in na muku laifi ku zo gare ni in kun cika maza, amma qauna ta? Qauna ta, mi tai muku halan, dole na sai kun tabe ta? Ka lalata wa qaunata rayuwa, ka mata tabon da ita kan ta ta na kyamatar kan ta, ta na zargin kan ta, me ya sa? Me ya sa kun ka taba qauna ta? Sai na yi ajalin duk wanda ke da hannu akan tabin qauna ta, wannan alqawarin Lawwali na,"
Wurgi ya yi da No1 gefe daya, ya fadi yaraf kamar tsumma, fuskar shi ta kumbura sintim, kamar wanda akai sukuwa akan ta,
Da rarrafe ya kama qafar Lawwali, ya ce,
"Oga...dan Allah,...dan Allah ...ka kashe ni ...in huta...na gaji....na gaji da shan kashin wahalar ga..dan Allah ka kashe ni..."
Damqo wuyan shi Lawwali ya yi, sannan ya ce,
"In kashe ka? In dinga huce haushi na a ina? Ai daga yau na dena kisan kowa in rayuwa ta ta ɓaci, wajen ka zan taho in huce haushi na"
Wani irin kuka mara hawaye No 1 ya saki, kuka ne na azaba, da tashin hankali, wurgi Lawwali ya yi da shi, ya fita ya bar wajen, wani dan bayan gida ya shiga dake a cikin wajen, ya samu ruwa a jarka ya tsiyaya a buta ya wanke hannun shi da fuskar shi, sannan ya bawa yaran shi umarnin, su ci gaba da gana wa No 1 azaba, amma kar su sake su bari ya mutu.
Amsawa suka yi da
"To Oga"
Sannan suka raka shi har bakin mota, ya tafi.
Sai da ya biya ta wani super market ya sayi kayan kwalama, da abin sha mai sanyi, sannan ya wuce, kafin ya isa sai da ya daidaita nutsuwar shi, sannan ya isa NGO din, ya na zuwa ya tadda ta zaune a saman kujera ta na ta danna laptop din ta, ta yi matuqar bada hankali akan laptop din ya shiga ba ko sallama, har yau ya kasa sabawa da yin sallama in zai shiga waje.
Daga kai ta yi, a dan tsorace ta kalle shi, murmushin da ta gani a saman fuskar shi, ya jawo nata murmushin waje, dan kuwa nan da nan ta bayyanar da haqoran ta a waje, kamar yaron da aka yi wa dariya ya rama.
Hannun shi na maqale a bayan shi ya shiga, sai da ya samu waje ya zauna sanan ya ce,
"Ran ki shi dade in shigo?"
Wata hararar wasa ta mishi sannan ta ce,
"Inna ce ah ah komawa za ka yi? Tunda har ka yi wa kan ka wajen zama"
"Eh sai in koma mana, tunda haka ki ke so"
Dan tura baki ta yi kadan sannan ta ce,
"Dan Allah ka daina hushi, ka daina hushin da zai tsorata ni har na kasa yi maka magana"
Dan bata rai ya yi, na wasu yan dakiku da ba za su wuce uku ba, ya sake fuskar shi,
"Mu bar waccan maganar, yanzu za ki sha wanga?"
Ledar ya dakko ya miqa mata, wani irin haske da annuri ke fita a fuskar ta, ba dan bata taɓa shan chocolates ba, ko sauran kayan kwalamar da ya kai mata ba, ah ah ,nashi na daban ne, kuma ko ba komai dama ta fara jin yunwa.
Lemo mai sanyi ta dauka za ta bude, hannu ya sanya ya karba, hannayen su sauran kadan su gogi na junan su, Lawwali ya yi saurin janye na shi.
Murmushi ya yi, sannan ya bude ya miqa mata, a baki, ta kawar da kan ta,
"Ran ki shi dade, mi na na ki ka tsoro, ni hwa ba dodo ba ne,"
"Ni dai ban ce maka dodo ba, kuma ni ban ji tsoro ba,"
Miqewa ya yi, zai zagaya inda take, ya na wani kashe mata idanu, ta na ganin haka ta fara tari, saboda kwarewa da ta yi, shi kuwa dariya ya fara sosai, ya zira hannayen shi duka biyun a aljihu, ya yi hanyar fita, sai da ya bude qofar sannan ya kalle ta ya ce,
"A haka ki ka son aure na ki na jin tsoro na? Ko kin zata na zuba wani abu ga lemon na? Ni ba dodo bane, Ni masoyin ki na Sultana, ina son ki, ina son ki da dukkan wata tsoka da jini na jiki na, ina son ki da ruhi na, duk randa aka ce maki Lawwali ya daina son ki, to ki tabbata ruhin shi ne babu"
Rufe qofar ya yi,ya na zuba Murmushi ya tafi, shin wannan ma kalaman yaudara ne? Domin jin su yake su na fita daga qasan zuciyar shi, ba qarya a cikin su.
