Taheer ya tafi da rabin awa, Sultana ma su ka yi haramar tafiya, zaune suke a cikin mota ita da Sultan, sai wanda zai kai su, dan ba za su gane hanyar fita ba.
Ido Sultana ta zubawa Lawwali kamar ta ce masa su je tare, ba ta so su rabu ko na awa guda ne, amma ta san ba ta da wannan damar, in ba shi ya sakko da kan shi daga fushi da Gwamna ba, ba wanda ya isa ya ce ya sauka din, to wataqila sai Mubaraka .
Mubaraka ta gama yadda da cewar hasashen ta na Sultan na son ta qarya ne, hasashen farko na ita din bata kai wadda zai so ba shi ne gaskiya, sallama ta musu, zuciyar ta na matuqar quna, ta bar wajen, za ta koma dakin ta, dan a yanzu ba ta so ta bude baki ta yi magana, za ta iya fashewa da kukan da ya tokare mata wuya.
Muryar shi ta ji a bayan ta, cikin sanyi ya kira sunan ta,
"Mubaraka"
Bata gasgata kunnen ta ba, dan haka bata juya ba, a zaton ta gizo Muryar shi ke mata, saboda ta na tsananin so ya kira ta din dan ya furta mata kalmar so.
Tafe take shi kuwa binta yake, tun da ta juya ta fara tafiya ya kasa samun sukuni, kasa jurewa ya yi, ya ce a jira shi, Sultana da Lawwali na tsaye su na kallon shi ya bi ta da gudu.
Maimaita kiran sunan nata ya yi, Ita kuwa a yanzu ta tabbata ba gizo Muryar shi ke mata ba, dan haka tsayawa ta yi cak, bakin ta dauke da murmushi, da hope din son jin kalmar so daga bakin shi,idanun ta taf hawaye,
"Mubaraka, na kasa tafiya ba tare da na bayyana maki saqon da zuciya da gangar jiki na ke ta bani ba, Mubaraka ina son ki, I love u so much, tun randa na fara dora ido na akan ki a gidan mu, na ji wani baqon lamari ya darsu a zuciya ta game da ke, ban fahimci ko me ne shi ba, saboda ni baqo ne a fagen so, tun daga lokacin nan ba ranar da za ta zo ta wuce ban tuna ki ba, amma na bar wa zuciya ta, dawowar ki daga Kano, na ga kin qara girma, kin qara nutsuwa sai na ji abinda nake ji game da ke ya na nunkuwa a rai na, a yanzu na tabbatar da cewa, ke kadai nake so, ke ce macen da na ke jira, shi ya sa na kasa kula kowacce mace da sunan soyayya"
Wata ajiyar Zuciya suka sauke kusan a tare, Mubaraka ta ji dadi kwarai, wanda ba shi da misali,Sultan kuwa ji ya yi kamar an sauke masa wani babban nauyi da ya jima ya na dauke da shi akan shi.
Juyawa ta yi a hankali suka hada ido, cikin jin kunya ta sauke nata idon,sannan ta saki murmushi, shi ma ita yake kallo, cike da so da qauna,amma ya tabbata da ta na kallon shi ne tun dazun da ba zai iya furta kalaman da suka dinga fita daga bakin shi ba kamar ruwa.
A hankali ya ce,
"Baki amsa min ba, kin karbi soyayya ta, ko dai ban miki ba ne?"
Da sauri ta kalle shi, daga sama har qasa, sannan ta ce,
"Wacce mace zaka ce wa ka na so ta ce bata son ka Yah Sultan?"
"Macen da ba ta son na miji mai kama ta, ko mai irin halaye na mana Mubaraka"
"To ni dai kamannin ka, da halayen ka duk sun yi min, ba ka da makusa a iya sanin da na maka"
"Hakan na nufin ki na so na kenan?"
Daga kai ta yi, ta juya cikin sauri ta nufi hanyar dakin ta, kallo ya bi ta da shi, Lawwali ne ya dafa shi, ya ce,
"Tau baban soyayya, tunda ka qare aman zucciyar ka, yi hankuri ka dena kallon qauna ta haka nan, kar ta faɗi"
Dariya Sultan yayi,ya ce,
"To babban Yaya za a bani?"
"Shi kadai ne buri na tun farko ,kuma gashi kun had'a kan ku, ya na daga cikin sharadin da nake da burin mahaifin ku ya cika min, sai ga shi kun hada kan ku da kan ku, Allah shi sanya albarka cikin wanga lamari"
"Ameeen, ina godiya, waccan matar taka ta matsu na san taji me ke hwaruwa, bari mu tai, sai ka iso,"
"Tau ya yi, Allah shi kiyaye hanya"
"Ameen"
Mota Sultan ya shiga cike da farin ciki,ya bayyana wa Sultana me ya faru,ta yi murna kwarai da jin hakan.
Mubaraka kuwa leqawa ta dinga yi ta window ta na kallon Sultan, bayan tafiyar su Lawwali ya kira kowa da kowa, ya fidda makullan gidajen da yake da su a hannun shi, wanda ba shi da su kuma a wajen shi Sultan ya ce zai bashi in sun hadu a cikin gari.
