yi Allah ya sa ya fahimci abinda take so ya fahimta......
*Ni ma fata na kenan amarya Sulty*
π π» *A GARIN MU* π π»
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 58:
"Ki shirya gobe ku je ku ga Daddyn ku, ki zauna a can nan da sati guda zan je na dauke ki, mu koma gidan mu"
Da wata iriyar murna ta fad'a jikin shi, ta qanqame shi ta na ihu, cikin hanzari ya daga ta ya na dariya, ya sanya hannun shi ya toshe mata baki, sannan ya sanya yatsan shi guda a kan labban shi da ke murmusawa,
"Shiiiiiiii, so ki ke a ce wani mugunta na ke miki?"
Janye hannun nashi ta yi, ta maida lips din ta, ta sunbace shi sau daya, sannan ta ce,
"Ko ma me zaka min, ko ma me ka min, ni taka ce, kai nawa ne, ina qaunar ka miji na, ina son ka miji na, kai ne abokin rayuwa ta har abada"
Shiru ya yi, ya ja ta ta zauna a jikin shi da kyau, sannan ya kama hannayen ta ya na wasa da su, kan ta ta Ιora a qirjin shi ta na sauraran bugun zuciyar shi, a hankali cikin sanyin jiki da murya ya ce,
"Sultyna sai yanzu na gano wani abu, wato duniyar ga aikin banza ce wallah, amma muke ta aikata sabon Allah, da ace na mutu ina kisan mutane fa? Da ace na mutu ina jagorantar ta'addanci da fasikanci fa? Da shi kenan wuta zani ko? da shi kenan ni rayuwa ta na zo a wahale zan koma a wahale, Sultana ba na jin na samu cikakke kuma ingantaccen jin dad'i, nutsuwa da kwanciyar hankali tunda an ka haihe ni na shekara hudu a duniya nake faman shan wahala, daga wannan na fad'a wancan, kullum cikin damuwa nake, shi kan shi farin cikin da ni ke ganin ina samu, ta hanyar shaye shaye, zunubi ne, kuma wahala ce wallah, indai har kin tabbata Allah zai yahe min duk kalar abinda na aikata, ko yanzu mutuwa ta risken ba ni da baqin ciki"
Da sauri ta kalle shi, tare da kada masa kan ta, murya na rawa ta ce,
"Auwal na tabbatar , kuma na yi imani da Allah, Allah ya yafe maka, domin shi ya yi alqawalin yafewa duk wanda ya nemi gafarar shi, ka kuma nemi gafarar shi, ina kyautata wa Allah zato, amma ba daidai bane ka dinga tunanin mutuwa ta dauke ka, in mutuwa ta dauke ka na zauna da wa?"
Hawaye ne suka fara zuba daga idanun ta, ita kan ta ba za ta iya tantance kalar soyayyar da take wa Lawwali ba, amma ta na da tabbacin duk sanda aka ce yau ba shi ba zata iya ci gaba da rayuwa mai kyau ba.
"Dan Allah ka dena irin maganar nan, ba na so"
"To ban koma wa, shi kenan?"
"Eh shi kenan,"
"To wace hira za mu yi?"
"Ina zuwa,"
Tashi ta yi ta tura ni waje, ta rufe musu qofar su, cikin jin haushin Sultana, na bar wajen ban tsaya a ko ina ba sai d'akin Mubaraka, ta na zaune, ta na shan ice cream, Taheer ya yi sallama, d'aga kai ta yi, ta kalle shi, dan ya riga ya shiga tun kafin ta amsa masa sallamar shi, balle ya jira ta bashi izinin shiga,
"Yah Taheer lafiya dai ko?"
"Lahiya qalou Mubaraka, sai dai abinda na ke tahe da shi, shi na iya jaddada zaman lahiya ko samar da rashin ta"
Cike da mamakin kalaman shi ta miqe ta daura zani a saman qaramin wandon dake jikin ta, Taheer kuwa ko irin d'an kauda kan nan, ta na gama daurawa ta zauna a bakin katifar dakin, ta bashi dukkan nutswar ta, dan sauraran abinda ya ke tafe da shi,
"Mubaraka, kin sani, na dauke ki kamar qauna ta ko?"