Bayan fitar shi Sultana narkewa ta yi a kujerar, da kyar ta iya daidaita zaman ta ta ci gaba da aikin da ke gaban ta, duk cikin wata daqiqa dake wucewa cike take da farin ciki, da annashuwa a wajen ta, wanda bata yi zato ba, mussmman in ta tuna yanda suka zo wajen, rai a bace.
Lokacin tashi na yi, Lawwali ya dauki Sultana ya wuce da ita wajen cin abincin da ya taba kai Mubaraka, a tare suka ci abincin ya na ta musu hotuna, sultana ba qaramin dadi ta ji ba ranar, ta tabbatar wa da zuciyar ta, ba ita kadai take haukan son Auwal ba, shi ma ya na son ta.
Basu koma gida ba sai yamma liss, Sultana ko duba lokaci bata yi ba, sakamakon ranar ta na cikin yanayi na mata, ba sallah zata yi ba,ta kula da abu daya, wanda ya tsaya mata arai game da Lawwali, haka za a kira sallah a gama, bai je ba,gashi har an yi la'asar, ba ta son bata moment din su, dan haka ta bari kawai, sai watarana za ta masa magana.
Hajiya Ikee na ta jimamin ina Sultana ta tsaya, dan dai ta san duk iskancin Lawwali ba zai taba diyar Gwamna ba, akan abinda ta yi dazu (hummm baki san oga ba lalinyaaa🤭)
Motar su na shiga ta tashi a guje har ta na buge qafa da jikin kujera, ta leqa window, dauke ta ga Sultana da ledojin shopping, shi kuma ya rataya jakar ta ya na yanga, irin na mata, Sultana na ta kyalkyala dariya.
"Kan uban can, wato yaron ga ta nan ya bullo ko? Zai ko ci uwar shi Lamishi, gobe Daddyn su zai dawo, sai na sa an yi gunduwa gunduwa da naman jikin ka, na kaiwa karnu (karnuka)sun canye"
Kallon su ta ci gaba da yi, ta ga ya je daf da Sultana kamar zai hada jiki da ita, ita kuma ta sunkuyar da kan ta qasa, hannu ya sa ya daga kan ta, cikin kasala, ta wara idanun ta akan fuskar shi, tare da cije leben bakin ta na qasa kadan.
"Sulty Babyn Daddy, da gaske za ki iya auren driver din ki, kuma mai tsaron lahiyar ki?"
Cikin bude kyakkyawan bakin ta, tare da sassanyar magana ta ce,
"Auwal alqawari fa na maka zan aure ka, ba zan taba saba wa ba, ni ba na daga mutane masu saba alqawari"
"Kin tabbata kin yi alqawari za ki aure ni? A kowanne hali nake, kuma a kowanne yanayi nake?"
"Auwal in ka sake min fuska natsuwa ta ta dawo jiki na zan baka amsa ta gaskiya"
Murmushi ya yi mai sauti, sannan ya sake mata fuska, Itan ma murmushin take, sannan ta gyara tsayuwar ta ta ce,
"Na maka alqawari zan aure ka, a kowane yanayi ka ke, ba ruwa na da yawa ko qarancin ilimin ka, ba ruwa na da nakasar ka in ma akwai, ba ruwa na da kyau ko rashin kyaun ka, ni dai kai nake so, zuciyar ka ce ta qulla soyayya da tawa, ruhin ka ne ya ga ruhi na soyayyar ta qullu, gangar jiki na ta yarda taka ta zama abokiyar rayuwar ta, Auwal zan aure ka, this is my promise to you"
Lawwali jin shi yake kamar ba ya duniyar,kalaman ta sun shige shi sosai .
"Idan Daddy ya dawo ki na ganin za ki iya tuntubar shi, maganar aure na, dan naturo manya na?"
"Ya ka ke magana kamar ka shiga zuciya ta ka yi leqen asiri?"
Hajiya Ikee fa ta kasa jure wannan iskancin, qoqarin barin wajen take dan ta isa ta ci wa Lawwali mutunci ta ga abinda bata taɓa tsammani ba, Lawwali ne ya duqa ya sumbaci kuncin Sultana, ita kan ta sai da ta saki ledojin hannun ta suka zube qasa, shi kuwa ko a jikin shi,ido ya kalli sama ya kashewa Hajiya Ikee dake tsaye a jikin window ya ajewa Sultana jakar ta ya tafi.
Sai da ya bar gidan gaba daya, ta dawo hayyacin ta, wajen da ya sumbata ta shafa, ta saki murmushi, can kuma ta ɗan bata rai ta ce,
"Auwal ba kyau fa,"
Kamar ya na ganin ta, wani sassanyar murmushi ne ya kubuce mata a karo na ba adadi, ita ta na taba shi, shi ya na guduwa, shi ne yanzu zai nuna mata ya iya taba jikin mutum yi ne kawai ba ya yi,daukan tarkacen ta tayi, ta shige gida cike da nishadi, Allah Allah take su hadu da Sultan ta bashi labari, ta na sanya qafar ta, a cikin gidan, ta ji an ce,
"Kee Sulatana, zo nan!"
