din da ka ke wa kallon zan shiga aljannah wataqila Allah ya sanya ka a aljannah din mu zauna tare saboda ni din, sannan Allah zai iya jarabta ta da wani abun, ni kuma na yi wasa da shi na aikata zunubin da zai kai ni wuta, hadisi ne fa guda, akwai mutanen da za su yi ta aikata ayyuka irin na 'yan aljannah, saura kad' an su shiga aljannar, amma se su aikata aiki irin na 'yan wuta, se Allah ya sanya su a wutar, sannan akwai mutanen da za su yi ta aiki irin na' yan wuta, sauran kad'an su shiga wutar se kawai su yi aiki irin na 'yan aljannah, sai Allah ya kare su ya sanya su a aljannah, ka gani? Allah ba ta inda baya wanzar da rahama da ikon shi"
"Sultana ban taba shirka ba, amma ina taimaka wa masu yi, duk abinda mahaifin ki ya buqata da sauran 'Yan siyasa a baya ko mene shi ina samar musu shi, duk da na san tsafi za a yi da abun"
Hawayen ta ne suka qaru, jin cewar har da mahaifin ta a aikata shirka,
"Ka yi istigfar Allah zai amsa, ka yi da kyayyawar niya, Allah zai yafe maka"
"Allah na tuba ka yahe min, Allah ka yahe min manya da qananan zunubbai na, Allah ka yi min rahama, ka cika min buri na,"
"Ameen,"
Kafin bacci ya ɗebe su, sun tattauna akan abubuwa da dama, sun kuma tsara duk wani abu da ya kamata su aikata a gaba, a haka bacci ya dauke su suna manne da junan su.
***************************
Kamar yanda Isah ya yi alqawari, ya siyi goro mai yawan gaske, dan tafiya Makka, wanan karon dubu hamsin casss ya cake wa Hansatu, amma bata ci su a banza ba, sai da ya mori jikin ta da kyau da kyau, dan duk girman ta, da jarumtar ta, sai da ta dinga shiga ruwan zafi, Ita dai ta sawa ran ta, ba zai sake ganin wani rawar kan son shi awajen ta ba, tunda ta yi a baya bai mata amfani ba, sannan ba zai sake ganin murmushin ta ba, tunda a baya sai da ta ce wa audiga bata iya murmushi ba,ta fita iyawa, duk bata samu ribar murmushin ba,hakan kuwa na matuqar damun Isah, kula da cewar ko sau nawa zai neme ta ba zata qi ba,shi ya sa ya ke fanshe haushin rashin sakewar a jikin ta.
Hajiyar Hansatu da Yaya Musa sun yi qoqari sosai wajen ba Isah wasu kudin da zai qara akan jarin shi, sai da ya musu sallama sannan aka bada mota kamar wancan karon aka kai shi airport, wannan karon ko kwalla Hansatu bata yi ba, balle ta koka, Isah kuwa ya ji haushi matuqa, sannan ta ce ba zata yi rakiya ba, a fusace ya fad'a mota, aka tafi kai shi,ko da takoma sai ta ce wa Hajiya ita bata so ta ga ya tafi ya barta, kuka za tai, kuma bata so ta daga masa hankali,dan haka Hajiya bata ce komai ba, sai suka ci gaba da hirar su.
Isah sun isa airport, ya sauke kayan shi da komai, cikin dabarar da suke yi kar a gane goro ne, ya na tsaye wani mutum fari ya tsaya gefen shi, sallama ya masa shi ma ya amsa, sai ya ji maganar kamar ta Inyamuri ko bayerabe,
Mutumin ya fara yi wa Isah magana da turanci, Isah ba turanci, fuska ta muzanta da kunya, sai bawan Allahn ya gane Isah fa wala ingilishi, cikin gurbatacciyar Hausar shi ya ke tambayar Isah, Makka zai je ko Madina in sun isa Saudiya?
"Makka zani"
"Masha Allah, ni ma can nake da zama, ina da gida da iyali a can, kai fa ina ka ke zama?"
"Ni a hotel kawai nake sauka, banda gidan zama,"
"Allah Sarki, ka fad'a min inda ka ke sauka in na samu natsuwa zan neme ka, se ka dawo gida na da zama, tunda duk qasar mu d'aya, in a foreign land in ka ga d'an qasar ku ji ka ke kamar d'an uwanka ne"
Sunan hotel din da yake sauka ya sanar da bawan Allahn nan ya na ta murna, a qalla ba shi ba biyan kudin hotel, zama suka yi tare, suna ta hira, kamar abokan juna, duk inda CCTV camera yake a wajen bawan Allahn nan ya sani, kuma daidai gwargwado juya bayan shi yake, ba ya bari fuskar shi ta hasku, ya yi shiga irin ta larabawa ya saka face mask, se surutu yake wa Isah da gurbatacciyar hausar shi, Isah kuwa banda washe baki ba abinda yake.
Sai da aka shiga jirgi ne suka rabu, saboda wajen zaman su ba daya bane.
