Hansatu ke dai sai dai ni ce Allah shi yi miki sauqi, kin bi kin koyawa yara baqar tabi'a, tunda sun ka shigo sun ka kawo abinci na yi godiya sun ka amsa, nace kwana (bacci) ki ke ne da Ameenatu tace ke ce su zauna sai kin taho, Diyan ga sun ka debo ijiya(ido) sun ka zuba min(Aminatu ta ce kin ce su zauna sai kin taho,suka dauki ido suka saka min) qalallahu qala ta'ala ba wanda yace min cikin su, har da wanga d'an tatsitsin yaro, maganar duniya sun manna min hauka, ba wanda yace min komi, sun yi didd'didd'ifff"
Dariya Hansatu ta sa, dan ta san wannan aikin Ameenatu ne, ita ce zata hana su magana kan su shiga, Bilkisu ta sha fad'a mata, in sun je waje Ameenatu na hana su magana, komai aka tambaye su, su ce su ma basu sani ba, ko su yi shiru su zubawa mutum ido kawai.
"Ki yi hankuri, na gode da ki ka aje min su, bari mu tafi gida, mangariba ta yi"
Tsaki 'Yabbuga ta yi, ta miqe daga gaban Ahmad, da tai Wa zaman neman gafara, ba kalar lallaba yaron da bata yi ba, dan ta ji labarai a wajen shi ya qi bude baki sam.
Ita kuma kamar mayya, a nan gaban su ta cinye abincin da suka kai mata, ta na yi ta na tambayar su gidan su, su kuma su na ta kallon ta, sun qi amsa ta.
Sai da Hansatu za su fita ta juya ta ce ma 'Yabbuga,
"Yau fa Baban su Ameenah ya dawo,"
Wata gud'a da shewa 'Yabbuga ta buga, ta buga cinya, kafin ta yi magana Hansatu ta tisa qeyar yaran, ta ce su yi gida, ita kuma ta tsaya, dan 'Yabbuga na iya bin ta, har gida, ta fadi abinda zai sa wa yaran ta tunanin me ake nufi da kazan nan da aka fada.
"Hahaiiiiii cassss! ko da na ji, yanzu na ji batu,dan ko na san ruwa da iska ba ki barin d'iyan nan zuwa ko ina, ku na nan manne da juna, ashe ashe uban su ne yaddawo ana can ana biyan bashi , shi yasa aka koro su, tauuuu, to ko za ki kawo su su kwana nan? Kar su yi mummunan gamo"
Cikin takaici Hansatu ta kalle ta tace,
"Bayan na haifi Ameenatu, Bilkisu ta biyo baya, duk su na nan sun fara wayo nayyi cikin Ahmad, kuma har yau idon su ko kunnen su bai gane musu komi ba in shaa Allahu, ke ga kuwa ba abinda za su gani a gaba ma, in shaa Allahu, na gode sai da safe"
Hansatu na fadin haka ta tafi, 'Yabbuga kuwa ran ta ya ɓaci, nan da nan ta hau sakin maganganu marasa dad'i.
"Keeeee wagga ban ce ki fada min baqa ba, yaushe na an ka jone da mijin har da za ki yi min kitihin yohi? Mijin da mun san komi, ba qaunar ki shi kai ba? Wanne irin kashin wahala ne baki sha hannun shi ba? Ba ci ba sha, ba sutura, nan nan gidan kin shigo shi kin yi maula ba a ko qirgawa, yo Allah na tuba wane dare ne jemage bai gani ba, kai ku ji min yarinya da kitihi,"
Hansatu na cikin gidan ta tana jin komai, kasa jurewa ta yi, ta fita, ta koma gidan 'Yabbuga dake ta sababi, ta ke yi mata gori kala kala.
'Yabbuga bata ji shigowar Hansatu ba sai kalaman ta,
"Na gode wa Allah, kuma na gode miki da Allah ya azurta mu a lokacin da muke cikin matsin rayuwa ta hanyar ki, na gode miki da kika taimaka mana a lokacin da muke da tsananin buqatar taimako, banda bakin yi miki godiya sai dai na roqi Allah da ya sauya maki halayen ki, daga munana zuwa kyawawa, shi saka maki da alkhairi, duk abinda kin ka fadi gaskiya ne, amma ki sani, in a baya Allah ya baki lada, to fa a yanzu zunubi ki ka dauka, domin kin zobe ladan da yabbaki ta hanyar yi min gori, kin san kuwa hanin da aka yi akan gori? kin tozarta ni akan abinda ki ka min a baya, kin yi min gori, ni kuma ba zan rama ba, amma kar ki manta abu guda, shi zama in ya hada ka da koma wane ne, abu guda dole sai ya faru, ko ku zauna lahiya kowa shi amfana da kowa, ko ku cutar da junan ku, ki dinga tuna baya kahin ki yi min gori, sai da safe"
Jikin 'Yabbuga bai taba sanyi ba irin na yau, ashe Hansatu na da baki? A fakaice wadannan maganganun da ta wa 'Yabbuga dukkan su suna da fassarar su da ma'anar su kala kala, da 'Yabbuga na tuna baya da bata yi wa Hansatu gori ba, domin sai da ta fara morar Hansatu kafin Hansatu ta more ta, sai dai duk abinda Hansatu ta yi wa 'Yabbuga Hansatun bata taɓa sanar da kowa ba, itama 'Yabbuga bata taɓa fadawa kowa ta mori Hansatu ba sanda ta na amarya, amma ko gishiri hansatu ta karba wajen ta, sai ta qara tace har da Maggi da mai ta bata.