Cikin tsananin firgita da tsoro ta taka zuwa babban parlour'n na su...........
*A yi hakuri da wanga sai zuwa anjima ko gobe inshaa Allahu zan ci gaba, thank u mutanen Ogaaa😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 38:
Mubaraka na matuqar jin dadin zama da su Taheer da iyalan shi,domin duk wani abu da take so, ko suka kula ta na da buqata da wuri za su yi mata shi.
Da kyar Fateema ta yarda ta ke taya ta girki,shi ma dan Mubaraka ta dage ne, kuma cikin ikon Allah, sai ya zamana su na samun qaruwa da juna, abinda dayan su bai iya ba, sai daya ya koya ma daya.
Yaran su kuwa kamar qannen ta haka ta dauke su, ita ke musu wanka, ta shirya su, su je islamiyya su dawo tare.
Ranar Monday mai zuwa za ta fara zuwa Makarantar boko, a tunanin Lawwali makarantar Army Day ne kawai za ta samar wa Mubaraka tsaro, dan haka can ya saka ta, ya sa Taheer ya nemar mata driver da zai dinga kai ta, saboda shi bashi da lokacin kai ta, ya fara zuwa kasuwa, ya na saida shaddodi.
Ranar farko da Mubaraka ta fara zuwa, ta samu masu son qawance da ita kala kala, musamman dan ganin a irin motar da aka kawo ta, amma dake tin kafin Lawwali ya bata gargadin yin qawaye barkatai, ita ba me son tarkacen qawaye bace.
Dan haka gaisuwa ke hada ta da kowa, ta raba ta da kowa lafiya.
Tun ranar da aka kai ta makaranta wasu sojoji wanda suka addabi d'alibai mata, suke kula da zuwan ta, da tafiyar ta.
Yanayin kamun kan ta, ya ja ra'ayin su, su na son sai sun lalata mata rayuwa, (wannan duniya yanda ta lalace Allah ne kawai zai gyara mana ita, in ka yi shigar banza, maza na kallon ka, su na dakon ka, in ka yi ta kirkin ma, wasu so suke su yaga maka rigar mutunci)
Lokuta da dama ta kan gan su, in ta je shago siyan wani abun, shagon na dan nesa da asalin cikin makaranta.
Watarana ta zo makaranta sai ta kula an sace pen din ta, gashi an basu assignment ta na son ta yi, in ta isa gida, dan haka tsayawa ta yi a shagon dan siyan pen.
Ta na tsaye ta na jiran a sallami wasu,sannan a bata abinda take buqata, kurtun sojan nan ne dai da ya sa mata ido shi da abokan shi ya zo shiga wajen, duk warin hayaqin sigari da wiwi ke tashi a jikin shi, ga hanya can da za ta ishe shi ya shiga shagon amma sai da ya rabi jikin Mubaraka har ya na gogar qirjin ta.
Tura shi baya tayi ta ce,
" Allah ya saka min azzalumi "
Kurawa sunan dake jikin rigar shi ido ta yi, ta kasa gane sunan nashi Saboda sunan arna ne da shi, kuma da yare aka rubuta,duk qoqarin ta na ta karanta sunan ta kasa.
Zuwa ya yi ya daddafe ko ina na jikin qofar, ya sanya ta a tsakiya kenan, da kyar take shaqar numfashi, hannun shi ya sa ya shaqe mata wuya, duk wajen ana tsoron shi, dan ya saba zuwa, in ya ga mata masu kyau, ya yi ta bibiyar su.
"Hey, what are you doing, pls let me go, stop touching me, I will tell my brother if I go home"
(Kai me ka ke yi ? Dan Allah barni na tafi, bari tab'a ni,se na fad'a wa yayana idan na ne gida )
Kuka ta fashe da shi, duk jikin ta na rawa ko ta ina, da kyar mutanen wajen suka bashi hakuri ya rabu da ita ta fita daga wajan a guje, motar ta ta nufa ta ga drivern da Taheer ya daukar mata baya ciki, ashe abokan sojan nan ne suka kira shi, suka tsare shi, sun tabbatar dole zata je inda motar take, daga nan za su kamata su tafi da ita, sai sun gama abinda suka so da ita su dawo da ita.
Haka kawai jikin ta ya bata ta gudu, tunda bata hango driver a motar ba, dan acaba ta gani, irin masu fitar da mutum wajen gate dinnan, ta haye, ta ce ya Kaita gida ko nawa ne zata bashi.