Tafiya ta miqa zuwa Saudiya, Isah ba abinda ya ke banda tunanin Hansatu, wannan karon ji yake kamar ya bar wani bangare na jikin shi, qudirtawa ya yi in Allah ya sauke shi lafiya, ita zai fara kira su gaisa.
**********************
A hanyar su ta zuwa garin na Zamfara duk wani motsi na Mubaraka na kan idon Taheer, zuciyar shi kuwa na ta kakkaryewa zuwa qananan pieces ,ya yi zurfi akan son ta ba tare da ya sani ba, wataqila dalilin gano ya na son nata, rabuwar da ta zo musu ba tare da shiri bane, da ya kula ya na son ta tun da, da ya yad'a manufar shi a wajen ta, gashi yanzu lokaci ya qure masa.
Mubaraka ce ta yi qarfin halin yi masa magana, ta ce,
"Yah Taheer akwai damuwa ne?"
Da sauri ya sanya murmushin yaqe ya ci gaba da tuqi, bai ce komai ba, tafiya suke kamar ba zai magana ba, can kamar wanda aka shaqe ya ce,
"Yanzu in kin tafi shikenan? Mantawa zakiyi da mu ko? Ga yaran ki can kin bar su suna ta kuka, ke kad'ai ka lallashin su in su na rikici, sun hi sabawa da ke,gashi zaki tafi ki bar su"
"Yah Taheer ku din wani bangare ne mai girma a rayuwa ta, ba zan taba manta wa da ku ba, ka sani na jima ban ga yayana ba, ina kewar shi sosai, amma in na je na gan su, ai zan koma wajen ku, in Allah ya yarda"
Wani irin murmushi Taheer ya sake, har da sosa kai, murmushin shi ya bawa Mubaraka mamaki, sai ita ma ta fara murmushin, cikin daurewar kai, dan ta kasa fahimtar inda Yah Taheer din ya dosa da wannan bayyanannen farin cikin................
*Allah kai ku lahiya ke dai, mu ai mun gane murmishin meye😂😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 53:
Jefi jefi suke hirar su, cikin nishadi, da kuma sabo, Taheer na matuqar jin dad'i da girmama wannan lokaci da hirar tasu baki daya, domin bai sani ba, ko na qarshe kenan da za su hadu har su yi hira haka, ko kuma akwai rabon haduwar su a gaba.
Sun isa garin zamfara da misalin qarfe 12 na rana, saboda gudu sosai da yake zubawa, hamdala Mubaraka ta yi, sannan ta kalli Taheer, ta na qoqarin motsa baki tai magana ta ga wasu sojoji na nuna ta, amma ba su tsaida motar su ba, sunkuyar da kan ta tayi qasa, dan ta san dalilin da ya sa suke nuna ta, da an basu dokar kama ta, yanzu an janye.
Sai da suka shiga gari sosai, Taheer na qoqarin daukan hanyar dajin nasu Mubaraka ta cire nauyin baki ta ce,
"Yah Taheer Dan Allah tsaya,"
Bai tsaya jin dalilin tsayawar ba, ya samu gefe ya tsaida motar, Sannan ya tattara duk wata nutsuwar shi ya miqa mata a hannun ta, d'an cizon leben ta tayi na qasa, cikin tsoron me zai je ya zo ta ce,
"Dan Allah ka fara kai ni gida wajen su Umma, dan ban sani ba ko Yah Auwal zai bari na je na gan su, dan Allah kar ka qi, in ka qi kai ni na ga Ummana zan yi maka kuka, kuma Yah Auwal zai ga na yi kuka, kuma..."
"Tau ya yi haka nan, ban ce ki bani tsoro ba daga shigowa ta, tau yanzu in munka tai ya ji labari fa? Kin dai san in kin tsira ni ina ruwa ko?"
Cikin zumudi da murna ta ce,
"Ba abinda zai yi maka, Indai na ce ni ta ni nace ka kai ni, Please Yah Taheer ka kai ni naga su Umma" ta qarasa magana cike da shagwaba.
Taheer dai bai so ba, amma an sa shi na dole, tiryan tiryan take nuna hanya, har suka isa, ya na tsaida motar ta fita a guje, ta fad'a gidan,shiru ta ji ba kowa, daga iyayen nasu, har yaran.
Cikin sanyin jiki, ta dinga leqa d'akuna,ta fita, gidan da ke manne da nasu ta shiga, suka gaisa,mutane ne na kirki, masu dattako, tambayar su ta yi inda iyayen ta suke, nan suka sanar da ita Kareeman 'Yabbuga ce ta haihu, yau suna, dan haka su na can gidan Kareema.
Sallama ta musu da godiya ta koma wajen Taheer jiki ba kuzari, idanun ta sun cika da kwalla.
Hakuri ya bata bayan ta masa bayanin komai, ya ce in sun je, ta roqi Auwal, ya san zai kai ta da kan shi.
Hanya suka miqa sai daji.