Jiki ba kwari ta yi alwala ta shige daki.
Hansatu kuwa ko da ta koma bata ga Isah ba, ba kuma ta ga akwati guda ba, a cikin kayan da ya zo da su,bata ce komai ba, ta jawo dan qaramin gas din su, ta ɗora ruwa, ta na so ta yi musu abincin dare.
**************************
Gwamna Halliru ya kira wayar Lawwali, cikin nasara kuwa ta shiga, ya na dauka Gwamna ya fara magana cikin fada.
"Lawwali ina ka kai min d'iya ta? Lawwali in wani abu ya samu d'iyaa ta..."
"Uban mi zaka min in wani abu ya same ta? Na ce uban mi za ka min? Ka ga.."
Sauke Sultana ya yi, da ke kwance a jikin shi, ta na wa kan shi susa, wai ta na so ya yi bacci, ya huta da horon da ya dage ya na bawa yaran shi, fita ya yi waje, dan baya so ta ji da wa yake magana, duk da ya kula hankalin ta ya tashi, da jin kalaman shi.
"...na ce uban mi ka isa ka min? Kai ka san ko ni wane ne, inna ga dama a yau ba zaka kwana gidan gwamnati ba ko gidan ka, ka san ba ka kwana ko? Kaiii inna so yau da kai da iyalan ka kafff ba ku kwana duniyar ga baku kwanan ta ko? To mi zaka min?"
Wasu irin jijiyoyi ne manya manya suka fito rudu rudu a goshin Lawwali, qirjin shi da babu riga, sai bugawa yake da qarfi, hannun shi d'aya ya dunqule kamar mai shirin kai naushi.
Gwamna Halliru ne ya sassauta murya ya ce,
"Lawwali kai wa Allah kar ka cutar da d'iyaa ta, she is innocent, ba ta da wani alaqa da abinda ke tsakanin mu, na amince, na yarda ban kyauta maka ba, duk yanda kake so ka yi ka yi da ni, amma kar ka cutar da diya ta"
Wata mahaukaciyar dariya Lawwali ya saki, sai da yaran shi da ke waje suka kalle shi, sun san kalar dariyar, dariya ce ta ɓacin rai matuqa, kuma ko waye Lawwali ke wa irin dariyar nan, ya na gab da d'and'ana azabar Lawwali.
Tafiya ya yi jikin wata bishiya ya tsaya, sannan ya ce,
"Kar na cutar da d'iyar ka fa kace, she is innocent, me qaunata ta yi maka? Bari in maka da Yaren da zaka fi ganewa Excellency you are going to regret making me the way I am today, ba dai turanci ne ba? Na iya shi, ga shi nan na yi ma, innocent d'iyar ka ka san yanzu haka ta na can na..."
Cikin b'acin rai Gwamna ya ce,
"LAWWALIII !"
Lawwalin ma a hasale ya ce,
"HALLIRU ! Babu yadda za ka yi da ni, sai na shayar da kai gubar da ka dura min ta ta'addanci, sai na lalata rayuwar ka ta inda baka yi zato ba, sai na qarar maka da duk wani abinda ka mallaka, ko me ne ne shi, sai na maida kai abin kwatanci a Nigeria kai har da wasu qasashen, sai na nuna maka ba kowanne d'a ya kamata Ku manya ku lalata wa rayuwa ba ! Sai na shayar da kai abinda ka shayar da ni na baqin cikin rayuwa da duhun ta"
Kashe wayar ya yi, ya wurgar, ya dinga sauke wani irin nishi, duka ya dinga kai wa bishiyar da ya ke tsaye a jikin ta, yaran shi duk sun tsaya cirko cirko, ba mai zamar da ya isa ya tunkare shi a wannan halin da yake ciki.
Gashi duk ya ji wa kan shi ciwo, da dane zuwa zai yi ya debo mutane ya yi ta kisa ba gaira ba dalili, amma yanzu ya na qoqarin sauyawa, daga yawan kashe kashen da yake.
A guje Barirah ta fad'a dakin su Sultanan ba tare da ta nemi izini ba, kwance ta ga sultana ta na ta tunanin da wa Lawwali ke waya, ta ga ran shi bace, har ya na kiran uban wa.