Ai kuwa ya na jin haka ya ce ta hau, ta haye ta rufe fuskar ta dan kar a gane ta, gudu suke zubawa, har suka kai gate, sun fita kenan, ta hango qaramar motar da sojojin uku suke ciki, dira qasa tayi daga machine din, ta buya a gefen wasu ciyayi da ke bakin kwata, duk abinda ta ke su na ganin ta, gani ta yi sun tunkaro ta, bayan sun rufe motar su, cikin Barack ta shiga da mugun gudu, duk ta daddauje jikin ta, ya na mata zafi,sojojin da ke bakin gate ta dinga roqa kar su bari su tafi da ita, ta na ta rusar kuka, bata fatan sake riskar abinda ya faru da ita a baya.
Su na ganin haka suka koma, domin ana ta complain akan su, kar akai rahoton su.
Cikin sa'a kuwa ta tarar da wani babban soja na qoqarin shiga motar shi, gefen shi wani karamin soja ke bude masa mota, wajen shi Mubaraka ta kwasa a guje, ta masa bayanin komai, akai akai ta fadi sunan shi ta kasa, sai ta rubuta a qasa, Sojan na gani, ya gane wa take nufi, duk da bata rubuta daidai ba.
A nan take ya bada umarni a je a nemo driver din ta, a cikin daji aka same shi an daure shi, ya sha duka ,har gida sojan ya raka ta shima a tashi motar.
Godiya ta dinga mishi, ya ce aikin shi ne, ba sai ta yi godiya ba, bayan ya koma Barack ya sa aka nemo wadannan sojojin, aka musu hukunci daidai da abinda suka aikata, su kuwa cikin zuciyar su sun qudirta duk inda suka hadu da Mubaraka sai sun dau fansar abinda aka musu.
Mubaraka kuwa Taheer na dawowa daga sabon wajen sana'ar da Oga Lawwali ya bude masa a kasuwa, wato shagon saida shaddodi na mata da maza, ta sanar da shi komai, ya kuma yi mata alqawarin daga ranar ta bar zuwa makarantar barikin sojoji, tunda ba diyar soja take ba.
Da kan shi ya sauya mata makarantar private da ba ta da nisa da su, a kai ta a maida ta hankali kwance.
Ya gargade ta da kar ta sake Lawwali ya ji wannan maganar, in ya ce me ya sa aka sauya mata makaranta su ce ba a karatu a can shi ya sa.
Dariya ta yi, ta daga kai, ko dama da ta ce za ta gayawa yayan ta shi take nufi ba Lawwali ba.
************************
Tun saukar shi a jirgi ya ke gwada layin No 1 bai dauka ba, Gashi dai ta na ta ringing amma ba a daga ba, lambar No 4 kuwa ma sam ba ta tafiya, damuwa ce qarara a fuskar shi, tsoron shi kar dai yaran sun hade masa kai da Ogan su?
Da sanyin safiyar masu tsaron lafiyar shi ne tsaye a bakin motocin da suka zo da su dan daukan shi, bude masa motar da zai shiga aka yi ya shige ya zauna, sake gwada No yake amma gashi ta na ringing ba a dauka.
Cikin zuciyar shi ya ke tunani,
'Na manta yanzu safiya ne, wataqila ko tashi ba su yi ba'
Maida wayar shi ya yi, ya ajiye, har suka isa gida bai dena jin yanayin da yake ji ba, na rashin dadi a zuciyar shi.
Hajiya Ikee da ta san da dawowar mijin ta, ta sha gayu, har ta gaji, ta bawa masu aiki umarnin hada abin karin kumallo masu rai da motsi, na musamman.
Kwararru kuma hadaddun masu girkin tuni suka fara bade gidan da qamshi, Sultana na zaune a saman sallaya, bayan idar da Sallah da azkar, ta fara karan ta qur'ani, ta na jin qamshi na tashi kala kala, ta tabbatar Daddyn su na tafe, murmushi ta yi, tare da qara qaimi wajen karatun ta, dan ta na so ta haɗa da addu'ar samun nasara daga wajen Allah.
Da misalin shida da hamsin da bakwai 6:57am Gwamna Halliru ne a zaune bakin katafaren gadon su, ya zubawa Hajiya Ikee ido, ta na ta rattaba masa bayanai, akan abubuwan da ke ta faruwa a bayan shi,(rashin iya tarbar miji, daga dawowar shi, ba a bashi ko da abin da zai sha ba, balle a bari ya huce gajiya an fara bashi munanan labarai)
Gwamna Halliru shiru ya yi ya na sauraron ta,
".....shi ya sa na fada maka, ka kori Yaron nan, ka qi, gani ka ke in ba shi Sultana ba zata iya takawa ko da gate bane ba tare da an halaka ta ba"
"Kwarai da gaske, baki da masaniyar waye shi, har yanzu cikin jahilcin sanin waye shi kk, shi ya sa ki ke wannan surutan,"
Miqewa ya yi ya shiga wanka, ko da ya fito be ga Hajiya Ikee ba, bai wani damu ba, dama ita ba mace bace mai taya mijin ta shirya wa, sai da ya gama shiri tsaf, ya ga wayar shi na ringing, dauka ya yi, ya na tsaki,
"Ko mi zata hwadi, da ba zata iya dawowa daki ba"
Amsawa ya yi, ya
Showing 78001 words to 81000 words out of 150481 words
Wurgi ya yi da No1 gefe daya, ya fadi yaraf kamar tsumma, fuskar shi ta kumbura sintim, kamar wanda akai sukuwa akan ta,
Da rarrafe ya kama qafar Lawwali, ya ce,
"Oga...dan Allah,...dan Allah ...ka kashe ni ...in huta...na gaji....na gaji da shan kashin wahalar ga..dan Allah ka kashe ni..."