A can dajin kuwa Sultana da Lawwali sai zumud'in zuwan mubaraka suke, sun yi kwalliya, sun sha ado gwanin ban sha'awa, kamar masu tarbar wani hamshaqin, su Barira da yaran Lawwali kuwa ,sun matsu su ga wace ce wannan yarinyar da ta shiga ran Ogan su? Ya take? Shin ta kai wadda za a gigice da so ko bata kai ba?
Abinci da abun sha, mahallin kwana, da duk abinda za su buqata komai an tanadar musu, su kawai ake jira.
Da misalin qarfe hudu da arba'in su Mubaraka ne a cikin jejin Oga Lawwali, tun daga hanya Mubaraka ta tsure, ganin mutane dauke da makamai, kamar masu zuwa yaqi,Taheer ne ya yi ta kwantar mata da hankali.
Lawwali ya kasa zama, sultana sai dariya take masa,Sultan da ke tsaye ya na kallon su, shi ma murmushi yake ta zabgawa, Lawwali na hango motar su No 4 ya zabura zai yi wajen, Sultana ta d'an kwalla qara kadan, juyawa ya yi ya kalle ta, ya ga ta dafe cikin ta, da sauri ya duqa gaban ta, ya na mata sannu, a lokaci daya kuma ya na juyawa dan ganin rabin ran nashi.
Sultana bata d'aga daga duqawar da ta yi ba sai da ta ga Mubaraka ta fita a motar, cikin washe baki, da murna, Sultana ta kwace hannun ta daga na Lawwali ta kwasa da gudu, ta nufi Mubaraka, suka rungume juna, mamaki da haushi ne suka kama Lawwali, kawai sai ya tsaya ya kama qugu, mutanen wajen kuwa me za su yi banda dariya.
Sultan kuwa har ya na duqawa dan dariya, ga dai Lawwali qatoto, maji da qarfi, amma Sultana yar firit ta masa wayo,Mubaraka gani ta yi ba shi da niyyar zuwa wajen ta, sai ta shanye dariyar ta ta daga murya ta ce,
"Yah Taheer mu juya kawai, ka kaini wajen su Umma na, tunda Yah Auwal din baya son gani na"
Wata harara Lawwali ya zuba mata, sannan ya taka da sauri, Itan ma da sauri ta ke zuwa wajen shi, rungume ta ya yi kamar ba zai rabu da ita ba, Ita kuwa kukan farin ciki ta saka, wani abu ya ji ya tokare masa maqoshin shi, wanda ya ke bayyana tsananin kewar ta da ya yi, ji ya ke dama zai iya kwaranyar da hawaye wataqila da ya ji sauqin abinda yake ji a ran shi,sake qanqame ta ya yi, ya na godewa Allah, da ya dawo masa da ita lafiya.
Sun jima a haka, sannan ya dago da kan ta ya juya ga mutanen da ke wajen, fuskar su dauke da kallo na sha'awar soyayyar da ke tsakanin yaya da qanwar shi.
"Kunga yanda qaunata ta dawo gare ni lahiya? Na muku alqawarin zan maida ku ga iyalin ku lahiya, da yardar Allah, ba zan gaji da neman yahiyar ku a gare ni ba, ku yahe min, ko ba yanzu ba, ko bama tare ne, ku yahe min dan Allah"
Hayaniya ce ta karade wajen, Sultan na gefe ya na murmushin jin dad'in ganin shaquwa da aminci da ke tsakanin Oga da mutanen shi.
Ta gaban shi su Sultana suka wuce, shi ma ya bi bayan su.
Kafin su qarasa ciki Mubaraka ta gaida shi, amsawa ya yi, cikin sakin fuska, sannan ya tambaye ta ya hanya, ta bashi amsa da,
"Alhamdu lilLAAHi"
"To masha Allahu, sannun ku da zuwa"
"Yauwa Muna godiya"
No 4 da Lawwali sun tsaya daga waje, su na tattaunawa, kafin daga baya suyi sallama, ya tafi tsohon dakin shi, da ya samu baqi a ciki, amma still gadon shi na nan, a ciki, ga abinci nan da abun sha an aje masa.
Sai da Mubaraka ta fara wanka, sannan suka hadu dikan su a saman carpet suka ci abinci, su na yi su na hira.
Sultana kan ta ta sallama, ta sani ba zata tab'a samun kalar soyayyar da Lawwali ke wa qanwar shi ba, Mubaraka ta yi gaba, ta na bayan ta, ta yarda da hakan, kuma bai dame ta ba, domin dama kowa da matsayin shi .
Ranar Lawwali ya sha labarin Kano, har tsokanar ta ya soma yi da cewar,
"Ohhh su Barakana daga zuwa Kano a yi watanni, har an koma yin kananci, Sultyna, qaunar nan taki bata ko yadda ba wallah, gani takai yanzu ta zama bakanuwa"
Dariya sukai tayi, ita kuma ta na qoqarin kare kan ta, haka suka yi ta shan hira, tare damurnar dawowar ta lafiya.