"Ran ki shi dad'e ki gafarce ni, na shigo ba tare da izini ba, amma Oga na buqatar ki a waje, ya na can shi na ji wa kan shi ciwo"
Ai kafin Barirah ta qarasa kalaman ta Sultana ta dire a qasa, jikin ta har rawa yake, wanne irin ciwo kuma? Dankwalin ta take ta ja, ya maqale a jikin gadon, sakin shi ta yi ta fita da gudu, Barirah na gaba, su na zuwa wajen Barirah ta nuna mata Lawwalin ta maqale a baya, Sultana na hango jini a hannun Lawwali ta sa kuka, ta tafi da gudu ta fada jikin shi da qarfi,hannu ya sa ya fizge ta daga jikin shi ya wurga ta gefe, ta fadi qasa, cikin bacin rai ya kalle ta, ya ce,
"Me ye laifi na dan na je neman abinda zan ci? Ashe ba su da kuddin da za su iya ciyar da dika mutanen unguwar mu ma ba ni kad'ai ba? Ashe ba su da kuddin da za su iya daukan nauyin rayuwa ta ta kyautatu kamar yanda suka yi wa nasu 'ya' yan? Ashe ba za su iya ciyar da ni domin Allah ba tare da sun koyar da ni mugayen abubuwan da sun ka koya min ba a yanzu? Ashe ba su da halin taimakon mutanen qasar su sun ka fito siyasa? Ba su da zuciya da kishin qasar su sun ka ce za su mulke mu? Ashe su din azzalumai ne, shedanu ne, mayaudara ne, maqaryata ne? Ashe kan su kawai suke so da iyalan su da abokan su, babu ruwan su da tallaka, ko tallaka ya ci abinci, ko tallaka ya sha Magani, ko ya sha ruwa, ko ya ga hasken wutar lantarki, ko kar ya samu wadannan abubuwa duk ba damuwar su ba ne? Idan na rantse da Allah, Allah ba zai kama ni da lehi ba, mutum guda a manyan 'yan siyasar ga ya na da kuddin da zai ciyar da unguwa guda, ya basu kuddin yanke talauci, amma ba za su yi hakan ba, sun gwammace su maishe mu lalatattu, su yi anfani da mu dan cikar burin su, sun gwammace su juyar mana da basirar da Allah ya mana dan kar mu amfanar da kanun mu komai, mu amfanar da wasu, sun gwammace mu lalace mu haukace da shaye shaye da kashe junan mu, daga yau ina musu albishirin su fara qirga lalacewar tasu rayuwar,wannan alqawarin Lawwali ne"
A guje ya bar wajen ya shiga dajin wajen, da qafa yake keta dajin cikin kuka, da hawayen shi, da Muryar shi,ya na jin yanda qayoyi ke huda kafar shi, amma bai tsaya ba, sai da ya koka duk wani baqin ciki, da bacin ran da yake ji, sai da ya fitar da duk wani qulli da ya dabaibaye masa zuciya, ya hana shi samun cikakken farin ciki.
A qasa ya zube da guiwowin shi, ya kifa kan shi cikin yashin da yake fitar da hucin zafin ranar da ya sha, sama ya kalla ya ga yanda hasken farin wata ya wadatar da dajin, sakamakon duhun dare da ya yi,ajiyar zuciya kawai yake saukewa mai qarfi, cikin wata iriyar murya ya ce,
"Na dau alqawari da Allah daga yau na ajiye duk wani abinda ni ke aikatawa mara kyawu, na kashe bayin Allah da qona gidaje da garuruwan su, na daina shaye shaye kuma zan yi hani da yin shi a sansani na, na dau alqawari da Allah da sani na ba za a qara aikata zina a sansani na ba, na dau alqawari da Allah sai na ga bayan duk wanda ke da hannu a lalacewar mu, na dau alqawari da Allah zan kawo qarshen ta'addanci a nahiyar nan tamu ta Zamfara da kewaye"
Motsi yaji, cikin duhun dajin, juyawa ya yi bayan shi,dan ganin me ne ne ke tahowa, ba ya ganin komai daga nesa, cikin itatuwan akwai duhu, inda yake kuwa fili ne fallau yashi ne sosai a wajen.
Da dukkan alamu koma me ke tahowa ya na ganin shi,amma shi baya ganin komai..........
Motsin na sake matsowa, Lawwali na sake yin shirin ko ta kwana, duk da ya na da tabbacin cewar wannan wajen dajin shi ne, hatta da namun daji masu cutar wa duk babu, sun kashe su.
Mazaje ne guda biyar daga cikin matasan da ke sansanin shi, kewaye shi suka yi, kowanen su. dauke da makamai, mamaki ne fal zuciyar shi.