Damqo wuyan shi Lawwali ya yi, sannan ya ce,
"In kashe ka? In dinga huce haushi na a ina? Ai daga yau na dena kisan kowa in rayuwa ta ta ɓaci, wajen ka zan taho in huce haushi na"
Wani irin kuka mara hawaye No 1 ya saki, kuka ne na azaba, da tashin hankali, wurgi Lawwali ya yi da shi, ya fita ya bar wajen, wani dan bayan gida ya shiga dake a cikin wajen, ya samu ruwa a jarka ya tsiyaya a buta ya wanke hannun shi da fuskar shi, sannan ya bawa yaran shi umarnin, su ci gaba da gana wa No 1 azaba, amma kar su sake su bari ya mutu.
Amsawa suka yi da
"To Oga"
Sannan suka raka shi har bakin mota, ya tafi.
Sai da ya biya ta wani super market ya sayi kayan kwalama, da abin sha mai sanyi, sannan ya wuce, kafin ya isa sai da ya daidaita nutsuwar shi, sannan ya isa NGO din, ya na zuwa ya tadda ta zaune a saman kujera ta na ta danna laptop din ta, ta yi matuqar bada hankali akan laptop din ya shiga ba ko sallama, har yau ya kasa sabawa da yin sallama in zai shiga waje.
Daga kai ta yi, a dan tsorace ta kalle shi, murmushin da ta gani a saman fuskar shi, ya jawo nata murmushin waje, dan kuwa nan da nan ta bayyanar da haqoran ta a waje, kamar yaron da aka yi wa dariya ya rama.
Hannun shi na maqale a bayan shi ya shiga, sai da ya samu waje ya zauna sanan ya ce,
"Ran ki shi dade in shigo?"
Wata hararar wasa ta mishi sannan ta ce,
"Inna ce ah ah komawa za ka yi? Tunda har ka yi wa kan ka wajen zama"
"Eh sai in koma mana, tunda haka ki ke so"
Dan tura baki ta yi kadan sannan ta ce,
"Dan Allah ka daina hushi, ka daina hushin da zai tsorata ni har na kasa yi maka magana"
Dan bata rai ya yi, na wasu yan dakiku da ba za su wuce uku ba, ya sake fuskar shi,
"Mu bar waccan maganar, yanzu za ki sha wanga?"
Ledar ya dakko ya miqa mata, wani irin haske da annuri ke fita a fuskar ta, ba dan bata taɓa shan chocolates ba, ko sauran kayan kwalamar da ya kai mata ba, ah ah ,nashi na daban ne, kuma ko ba komai dama ta fara jin yunwa.
Lemo mai sanyi ta dauka za ta bude, hannu ya sanya ya karba, hannayen su sauran kadan su gogi na junan su, Lawwali ya yi saurin janye na shi.
Murmushi ya yi, sannan ya bude ya miqa mata, a baki, ta kawar da kan ta,
"Ran ki shi dade, mi na na ki ka tsoro, ni hwa ba dodo ba ne,"
"Ni dai ban ce maka dodo ba, kuma ni ban ji tsoro ba,"
Miqewa ya yi, zai zagaya inda take, ya na wani kashe mata idanu, ta na ganin haka ta fara tari, saboda kwarewa da ta yi, shi kuwa dariya ya fara sosai, ya zira hannayen shi duka biyun a aljihu, ya yi hanyar fita, sai da ya bude qofar sannan ya kalle ta ya ce,
"A haka ki ka son aure na ki na jin tsoro na? Ko kin zata na zuba wani abu ga lemon na? Ni ba dodo bane, Ni masoyin ki na Sultana, ina son ki, ina son ki da dukkan wata tsoka da jini na jiki na, ina son ki da ruhi na, duk randa aka ce maki Lawwali ya daina son ki, to ki tabbata ruhin shi ne babu"
Rufe qofar ya yi,ya na zuba Murmushi ya tafi, shin wannan ma kalaman yaudara ne? Domin jin su yake su na fita daga qasan zuciyar shi, ba qarya a cikin su.
Bayan fitar shi Sultana narkewa ta yi a kujerar, da kyar ta iya daidaita zaman ta ta ci gaba da aikin da ke gaban ta, duk cikin wata daqiqa dake wucewa cike take da farin ciki, da annashuwa a wajen ta, wanda bata yi zato ba, mussmman in ta tuna yanda suka zo wajen, rai a bace.