Daga kan ta tayi, cikin gasgata maganar shi,
"Mubaraka son da ni kai miki a matsayin qauna, ya rikid'e ya koma soyayyar da na ke hwatan ta kai mu ga yin aure, amma har sai kin amince, zan sanar da Oga da Fateema, amma in ki ka tabbatar min da baki so na, gobe zan koma Kano, na hakura da ke har abada"
Wani irin nauyi ta ji Taheer ya dora Mata akai, wanda ta rasa ma na mene ne, shin kunyar shi take ji, ko ganin rashin dacewa ya ce ya na son ta ne ya sa ta jin nauyin shi? Bakin ta na so ya fadi abinda ke zuciyar ta amma ya kasa furta komai, gyara zaman ta tayi,cikin sanya jarumta a Muryar ta ta ce,
"Yah Taheer, ba zan boye maka komai ba, dan in na boye maka ban kyauta ba, saboda matsayin da na baka na yaya na, Yah Taheer ina matuqar Son ka amma a matsayin yaya na, da ace ba Aunty Fateema ko ba na maka so irin na soyayya, zan aure ka, saboda ban ga wani abun kushewa a tare da kai ba, amma ba zan taba iya auren mijin auty Fateema ba, ana barin halal dan kunya in ji bahaushe, jin ta ni kai kamar uwa daya Uba daya muke da ita, dan Allah Yah Taheer ka yi hankuri, wannan maganar ba mai yiwa bace"
Kalaman ta sun masa zafi a zuciya, amma ya fuskanci abinda take nufi, ta kuma fad'a masa iyakar gaskiyar ta, ba boye boye, ya ji dad'in yanda suka fahimci juna shi da ita, ko ba komai magana bata je wajen Oga ba, ballanta zumuncin da aka fara ya rushe, ko kuma ya qara kulluwa.
"Na fahimce ki, kuma na gode da hwada min gaskiya da kin ka yi, baki boye ba,amma dai ke san ya zama dole ki hidda miji ko? Dan kuwa girma d'ai ki kai, bai kamata ace har yanzu ba ki da wanda ki ke so ba"
Rufe fuskar ta tayi, shi kuma ya na kallon ta, da wani irin yanayin da bai san ya zai fassara shi ba, ya sani ba hurumin shi bane, amma tunda shi be samu ba, bari ya taya Sultan campaign,
"Ya kin ka ruhe huska? Ki dauke ni kamar Aunty Fateema, ki sanar da ni ,ko dai can Kano mun yi suruki na?"
Da sauri ta bude ido ta na kada kai alamar ah ah.
"To a ina ne?"
"Yah Taheer ni kunya nake ji"
Sake rufe fuskar ta tayi, sannan ta juya bayan ta,
"To ko na kira maki fateema ne sai ki sanar da ita, ko kuma na kira Oga shi kenan ma bari na kira Oga"
Miqewa ya yi kamar zai fita, da sauri ta juya ta ce,
"Yah Sultan na ke so"
Taheer ji ya yi kamar ta soka masa wuqa a qahon zuciya, ya jima a tsaye bai juya ba,ita ma ta na can tsaye ta rufe fuska cikin jin kunya, Taheer kuwa cikin ran shi ya ce,
'shegen yaro ya yi nasarar sace Mata zuciya ba tare da ya sha wahala ba,'
A zahiri kuwa cewa ya yi,
"Lallai na taya ki murnar samun saurayi nagari, amma kina ganin shi ya na son ki?"
Ya fadi haka ne dan ya ji me za ta ce,zama ta yi ta tankwashe qafar ta, ta tura baki, cikin shagwaba ta ce,
"Yah Taheer ba zai taba so na ba, ni na sani, kar ka manta hwa ni diyan tallaka nike, shi kuwa mahaifan shi manya na,sannan yarinya nike qarama, kuma ka san dai yanda ya waye, ya yi karatu a qasar waje ba zai auri baqar mace kamar ni ba, shi ya sa ma tun sanda na fara ganin shi, na ji ina son shi nake addu'a Allah ya zaba min abinda shike alkhairi"
"Ba zan so sanar dake wani sirri ba, amma ina maki hwatan alkhairi, sannan ina miki albishir da samun kyakkyawar kyauta kahin ta riske ki"
Cikin rudanin da ya jefa ta da kalaman shi ta kalle shi, ta ce,
"Yah Taheer mi ka ke nuhi?"
"Babu komi, lokaci zai sanar dake komai, bari na tai na hwara shiri, gobe zan koma"
Sabo turken wawa, tabbas Mubaraka ta ji dad'in zama da su Taheer,dan haka sai ta ji wata kewar shi mai girma ta mamaye zuciyar ta, nan da nan idanun ta suka fara zubar da hawaye,
"Yah Taheer ba na so ka koma ka barmu, dama ka dawo da su Aunty Fateema nan garin,"
"Ki dena kuka dan Allah, yanzu Oga yaggane ki ki na kuka ai bone ya ci ni,kar ki damu kuma, za mu zanka zuwa akai akai,ga waya, duk dai, ai ba a rabu ba, bari in tai na sanar da oga batun tahiya ta gobe"
"To Yah Taheer, Allah ya kaimu goben, bari na hada maka saqo ka kaiwa yarana"
"To shi kenan, sai da swahe,"
"Allah shi kai mu"
Daga nan dakin Oga ya je ya kwankwasa ya jima tsaye kafin a bude, a nan ya sanar da Oga duk tattaunawar da sukai da Mubaraka, amma bai fada masa maganar ta na son Sultan ba,sannan ya sanar da shi tafiyar shi a gobe,Lawwali ma ya so a ce ta amince da Taheer, dan ya na son Taheer a duk yaran shi,amma tunda mubaraka ta ce bata yi, ba zai tursasa ta ba, duk abinda take so shi ma shi yake so.