*************************
Jirgi ya d'aga sai Saudiya, Isah kuwa wayar shi ya zaro a aljihun gaban rigar shi, ya na ta kallon hotunan Hansatu, wanda ya mata, ta na bacci, da wanda ya mata ta na aiki, duk bata sani ba, sai murmushi ya ke zubawa, ashe akwai ranar da zai kalle ta da soyayya a ciki? Ni kuwa nace ba soyayya ba ce sha'awa ce, ai da can da take son ka san da baka da komai, kai baka so ta ba, sai yanzu da ka ga ita Allah ya mata komai ka ke son ta.
Jirgi ya tsaya a king Fahad international airport, mutane na ta qoqarin sauka, Isah na tafe shima cikin ayari, wayar shi ya mayar a aljihu, ya riqe 'yar qaramar jakar kayan shi,ya sauka.
Wannan bawan Allahn ya gani daga nesa da shi, ya na masa murmushi, tare da yi masa sallama.
Mayar masa da sallamar shi ya yi, ya nufe shi, dan su je su d'auki kayan su, sai bawan Allahn nan ya nuna wa Isah qaramar jakar shi, ya sanar da shi ita kenan yake da, dan haka anan suka yi sallama, ya tafi, Isah kuwa dole sai da ya je daukan manyan jakunkunan da ya isa da su.
Ina can ina kalle kalle Hameeda ta shiga Saudiya (Allah ka amsa ka bama duk wanda be je ba ikon zuwa) sai na ji ihun mutane, larabci na tashi ko ta ina, kafin na koma wajen dan ganin me ke faruwa sai na hango askar sun kewaye Alhaji Isah, Isah ya durqusa qasa ya na rantsuwa tare da baza musu Hausa, ya na bayani ba na shi bane.
Ko da na leqa da kyau, sai na ga wani abu fari tasss a leda guda hudu, da na kasa kunne da kyau, sai na ji ana fad'in koken ne abun, hankali na ya tashi nai baya, ina leqe daga nesa, bawan Allah'n nan na hango cikin tsananin damuwa da b'acin rai ya na kiran
"Shit, shit, this man na mumu, de don catch am"
(Wannan mutumin Wawa ne sun mama shi)
Da sauri ya rataya jakar shi ya bar wajen, a cikin gudu-gudu, sauri-sauri.
Tuni an sanqame Isah, ya na ihu ya na kuka, sai fadi yake ya na kumawa.
"Goro ne kaɗai nawa na rantse, koken din ban san na waye ba, dan Allah ku maida ni Nigeria ba zan sake safarar goron ba,ni Ko zuwa ma ba zan sake yi ba"
Gaba daya fuskar Isah ta sauya, cikin qanqanin lokaci ya zama kamar ba shi ba, saboda shiga tashin hankali.
Ba su tsaya da shi ko ina ba sai wajen ajiye masu manyan laifuka.
Isah na nan na kuka, da roqon gafara, tare da qoqarin bayyana musu gaskiyar shi, amma ba mai sauraron shi, balarabe d'aya aka kawo wanda ya ke dan jin Hausa, duk wani bayani da Isah yake yi, abu dai na komawa kan shi ne, tunda ya kawo goro ta boyayyiyar hanya to tabbas koken tashi ce,
"Innalillahi, yau na shiga uku, na lalace, wai da wane yare kuke so na muku bayani ne, ba tawa bace,"
Wani baqar fata Isah ya gani, da uniform din 'yan sandar qasar, cikin yaqe Isah ya yafice shi, ya na washe baki,
"Yauwaa ga na gida nan, bawan Allah, dan Allah zo kai mana tafinta, ka fada musu goro kawai na kawo, yasin ban san koken din waye ba, ni ma yanda suka gan ta haka na gan ta, dan Allah fassara musu, ni na yarda su karbi goron su zubar, ai dama haka ake yi ko, amma kar su hukunta ni da laifin da ban aikata ba"
Sai da Isah ya gama jawabi, ya kalli baqar fatar nan, ya kalli larabawan nan, ya na jiran ya ji baqar fatar na zuba Hausa, sai ya ga baqar fatan na kallon shi ya ce masa,
"Ana la afham ma taqool" (ban fahimci me ka ke fada ba)
"Bawan Allah me ka ce? Dan girman Allah in ka iya hausa ka yi min mu fahimci juna,yasin ba kaya na bane,"
Tafiyar shi baqar fatar ya yi, Isah na ta kiran shi ya na fadin,
"Malam musulmi fa dan uwan musulmi ne, ka zo ka fassara musu, ba kaya na bane, goro ne kawai nawa"
Qarshe dai dole suka sa Isah yin shiru.
Isah ba baki sai hawaye, dan kuwa ya riga ya san hukuncin masu shigar da ƙwaya musamman manyan miyagun kwaya irin wannan shi ne kisa.