Miqawa wasun su makullan yayi sannan ya sanar da su, ba zai yu kowa ya samu gida shi daya da matar shi ba, wani gidan sai dai mutum biyu, wani gidan ma sai dai mutum uku, daga baya duk wanda Allah ya horewa ya tashi.
Godiya suka dinga yi, tare da addu'a da fatan alkhairi,wasu daga cikin matan har ma da mazan kuka suka dinga yi, sabo kenan, turken wawa.
Suna nan su na jajanta rabuwar su da juna mazajen da suka maida Limaman da suka daura musu aure suka dawo, nan aka sanar da su me ya faru, sun yi godiya sosai, sannan suma sun jimanta rabuwa da junan su.
Lawwali dakin su ya je, ya aika a kira masa Mubaraka.
Ita ta taya shi hade kayan su shi da Sultana, ya bada umarnin kayan gadon a kai masa gidan su, can dakin Mubaraka za a saka.
Su na gyara dakin ne ya bijiro mata da maganar Sultan, kunya ce ta kama ta, shi kuma dariya ya yi, ya ce,
"Ohhh rayuwar duniya kenan, wai Mubaraka 'yar qararramar nan ce yanzu ta girma har ta kai ga saurayi, Allah to shi sanya alkhairi, "
"Kaiii Yah Auwal ni fa ba yanzu za ka yi min auren ba, ni dai ba na so na rabu da ku"
"Tabbb ai kuwa ya zama dole, ko ba aure ai akwai mutuwa ko? Ballantana mace dama ita ba mazauniyar gidan iyayen ta bace, komai daren dad'ewa za ta yi aure, sai wadda Allah ya nufa ba zata taba aure ba a rayuwar ta"
"Haka ne, Allah ya sa mu dace,...Yah Auwal yau za mu bar nan?"
"Ahh ahh, sai gobe ko jibi ma, sai an kai kayan ga gida, an gyara miki d'akin ki, sannan zan maishe ki da hannu na, na damqa musu amanar ki,na gaji da faɗa da kowa ni yanzu, ba na son tashin hankali da kowa, in kin koma ki sanya wa zuciyar ki hankurin zama da su, tunda kin dai san yanda halin su shike,"
"Haka ne Yah Auwal, in shaa Allahu, za ka same ni mai hakuri"
"Allah ya miki albarka Barakana, dama can ke mai hakuri ce,Allah shi qara maki hankuri akan duk abinda zai same ki"
Ameeen, Yah Auwal dina"
Haka sukai ta hirar su, su na tattara kayayyakin Sultana.
*************************
Wata mata ce a tsaye a jikin mota, a gaban wani babban super market ta na waya, kaya aka debo niqi niqi za a saka a bayan mota, ta danna key din hannun ta, ma'aikatan super market din suka zuba kayan, Laminu na can gefe ya na kallon ta, ya jima ya na bin matar tun safe da ya fito daga gida, har yamman nan.
Su na gamawa ta sallame su,ta shige motar ta, ta tada ta, ta hau titi, Laminu ma bin ta ya yi a baya, wata hanya ta dauka, wadda take shiru ba mutane sosai, shi ma binta ya yi, ya sha gaban ta, wani burki ta ci, tare da daga kai, a tsorace, ta kalle shi.
A tare suka fito daga motocin su, Laminu ne ya nufe ta da fuskar tausaya wa, da ban hakuri, ya shammace ta ya shaqa mata wani tsumma a hanci, dauke numfashin ta tayi, ta kama hannun shi ta juyar da shi ta murde shi, ya fadi qasa da guiwowin shi, su na haka wasu motocin jami'an tsaro suka qaraso, su ma tafe suke su na bin su a boye dama.
Sake numfashin ta tayi, ta shaqi iska, duk da haka sai da d'an wanda ta shaqa ya sa ta jiri.
Kamata wani daga jami'an tsaron ya yi, suka sa ta a mota, Laminu kuwa tuni an danna shi a motar 'yan sandan, nan suka dunguma baki dayan su, sai police station, ana zuwa dakin tuhuma aka miqa Laminu.
Binciken da jami'an tsaron suka yi akan mutuwar yaron da suka kama dan ya bada shaida akan wanda ya sa su sace Hajiyan Hansatu ya nuna musu cewa akwai sa hannun Laminu, dan haka suka had'a masa wannan tarkon da jami'ar tsaro mace, suka samu nasarar kama shi.
Laminu ya qi bayyana abokan ta'addancin shi da fari sai da ya ci na jaki, ya ga za su masa lahani a banza, shi ne kuwa ya bayyana sunan Isah, nan da nan kuwa aka kira Yaya Musa aka sanar da shi su na buqatar su a station din, dan jin yanda ta kaya.
Hajiya na ta murna ta shirya ta ce ma Yaya Musa su je,a hanya ta kira Hansatu ta sanar da ita an kira su a police station, an ce a samu wani mahimmin bayani, da ya kamata su sani.