Daga nan dakin Sultan ya nufa, zaune ya gan shi saman sallaya, da alama sallah ya idar, ko kuma karatun Alkur'ani, sallama suka yi wa junan su, sannan Taheer ya samu waje ya zauna.
"Sultan ni hwa gobe zan koma Kano, saboda na gabatar da kai na wajen Mubaraka, ta ce bata yi,ban ga ta zama ba, zan koma ga iyali na,na zo ne na maka sallama, kuma na baka shawara, ka gaggauta sanar da Mubaraka soyayyar ka, dan kuwa yarinya ce, daga sanda kun ka bar dajin ga ta shiga gari, ta samu wani, sai dai na zo maka Jaje,"
Siririyar dariya Sultan ya yi, sannan ya ce,
"Kar ka damu, in shaa Allahu ka na daga cikin manyan abokan ango, na gode da shawarar ka, Allah kuma ya sa haka shi ne yafi alkhairi, Allah shi maida ka gida lahiya"
"Ameen, na gode, sai da swahe"
"Allah ya tashe mu lahiya"
Bayan fitar Taheer daki ya koma, ya gyara kayan shi,Sultan kuwa kasa kwanciya ya yi, ya rasa ta ya zai ya tunkari Mubaraka da maganar soyayya, shi dai be taba budurwa ba, bai san ya ze yi ba, ko Sultana zai sa ta sanar da ita? Kaiii inaa, ko Lawwali zai gaya wa direct??
Mubaraka ita ma da tunanin Sultan ta kwana cikin ran ta, tun daga ranar da suka fara zuwa ta Ιora idon ta akan shi, ta ga ya qara haske, da kwarjini, akan sanin da ta masa a baya, sai ta ji qaunar shi ta kama ta, amma haka ta daure bata nuna ba, kasancewar ta sa wa ran ta cewa ya fi qarfin ta.
Amma daga baya ta ga wasu alamu da ke mata nuni da cewa wataqila shi ma ya na son ta, duk da dai ba ta tabbatar ba.
********
Washegari kuwa Sultana da Murna ta tashi, da asuba ta yi wanka, ta shirya, Lawwali na ganin zumudin da take ya kira ta, ta je gaban shi, ta na dariya, zama yayi ya na nannade hannun rigar shi, wanda hakan ya zamar masa kamar wata al'ada,
"Shin ba ki bari a d'aura auren su Barira sannan ku tai?"
Dafe goshin ta ta yi, sannan ta ce,
"Kashhh, ka ko ga na mance wallah, qarhe goma kacce limaman da kun ka samo za a kawo su ko? To wa zai tsaya a matsayin waliyyin su Bariran?"
"Wai yaran ga sun ce ni suka so, ni Ko ban san wad-da ake ba, kunya suke son bani cikin mutane"
Dariya sosai Sultana ke yi, saboda yanda ta ga damuwa sosai a fuskar shi, to shi daurin auren wata ibada ce me wahala? An bayar na karba ne fa, tsokanar shi ta dinga yi, ya na daure fuska, dan shi da gaske yake bai san ya ake yi ba.
Da misalin bakwai daidai, matasan suka shiga gari, dan shigo da Limamai guda biyar da suka roqa arziki, za su daura musu aure, cikin rashin sanin ina za a je limaman suka amince, sai da aka dakko hanya suka ga ana nausawa daji hankulan su ya tashi.
Wasu masu raunin zuciyar har da kuka.
Ko da aka iso, suka ga waje masha Allah, an gyare shi, ya yi tass, kowa cikin kwalliya mazan da matan, ga abinci da abun sha, sai hankula su ya fara kwanciya, amma sun dasa wa zuqatan su ayar tambayar me ya kawo mutane cikin wannan surquqin daji?
Kamar yanda Lawwali ya ce, da misalin qarfe goma na safiya, aka daura auren mutum goma sha huΙu,a kan sadaki dubu talatin talatin.
Lawwali ana gama daura auren ya bar wajen, wani waje ya nufa da ba mutane ya zauna shi kadai, ya na hawaye, tunanin rayuwar shi tun daga farkon ta zuwa yanzu yake yi,daga gobe zai bar wannan dajin ya koma zama a cikin gari kamar kowanne mutum mai 'yan ci, sai yanzu ya gane su aka sa a kurkuku, ba su suka sa a kurkuku ba, tunani ya ke, shin tuban da ya yi ya karbu kuwa? Ko dai har yanzu Allah na hushi da shi? Abubuwan da ya aikata manya ne, masu girma ne,tunanin kalaman Mubarakan shi ya yi, a duk sanda take masa nasiha, ta na sanar da shi cewar,
'Yah Auwal ka tuba ka dena wanga harkar, ka samu aiki na halal ka yi, in ka tuba Allah mai yawan gafara ne, mai son bayin shi masu yawan tuba ne, kar ka yanke tsammani daga rahamar Allah'
Nan da nan ya ji wani qarfin imani da Allah na ratsa shi, ya na jin tabbas Indai tuba da yarda da Allah na sa Allah Ya yafewa bawan shi, to tabbas ya na saka rai Allah ya yafe masa.