**************************
Hansatu kuwa bayan sun koma gida,hankalin ta kwance ta yi wanka, ta yi wa Ahmad da Bilkisu, Ameenatu ta yi, suka yi alwala, suka shige ciki, sai da suka yi magariba, sannan suka ci abincin da suka je da shi daga gidan Hajiya.
Suka yi hirar su har isha'i, ta riga ta san ba zai kira ta ba kamar wancan karon,amma bata san me ya sa ba, ta nace ta saka rai, ta
Showing 114001 words to 117000 words out of 150481 words
"Sultana ban taba shirka ba, amma ina taimaka wa masu yi, duk abinda mahaifin ki ya buqata da sauran 'Yan siyasa a baya ko mene shi ina samar musu shi, duk da na san tsafi za a yi da abun"
Hawayen ta ne suka qaru, jin cewar har da mahaifin ta a aikata shirka,
"Ka yi istigfar Allah zai amsa, ka yi da kyayyawar niya, Allah zai yafe maka"
"Allah na tuba ka yahe min, Allah ka yahe min manya da qananan zunubbai na, Allah ka yi min rahama, ka cika min buri na,"
"Ameen,"
Kafin bacci ya ɗebe su, sun tattauna akan abubuwa da dama, sun kuma tsara duk wani abu da ya kamata su aikata a gaba, a haka bacci ya dauke su suna manne da junan su.
***************************
Kamar yanda Isah ya yi alqawari, ya siyi goro mai yawan gaske, dan tafiya Makka, wanan karon dubu hamsin casss ya cake wa Hansatu, amma bata ci su a banza ba, sai da ya mori jikin ta da kyau da kyau, dan duk girman ta, da jarumtar ta, sai da ta dinga shiga ruwan zafi, Ita dai ta sawa ran ta, ba zai sake ganin wani rawar kan son shi awajen ta ba, tunda ta yi a baya bai mata amfani ba, sannan ba zai sake ganin murmushin ta ba, tunda a baya sai da ta ce wa audiga bata iya murmushi ba,ta fita iyawa, duk bata samu ribar murmushin ba,hakan kuwa na matuqar damun Isah, kula da cewar ko sau nawa zai neme ta ba zata qi ba,shi ya sa ya ke fanshe haushin rashin sakewar a jikin ta.
Hajiyar Hansatu da Yaya Musa sun yi qoqari sosai wajen ba Isah wasu kudin da zai qara akan jarin shi, sai da ya musu sallama sannan aka bada mota kamar wancan karon aka kai shi airport, wannan karon ko kwalla Hansatu bata yi ba, balle ta koka, Isah kuwa ya ji haushi matuqa, sannan ta ce ba zata yi rakiya ba, a fusace ya fad'a mota, aka tafi kai shi,ko da takoma sai ta ce wa Hajiya ita bata so ta ga ya tafi ya barta, kuka za tai, kuma bata so ta daga masa hankali,dan haka Hajiya bata ce komai ba, sai suka ci gaba da hirar su.
Isah sun isa airport, ya sauke kayan shi da komai, cikin dabarar da suke yi kar a gane goro ne, ya na tsaye wani mutum fari ya tsaya gefen shi, sallama ya masa shi ma ya amsa, sai ya ji maganar kamar ta Inyamuri ko bayerabe,
Mutumin ya fara yi wa Isah magana da turanci, Isah ba turanci, fuska ta muzanta da kunya, sai bawan Allahn ya gane Isah fa wala ingilishi, cikin gurbatacciyar Hausar shi ya ke tambayar Isah, Makka zai je ko Madina in sun isa Saudiya?
"Makka zani"
"Masha Allah, ni ma can nake da zama, ina da gida da iyali a can, kai fa ina ka ke zama?"
"Ni a hotel kawai nake sauka, banda gidan zama,"
"Allah Sarki, ka fad'a min inda ka ke sauka in na samu natsuwa zan neme ka, se ka dawo gida na da zama, tunda duk qasar mu d'aya, in a foreign land in ka ga d'an qasar ku ji ka ke kamar d'an uwanka ne"
Sunan hotel din da yake sauka ya sanar da bawan Allahn nan ya na ta murna, a qalla ba shi ba biyan kudin hotel, zama suka yi tare, suna ta hira, kamar abokan juna, duk inda CCTV camera yake a wajen bawan Allahn nan ya sani, kuma daidai gwargwado juya bayan shi yake, ba ya bari fuskar shi ta hasku, ya yi shiga irin ta larabawa ya saka face mask, se surutu yake wa Isah da gurbatacciyar hausar shi, Isah kuwa banda washe baki ba abinda yake.
Sai da aka shiga jirgi ne suka rabu, saboda wajen zaman su ba daya bane.
Tafiya ta miqa zuwa Saudiya, Isah ba abinda ya ke banda tunanin Hansatu, wannan karon ji yake kamar ya bar wani bangare na jikin shi, qudirtawa ya yi in Allah ya sauke shi lafiya, ita zai fara kira su gaisa.