Fatan alkhairi ta musu sannan ta ce in su Ameenatu sun taso daga makaranta za su zo.
Su na isa station din aka sanar da su mummunan labarin da ya sanya Hajiya kuka wiwi, da idanun ta, sai lallashin ta ake ta kasa denawa, ta dauki soyayya mai tsafta ta sanya a zuciyar ta wa Isah ashe mutumin banza ne.
Har wajen Laminu aka je da su, ta kalle shi ta ce,
"Allah wadai da samuwar irin ku cikin al'ummar Annabi Muhammad, Allah ya shirya masu hali irin naku, yanzu ka dube ka, yaro kyakkyawa, wa ze ce za ka aikata wannan mugun abu? Yanzu shi abokin naka kuna waya ne? Dan tun da ya tahi bai kire ni ba, wancan karon kuwa ya na kira na"
Cikin jin kunyar dattijuwar Laminu ya ce,
"Hajiya Isah bai dawo wa yanzu gaskiya, dan kuwa abokin harka ta ta saida koken wani inyamuri ya ce ya sanya koken cikin kayan Isah kamar yanda mun ka tsara, kuma an kama Isah, an kulle shekara goma zai yi a kurkuku,"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'una, kaiii wanga yaro kwai baqin mugu, wato abokin naka ka ci wa amana haka? Shi na can daure ga hukumar da bata san sassauci ba, ka mayar min da d'iya ita da zaura (bazawara) ba su da banbanci, Allah ka isar min, Allah ka isar mana abinda yaran nan su ka yi muna"
Kuka sosai Hajiya take faman yi, a haka suka koma gida, Laminu na nan ana shirye shiryen miqa shi ga kotu, asirin shi ya gama tonuwa.
Tun a hanya Hajiya ta kira Hansatu ta ce ta samu abun hawa ta taho,ta wa driver waya ya kawo su Ameenatu gidan ta, cike da damuwa Hansatu ta ce to, bata so ta tsaya tambayar Hajiyan meke faruwa ta waya.
Rurrufe ko ina ta yi, sannan ta leqa gidan 'Yabbuga ta gaishe ta, ta sanar da ita zata gidan su,a hanyar ta ta zuwa bakin titi, ta wuce ta qofar gidan su Lamishi ta ga ana ta shiga da kayan gado.
Ga wata rumfa nan Dan Talo na ta bugawa a qofar gidan da kan shi.
A bakin gate din gidan su aka ajiye ta, ta shiga, bayan ta gaida mai gadi ta wuce cikin gidan.
A parlour ta tadda Yaya Musa da Yaya Abdullahi (Yayan matar Musa) su na zaune cikin jimami, su na ganin ta kowannen su fuskar shi ta sake danyancewa da tausayin ta.
Hajiya kuwa kuka ta sanya, ta dinga yafitar Hansatu da hannu, wajen ta ta nufa ta zauna daf da ita, ta na so ta yi kuka, dan ta san duk abinda ya sanya Hajiya kuka ba qarami bane.
"Hajiya mi ya faru? Mutuwa an kai? Me ya samu Aunty Azizah?"
Ta na fada ta na kallon Abdullahi, da sauri ya kada mata kai, alamar Ah ah,
"Lafiyar ta qlou, ta na Spain ma yanzu haka,"
"To me ya faru?"
Yaya Musa ne ya daure ya labarta mata komai, Hansatu kuka ta sanya, tare da fadin
"Ba zan taba yafe maka ba Isah, soyayyar ka ba ta amfanar da ni komi ba,ka cutar dani, ba iyaka, na hakura, amma sai da ka haɗa da mahaifiya ta, Isah me ta yi maka? In ni ce baka so sai ka sawwaqe min, me mahaifiya ta ta maka?......Hajiya, Hajiya, kin tuna sanda an ka sace su Ameenatu? Tabbas Isah na da hannu a wannan satar"
"Ahh ahh Hansatu, babu kyau zargi, dan kuwa wannan zargi ne, ba ki tabbatar ba"
"Hajiya ina da yaqinin da sa hannun Isah a wannan lamarin saboda tun sannan suke abota shi da Laminu, Hajiya akwai abubuwan da ban sanar da ke ba saboda bana so hankalin ki ya tashi, na dauki alqawarin tunda ni na bijire muku na zabe shi, komi ze yi min zan shanye ba zan fada wa kowa ba, Hajiya Isah na min......"
Nan dai Hansatu ta dage ta sanar ma da mahaifiyar ta komai da Isah yake mata, Hajiya da kowa da ke wajen ya tausaya mata,sannan sun mata faɗa sosai, musamman akan qin sanar da Hajiya tunda ya tafi wancan karon bai neme ta ba, ai da ta sanar tun a sannan da an dau mataki.
"Tau shi kenan yawuce ,Musa ai ka ga da rabon Allah shi hannunta shi can ga hukumar da sun ka fi mu iya hukunci, yanzu yanda za a yi, kai da Abdullahi,ku shirya ku je can wajen shi, ya sakar min d'iya ta, walle ta gama auren shi, ya qarasa shekarar shi goma ya bid'i wata ya aura, ina dalili.