Lokacin tashi na yi, Lawwali ya dauki Sultana ya wuce da ita wajen cin abincin da ya taba kai Mubaraka, a tare suka ci abincin ya na ta musu hotuna, sultana ba qaramin dadi ta ji ba ranar, ta tabbatar wa da zuciyar ta, ba ita kadai take haukan son Auwal ba, shi ma ya na son ta.
Basu koma gida ba sai yamma liss, Sultana ko duba lokaci bata yi ba, sakamakon ranar ta na cikin yanayi na mata, ba sallah zata yi ba,ta kula da abu daya, wanda ya tsaya mata arai game da Lawwali, haka za a kira sallah a gama, bai je ba,gashi har an yi la'asar, ba ta son bata moment din su, dan haka ta bari kawai, sai watarana za ta masa magana.
Hajiya Ikee na ta jimamin ina Sultana ta tsaya, dan dai ta san duk iskancin Lawwali ba zai taba diyar Gwamna ba, akan abinda ta yi dazu (hummm baki san oga ba lalinyaaa🤭)
Motar su na shiga ta tashi a guje har ta na buge qafa da jikin kujera, ta leqa window, dauke ta ga Sultana da ledojin shopping, shi kuma ya rataya jakar ta ya na yanga, irin na mata, Sultana na ta kyalkyala dariya.
"Kan uban can, wato yaron ga ta nan ya bullo ko? Zai ko ci uwar shi Lamishi, gobe Daddyn su zai dawo, sai na sa an yi gunduwa gunduwa da naman jikin ka, na kaiwa karnu (karnuka)sun canye"
Kallon su ta ci gaba da yi, ta ga ya je daf da Sultana kamar zai hada jiki da ita, ita kuma ta sunkuyar da kan ta qasa, hannu ya sa ya daga kan ta, cikin kasala, ta wara idanun ta akan fuskar shi, tare da cije leben bakin ta na qasa kadan.
"Sulty Babyn Daddy, da gaske za ki iya auren driver din ki, kuma mai tsaron lahiyar ki?"
Cikin bude kyakkyawan bakin ta, tare da sassanyar magana ta ce,
"Auwal alqawari fa na maka zan aure ka, ba zan taba saba wa ba, ni ba na daga mutane masu saba alqawari"
"Kin tabbata kin yi alqawari za ki aure ni? A kowanne hali nake, kuma a kowanne yanayi nake?"
"Auwal in ka sake min fuska natsuwa ta ta dawo jiki na zan baka amsa ta gaskiya"
Murmushi ya yi mai sauti, sannan ya sake mata fuska, Itan ma murmushin take, sannan ta gyara tsayuwar ta ta ce,
"Na maka alqawari zan aure ka, a kowane yanayi ka ke, ba ruwa na da yawa ko qarancin ilimin ka, ba ruwa na da nakasar ka in ma akwai, ba ruwa na da kyau ko rashin kyaun ka, ni dai kai nake so, zuciyar ka ce ta qulla soyayya da tawa, ruhin ka ne ya ga ruhi na soyayyar ta qullu, gangar jiki na ta yarda taka ta zama abokiyar rayuwar ta, Auwal zan aure ka, this is my promise to you"
Lawwali jin shi yake kamar ba ya duniyar,kalaman ta sun shige shi sosai .
"Idan Daddy ya dawo ki na ganin za ki iya tuntubar shi, maganar aure na, dan naturo manya na?"
"Ya ka ke magana kamar ka shiga zuciya ta ka yi leqen asiri?"
Hajiya Ikee fa ta kasa jure wannan iskancin, qoqarin barin wajen take dan ta isa ta ci wa Lawwali mutunci ta ga abinda bata taɓa tsammani ba, Lawwali ne ya duqa ya sumbaci kuncin Sultana, ita kan ta sai da ta saki ledojin hannun ta suka zube qasa, shi kuwa ko a jikin shi,ido ya kalli sama ya kashewa Hajiya Ikee dake tsaye a jikin window ya ajewa Sultana jakar ta ya tafi.
Sai da ya bar gidan gaba daya, ta dawo hayyacin ta, wajen da ya sumbata ta shafa, ta saki murmushi, can kuma ta ɗan bata rai ta ce,
"Auwal ba kyau fa,"
Kamar ya na ganin ta, wani sassanyar murmushi ne ya kubuce mata a karo na ba adadi, ita ta na taba shi, shi ya na guduwa, shi ne yanzu zai nuna mata ya iya taba jikin mutum yi ne kawai ba ya yi,daukan tarkacen ta tayi, ta shige gida cike da nishadi, Allah Allah take su hadu da Sultan ta bashi labari, ta na sanya qafar ta, a cikin gidan, ta ji an ce,
"Kee Sulatana, zo nan!"