**********************
A hanyar su ta zuwa garin na Zamfara duk wani motsi na Mubaraka na kan idon Taheer, zuciyar shi kuwa na ta kakkaryewa zuwa qananan pieces ,ya yi zurfi akan son ta ba tare da ya sani ba, wataqila dalilin gano ya na son nata, rabuwar da ta zo musu ba tare da shiri bane, da ya kula ya na son ta tun da, da ya yad'a manufar shi a wajen ta, gashi yanzu lokaci ya qure masa.
Mubaraka ce ta yi qarfin halin yi masa magana, ta ce,
"Yah Taheer akwai damuwa ne?"
Da sauri ya sanya murmushin yaqe ya ci gaba da tuqi, bai ce komai ba, tafiya suke kamar ba zai magana ba, can kamar wanda aka shaqe ya ce,
"Yanzu in kin tafi shikenan? Mantawa zakiyi da mu ko? Ga yaran ki can kin bar su suna ta kuka, ke kad'ai ka lallashin su in su na rikici, sun hi sabawa da ke,gashi zaki tafi ki bar su"
"Yah Taheer ku din wani bangare ne mai girma a rayuwa ta, ba zan taba manta wa da ku ba, ka sani na jima ban ga yayana ba, ina kewar shi sosai, amma in na je na gan su, ai zan koma wajen ku, in Allah ya yarda"
Wani irin murmushi Taheer ya sake, har da sosa kai, murmushin shi ya bawa Mubaraka mamaki, sai ita ma ta fara murmushin, cikin daurewar kai, dan ta kasa fahimtar inda Yah Taheer din ya dosa da wannan bayyanannen farin cikin................
*Allah kai ku lahiya ke dai, mu ai mun gane murmishin meye😂😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 53:
Jefi jefi suke hirar su, cikin nishadi, da kuma sabo, Taheer na matuqar jin dad'i da girmama wannan lokaci da hirar tasu baki daya, domin bai sani ba, ko na qarshe kenan da za su hadu har su yi hira haka, ko kuma akwai rabon haduwar su a gaba.
Sun isa garin zamfara da misalin qarfe 12 na rana, saboda gudu sosai da yake zubawa, hamdala Mubaraka ta yi, sannan ta kalli Taheer, ta na qoqarin motsa baki tai magana ta ga wasu sojoji na nuna ta, amma ba su tsaida motar su ba, sunkuyar da kan ta tayi qasa, dan ta san dalilin da ya sa suke nuna ta, da an basu dokar kama ta, yanzu an janye.
Sai da suka shiga gari sosai, Taheer na qoqarin daukan hanyar dajin nasu Mubaraka ta cire nauyin baki ta ce,
"Yah Taheer Dan Allah tsaya,"
Bai tsaya jin dalilin tsayawar ba, ya samu gefe ya tsaida motar, Sannan ya tattara duk wata nutsuwar shi ya miqa mata a hannun ta, d'an cizon leben ta tayi na qasa, cikin tsoron me zai je ya zo ta ce,
"Dan Allah ka fara kai ni gida wajen su Umma, dan ban sani ba ko Yah Auwal zai bari na je na gan su, dan Allah kar ka qi, in ka qi kai ni na ga Ummana zan yi maka kuka, kuma Yah Auwal zai ga na yi kuka, kuma..."
"Tau ya yi haka nan, ban ce ki bani tsoro ba daga shigowa ta, tau yanzu in munka tai ya ji labari fa? Kin dai san in kin tsira ni ina ruwa ko?"
Cikin zumudi da murna ta ce,
"Ba abinda zai yi maka, Indai na ce ni ta ni nace ka kai ni, Please Yah Taheer ka kai ni naga su Umma" ta qarasa magana cike da shagwaba.
Taheer dai bai so ba, amma an sa shi na dole, tiryan tiryan take nuna hanya, har suka isa, ya na tsaida motar ta fita a guje, ta fad'a gidan,shiru ta ji ba kowa, daga iyayen nasu, har yaran.
Cikin sanyin jiki, ta dinga leqa d'akuna,ta fita, gidan da ke manne da nasu ta shiga, suka gaisa,mutane ne na kirki, masu dattako, tambayar su ta yi inda iyayen ta suke, nan suka sanar da ita Kareeman 'Yabbuga ce ta haihu, yau suna, dan haka su na can gidan Kareema.
Sallama ta musu da godiya ta koma wajen Taheer jiki ba kuzari, idanun ta sun cika da kwalla.
Hakuri ya bata bayan ta masa bayanin komai, ya ce in sun je, ta roqi Auwal, ya san zai kai ta da kan shi.
Hanya suka miqa sai daji.
A can dajin kuwa Sultana da Lawwali sai zumud'in zuwan mubaraka suke, sun yi kwalliya, sun sha ado gwanin ban sha'awa, kamar masu tarbar wani hamshaqin, su Barira da yaran Lawwali kuwa ,sun matsu su ga wace ce wannan yarinyar da ta shiga ran Ogan su? Ya take? Shin ta kai wadda za a gigice da so ko bata kai ba?