In ya tsaya muku taurin kai, ku faɗa masa za ku yi qarar shi akan abinda ya yi wa hansatu a can, ku tsoratar da d'an nema, ya sake ta dolen shi, yarinya ta da kyawun ta ba zata rasa mashinshini ba"
Abdullahi ne ya kalli Hansatu da sauri, a zuciyar shi ya na ayyana abubuwa da dama, babban abinda ya sani shi ne, wannan karon ba me auren ta sai shi, ba zai bari ta sake kufce masa ba.
An tsaida magana a cikin sati na sama za su tafi zuwa saudiya, Hansatu kuwa ta ce ba za ta koma unguwar su ba, unguwar gulma, dan ta san yanzu magana ta karade unguwar, za a yi ta nuna ta da baki da ido ne.
Hajiya ma cewa ta yi ta yi zaman ta, ai kuwa ita da yara nan suka samu wajen zama abun su, tun daga ranar Hansatu ta samu abokiyar hira, haka zata zauna ta yi ta bawa Hajiya labarin abubuwan da Isah ke mata, Hajiya kuwa ta ce,
"Ke ko gama zama da baqin mugu,dan neman sallamamme kawai"
****************************
Da isar su asibiti, Hajiya Ikee ta ɗora idon ta akan yaran nata, sai ta fashe da kukan murna, fess ta gan su, wanda ba haka suka zata ba gaba dayan su, wani haske da sheqi ma taga su nayi, musamman Sultana.
Bayan sun gaisa ne, ta ja su har gaban gadon da gwamna yake kai, duk ya fada ya rame,sai gulu gulun idanuwa, bakin shi ya karkace hannu da qafar shi kamar wanda Inna ta taba,asibiti sun tabbatar da cewa ba shi da wani ciwo da ya danganci asibiti a yanzu,sai qarancin jini da yake fama da shi,kullum ana qara masa jini leda biyu zuwa uku, hawan jinin da ya kama shi ma ya sauka, tun da jimawa, sun yi gwaje gwaje sun rasa dalilin da ya sa yake a shanye haka, kuma jinin shi ke yawan qarewa.
Hajiya Ikee na gama basu labarin rashin lafiyar mahaifin nasu Sultan ya ce,
"Hajiya ai da wahala Daddy ya warke,ko da zai warke din ma, domin kuwa mutane irin shi na fama da cututtukan da ake rasa gane kan su ne sakamakon Allah ya isa da mutane ke yi musu, da za a ce za a tara duk mutanen da ya zalunta, su yahe masa, na miki alqawalin sai ya miqe, amma in basu yahe masa ba, zai wahala ya tashi "
"Innalillahi, na shiga uku ni Ikilima, ina zan saka rayuwa ta? Yanzu fissbillahi haka ka ke ganin ba zai tashi ba sai mutane sun yahe masa? To mu yanzu ina mun ka san adadin wanda ya zalunta?"
"Ba lallai bane kuma, ta yu Allah shi bashi lafiya, amma fa zai karbi hukuncin da ya aikata a ranar gobe, in dai be tuba ba"
"Yau na shiga uku na lalace ni ikilima"
Kuka sosai Hajiya Ikee ke yi, shawara Sultana ta kawo, akan su maida Gwamna gida a na maganin Islamic, saboda yanzu kusan watan shi biyu a kwance, komai sai an masa, Hajiya duk ta rame,
"Ai dole gida zamu kai shi, in kunka ji kuddin da asibitin ga ke karba duk kwana guda sai tsoron Allah ya kama mutum, gwamnan da an ka mayar yanzu so guda ya taho da tawagar shi sun ka duba Daddyn ku, da 'yan jarida, akai ta hotuna da video, ko sisi basu bamu ba, amma sun ce sun basuwa kuddin jinya har ya ji sauqi, kuma ga shi asibiti kullum ni ka biyan kuddi"
"Hummm Mum kenan, a bar tone tone, mu samu yanzu a kama muna shi mu tai gida"
Bayan komawar su gida ne suka sha kallon ikon Allah, gwamna banda ihu da shure shure ba abinda yake, abun ya yi matuqar basu mamaki,Sultan ne ya ce su fitar da shi waje, ai kuwa ana fita waje ya dena ihun, sai zare ido kawai yake, da jin tsoron kar a maida shi ciki.
"Sultan mu tai gidan mu na can titin zanna, wataqilan nan ne bashi so"
"Bamu da wani gida da ya yi saura sai wanga, dan kuwa duk na bayar, anjima ma za a taho amsar makullai,nan din dai zamu koma, dole ya yi hankuri,"
"Yau na shiga uku na lalace ni Ikillma, kai wa Allah ku bamu makullin guda, wanda ka bawa wancan su amshi wanga"
"Muka san menene acikin gidan da za mu ba wa wasu shi? Mu din dai mu za
Showing 129001 words to 132000 words out of 150481 words
PAGE 59:
Taheer ya tafi da rabin awa, Sultana ma su ka yi haramar tafiya, zaune suke a cikin mota ita da Sultan, sai wanda zai kai su, dan ba za su gane hanyar fita ba.
