hijabi,an riqe carbi, amma ba abinda suke sai hira.
A haka ya fita ya na takaicin yanda gidan rasuwa ya ke komawa kamar na biki, a wannan zamani.
Bai sake komawa wajen Sultana ba, gaisawa suka sake yi da su Sultan, ya tafi gida.
Sai sha d'aya na dare wasu mutanen suka dinga tafiya.
Sai da Hajiya Ikee ta zo bacci hankalin ta ya sake tashi, ita kuka Sultana kuka, ba mai lallashin wani,tabbas ba su taba zaton sun shaqu da shi har haka ba sai yanzu, ko ba komai shi din uba ne mai kulawa, ko sun ci, ko basu ci ba, ko suna da wata damuwa, ko basu da ita, shin farin cikin fuskar su ya ishe shi? Ko ya na so su fi haka farin ciki?
Har safiya Sultana bata rintsa ba, ta na kan sallaya, ga yunwa ta na ji, ta kasa cin komai.
Hajiya kuwa ba zata iya tuna sanda ta saka ko da ruwa bane a bakin ta.
Tausayin Hajiyar ne ya sa ta miqe da kyar, marar ta na murdawa, ta nufi hanyar parlour, za ta hado mata tea, wani irin jiri ne ya ɗebe ta, ta kusan faduwa, daddafe jikin bango ta yi, Hajiya Ikee da sauri ta isa wajen ta,cikin kuka ta ce,
"Dan Allah samu waje ki zauna, ko me ki ke so za a miki,dan Allah kar ki sa wa kan ki damuwa ke ma na rasa ki, ba zan iya daukan rashin ku ba,"
Kuka Hajiya Ikee ke yi sosai, Sultana kasa bata hakuri ta yi, sai da wasu 'yan uwan Hajiyan suka sa baki, sannan ta rage kukan.
Zama suka koma suka yi,tace a hadowa Hajiya Tea, da kyar aka tursasa ta ta sha, jin shi ta yi kamar mad'aci, amma haka ta daure ta sha.
A haka, a haka dai har sai da akai sadakar bakwai,sannan mutane suka tattafi gidajen su, dan yanda suka saba in sun zo a ci a sha a raqashe da kaji babu, duk da ana kawo na sadaka, amma ba kamar da gwamna na da rai ba.
*******************
A kwana na goma sha biyu, Lawwali ya je gidan Gwamna,dan gaishe da Hajiya, yanzu ya na bata girma sosai, saboda tausayi take bashi.
Ya na nan duqe gaban ta, ta na ta bashi labaran yanda tsohon gwamnan yake kyautatawa iyalan shi, da yanda ya ke matuqar son su, su Lamishi suka yi sallama, amsawa Hajiya Ikee ta yi, cikin d'an sakin fuska .
Zama su Lamishi za su yi a qasa, da sauri Hajiya Ikee ta ce,
"Dan Allah ku tashi daga qasa, rayuwar ga duk labari ce watarana, dan Allah mu yahe wa juna, abubuwan da sun ka hwaru a baya,"
"Allah Sarki Hajiya komi ya wuce, ya hankuri?"
"Alhamdu lilLAAHi,"
"Allah shi jiqan gwauna, shi mai rahama, Allah shi gafarta mai"
"Ameen Allah shi bada lada"
Mai Buruji, Mubaraka, duk sai da suma su ka bada gaisuwar su wajen Hajiya,da Sultana.
Sultana ce da ta fito daga ciki, ta je yin alwala, ta ga su Lamishi, da sauri ta je ta durqusa gaban su, suka gaisa, suka mata ta'aziyya, Mubaraka ce ta zauna kusa da ita, ta na sake mata ta'aziyya,
"Ameeen na gode, amma dai nan za a bar ki ko? Sai an yi arba'in"
Kallon Lamishi ta yi, ta na neman izini, da ido,daga baya ta maida duban ta wajen oga Lawwali, ta dire shi akan Sultan,da ya kafe ta da ido ya na jiran jin amsar ta, kowa ya yi Mamakin yanda Lamishi ta yi sanyi, ta koma kamar ba ita ba,
"Ki zauna, ba ya da komi, ai duk ɗaya ne"
A tare Mubaraka da Sultana suka ce
"Na/na gode Ummaa"
Wani qayataccen murmushi ne ya bayyana a fuskar Lawwali, miqewa ya yi, ya ce in sun gama su masa magana, zai maida su gida
Duk wani motsin Mubaraka na kan idon Sultan, duk ya sa ta ta kasa sakewa, qarshe sai da suka hau sama yin Sallah, sannan ta samu ta ji kamar an zare mata wani abu da ya takura walwalar ta.