Abinci da abun sha, mahallin kwana, da duk abinda za su buqata komai an tanadar musu, su kawai ake jira.
Da misalin qarfe hudu da arba'in su Mubaraka ne a cikin jejin Oga Lawwali, tun daga hanya Mubaraka ta tsure, ganin mutane dauke da makamai, kamar masu zuwa yaqi,Taheer ne ya yi ta kwantar mata da hankali.
Lawwali ya kasa zama, sultana sai dariya take masa,Sultan da ke tsaye ya na kallon su, shi ma murmushi yake ta zabgawa, Lawwali na hango motar su No 4 ya zabura zai yi wajen, Sultana ta d'an kwalla qara kadan, juyawa ya yi ya kalle ta, ya ga ta dafe cikin ta, da sauri ya duqa gaban ta, ya na mata sannu, a lokaci daya kuma ya na juyawa dan ganin rabin ran nashi.
Sultana bata d'aga daga duqawar da ta yi ba sai da ta ga Mubaraka ta fita a motar, cikin washe baki, da murna, Sultana ta kwace hannun ta daga na Lawwali ta kwasa da gudu, ta nufi Mubaraka, suka rungume juna, mamaki da haushi ne suka kama Lawwali, kawai sai ya tsaya ya kama qugu, mutanen wajen kuwa me za su yi banda dariya.
Sultan kuwa har ya na duqawa dan dariya, ga dai Lawwali qatoto, maji da qarfi, amma Sultana yar firit ta masa wayo,Mubaraka gani ta yi ba shi da niyyar zuwa wajen ta, sai ta shanye dariyar ta ta daga murya ta ce,
"Yah Taheer mu juya kawai, ka kaini wajen su Umma na, tunda Yah Auwal din baya son gani na"
Wata harara Lawwali ya zuba mata, sannan ya taka da sauri, Itan ma da sauri ta ke zuwa wajen shi, rungume ta ya yi kamar ba zai rabu da ita ba, Ita kuwa kukan farin ciki ta saka, wani abu ya ji ya tokare masa maqoshin shi, wanda ya ke bayyana tsananin kewar ta da ya yi, ji ya ke dama zai iya kwaranyar da hawaye wataqila da ya ji sauqin abinda yake ji a ran shi,sake qanqame ta ya yi, ya na godewa Allah, da ya dawo masa da ita lafiya.
Sun jima a haka, sannan ya dago da kan ta ya juya ga mutanen da ke wajen, fuskar su dauke da kallo na sha'awar soyayyar da ke tsakanin yaya da qanwar shi.
"Kunga yanda qaunata ta dawo gare ni lahiya? Na muku alqawarin zan maida ku ga iyalin ku lahiya, da yardar Allah, ba zan gaji da neman yahiyar ku a gare ni ba, ku yahe min, ko ba yanzu ba, ko bama tare ne, ku yahe min dan Allah"
Hayaniya ce ta karade wajen, Sultan na gefe ya na murmushin jin dad'in ganin shaquwa da aminci da ke tsakanin Oga da mutanen shi.
Ta gaban shi su Sultana suka wuce, shi ma ya bi bayan su.
Kafin su qarasa ciki Mubaraka ta gaida shi, amsawa ya yi, cikin sakin fuska, sannan ya tambaye ta ya hanya, ta bashi amsa da,
"Alhamdu lilLAAHi"
"To masha Allahu, sannun ku da zuwa"
"Yauwa Muna godiya"
No 4 da Lawwali sun tsaya daga waje, su na tattaunawa, kafin daga baya suyi sallama, ya tafi tsohon dakin shi, da ya samu baqi a ciki, amma still gadon shi na nan, a ciki, ga abinci nan da abun sha an aje masa.
Sai da Mubaraka ta fara wanka, sannan suka hadu dikan su a saman carpet suka ci abinci, su na yi su na hira.
Sultana kan ta ta sallama, ta sani ba zata tab'a samun kalar soyayyar da Lawwali ke wa qanwar shi ba, Mubaraka ta yi gaba, ta na bayan ta, ta yarda da hakan, kuma bai dame ta ba, domin dama kowa da matsayin shi .
Ranar Lawwali ya sha labarin Kano, har tsokanar ta ya soma yi da cewar,
"Ohhh su Barakana daga zuwa Kano a yi watanni, har an koma yin kananci, Sultyna, qaunar nan taki bata ko yadda ba wallah, gani takai yanzu ta zama bakanuwa"
Dariya sukai tayi, ita kuma ta na qoqarin kare kan ta, haka suka yi ta shan hira, tare damurnar dawowar ta lafiya.
*************************
Jirgi ya d'aga sai Saudiya, Isah kuwa wayar shi ya zaro a aljihun gaban rigar shi, ya na ta kallon hotunan Hansatu, wanda ya mata, ta na bacci, da wanda ya mata ta na aiki, duk bata sani ba, sai murmushi ya ke zubawa, ashe akwai ranar da zai kalle ta da soyayya a ciki? Ni kuwa nace ba soyayya ba ce sha'awa ce, ai da can da take son ka san da baka da komai, kai baka so ta ba, sai yanzu da ka ga ita Allah ya mata komai ka ke son ta.