Ido Sultana ta zubawa Lawwali kamar ta ce masa su je tare, ba ta so su rabu ko na awa guda ne, amma ta san ba ta da wannan damar, in ba shi ya sakko da kan shi daga fushi da Gwamna ba, ba wanda ya isa ya ce ya sauka din, to wataqila sai Mubaraka .
Mubaraka ta gama yadda da cewar hasashen ta na Sultan na son ta qarya ne, hasashen farko na ita din bata kai wadda zai so ba shi ne gaskiya, sallama ta musu, zuciyar ta na matuqar quna, ta bar wajen, za ta koma dakin ta, dan a yanzu ba ta so ta bude baki ta yi magana, za ta iya fashewa da kukan da ya tokare mata wuya.
Muryar shi ta ji a bayan ta, cikin sanyi ya kira sunan ta,
"Mubaraka"
Bata gasgata kunnen ta ba, dan haka bata juya ba, a zaton ta gizo Muryar shi ke mata, saboda ta na tsananin so ya kira ta din dan ya furta mata kalmar so.
Tafe take shi kuwa binta yake, tun da ta juya ta fara tafiya ya kasa samun sukuni, kasa jurewa ya yi, ya ce a jira shi, Sultana da Lawwali na tsaye su na kallon shi ya bi ta da gudu.
Maimaita kiran sunan nata ya yi, Ita kuwa a yanzu ta tabbata ba gizo Muryar shi ke mata ba, dan haka tsayawa ta yi cak, bakin ta dauke da murmushi, da hope din son jin kalmar so daga bakin shi,idanun ta taf hawaye,
"Mubaraka, na kasa tafiya ba tare da na bayyana maki saqon da zuciya da gangar jiki na ke ta bani ba, Mubaraka ina son ki, I love u so much, tun randa na fara dora ido na akan ki a gidan mu, na ji wani baqon lamari ya darsu a zuciya ta game da ke, ban fahimci ko me ne shi ba, saboda ni baqo ne a fagen so, tun daga lokacin nan ba ranar da za ta zo ta wuce ban tuna ki ba, amma na bar wa zuciya ta, dawowar ki daga Kano, na ga kin qara girma, kin qara nutsuwa sai na ji abinda nake ji game da ke ya na nunkuwa a rai na, a yanzu na tabbatar da cewa, ke kadai nake so, ke ce macen da na ke jira, shi ya sa na kasa kula kowacce mace da sunan soyayya"
Wata ajiyar Zuciya suka sauke kusan a tare, Mubaraka ta ji dadi kwarai, wanda ba shi da misali,Sultan kuwa ji ya yi kamar an sauke masa wani babban nauyi da ya jima ya na dauke da shi akan shi.
Juyawa ta yi a hankali suka hada ido, cikin jin kunya ta sauke nata idon,sannan ta saki murmushi, shi ma ita yake kallo, cike da so da qauna,amma ya tabbata da ta na kallon shi ne tun dazun da ba zai iya furta kalaman da suka dinga fita daga bakin shi ba kamar ruwa.
A hankali ya ce,
"Baki amsa min ba, kin karbi soyayya ta, ko dai ban miki ba ne?"
Da sauri ta kalle shi, daga sama har qasa, sannan ta ce,
"Wacce mace zaka ce wa ka na so ta ce bata son ka Yah Sultan?"
"Macen da ba ta son na miji mai kama ta, ko mai irin halaye na mana Mubaraka"
"To ni dai kamannin ka, da halayen ka duk sun yi min, ba ka da makusa a iya sanin da na maka"
"Hakan na nufin ki na so na kenan?"
Daga kai ta yi, ta juya cikin sauri ta nufi hanyar dakin ta, kallo ya bi ta da shi, Lawwali ne ya dafa shi, ya ce,
"Tau baban soyayya, tunda ka qare aman zucciyar ka, yi hankuri ka dena kallon qauna ta haka nan, kar ta faɗi"
Dariya Sultan yayi,ya ce,
"To babban Yaya za a bani?"
"Shi kadai ne buri na tun farko ,kuma gashi kun had'a kan ku, ya na daga cikin sharadin da nake da burin mahaifin ku ya cika min, sai ga shi kun hada kan ku da kan ku, Allah shi sanya albarka cikin wanga lamari"
"Ameeen, ina godiya, waccan matar taka ta matsu na san taji me ke hwaruwa, bari mu tai, sai ka iso,"
"Tau ya yi, Allah shi kiyaye hanya"
"Ameen"
Mota Sultan ya shiga cike da farin ciki,ya bayyana wa Sultana me ya faru,ta yi murna kwarai da jin hakan.
Mubaraka kuwa leqawa ta dinga yi ta window ta na kallon Sultan, bayan tafiyar su Lawwali ya kira kowa da kowa, ya fidda makullan gidajen da yake da su a hannun shi, wanda ba shi da su kuma a wajen shi Sultan ya ce zai bashi in sun hadu a cikin gari.