Ta ya akai ya ke tare da mutanen da za su cutar da shi be sani ba? Har ma yake basu horo da kan shi.
Bai gama tunani ba, daya daga cikin su ya kai mishi wani irin sara, cikin rashin sa'a kuwa ya same shi a dantsen hannun shi.
Cikin kwarewa da jajircewa ya murde hannun shi wuqar ta fadi qasa ya dauke ta ya yanka wuyan shi.
Fada ne sosai ya kaure tsakanin Lawwali da matasan nan, sai dai ko minti biyar ba a cika ba Lawwali ya gama da mutum hudu, ya raunata na qarshen, wuyan matashin na hannun Lawwali, ya ke tambayar shi, wanda ya aiko su, cikin kakari da azaba ya ce,
"No 5 ne Oga, shi ya ce in mun ka yi nasarar kashe ka, zai maishe mu mu zam na kusa da shi, gwamna ya yi muna alqawarin manyan kudi"
Ya na gama jin bayanin da yake so ya ji ya murde wuyan shi, makaman da suka zo da shi, ya diba, ya nufi sansanin nasu, hannun shi na zubar da jini.
Sultana na nan tsaye a bakin dajin, ta kai ta dawo, ta kai ta dawo, su Barirah na tsaye a gefen ta, suma cikin damuwa,
Ta na jin motsin tafiya ta nufi wajen da gudu, ganin Lawwali cikin jini ne ya sanya ta sanya kuka mai cin rai, ko kallon inda take be ba, No 5 na ganin Lawwali ya dawo ya diba da gudu zai bar wajen, wuqa daya Lawwali ya zaro ya saita bayan No 5 ya wurga masa, qara ya saki, tare da gantsare wa.
Lawwali ne ya isa gaban shi ya zare wuqar da qarfi, sannan ya shaqe wuyan shi, filin da suke taruwa Lawwali ya ja shi a qasa ya kai shi wajen ya wurgar.
Nan da nan ya bada umarnin kowa da kowa ya taru a wajen, cikin abinda bai kai minti hudu ba kowa ya hallara, mamaki da tsoro duk ya cika su, hasken fitilar su na solar na haske ko ina na wajen.
Sultana na gefen su Barirah a tsorace, Ita dai wannan rayuwa ta zubda jini ta fara sanya ta jiri.
"A cikin ku akwai wanda ke jin haushi na? Akwai wanda ya yi saura da ke so shi ga baya na? A cikin ku akwai wanda ya ke ganin zai hada kai da gwaunan da ya cutar da rayuwar mu dika, sannan ya yi sanadin zaman mu 'yan ta'adda, kuma ya cutar da rayuwar mu duka, akwai wanda zai taimaka masa wajen kawar dani saboda na gano gaskiya? ina so kowa a cikin mu ya samu 'yancin shi, kuma mu bar zama bayin su mu ci gashin kammu, ku na ganin akwai me so ya kauda ni saboda wannan manufar tawa? Wane ne ya yi saura? Kar na bincika daga baya na samu wanda ya yi saura,"
Shiru wajen ya dauka, damqo No 5 ya yi, ya shaqe shi da kyau, sai da ya ga idon shi ya fara alamun dauke baqi sannan ya sake shi, cikin wani irin wahalallen nunfashi yake tari, da kyar ya daidaita numfashin shi,
"Fada wa mutane me ya faru, da ka ganni ka ke so ka gudu"
Shiru ya yi kamar ba zai magana ba, Lawwali na daga hannu zai make shi ya fara bayani.
"Oga ka yi hakuri, sharrin shaidan ne wallah, tun ranar auren ku mun ka haɗa da gwamna zan kashe ka, na gaje ka, ya yi min alqawarin manyan kudi, ya kuma yi min alqawarin in na kashe ka zai aura min diyar shi, ya......"
Jinin Lawwali ne ya tafarfaso, da jin kalmar wani zai auri sultana ba shi ba, No 5 bai gama magana ba, Lawwali ya sa wuqar hannun shi ya yanke wuyan shi, jini ne ya yi tsartuwa, sultana kuwa ta zube a wajen a sume, bayan ta kwalla wata iriyar razananniyar qara.
Lawwali ne ya wurgar da wuqar a wajen, ya bada umarni a binne shi, a je can inda sauran yaran suka mutu a binne su.
Durqusawa ya yi a gaban Sultana ya dauke ta da hannu daya, ya nufi dakin su da ita.
A saman gado ya ajiye ta, ya debi ruwa ya watsa mata, zubewa ya yi a qasa, idanun shi na lumshe wa, saboda jinin da ke zuba a jikin shi.
Ko da ta farfado ta ga baya motsi, sai hankalin ta ya tashi, taimako ta nema a wajen, nan da nan masu kula da lafiyar mutanen wajen suka zo aka duba shi, aka yi ma wajen ɗinki ,sannan suka masa allurar da zata kashe masa zafi, sai magunguna na kashe zafi da aka bawa Sultana suka fita, suka barta ta na kallon ikon Allah.