Ya na nan zaune ya ji kan reshen da yake kai ya yi qasa,alamar an zauna, kafin ya duba gefen shi qamshin ta ya sanar da shi wace ce, kwantar da kan ta tayi a kafadar shi tare da zira hannun ta a nashi.
Za ta yi magana ya ce,
"Shiiii, kawai mu yi shiru,mu saurari iska, da karar busassun ganyayyaki, mu saurari kukan tsuntsaye da bugun zuciyar mu, ina so na zauna da ke a haka na wasu mintuna kahin ku tahi"
Kissing din hannun shi ta yi, ta sake qanqame hannun, ta kwanta a jikin shi sukai shiru.
Suna nan zaune Mubaraka ta same su, murmushi ta yi, da ta ji sun yi shiru, ba abinda suke fadi, manne da junan su, a hankali ta taka, duk da qarar ganye da ke qoqarin tona asirin zuwan ta, ta na isa daf da su ta sanya hannayen ta ta rungume su a tare ta baya, Lawwali lumshe ido ya yi, sannan ya kama hannun ta ta gefe ya sumbaci yatsun ta,
"Barakana ya akai kin ka san muna nan?"
"Duba ku muke kawai sai na samu nasarar ganin ku anan"
Murmushi suka yi, a tare dukan su,
"Yah Sultan na jiran ki ku tai"
Kamo su duka biyun Lawwali ya yi, ya rungume su a jikin shi da kyau, suka fara takawa a hankali,sannan ya yi kissing goshin kowaccen su, ya ce,
"Ina son ku, ina qaunar ku, ku ne rayuwa ta, ina hwata mu dawwama a tare cikin hwarin ciki, duk da na san hakan ba lallai shi kasance ba, dan kuwa a rayuwa ta kaff na koyi wani abu sabo, ka na naka shirin duniyar ne, Allah shi na maka shirin komawa gare shi,kai d'an Adam, ba zaka taba gama naka shiri ba, shi ko Allah ya gama nashi Shirin akan ka Dan Adam,lokaci ne kawai da ya yi zai kire ka gare shi, kuma dole ka amsa kira nai, ina muku nasiha ku had'a kan ku, ku so junan ku, kuma ku riqe gaskiya da amana, kar ku ha'inci kowa a rayuwa, kuma ku nemi sanin Allah kahin ku bauta masa, da ace nasan Allah yanda ya kamata, da duk abinda ya hwaru bai hwaru ba, amma sai na aje neman ilimin sanin Allah, na nemi duniya, ina roqon Allah ya bar mu tare har a aljanna"
"Ameeen Yah Auwal /Auwal"
Suka hada baki suka fada, Lawwali ne ya sake Sultana ya dan tura baki,
"Ni dai gaskiya Sultyna ban yarda ba, wai shin ke ko dan sweetheart dinnan ko dan honey din nan baki iya ce min?"
Haba me za su yi banda dariya, shi kuwa tafiyar shi ya fara, ya na ta fadan rashin jin dad'in shi akan kiran shi da Auwal da Sultana ke yi, ba dan sunan soyayyar nan.
Bin shi ta yi da gudu, dan ya kusan isa filin wajen nasu, ta kama hannun shi ta ce,
"Zan fada maka wani suna mai daaadii, amma ba yanzu ba, sai mun koma gidan mu"
"Ni dai yanzu nake so"
"Ah ahh ba yanzu ba"
"To ke Aunty Sultana ki sanar da shi mana, ba a fa jinkirta bayyana soyayya, sai wata ta kwace miki shi"
Kukan shagwaba Sultana ta saka, ta na nuna Mubaraka,
"Ka gan ta ko? Har ta hwara yi min fatan kishiya ko shekara ban yi ba"
Dariya kowa ya ke yi a wajen,Sultan kuwa hankalin shi ya tashi, dan maganar da Mubaraka ta yi sai ya ji kamar da shi take, duk da bai ga alama ba,abinda bai sani ba kuwa shi ne, Mubaraka da shi take, amma ta yi kamar bata san ma ya na wajen ba, ta na so ta san shin hasashen ta gaskiya ne? Ya na son ta ko dan ta na son shi ne ya sa take ganin kamar ya na son ta?
Sallama Lawwali da Taheer suka yi, Taheer na qoqarin barin motar Mubaraka a nan, Lawwali ya ce ya je da ita, ya dinga kai yara makaranta, godiya ya dinga yi sosai, sannan ya cire yar qaramar jakar shi daga motar da za akai shi tasha ya mayar a wadda suka zo da ita.