Sun kai kimanin awa guda,kafin Baraka ta raka su waje.
A bakin motar shi ya tsaya, ya na jiran su, da kan shi ya budewa Lamishi mota, ta shiga, ta na mai jin dadi, da da suke tsananin maitar mota ma ko kusa da ita ya hana su zuwa, amma yanzu gashi shi ke bude musu su zauna.
Sallama suka yi da Mubaraka, ya ce zai debo mata kayan ta, in ya kai su Lamishi, nan ta fara shagwaba, ita Umman ta ne za ta debar mata kayan, ta yi ajiya ba ta so ya gani, yafitar ta yayi, ta kai kunnen ta saitin bakin shi,
"Na hwa san mi ki ke boye min, yo ni ma mata ta ta na da su, ko d'azu a gida sai da na wanke mata su, mi na na acciki to dan na gani, ni ne fa Yah Auwal d'in ki"
Dariya take son ta yi amma dole ta daure, dan ko ba komai gidan rasuwa suke
Shi kuwa fita ya yi da mota ya na dariya,.
Lamishi kuwa cikin ran ta, ta na jin wani irin dad'i na ratsa ta, a baya haushi take ji, ta ga Lawwali na fifita Mubaraka akan su, amma yanzu sai ta gane hakan ba wata matsala bace da zata sa ta dinga jin haushi, hakan na nuna su din su na son junan su, da bawa juna kulawa.
Bayan sun Isah gidan, ya sha mamakin ganin Icce da gawayi buhu uku, a aje a rumfar da Dan Talo ke ta yi da kan shi, juyawa Lawwali ya yi bayan motar ya ce ma su Lamishi,
"Wa ka sai da ic-ce a unguwar nan?"
"Baban ku ne, ya ce yanzu in shaa Allahu ba zai sake zaman banza ba,da kuddin da ka bamu, ya samu ya siyo komai da shika bid'a, abokan shi na masa dariya, shi ko ko a jikin shi, sai da ya qare ya siyo motar icce guda an ka juye mai, ya sa gawaiyi, har da barahuni (kananzir)yaka sayarwa"
"Ikon Allah"
Daga haka bai qara magana ba, fuskar shi dauke da murmushi ya qarasa rumfar.
Sallama suka wa juna, Dan Talo ya dinga neman afuwa da gafarar Lawwali, ya ce ya nemi gafarar sauran yaran shi, ya kuma yi alqawarin zai zama uba na gari
"Allah shi bada iko baba, ni ma ka yahe ni, in shaa Allahu, sana'ar ga sai tayi albarka, yanzu mi ka ke buqata a qaro?"
"Babu komi, in ma akwai ina da kud-din siye, yafe min da ka yi ma ya ishe ni, ban san cin iyali na ba, ban san shan su ba, ban san suturar su ba, balle wajen kwanan su, ba su da lahiya, ko su na cikin b'acin rai, da quncin rayuwa duk ban sani ba, a da ji na nikai kamar wanda an ka d'ebewa tunani,amma yanzu hankali na ya dawo jiki na, na san fari na san baqi yanzu, da yardar Allah sai iyali na sun yi farin ciki da ni kamar yadda kowanne iyali ke jin dad'in mai gidan su"
Lawwali ya kasa cewa komai, sai murmushin jin dad'i kawai ya ke zubawa, nan ya zauna su ka yi ta hira da mahaifin shi, daga qarshe shi ma ya yanke shawarar Kano zai dinga zuwa ya na kasuwanci, duk qarshen wata ya na dawowa.
************************
Zaman mubaraka da su sultana ya sa sun rage kewa kadan, dan kuwa, tare suke haduwa, da Sultanan su yi ta karanta qur'ani, Hajiya Ikee ba a iya karatu ba, ita daga qulhuwallahu sai Fateeha su ma a sallah take yin su, da mutum zai saurara zai rantse da Allah Yaren mutan China take ba larabci ba, rayuwar ta kafff ta qare ta ne wajen neman duniya, amma harafin alif da baa na mata wuyar haɗawa, balle ta kai ga karanta qur'anin sukutum.
Mubaraka ta kula da hakan, dan haka ta qudirta a ranta, za ta taimaka wa Hajiya, dan ganin ta samu tagomashin alkhairi da ladan da ake samu, wajen karanta littafin Allah.
A hankali kuwa Hajiyan ta fuskanci me Mubarakan ke so ta yi,da sauri ta ajiye girman kan ta, ta na koya, Mubaraka ta yi amfani da koyar da Hajiya ta na rage mata kewa, da yawan tunani.