Nan kuma Allah ya kawo ta, ba komai da sanin shi, zata yi hakuri da qaddarar ta, fatan ta Allah ya bata ikon
Showing 102001 words to 105000 words out of 150481 words
Dariya Hansatu ta sa, dan ta san wannan aikin Ameenatu ne, ita ce zata hana su magana kan su shiga, Bilkisu ta sha fad'a mata, in sun je waje Ameenatu na hana su magana, komai aka tambaye su, su ce su ma basu sani ba, ko su yi shiru su zubawa mutum ido kawai.
"Ki yi hankuri, na gode da ki ka aje min su, bari mu tafi gida, mangariba ta yi"
Tsaki 'Yabbuga ta yi, ta miqe daga gaban Ahmad, da tai Wa zaman neman gafara, ba kalar lallaba yaron da bata yi ba, dan ta ji labarai a wajen shi ya qi bude baki sam.
Ita kuma kamar mayya, a nan gaban su ta cinye abincin da suka kai mata, ta na yi ta na tambayar su gidan su, su kuma su na ta kallon ta, sun qi amsa ta.
Sai da Hansatu za su fita ta juya ta ce ma 'Yabbuga,
"Yau fa Baban su Ameenah ya dawo,"
Wata gud'a da shewa 'Yabbuga ta buga, ta buga cinya, kafin ta yi magana Hansatu ta tisa qeyar yaran, ta ce su yi gida, ita kuma ta tsaya, dan 'Yabbuga na iya bin ta, har gida, ta fadi abinda zai sa wa yaran ta tunanin me ake nufi da kazan nan da aka fada.
"Hahaiiiiii cassss! ko da na ji, yanzu na ji batu,dan ko na san ruwa da iska ba ki barin d'iyan nan zuwa ko ina, ku na nan manne da juna, ashe ashe uban su ne yaddawo ana can ana biyan bashi , shi yasa aka koro su, tauuuu, to ko za ki kawo su su kwana nan? Kar su yi mummunan gamo"
Cikin takaici Hansatu ta kalle ta tace,
"Bayan na haifi Ameenatu, Bilkisu ta biyo baya, duk su na nan sun fara wayo nayyi cikin Ahmad, kuma har yau idon su ko kunnen su bai gane musu komi ba in shaa Allahu, ke ga kuwa ba abinda za su gani a gaba ma, in shaa Allahu, na gode sai da safe"
Hansatu na fadin haka ta tafi, 'Yabbuga kuwa ran ta ya ɓaci, nan da nan ta hau sakin maganganu marasa dad'i.
"Keeeee wagga ban ce ki fada min baqa ba, yaushe na an ka jone da mijin har da za ki yi min kitihin yohi? Mijin da mun san komi, ba qaunar ki shi kai ba? Wanne irin kashin wahala ne baki sha hannun shi ba? Ba ci ba sha, ba sutura, nan nan gidan kin shigo shi kin yi maula ba a ko qirgawa, yo Allah na tuba wane dare ne jemage bai gani ba, kai ku ji min yarinya da kitihi,"
Hansatu na cikin gidan ta tana jin komai, kasa jurewa ta yi, ta fita, ta koma gidan 'Yabbuga dake ta sababi, ta ke yi mata gori kala kala.
'Yabbuga bata ji shigowar Hansatu ba sai kalaman ta,
"Na gode wa Allah, kuma na gode miki da Allah ya azurta mu a lokacin da muke cikin matsin rayuwa ta hanyar ki, na gode miki da kika taimaka mana a lokacin da muke da tsananin buqatar taimako, banda bakin yi miki godiya sai dai na roqi Allah da ya sauya maki halayen ki, daga munana zuwa kyawawa, shi saka maki da alkhairi, duk abinda kin ka fadi gaskiya ne, amma ki sani, in a baya Allah ya baki lada, to fa a yanzu zunubi ki ka dauka, domin kin zobe ladan da yabbaki ta hanyar yi min gori, kin san kuwa hanin da aka yi akan gori? kin tozarta ni akan abinda ki ka min a baya, kin yi min gori, ni kuma ba zan rama ba, amma kar ki manta abu guda, shi zama in ya hada ka da koma wane ne, abu guda dole sai ya faru, ko ku zauna lahiya kowa shi amfana da kowa, ko ku cutar da junan ku, ki dinga tuna baya kahin ki yi min gori, sai da safe"
Jikin 'Yabbuga bai taba sanyi ba irin na yau, ashe Hansatu na da baki? A fakaice wadannan maganganun da ta wa 'Yabbuga dukkan su suna da fassarar su da ma'anar su kala kala, da 'Yabbuga na tuna baya da bata yi wa Hansatu gori ba, domin sai da ta fara morar Hansatu kafin Hansatu ta more ta, sai dai duk abinda Hansatu ta yi wa 'Yabbuga Hansatun bata taɓa sanar da kowa ba, itama 'Yabbuga bata taɓa fadawa kowa ta mori Hansatu ba sanda ta na amarya, amma ko gishiri hansatu ta karba wajen ta, sai ta qara tace har da Maggi da mai ta bata.