Sallama ya dinga yi da mutanen wajen d'aya bayan d'aya,sai da ya zo kan Sultan ya rage murya ya ce,
"Kar ka tsaya kallon ruwa kwado ya maka qahwa wallah"
Kada kai Sultan ya yi, cikin yaqe, dan gaba d'aya hankalin shi ya tashi, ga dai Mubaraka ba wata babba ba, amma kwarjinin ta ya cika masa ido matuqa........
*Washhh na gaji,amma ya kuke gani mutanen kirki, shin ya kamata Sultan ya bayyana soyayyar shi a dajin Oga, ko kuma ya bari sai sun shaqi iskar gari???*
π π» *A GARIN MU* π π»
BY
Showing 126001 words to 129000 words out of 150481 words
*Ni ma fata na kenan amarya Sulty*
π π» *A GARIN MU* π π»
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 58:
"Ki shirya gobe ku je ku ga Daddyn ku, ki zauna a can nan da sati guda zan je na dauke ki, mu koma gidan mu"
Da wata iriyar murna ta fad'a jikin shi, ta qanqame shi ta na ihu, cikin hanzari ya daga ta ya na dariya, ya sanya hannun shi ya toshe mata baki, sannan ya sanya yatsan shi guda a kan labban shi da ke murmusawa,
"Shiiiiiiii, so ki ke a ce wani mugunta na ke miki?"
Janye hannun nashi ta yi, ta maida lips din ta, ta sunbace shi sau daya, sannan ta ce,
"Ko ma me zaka min, ko ma me ka min, ni taka ce, kai nawa ne, ina qaunar ka miji na, ina son ka miji na, kai ne abokin rayuwa ta har abada"
Shiru ya yi, ya ja ta ta zauna a jikin shi da kyau, sannan ya kama hannayen ta ya na wasa da su, kan ta ta Ιora a qirjin shi ta na sauraran bugun zuciyar shi, a hankali cikin sanyin jiki da murya ya ce,
"Sultyna sai yanzu na gano wani abu, wato duniyar ga aikin banza ce wallah, amma muke ta aikata sabon Allah, da ace na mutu ina kisan mutane fa? Da ace na mutu ina jagorantar ta'addanci da fasikanci fa? Da shi kenan wuta zani ko? da shi kenan ni rayuwa ta na zo a wahale zan koma a wahale, Sultana ba na jin na samu cikakke kuma ingantaccen jin dad'i, nutsuwa da kwanciyar hankali tunda an ka haihe ni na shekara hudu a duniya nake faman shan wahala, daga wannan na fad'a wancan, kullum cikin damuwa nake, shi kan shi farin cikin da ni ke ganin ina samu, ta hanyar shaye shaye, zunubi ne, kuma wahala ce wallah, indai har kin tabbata Allah zai yahe min duk kalar abinda na aikata, ko yanzu mutuwa ta risken ba ni da baqin ciki"
Da sauri ta kalle shi, tare da kada masa kan ta, murya na rawa ta ce,
"Auwal na tabbatar , kuma na yi imani da Allah, Allah ya yafe maka, domin shi ya yi alqawalin yafewa duk wanda ya nemi gafarar shi, ka kuma nemi gafarar shi, ina kyautata wa Allah zato, amma ba daidai bane ka dinga tunanin mutuwa ta dauke ka, in mutuwa ta dauke ka na zauna da wa?"
Hawaye ne suka fara zuba daga idanun ta, ita kan ta ba za ta iya tantance kalar soyayyar da take wa Lawwali ba, amma ta na da tabbacin duk sanda aka ce yau ba shi ba zata iya ci gaba da rayuwa mai kyau ba.
"Dan Allah ka dena irin maganar nan, ba na so"
"To ban koma wa, shi kenan?"
"Eh shi kenan,"
"To wace hira za mu yi?"
"Ina zuwa,"
Tashi ta yi ta tura ni waje, ta rufe musu qofar su, cikin jin haushin Sultana, na bar wajen ban tsaya a ko ina ba sai d'akin Mubaraka, ta na zaune, ta na shan ice cream, Taheer ya yi sallama, d'aga kai ta yi, ta kalle shi, dan ya riga ya shiga tun kafin ta amsa masa sallamar shi, balle ya jira ta bashi izinin shiga,
"Yah Taheer lafiya dai ko?"
"Lahiya qalou Mubaraka, sai dai abinda na ke tahe da shi, shi na iya jaddada zaman lahiya ko samar da rashin ta"
Cike da mamakin kalaman shi ta miqe ta daura zani a saman qaramin wandon dake jikin ta, Taheer kuwa ko irin d'an kauda kan nan, ta na gama daurawa ta zauna a bakin katifar dakin, ta bashi dukkan nutswar ta, dan sauraran abinda ya ke tafe da shi,
"Mubaraka, kin sani, na dauke ki kamar qauna ta ko?"