Da ta gilma ta gan ta tana kuka, ko tunani, za ta ce,
"Hajiya, in an had'a, ba'un da fataha, da mimun da fataha, me zai baki?"
Sai ta yi shiruuuu ta na nazari, can sai ta washe baki ta ce,
"Bama"
"Yeeehhh Hajiya za ta ci Bama"
"Yannema ni dai a dinga yi min kad'an kad'an, kar karatun ga shi yi min yawa, in taho banni gane komi"
"Ganewa ki kai inshaa Allahu, kahin Ramadan mai zuwa ke zaki zanka ja wa Aunty Sultana baqi, ita kau ta na fassarawa,tafsirin cikin gida za mu yi"
Dariya sosai suke yi, in Mubaraka na musu irin wannan barkwancin.
Sultan kuwa da ya gan ta zaune da su Hajiya, shi ba ta masa hira kamar ta su Hajiya, sai ya yi ta bata rai,ya na wani abu kamar qaramin yaro, ya na sane sai ya zubar da ruwa, ko tea, ko ya b'ata waje,ya kwala mata kira, Ita kuwa ta gane me yake nufi, ba ta kula shi, sai dai ta je ta gyara wajen, fuskar ta dauke da Murmushi, kallon ta zai ta yi, kamar ya samu TV, da ya ga za ta tafi, zai qara yin wata barnar,dan kawai ta tsaya.
Watarana suna can sama su na hira, Hajiya na basu labarin yanda ta hadu da Daddy, har suka yi aure.
Sultan ya zubar da tea, ya kwalawa Mubaraka kira, tare da sanar da ita ta je da abun gogewa.
Har za ta miqe Hajiya ta ce,
"Zauna, baki zuwa, ni bari na je, na goge masa, in ba ze zo ya ce Hajiya aramin ita ni ma muyi hira ba,ba ki zuwa yi mai aiki, danneman rainin wayo kai, ya zaci ban gane komi ba, tunda takkwala na ke, na hi kowa qaramar kwanya gidan ga"
(Tunda daqiqiya ce ni na fi kowa karamar ƙwaƙwalwa a gidan nan)
Da kan ta ta shiga dakin na shi, Sultan an sha wanka da wata shadda da akai wa d'inkin half jumpa, kan shi ba hula, sai qamshi yake zubawa, ya na tsaye jikin TV, ya na rage volume Hajiya ta shiga, ba tare da ya juya baya ba, ya fara magana,
"Mubaraka, ki yi hankuri da aikin da ni ke saka ki, ta haka ne kawai zan gan ki, dan na kula yanzu ke hi son su Hajiya akai na, jiya Daddy ya cika kwana arba'in da rasuwa, ina fatan nan da wasu kwanaki mu bayyana wa h......"
Maganar shi ce ta maqale da ya juya suka yi ido hudu da Hajiya, fuskar ta ba wani emotion a jiki, ji ya yi gaban shi ya yanke ya fad'i, dube dube ya fara yi, ya na neman Mubaraka, bai gan ta ba,
"Ha...haaajiya Mum, inaa Mubaraka?"
"Dama kenan ta san ka na son ta?"
Yanayin yanda ta yi maganar ya so ya bashi tsoro, cikin zuciyar shi ya fara tsoron kar dai Hajiya har yanzu ba ta dena qin jinin talaka ba? Bai san ya zai da rayuwar shi ba in ta ce ba zai auri mubaraka ba.
Juya baya ta yi, Sultan na nan tsaye ya kasa magana, saboda rashin sanin me ne ne a zuciyar Hajiya Ikee game da zabin shi..........
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 62:
"Dan Allah Hajiya kar ki qi wannan auren, Mubaraka alkhairi ce a gare mu baki d'aya in shaa Allahu, ban ga wata mace da zan iya aura na ji dad'in rayuwa ta ba sama da ita,Kuma na ga yanzu ki na son ta, ko?"
A hankali Hajiya Ikee ta samu waje ta zauna, idanun ta sun sauya kala, daga farare tass zuwa jajaye, saboda hawayen da ke barazanar sauka mata, hancin ta ta ja, sannan ta dora idanun ga a saman fuskar Sultan, da ke a tsugunne a gaban ta, kamar me neman gafara, ya na jiran ya jin kalar hukuncin da za ta yanke.
"Wato Sultan na koyi darrussan rayuwa a qarshen shekarar ga, ba kadan ba, na koyi abubuwa kala kala, ciki ko har da sanin darajar Dan Adam, a
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46 Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51