Jirgi ya tsaya a king Fahad international airport, mutane na ta qoqarin sauka, Isah na tafe shima cikin ayari, wayar shi ya mayar a aljihu, ya riqe 'yar qaramar jakar kayan shi,ya sauka.
Wannan bawan Allahn ya gani daga nesa da shi, ya na masa murmushi, tare da yi masa sallama.
Mayar masa da sallamar shi ya yi, ya nufe shi, dan su je su d'auki kayan su, sai bawan Allahn nan ya nuna wa Isah qaramar jakar shi, ya sanar da shi ita kenan yake da, dan haka anan suka yi sallama, ya tafi, Isah kuwa dole sai da ya je daukan manyan jakunkunan da ya isa da su.
Ina can ina kalle kalle Hameeda ta shiga Saudiya (Allah ka amsa ka bama duk wanda be je ba ikon zuwa) sai na ji ihun mutane, larabci na tashi ko ta ina, kafin na koma wajen dan ganin me ke faruwa sai na hango askar sun kewaye Alhaji Isah, Isah ya durqusa qasa ya na rantsuwa tare da baza musu Hausa, ya na bayani ba na shi bane.
Ko da na leqa da kyau, sai na ga wani abu fari tasss a leda guda hudu, da na kasa kunne da kyau, sai na ji ana fad'in koken ne abun, hankali na ya tashi nai baya, ina leqe daga nesa, bawan Allah'n nan na hango cikin tsananin damuwa da b'acin rai ya na kiran
"Shit, shit, this man na mumu, de don catch am"
(Wannan mutumin Wawa ne sun mama shi)
Da sauri ya rataya jakar shi ya bar wajen, a cikin gudu-gudu, sauri-sauri.
Tuni an sanqame Isah, ya na ihu ya na kuka, sai fadi yake ya na kumawa.
"Goro ne kaɗai nawa na rantse, koken din ban san na waye ba, dan Allah ku maida ni Nigeria ba zan sake safarar goron ba,ni Ko zuwa ma ba zan sake yi ba"
Gaba daya fuskar Isah ta sauya, cikin qanqanin lokaci ya zama kamar ba shi ba, saboda shiga tashin hankali.
Ba su tsaya da shi ko ina ba sai wajen ajiye masu manyan laifuka.
Isah na nan na kuka, da roqon gafara, tare da qoqarin bayyana musu gaskiyar shi, amma ba mai sauraron shi, balarabe d'aya aka kawo wanda ya ke dan jin Hausa, duk wani bayani da Isah yake yi, abu dai na komawa kan shi ne, tunda ya kawo goro ta boyayyiyar hanya to tabbas koken tashi ce,
"Innalillahi, yau na shiga uku, na lalace, wai da wane yare kuke so na muku bayani ne, ba tawa bace,"
Wani baqar fata Isah ya gani, da uniform din 'yan sandar qasar, cikin yaqe Isah ya yafice shi, ya na washe baki,
"Yauwaa ga na gida nan, bawan Allah, dan Allah zo kai mana tafinta, ka fada musu goro kawai na kawo, yasin ban san koken din waye ba, ni ma yanda suka gan ta haka na gan ta, dan Allah fassara musu, ni na yarda su karbi goron su zubar, ai dama haka ake yi ko, amma kar su hukunta ni da laifin da ban aikata ba"
Sai da Isah ya gama jawabi, ya kalli baqar fatar nan, ya kalli larabawan nan, ya na jiran ya ji baqar fatar na zuba Hausa, sai ya ga baqar fatan na kallon shi ya ce masa,
"Ana la afham ma taqool" (ban fahimci me ka ke fada ba)
"Bawan Allah me ka ce? Dan girman Allah in ka iya hausa ka yi min mu fahimci juna,yasin ba kaya na bane,"
Tafiyar shi baqar fatar ya yi, Isah na ta kiran shi ya na fadin,
"Malam musulmi fa dan uwan musulmi ne, ka zo ka fassara musu, ba kaya na bane, goro ne kawai nawa"
Qarshe dai dole suka sa Isah yin shiru.
Isah ba baki sai hawaye, dan kuwa ya riga ya san hukuncin masu shigar da ƙwaya musamman manyan miyagun kwaya irin wannan shi ne kisa.
**************************
Hansatu kuwa bayan sun koma gida,hankalin ta kwance ta yi wanka, ta yi wa Ahmad da Bilkisu, Ameenatu ta yi, suka yi alwala, suka shige ciki, sai da suka yi magariba, sannan suka ci abincin da suka je da shi daga gidan Hajiya.
Suka yi hirar su har isha'i, ta riga ta san ba zai kira ta ba kamar wancan karon,amma bata san me ya sa ba, ta nace ta saka rai, ta
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39 Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51