Daga kan ta tayi, cikin gasgata maganar shi,
"Mubaraka son da ni kai miki a matsayin qauna, ya rikid'e ya koma soyayyar da na ke hwatan ta kai mu ga yin aure, amma har sai kin amince, zan sanar da Oga da Fateema, amma in ki ka tabbatar min da baki so na, gobe zan koma Kano, na hakura da ke har abada"
Wani irin nauyi ta ji Taheer ya dora Mata akai, wanda ta rasa ma na mene ne, shin kunyar shi take ji, ko ganin rashin dacewa ya ce ya na son ta ne ya sa ta jin nauyin shi? Bakin ta na so ya fadi abinda ke zuciyar ta amma ya kasa furta komai, gyara zaman ta tayi,cikin sanya jarumta a Muryar ta ta ce,
"Yah Taheer, ba zan boye maka komai ba, dan in na boye maka ban kyauta ba, saboda matsayin da na baka na yaya na, Yah Taheer ina matuqar Son ka amma a matsayin yaya na, da ace ba Aunty Fateema ko ba na maka so irin na soyayya, zan aure ka, saboda ban ga wani abun kushewa a tare da kai ba, amma ba zan taba iya auren mijin auty Fateema ba, ana barin halal dan kunya in ji bahaushe, jin ta ni kai kamar uwa daya Uba daya muke da ita, dan Allah Yah Taheer ka yi hankuri, wannan maganar ba mai yiwa bace"
Kalaman ta sun masa zafi a zuciya, amma ya fuskanci abinda take nufi, ta kuma fad'a masa iyakar gaskiyar ta, ba boye boye, ya ji dad'in yanda suka fahimci juna shi da ita, ko ba komai magana bata je wajen Oga ba, ballanta zumuncin da aka fara ya rushe, ko kuma ya qara kulluwa.
"Na fahimce ki, kuma na gode da hwada min gaskiya da kin ka yi, baki boye ba,amma dai ke san ya zama dole ki hidda miji ko? Dan kuwa girma d'ai ki kai, bai kamata ace har yanzu ba ki da wanda ki ke so ba"
Rufe fuskar ta tayi, shi kuma ya na kallon ta, da wani irin yanayin da bai san ya zai fassara shi ba, ya sani ba hurumin shi bane, amma tunda shi be samu ba, bari ya taya Sultan campaign,
"Ya kin ka ruhe huska? Ki dauke ni kamar Aunty Fateema, ki sanar da ni ,ko dai can Kano mun yi suruki na?"
Da sauri ta bude ido ta na kada kai alamar ah ah.
"To a ina ne?"
"Yah Taheer ni kunya nake ji"
Sake rufe fuskar ta tayi, sannan ta juya bayan ta,
"To ko na kira maki fateema ne sai ki sanar da ita, ko kuma na kira Oga shi kenan ma bari na kira Oga"
Miqewa ya yi kamar zai fita, da sauri ta juya ta ce,
"Yah Sultan na ke so"
Taheer ji ya yi kamar ta soka masa wuqa a qahon zuciya, ya jima a tsaye bai juya ba,ita ma ta na can tsaye ta rufe fuska cikin jin kunya, Taheer kuwa cikin ran shi ya ce,
'shegen yaro ya yi nasarar sace Mata zuciya ba tare da ya sha wahala ba,'
A zahiri kuwa cewa ya yi,
"Lallai na taya ki murnar samun saurayi nagari, amma kina ganin shi ya na son ki?"
Ya fadi haka ne dan ya ji me za ta ce,zama ta yi ta tankwashe qafar ta, ta tura baki, cikin shagwaba ta ce,
"Yah Taheer ba zai taba so na ba, ni na sani, kar ka manta hwa ni diyan tallaka nike, shi kuwa mahaifan shi manya na,sannan yarinya nike qarama, kuma ka san dai yanda ya waye, ya yi karatu a qasar waje ba zai auri baqar mace kamar ni ba, shi ya sa ma tun sanda na fara ganin shi, na ji ina son shi nake addu'a Allah ya zaba min abinda shike alkhairi"
"Ba zan so sanar dake wani sirri ba, amma ina maki hwatan alkhairi, sannan ina miki albishir da samun kyakkyawar kyauta kahin ta riske ki"
Cikin rudanin da ya jefa ta da kalaman shi ta kalle shi, ta ce,
"Yah Taheer mi ka ke nuhi?"