Miqawa wasun su makullan yayi sannan ya sanar da su, ba zai yu kowa ya samu gida shi daya da matar shi ba, wani gidan sai dai mutum biyu, wani gidan ma sai dai mutum uku, daga baya duk wanda Allah ya horewa ya tashi.
Godiya suka dinga yi, tare da addu'a da fatan alkhairi,wasu daga cikin matan har ma da mazan kuka suka dinga yi, sabo kenan, turken wawa.
Suna nan su na jajanta rabuwar su da juna mazajen da suka maida Limaman da suka daura musu aure suka dawo, nan aka sanar da su me ya faru, sun yi godiya sosai, sannan suma sun jimanta rabuwa da junan su.
Lawwali dakin su ya je, ya aika a kira masa Mubaraka.
Ita ta taya shi hade kayan su shi da Sultana, ya bada umarnin kayan gadon a kai masa gidan su, can dakin Mubaraka za a saka.
Su na gyara dakin ne ya bijiro mata da maganar Sultan, kunya ce ta kama ta, shi kuma dariya ya yi, ya ce,
"Ohhh rayuwar duniya kenan, wai Mubaraka 'yar qararramar nan ce yanzu ta girma har ta kai ga saurayi, Allah to shi sanya alkhairi, "
"Kaiii Yah Auwal ni fa ba yanzu za ka yi min auren ba, ni dai ba na so na rabu da ku"
"Tabbb ai kuwa ya zama dole, ko ba aure ai akwai mutuwa ko? Ballantana mace dama ita ba mazauniyar gidan iyayen ta bace, komai daren dad'ewa za ta yi aure, sai wadda Allah ya nufa ba zata taba aure ba a rayuwar ta"
"Haka ne, Allah ya sa mu dace,...Yah Auwal yau za mu bar nan?"
"Ahh ahh, sai gobe ko jibi ma, sai an kai kayan ga gida, an gyara miki d'akin ki, sannan zan maishe ki da hannu na, na damqa musu amanar ki,na gaji da faɗa da kowa ni yanzu, ba na son tashin hankali da kowa, in kin koma ki sanya wa zuciyar ki hankurin zama da su, tunda kin dai san yanda halin su shike,"
"Haka ne Yah Auwal, in shaa Allahu, za ka same ni mai hakuri"
"Allah ya miki albarka Barakana, dama can ke mai hakuri ce,Allah shi qara maki hankuri akan duk abinda zai same ki"
Ameeen, Yah Auwal dina"
Haka sukai ta hirar su, su na tattara kayayyakin Sultana.
*************************
Wata mata ce a tsaye a jikin mota, a gaban wani babban super market ta na waya, kaya aka debo niqi niqi za a saka a bayan mota, ta danna key din hannun ta, ma'aikatan super market din suka zuba kayan, Laminu na can gefe ya na kallon ta, ya jima ya na bin matar tun safe da ya fito daga gida, har yamman nan.
Su na gamawa ta sallame su,ta shige motar ta, ta tada ta, ta hau titi, Laminu ma bin ta ya yi a baya, wata hanya ta dauka, wadda take shiru ba mutane sosai, shi ma binta ya yi, ya sha gaban ta, wani burki ta ci, tare da daga kai, a tsorace, ta kalle shi.
A tare suka fito daga motocin su, Laminu ne ya nufe ta da fuskar tausaya wa, da ban hakuri, ya shammace ta ya shaqa mata wani tsumma a hanci, dauke numfashin ta tayi, ta kama hannun shi ta juyar da shi ta murde shi, ya fadi qasa da guiwowin shi, su na haka wasu motocin jami'an tsaro suka qaraso, su ma tafe suke su na bin su a boye dama.
Sake numfashin ta tayi, ta shaqi iska, duk da haka sai da d'an wanda ta shaqa ya sa ta jiri.
Kamata wani daga jami'an tsaron ya yi, suka sa ta a mota, Laminu kuwa tuni an danna shi a motar 'yan sandan, nan suka dunguma baki dayan su, sai police station, ana zuwa dakin tuhuma aka miqa Laminu.
Binciken da jami'an tsaron suka yi akan mutuwar yaron da suka kama dan ya bada shaida akan wanda ya sa su sace Hajiyan Hansatu ya nuna musu cewa akwai sa hannun Laminu, dan haka suka had'a masa wannan tarkon da jami'ar tsaro mace, suka samu nasarar kama shi.
Laminu ya qi bayyana abokan ta'addancin shi da fari sai da ya ci na jaki, ya ga za su masa lahani a banza, shi ne kuwa ya bayyana sunan Isah, nan da nan kuwa aka kira Yaya Musa aka sanar da shi su na buqatar su a station din, dan jin yanda ta kaya.
Hajiya na ta murna ta shirya ta ce ma Yaya Musa su je,a hanya ta kira Hansatu ta sanar da ita an kira su a police station, an ce a samu wani mahimmin bayani, da ya kamata su sani.