Cikin tsananin firgita da tsoro ta taka zuwa babban parlour'n na su...........
*A yi hakuri da wanga sai zuwa anjima ko gobe inshaa Allahu zan ci gaba, thank u mutanen Ogaaa😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 38:
Mubaraka na matuqar jin dadin zama da su Taheer da iyalan shi,domin duk wani abu da take so, ko suka kula ta na da buqata da wuri za su yi mata shi.
Da kyar Fateema ta yarda ta ke taya ta girki,shi ma dan Mubaraka ta dage ne, kuma cikin ikon Allah, sai ya zamana su na samun qaruwa da juna, abinda dayan su bai iya ba, sai daya ya koya ma daya.
Yaran su kuwa kamar qannen ta haka ta dauke su, ita ke musu wanka, ta shirya su, su je islamiyya su dawo tare.
Ranar Monday mai zuwa za ta fara zuwa Makarantar boko, a tunanin Lawwali makarantar Army Day ne kawai za ta samar wa Mubaraka tsaro, dan haka can ya saka ta, ya sa Taheer ya nemar mata driver da zai dinga kai ta, saboda shi bashi da lokacin kai ta, ya fara zuwa kasuwa, ya na saida shaddodi.
Ranar farko da Mubaraka ta fara zuwa, ta samu masu son qawance da ita kala kala, musamman dan ganin a irin motar da aka kawo ta, amma dake tin kafin Lawwali ya bata gargadin yin qawaye barkatai, ita ba me son tarkacen qawaye bace.
Dan haka gaisuwa ke hada ta da kowa, ta raba ta da kowa lafiya.
Tun ranar da aka kai ta makaranta wasu sojoji wanda suka addabi d'alibai mata, suke kula da zuwan ta, da tafiyar ta.
Yanayin kamun kan ta, ya ja ra'ayin su, su na son sai sun lalata mata rayuwa, (wannan duniya yanda ta lalace Allah ne kawai zai gyara mana ita, in ka yi shigar banza, maza na kallon ka, su na dakon ka, in ka yi ta kirkin ma, wasu so suke su yaga maka rigar mutunci)
Lokuta da dama ta kan gan su, in ta je shago siyan wani abun, shagon na dan nesa da asalin cikin makaranta.
Watarana ta zo makaranta sai ta kula an sace pen din ta, gashi an basu assignment ta na son ta yi, in ta isa gida, dan haka tsayawa ta yi a shagon dan siyan pen.
Ta na tsaye ta na jiran a sallami wasu,sannan a bata abinda take buqata, kurtun sojan nan ne dai da ya sa mata ido shi da abokan shi ya zo shiga wajen, duk warin hayaqin sigari da wiwi ke tashi a jikin shi, ga hanya can da za ta ishe shi ya shiga shagon amma sai da ya rabi jikin Mubaraka har ya na gogar qirjin ta.
Tura shi baya tayi ta ce,
" Allah ya saka min azzalumi "
Kurawa sunan dake jikin rigar shi ido ta yi, ta kasa gane sunan nashi Saboda sunan arna ne da shi, kuma da yare aka rubuta,duk qoqarin ta na ta karanta sunan ta kasa.
Zuwa ya yi ya daddafe ko ina na jikin qofar, ya sanya ta a tsakiya kenan, da kyar take shaqar numfashi, hannun shi ya sa ya shaqe mata wuya, duk wajen ana tsoron shi, dan ya saba zuwa, in ya ga mata masu kyau, ya yi ta bibiyar su.
"Hey, what are you doing, pls let me go, stop touching me, I will tell my brother if I go home"
(Kai me ka ke yi ? Dan Allah barni na tafi, bari tab'a ni,se na fad'a wa yayana idan na ne gida )
Kuka ta fashe da shi, duk jikin ta na rawa ko ta ina, da kyar mutanen wajen suka bashi hakuri ya rabu da ita ta fita daga wajan a guje, motar ta ta nufa ta ga drivern da Taheer ya daukar mata baya ciki, ashe abokan sojan nan ne suka kira shi, suka tsare shi, sun tabbatar dole zata je inda motar take, daga nan za su kamata su tafi da ita, sai sun gama abinda suka so da ita su dawo da ita.
Haka kawai jikin ta ya bata ta gudu, tunda bata hango driver a motar ba, dan acaba ta gani, irin masu fitar da mutum wajen gate dinnan, ta haye, ta ce ya Kaita gida ko nawa ne zata bashi.
Ai kuwa ya na jin haka ya ce ta hau, ta haye ta rufe fuskar ta dan kar a gane ta, gudu suke zubawa, har suka kai gate, sun fita kenan, ta hango qaramar motar da sojojin uku suke ciki, dira qasa tayi daga machine din, ta buya a gefen wasu ciyayi da ke bakin kwata, duk abinda ta ke su na ganin ta, gani ta yi sun tunkaro ta, bayan sun rufe motar su, cikin Barack ta shiga da mugun gudu, duk ta daddauje jikin ta, ya na mata zafi,sojojin da ke bakin gate ta dinga roqa kar su bari su tafi da ita, ta na ta rusar kuka, bata fatan sake riskar abinda ya faru da ita a baya.