Jiki ba kwari ta yi alwala ta shige daki.
Hansatu kuwa ko da ta koma bata ga Isah ba, ba kuma ta ga akwati guda ba, a cikin kayan da ya zo da su,bata ce komai ba, ta jawo dan qaramin gas din su, ta ɗora ruwa, ta na so ta yi musu abincin dare.
**************************
Gwamna Halliru ya kira wayar Lawwali, cikin nasara kuwa ta shiga, ya na dauka Gwamna ya fara magana cikin fada.
"Lawwali ina ka kai min d'iya ta? Lawwali in wani abu ya samu d'iyaa ta..."
"Uban mi zaka min in wani abu ya same ta? Na ce uban mi za ka min? Ka ga.."
Sauke Sultana ya yi, da ke kwance a jikin shi, ta na wa kan shi susa, wai ta na so ya yi bacci, ya huta da horon da ya dage ya na bawa yaran shi, fita ya yi waje, dan baya so ta ji da wa yake magana, duk da ya kula hankalin ta ya tashi, da jin kalaman shi.
"...na ce uban mi ka isa ka min? Kai ka san ko ni wane ne, inna ga dama a yau ba zaka kwana gidan gwamnati ba ko gidan ka, ka san ba ka kwana ko? Kaiii inna so yau da kai da iyalan ka kafff ba ku kwana duniyar ga baku kwanan ta ko? To mi zaka min?"
Wasu irin jijiyoyi ne manya manya suka fito rudu rudu a goshin Lawwali, qirjin shi da babu riga, sai bugawa yake da qarfi, hannun shi d'aya ya dunqule kamar mai shirin kai naushi.
Gwamna Halliru ne ya sassauta murya ya ce,
"Lawwali kai wa Allah kar ka cutar da d'iyaa ta, she is innocent, ba ta da wani alaqa da abinda ke tsakanin mu, na amince, na yarda ban kyauta maka ba, duk yanda kake so ka yi ka yi da ni, amma kar ka cutar da diya ta"
Wata mahaukaciyar dariya Lawwali ya saki, sai da yaran shi da ke waje suka kalle shi, sun san kalar dariyar, dariya ce ta ɓacin rai matuqa, kuma ko waye Lawwali ke wa irin dariyar nan, ya na gab da d'and'ana azabar Lawwali.
Tafiya ya yi jikin wata bishiya ya tsaya, sannan ya ce,
"Kar na cutar da d'iyar ka fa kace, she is innocent, me qaunata ta yi maka? Bari in maka da Yaren da zaka fi ganewa Excellency you are going to regret making me the way I am today, ba dai turanci ne ba? Na iya shi, ga shi nan na yi ma, innocent d'iyar ka ka san yanzu haka ta na can na..."
Cikin b'acin rai Gwamna ya ce,
"LAWWALIII !"
Lawwalin ma a hasale ya ce,
"HALLIRU ! Babu yadda za ka yi da ni, sai na shayar da kai gubar da ka dura min ta ta'addanci, sai na lalata rayuwar ka ta inda baka yi zato ba, sai na qarar maka da duk wani abinda ka mallaka, ko me ne ne shi, sai na maida kai abin kwatanci a Nigeria kai har da wasu qasashen, sai na nuna maka ba kowanne d'a ya kamata Ku manya ku lalata wa rayuwa ba ! Sai na shayar da kai abinda ka shayar da ni na baqin cikin rayuwa da duhun ta"
Kashe wayar ya yi, ya wurgar, ya dinga sauke wani irin nishi, duka ya dinga kai wa bishiyar da ya ke tsaye a jikin ta, yaran shi duk sun tsaya cirko cirko, ba mai zamar da ya isa ya tunkare shi a wannan halin da yake ciki.
Gashi duk ya ji wa kan shi ciwo, da dane zuwa zai yi ya debo mutane ya yi ta kisa ba gaira ba dalili, amma yanzu ya na qoqarin sauyawa, daga yawan kashe kashen da yake.
A guje Barirah ta fad'a dakin su Sultanan ba tare da ta nemi izini ba, kwance ta ga sultana ta na ta tunanin da wa Lawwali ke waya, ta ga ran shi bace, har ya na kiran uban wa.