"Babu komi, lokaci zai sanar dake komai, bari na tai na hwara shiri, gobe zan koma"
Sabo turken wawa, tabbas Mubaraka ta ji dad'in zama da su Taheer,dan haka sai ta ji wata kewar shi mai girma ta mamaye zuciyar ta, nan da nan idanun ta suka fara zubar da hawaye,
"Yah Taheer ba na so ka koma ka barmu, dama ka dawo da su Aunty Fateema nan garin,"
"Ki dena kuka dan Allah, yanzu Oga yaggane ki ki na kuka ai bone ya ci ni,kar ki damu kuma, za mu zanka zuwa akai akai,ga waya, duk dai, ai ba a rabu ba, bari in tai na sanar da oga batun tahiya ta gobe"
"To Yah Taheer, Allah ya kaimu goben, bari na hada maka saqo ka kaiwa yarana"
"To shi kenan, sai da swahe,"
"Allah shi kai mu"
Daga nan dakin Oga ya je ya kwankwasa ya jima tsaye kafin a bude, a nan ya sanar da Oga duk tattaunawar da sukai da Mubaraka, amma bai fada masa maganar ta na son Sultan ba,sannan ya sanar da shi tafiyar shi a gobe,Lawwali ma ya so a ce ta amince da Taheer, dan ya na son Taheer a duk yaran shi,amma tunda mubaraka ta ce bata yi, ba zai tursasa ta ba, duk abinda take so shi ma shi yake so.
Daga nan dakin Sultan ya nufa, zaune ya gan shi saman sallaya, da alama sallah ya idar, ko kuma karatun Alkur'ani, sallama suka yi wa junan su, sannan Taheer ya samu waje ya zauna.
"Sultan ni hwa gobe zan koma Kano, saboda na gabatar da kai na wajen Mubaraka, ta ce bata yi,ban ga ta zama ba, zan koma ga iyali na,na zo ne na maka sallama, kuma na baka shawara, ka gaggauta sanar da Mubaraka soyayyar ka, dan kuwa yarinya ce, daga sanda kun ka bar dajin ga ta shiga gari, ta samu wani, sai dai na zo maka Jaje,"
Siririyar dariya Sultan ya yi, sannan ya ce,
"Kar ka damu, in shaa Allahu ka na daga cikin manyan abokan ango, na gode da shawarar ka, Allah kuma ya sa haka shi ne yafi alkhairi, Allah shi maida ka gida lahiya"
"Ameen, na gode, sai da swahe"
"Allah ya tashe mu lahiya"
Bayan fitar Taheer daki ya koma, ya gyara kayan shi,Sultan kuwa kasa kwanciya ya yi, ya rasa ta ya zai ya tunkari Mubaraka da maganar soyayya, shi dai be taba budurwa ba, bai san ya ze yi ba, ko Sultana zai sa ta sanar da ita? Kaiii inaa, ko Lawwali zai gaya wa direct??
Mubaraka ita ma da tunanin Sultan ta kwana cikin ran ta, tun daga ranar da suka fara zuwa ta Ιora idon ta akan shi, ta ga ya qara haske, da kwarjini, akan sanin da ta masa a baya, sai ta ji qaunar shi ta kama ta, amma haka ta daure bata nuna ba, kasancewar ta sa wa ran ta cewa ya fi qarfin ta.
Amma daga baya ta ga wasu alamu da ke mata nuni da cewa wataqila shi ma ya na son ta, duk da dai ba ta tabbatar ba.
********
Washegari kuwa Sultana da Murna ta tashi, da asuba ta yi wanka, ta shirya, Lawwali na ganin zumudin da take ya kira ta, ta je gaban shi, ta na dariya, zama yayi ya na nannade hannun rigar shi, wanda hakan ya zamar masa kamar wata al'ada,
"Shin ba ki bari a d'aura auren su Barira sannan ku tai?"
Dafe goshin ta ta yi, sannan ta ce,
"Kashhh, ka ko ga na mance wallah, qarhe goma kacce limaman da kun ka samo za a kawo su ko? To wa zai tsaya a matsayin waliyyin su Bariran?"
"Wai yaran ga sun ce ni suka so, ni Ko ban san wad-da ake ba, kunya suke son bani cikin mutane"
Dariya sosai Sultana ke yi, saboda yanda ta ga damuwa sosai a fuskar shi, to shi daurin auren wata ibada ce me wahala? An bayar na karba ne fa, tsokanar shi ta dinga yi, ya na daure fuska, dan shi da gaske yake bai san ya ake yi ba.
Da misalin bakwai daidai, matasan suka shiga gari, dan shigo da Limamai guda biyar da suka roqa arziki, za su daura musu aure, cikin rashin sanin ina za a je limaman suka amince, sai da aka dakko hanya suka ga ana nausawa daji hankulan su ya tashi.
Wasu masu raunin zuciyar har da kuka.
Ko da aka iso, suka ga waje masha Allah, an gyare shi, ya yi tass, kowa cikin kwalliya mazan da matan, ga abinci da abun sha, sai hankula su ya fara kwanciya, amma sun dasa wa zuqatan su ayar tambayar me ya kawo mutane cikin wannan surquqin daji?