Su na ganin haka suka koma, domin ana ta complain akan su, kar akai rahoton su.
Cikin sa'a kuwa ta tarar da wani babban soja na qoqarin shiga motar shi, gefen shi wani karamin soja ke bude masa mota, wajen shi Mubaraka ta kwasa a guje, ta masa bayanin komai, akai akai ta fadi sunan shi ta kasa, sai ta rubuta a qasa, Sojan na gani, ya gane wa take nufi, duk da bata rubuta daidai ba.
A nan take ya bada umarni a je a nemo driver din ta, a cikin daji aka same shi an daure shi, ya sha duka ,har gida sojan ya raka ta shima a tashi motar.
Godiya ta dinga mishi, ya ce aikin shi ne, ba sai ta yi godiya ba, bayan ya koma Barack ya sa aka nemo wadannan sojojin, aka musu hukunci daidai da abinda suka aikata, su kuwa cikin zuciyar su sun qudirta duk inda suka hadu da Mubaraka sai sun dau fansar abinda aka musu.
Mubaraka kuwa Taheer na dawowa daga sabon wajen sana'ar da Oga Lawwali ya bude masa a kasuwa, wato shagon saida shaddodi na mata da maza, ta sanar da shi komai, ya kuma yi mata alqawarin daga ranar ta bar zuwa makarantar barikin sojoji, tunda ba diyar soja take ba.
Da kan shi ya sauya mata makarantar private da ba ta da nisa da su, a kai ta a maida ta hankali kwance.
Ya gargade ta da kar ta sake Lawwali ya ji wannan maganar, in ya ce me ya sa aka sauya mata makaranta su ce ba a karatu a can shi ya sa.
Dariya ta yi, ta daga kai, ko dama da ta ce za ta gayawa yayan ta shi take nufi ba Lawwali ba.
************************
Tun saukar shi a jirgi ya ke gwada layin No 1 bai dauka ba, Gashi dai ta na ta ringing amma ba a daga ba, lambar No 4 kuwa ma sam ba ta tafiya, damuwa ce qarara a fuskar shi, tsoron shi kar dai yaran sun hade masa kai da Ogan su?
Da sanyin safiyar masu tsaron lafiyar shi ne tsaye a bakin motocin da suka zo da su dan daukan shi, bude masa motar da zai shiga aka yi ya shige ya zauna, sake gwada No yake amma gashi ta na ringing ba a dauka.
Cikin zuciyar shi ya ke tunani,
'Na manta yanzu safiya ne, wataqila ko tashi ba su yi ba'
Maida wayar shi ya yi, ya ajiye, har suka isa gida bai dena jin yanayin da yake ji ba, na rashin dadi a zuciyar shi.
Hajiya Ikee da ta san da dawowar mijin ta, ta sha gayu, har ta gaji, ta bawa masu aiki umarnin hada abin karin kumallo masu rai da motsi, na musamman.
Kwararru kuma hadaddun masu girkin tuni suka fara bade gidan da qamshi, Sultana na zaune a saman sallaya, bayan idar da Sallah da azkar, ta fara karan ta qur'ani, ta na jin qamshi na tashi kala kala, ta tabbatar Daddyn su na tafe, murmushi ta yi, tare da qara qaimi wajen karatun ta, dan ta na so ta haɗa da addu'ar samun nasara daga wajen Allah.
Da misalin shida da hamsin da bakwai 6:57am Gwamna Halliru ne a zaune bakin katafaren gadon su, ya zubawa Hajiya Ikee ido, ta na ta rattaba masa bayanai, akan abubuwan da ke ta faruwa a bayan shi,(rashin iya tarbar miji, daga dawowar shi, ba a bashi ko da abin da zai sha ba, balle a bari ya huce gajiya an fara bashi munanan labarai)
Gwamna Halliru shiru ya yi ya na sauraron ta,
".....shi ya sa na fada maka, ka kori Yaron nan, ka qi, gani ka ke in ba shi Sultana ba zata iya takawa ko da gate bane ba tare da an halaka ta ba"
"Kwarai da gaske, baki da masaniyar waye shi, har yanzu cikin jahilcin sanin waye shi kk, shi ya sa ki ke wannan surutan,"
Miqewa ya yi ya shiga wanka, ko da ya fito be ga Hajiya Ikee ba, bai wani damu ba, dama ita ba mace bace mai taya mijin ta shirya wa, sai da ya gama shiri tsaf, ya ga wayar shi na ringing, dauka ya yi, ya na tsaki,
"Ko mi zata hwadi, da ba zata iya dawowa daki ba"
Amsawa ya yi, ya
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27 Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51