"Ran ki shi dad'e ki gafarce ni, na shigo ba tare da izini ba, amma Oga na buqatar ki a waje, ya na can shi na ji wa kan shi ciwo"
Ai kafin Barirah ta qarasa kalaman ta Sultana ta dire a qasa, jikin ta har rawa yake, wanne irin ciwo kuma? Dankwalin ta take ta ja, ya maqale a jikin gadon, sakin shi ta yi ta fita da gudu, Barirah na gaba, su na zuwa wajen Barirah ta nuna mata Lawwalin ta maqale a baya, Sultana na hango jini a hannun Lawwali ta sa kuka, ta tafi da gudu ta fada jikin shi da qarfi,hannu ya sa ya fizge ta daga jikin shi ya wurga ta gefe, ta fadi qasa, cikin bacin rai ya kalle ta, ya ce,
"Me ye laifi na dan na je neman abinda zan ci? Ashe ba su da kuddin da za su iya ciyar da dika mutanen unguwar mu ma ba ni kad'ai ba? Ashe ba su da kuddin da za su iya daukan nauyin rayuwa ta ta kyautatu kamar yanda suka yi wa nasu 'ya' yan? Ashe ba za su iya ciyar da ni domin Allah ba tare da sun koyar da ni mugayen abubuwan da sun ka koya min ba a yanzu? Ashe ba su da halin taimakon mutanen qasar su sun ka fito siyasa? Ba su da zuciya da kishin qasar su sun ka ce za su mulke mu? Ashe su din azzalumai ne, shedanu ne, mayaudara ne, maqaryata ne? Ashe kan su kawai suke so da iyalan su da abokan su, babu ruwan su da tallaka, ko tallaka ya ci abinci, ko tallaka ya sha Magani, ko ya sha ruwa, ko ya ga hasken wutar lantarki, ko kar ya samu wadannan abubuwa duk ba damuwar su ba ne? Idan na rantse da Allah, Allah ba zai kama ni da lehi ba, mutum guda a manyan 'yan siyasar ga ya na da kuddin da zai ciyar da unguwa guda, ya basu kuddin yanke talauci, amma ba za su yi hakan ba, sun gwammace su maishe mu lalatattu, su yi anfani da mu dan cikar burin su, sun gwammace su juyar mana da basirar da Allah ya mana dan kar mu amfanar da kanun mu komai, mu amfanar da wasu, sun gwammace mu lalace mu haukace da shaye shaye da kashe junan mu, daga yau ina musu albishirin su fara qirga lalacewar tasu rayuwar,wannan alqawarin Lawwali ne"
A guje ya bar wajen ya shiga dajin wajen, da qafa yake keta dajin cikin kuka, da hawayen shi, da Muryar shi,ya na jin yanda qayoyi ke huda kafar shi, amma bai tsaya ba, sai da ya koka duk wani baqin ciki, da bacin ran da yake ji, sai da ya fitar da duk wani qulli da ya dabaibaye masa zuciya, ya hana shi samun cikakken farin ciki.
A qasa ya zube da guiwowin shi, ya kifa kan shi cikin yashin da yake fitar da hucin zafin ranar da ya sha, sama ya kalla ya ga yanda hasken farin wata ya wadatar da dajin, sakamakon duhun dare da ya yi,ajiyar zuciya kawai yake saukewa mai qarfi, cikin wata iriyar murya ya ce,
"Na dau alqawari da Allah daga yau na ajiye duk wani abinda ni ke aikatawa mara kyawu, na kashe bayin Allah da qona gidaje da garuruwan su, na daina shaye shaye kuma zan yi hani da yin shi a sansani na, na dau alqawari da Allah da sani na ba za a qara aikata zina a sansani na ba, na dau alqawari da Allah sai na ga bayan duk wanda ke da hannu a lalacewar mu, na dau alqawari da Allah zan kawo qarshen ta'addanci a nahiyar nan tamu ta Zamfara da kewaye"
Motsi yaji, cikin duhun dajin, juyawa ya yi bayan shi,dan ganin me ne ne ke tahowa, ba ya ganin komai daga nesa, cikin itatuwan akwai duhu, inda yake kuwa fili ne fallau yashi ne sosai a wajen.
Da dukkan alamu koma me ke tahowa ya na ganin shi,amma shi baya ganin komai..........
*Hummmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmm*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 48:
Motsin na sake matsowa, Lawwali na sake yin shirin ko ta kwana, duk da ya na da tabbacin cewar wannan wajen dajin shi ne, hatta da namun daji masu cutar wa duk babu, sun kashe su.
Mazaje ne guda biyar daga cikin matasan da ke sansanin shi, kewaye shi suka yi, kowanen su. dauke da makamai, mamaki ne fal zuciyar shi.
Ta ya akai ya ke tare da mutanen da za su cutar da shi be sani ba? Har ma yake basu horo da kan shi.
Bai gama tunani ba, daya daga cikin su ya kai mishi wani irin sara, cikin rashin sa'a kuwa ya same shi a dantsen hannun shi.