Fatan alkhairi ta musu sannan ta ce in su Ameenatu sun taso daga makaranta za su zo.
Su na isa station din aka sanar da su mummunan labarin da ya sanya Hajiya kuka wiwi, da idanun ta, sai lallashin ta ake ta kasa denawa, ta dauki soyayya mai tsafta ta sanya a zuciyar ta wa Isah ashe mutumin banza ne.
Har wajen Laminu aka je da su, ta kalle shi ta ce,
"Allah wadai da samuwar irin ku cikin al'ummar Annabi Muhammad, Allah ya shirya masu hali irin naku, yanzu ka dube ka, yaro kyakkyawa, wa ze ce za ka aikata wannan mugun abu? Yanzu shi abokin naka kuna waya ne? Dan tun da ya tahi bai kire ni ba, wancan karon kuwa ya na kira na"
Cikin jin kunyar dattijuwar Laminu ya ce,
"Hajiya Isah bai dawo wa yanzu gaskiya, dan kuwa abokin harka ta ta saida koken wani inyamuri ya ce ya sanya koken cikin kayan Isah kamar yanda mun ka tsara, kuma an kama Isah, an kulle shekara goma zai yi a kurkuku,"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'una, kaiii wanga yaro kwai baqin mugu, wato abokin naka ka ci wa amana haka? Shi na can daure ga hukumar da bata san sassauci ba, ka mayar min da d'iya ita da zaura (bazawara) ba su da banbanci, Allah ka isar min, Allah ka isar mana abinda yaran nan su ka yi muna"
Kuka sosai Hajiya take faman yi, a haka suka koma gida, Laminu na nan ana shirye shiryen miqa shi ga kotu, asirin shi ya gama tonuwa.
Tun a hanya Hajiya ta kira Hansatu ta ce ta samu abun hawa ta taho,ta wa driver waya ya kawo su Ameenatu gidan ta, cike da damuwa Hansatu ta ce to, bata so ta tsaya tambayar Hajiyan meke faruwa ta waya.
Rurrufe ko ina ta yi, sannan ta leqa gidan 'Yabbuga ta gaishe ta, ta sanar da ita zata gidan su,a hanyar ta ta zuwa bakin titi, ta wuce ta qofar gidan su Lamishi ta ga ana ta shiga da kayan gado.
Ga wata rumfa nan Dan Talo na ta bugawa a qofar gidan da kan shi.
A bakin gate din gidan su aka ajiye ta, ta shiga, bayan ta gaida mai gadi ta wuce cikin gidan.
A parlour ta tadda Yaya Musa da Yaya Abdullahi (Yayan matar Musa) su na zaune cikin jimami, su na ganin ta kowannen su fuskar shi ta sake danyancewa da tausayin ta.
Hajiya kuwa kuka ta sanya, ta dinga yafitar Hansatu da hannu, wajen ta ta nufa ta zauna daf da ita, ta na so ta yi kuka, dan ta san duk abinda ya sanya Hajiya kuka ba qarami bane.
"Hajiya mi ya faru? Mutuwa an kai? Me ya samu Aunty Azizah?"
Ta na fada ta na kallon Abdullahi, da sauri ya kada mata kai, alamar Ah ah,
"Lafiyar ta qlou, ta na Spain ma yanzu haka,"
"To me ya faru?"
Yaya Musa ne ya daure ya labarta mata komai, Hansatu kuka ta sanya, tare da fadin
"Ba zan taba yafe maka ba Isah, soyayyar ka ba ta amfanar da ni komi ba,ka cutar dani, ba iyaka, na hakura, amma sai da ka haɗa da mahaifiya ta, Isah me ta yi maka? In ni ce baka so sai ka sawwaqe min, me mahaifiya ta ta maka?......Hajiya, Hajiya, kin tuna sanda an ka sace su Ameenatu? Tabbas Isah na da hannu a wannan satar"
"Ahh ahh Hansatu, babu kyau zargi, dan kuwa wannan zargi ne, ba ki tabbatar ba"
"Hajiya ina da yaqinin da sa hannun Isah a wannan lamarin saboda tun sannan suke abota shi da Laminu, Hajiya akwai abubuwan da ban sanar da ke ba saboda bana so hankalin ki ya tashi, na dauki alqawarin tunda ni na bijire muku na zabe shi, komi ze yi min zan shanye ba zan fada wa kowa ba, Hajiya Isah na min......"
Nan dai Hansatu ta dage ta sanar ma da mahaifiyar ta komai da Isah yake mata, Hajiya da kowa da ke wajen ya tausaya mata,sannan sun mata faɗa sosai, musamman akan qin sanar da Hajiya tunda ya tafi wancan karon bai neme ta ba, ai da ta sanar tun a sannan da an dau mataki.
"Tau shi kenan yawuce ,Musa ai ka ga da rabon Allah shi hannunta shi can ga hukumar da sun ka fi mu iya hukunci, yanzu yanda za a yi, kai da Abdullahi,ku shirya ku je can wajen shi, ya sakar min d'iya ta, walle ta gama auren shi, ya qarasa shekarar shi goma ya bid'i wata ya aura, ina dalili.