Cikin kwarewa da jajircewa ya murde hannun shi wuqar ta fadi qasa ya dauke ta ya yanka wuyan shi.
Fada ne sosai ya kaure tsakanin Lawwali da matasan nan, sai dai ko minti biyar ba a cika ba Lawwali ya gama da mutum hudu, ya raunata na qarshen, wuyan matashin na hannun Lawwali, ya ke tambayar shi, wanda ya aiko su, cikin kakari da azaba ya ce,
"No 5 ne Oga, shi ya ce in mun ka yi nasarar kashe ka, zai maishe mu mu zam na kusa da shi, gwamna ya yi muna alqawarin manyan kudi"
Ya na gama jin bayanin da yake so ya ji ya murde wuyan shi, makaman da suka zo da shi, ya diba, ya nufi sansanin nasu, hannun shi na zubar da jini.
Sultana na nan tsaye a bakin dajin, ta kai ta dawo, ta kai ta dawo, su Barirah na tsaye a gefen ta, suma cikin damuwa,
Ta na jin motsin tafiya ta nufi wajen da gudu, ganin Lawwali cikin jini ne ya sanya ta sanya kuka mai cin rai, ko kallon inda take be ba, No 5 na ganin Lawwali ya dawo ya diba da gudu zai bar wajen, wuqa daya Lawwali ya zaro ya saita bayan No 5 ya wurga masa, qara ya saki, tare da gantsare wa.
Lawwali ne ya isa gaban shi ya zare wuqar da qarfi, sannan ya shaqe wuyan shi, filin da suke taruwa Lawwali ya ja shi a qasa ya kai shi wajen ya wurgar.
Nan da nan ya bada umarnin kowa da kowa ya taru a wajen, cikin abinda bai kai minti hudu ba kowa ya hallara, mamaki da tsoro duk ya cika su, hasken fitilar su na solar na haske ko ina na wajen.
Sultana na gefen su Barirah a tsorace, Ita dai wannan rayuwa ta zubda jini ta fara sanya ta jiri.
"A cikin ku akwai wanda ke jin haushi na? Akwai wanda ya yi saura da ke so shi ga baya na? A cikin ku akwai wanda ya ke ganin zai hada kai da gwaunan da ya cutar da rayuwar mu dika, sannan ya yi sanadin zaman mu 'yan ta'adda, kuma ya cutar da rayuwar mu duka, akwai wanda zai taimaka masa wajen kawar dani saboda na gano gaskiya? ina so kowa a cikin mu ya samu 'yancin shi, kuma mu bar zama bayin su mu ci gashin kammu, ku na ganin akwai me so ya kauda ni saboda wannan manufar tawa? Wane ne ya yi saura? Kar na bincika daga baya na samu wanda ya yi saura,"
Shiru wajen ya dauka, damqo No 5 ya yi, ya shaqe shi da kyau, sai da ya ga idon shi ya fara alamun dauke baqi sannan ya sake shi, cikin wani irin wahalallen nunfashi yake tari, da kyar ya daidaita numfashin shi,
"Fada wa mutane me ya faru, da ka ganni ka ke so ka gudu"
Shiru ya yi kamar ba zai magana ba, Lawwali na daga hannu zai make shi ya fara bayani.
"Oga ka yi hakuri, sharrin shaidan ne wallah, tun ranar auren ku mun ka haɗa da gwamna zan kashe ka, na gaje ka, ya yi min alqawarin manyan kudi, ya kuma yi min alqawarin in na kashe ka zai aura min diyar shi, ya......"
Jinin Lawwali ne ya tafarfaso, da jin kalmar wani zai auri sultana ba shi ba, No 5 bai gama magana ba, Lawwali ya sa wuqar hannun shi ya yanke wuyan shi, jini ne ya yi tsartuwa, sultana kuwa ta zube a wajen a sume, bayan ta kwalla wata iriyar razananniyar qara.
Lawwali ne ya wurgar da wuqar a wajen, ya bada umarni a binne shi, a je can inda sauran yaran suka mutu a binne su.
Durqusawa ya yi a gaban Sultana ya dauke ta da hannu daya, ya nufi dakin su da ita.
A saman gado ya ajiye ta, ya debi ruwa ya watsa mata, zubewa ya yi a qasa, idanun shi na lumshe wa, saboda jinin da ke zuba a jikin shi.
Ko da ta farfado ta ga baya motsi, sai hankalin ta ya tashi, taimako ta nema a wajen, nan da nan masu kula da lafiyar mutanen wajen suka zo aka duba shi, aka yi ma wajen ɗinki ,sannan suka masa allurar da zata kashe masa zafi, sai magunguna na kashe zafi da aka bawa Sultana suka fita, suka barta ta na kallon ikon Allah.
Nan kuma Allah ya kawo ta, ba komai da sanin shi, zata yi hakuri da qaddarar ta, fatan ta Allah ya bata ikon
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35 Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51