In ya tsaya muku taurin kai, ku faɗa masa za ku yi qarar shi akan abinda ya yi wa hansatu a can, ku tsoratar da d'an nema, ya sake ta dolen shi, yarinya ta da kyawun ta ba zata rasa mashinshini ba"
Abdullahi ne ya kalli Hansatu da sauri, a zuciyar shi ya na ayyana abubuwa da dama, babban abinda ya sani shi ne, wannan karon ba me auren ta sai shi, ba zai bari ta sake kufce masa ba.
An tsaida magana a cikin sati na sama za su tafi zuwa saudiya, Hansatu kuwa ta ce ba za ta koma unguwar su ba, unguwar gulma, dan ta san yanzu magana ta karade unguwar, za a yi ta nuna ta da baki da ido ne.
Hajiya ma cewa ta yi ta yi zaman ta, ai kuwa ita da yara nan suka samu wajen zama abun su, tun daga ranar Hansatu ta samu abokiyar hira, haka zata zauna ta yi ta bawa Hajiya labarin abubuwan da Isah ke mata, Hajiya kuwa ta ce,
"Ke ko gama zama da baqin mugu,dan neman sallamamme kawai"
****************************
Da isar su asibiti, Hajiya Ikee ta ɗora idon ta akan yaran nata, sai ta fashe da kukan murna, fess ta gan su, wanda ba haka suka zata ba gaba dayan su, wani haske da sheqi ma taga su nayi, musamman Sultana.
Bayan sun gaisa ne, ta ja su har gaban gadon da gwamna yake kai, duk ya fada ya rame,sai gulu gulun idanuwa, bakin shi ya karkace hannu da qafar shi kamar wanda Inna ta taba,asibiti sun tabbatar da cewa ba shi da wani ciwo da ya danganci asibiti a yanzu,sai qarancin jini da yake fama da shi,kullum ana qara masa jini leda biyu zuwa uku, hawan jinin da ya kama shi ma ya sauka, tun da jimawa, sun yi gwaje gwaje sun rasa dalilin da ya sa yake a shanye haka, kuma jinin shi ke yawan qarewa.
Hajiya Ikee na gama basu labarin rashin lafiyar mahaifin nasu Sultan ya ce,
"Hajiya ai da wahala Daddy ya warke,ko da zai warke din ma, domin kuwa mutane irin shi na fama da cututtukan da ake rasa gane kan su ne sakamakon Allah ya isa da mutane ke yi musu, da za a ce za a tara duk mutanen da ya zalunta, su yahe masa, na miki alqawalin sai ya miqe, amma in basu yahe masa ba, zai wahala ya tashi "
"Innalillahi, na shiga uku ni Ikilima, ina zan saka rayuwa ta? Yanzu fissbillahi haka ka ke ganin ba zai tashi ba sai mutane sun yahe masa? To mu yanzu ina mun ka san adadin wanda ya zalunta?"
"Ba lallai bane kuma, ta yu Allah shi bashi lafiya, amma fa zai karbi hukuncin da ya aikata a ranar gobe, in dai be tuba ba"
"Yau na shiga uku na lalace ni ikilima"
Kuka sosai Hajiya Ikee ke yi, shawara Sultana ta kawo, akan su maida Gwamna gida a na maganin Islamic, saboda yanzu kusan watan shi biyu a kwance, komai sai an masa, Hajiya duk ta rame,
"Ai dole gida zamu kai shi, in kunka ji kuddin da asibitin ga ke karba duk kwana guda sai tsoron Allah ya kama mutum, gwamnan da an ka mayar yanzu so guda ya taho da tawagar shi sun ka duba Daddyn ku, da 'yan jarida, akai ta hotuna da video, ko sisi basu bamu ba, amma sun ce sun basuwa kuddin jinya har ya ji sauqi, kuma ga shi asibiti kullum ni ka biyan kuddi"
"Hummm Mum kenan, a bar tone tone, mu samu yanzu a kama muna shi mu tai gida"
Bayan komawar su gida ne suka sha kallon ikon Allah, gwamna banda ihu da shure shure ba abinda yake, abun ya yi matuqar basu mamaki,Sultan ne ya ce su fitar da shi waje, ai kuwa ana fita waje ya dena ihun, sai zare ido kawai yake, da jin tsoron kar a maida shi ciki.
"Sultan mu tai gidan mu na can titin zanna, wataqilan nan ne bashi so"
"Bamu da wani gida da ya yi saura sai wanga, dan kuwa duk na bayar, anjima ma za a taho amsar makullai,nan din dai zamu koma, dole ya yi hankuri,"
"Yau na shiga uku na lalace ni Ikillma, kai wa Allah ku bamu makullin guda, wanda ka bawa wancan su amshi wanga"
"Muka san menene acikin gidan da za mu ba wa wasu shi? Mu din dai mu za
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44 Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51