Kamar yanda Lawwali ya ce, da misalin qarfe goma na safiya, aka daura auren mutum goma sha huΙu,a kan sadaki dubu talatin talatin.
Lawwali ana gama daura auren ya bar wajen, wani waje ya nufa da ba mutane ya zauna shi kadai, ya na hawaye, tunanin rayuwar shi tun daga farkon ta zuwa yanzu yake yi,daga gobe zai bar wannan dajin ya koma zama a cikin gari kamar kowanne mutum mai 'yan ci, sai yanzu ya gane su aka sa a kurkuku, ba su suka sa a kurkuku ba, tunani ya ke, shin tuban da ya yi ya karbu kuwa? Ko dai har yanzu Allah na hushi da shi? Abubuwan da ya aikata manya ne, masu girma ne,tunanin kalaman Mubarakan shi ya yi, a duk sanda take masa nasiha, ta na sanar da shi cewar,
'Yah Auwal ka tuba ka dena wanga harkar, ka samu aiki na halal ka yi, in ka tuba Allah mai yawan gafara ne, mai son bayin shi masu yawan tuba ne, kar ka yanke tsammani daga rahamar Allah'
Nan da nan ya ji wani qarfin imani da Allah na ratsa shi, ya na jin tabbas Indai tuba da yarda da Allah na sa Allah Ya yafewa bawan shi, to tabbas ya na saka rai Allah ya yafe masa.
Ya na nan zaune ya ji kan reshen da yake kai ya yi qasa,alamar an zauna, kafin ya duba gefen shi qamshin ta ya sanar da shi wace ce, kwantar da kan ta tayi a kafadar shi tare da zira hannun ta a nashi.
Za ta yi magana ya ce,
"Shiiii, kawai mu yi shiru,mu saurari iska, da karar busassun ganyayyaki, mu saurari kukan tsuntsaye da bugun zuciyar mu, ina so na zauna da ke a haka na wasu mintuna kahin ku tahi"
Kissing din hannun shi ta yi, ta sake qanqame hannun, ta kwanta a jikin shi sukai shiru.
Suna nan zaune Mubaraka ta same su, murmushi ta yi, da ta ji sun yi shiru, ba abinda suke fadi, manne da junan su, a hankali ta taka, duk da qarar ganye da ke qoqarin tona asirin zuwan ta, ta na isa daf da su ta sanya hannayen ta ta rungume su a tare ta baya, Lawwali lumshe ido ya yi, sannan ya kama hannun ta ta gefe ya sumbaci yatsun ta,
"Barakana ya akai kin ka san muna nan?"
"Duba ku muke kawai sai na samu nasarar ganin ku anan"
Murmushi suka yi, a tare dukan su,
"Yah Sultan na jiran ki ku tai"
Kamo su duka biyun Lawwali ya yi, ya rungume su a jikin shi da kyau, suka fara takawa a hankali,sannan ya yi kissing goshin kowaccen su, ya ce,
"Ina son ku, ina qaunar ku, ku ne rayuwa ta, ina hwata mu dawwama a tare cikin hwarin ciki, duk da na san hakan ba lallai shi kasance ba, dan kuwa a rayuwa ta kaff na koyi wani abu sabo, ka na naka shirin duniyar ne, Allah shi na maka shirin komawa gare shi,kai d'an Adam, ba zaka taba gama naka shiri ba, shi ko Allah ya gama nashi Shirin akan ka Dan Adam,lokaci ne kawai da ya yi zai kire ka gare shi, kuma dole ka amsa kira nai, ina muku nasiha ku had'a kan ku, ku so junan ku, kuma ku riqe gaskiya da amana, kar ku ha'inci kowa a rayuwa, kuma ku nemi sanin Allah kahin ku bauta masa, da ace nasan Allah yanda ya kamata, da duk abinda ya hwaru bai hwaru ba, amma sai na aje neman ilimin sanin Allah, na nemi duniya, ina roqon Allah ya bar mu tare har a aljanna"
"Ameeen Yah Auwal /Auwal"
Suka hada baki suka fada, Lawwali ne ya sake Sultana ya dan tura baki,
"Ni dai gaskiya Sultyna ban yarda ba, wai shin ke ko dan sweetheart dinnan ko dan honey din nan baki iya ce min?"
Haba me za su yi banda dariya, shi kuwa tafiyar shi ya fara, ya na ta fadan rashin jin dad'in shi akan kiran shi da Auwal da Sultana ke yi, ba dan sunan soyayyar nan.
Bin shi ta yi da gudu, dan ya kusan isa filin wajen nasu, ta kama hannun shi ta ce,
"Zan fada maka wani suna mai daaadii, amma ba yanzu ba, sai mun koma gidan mu"
"Ni dai yanzu nake so"
"Ah ahh ba yanzu ba"
"To ke Aunty Sultana ki sanar da shi mana, ba a fa jinkirta bayyana soyayya, sai wata ta kwace miki shi"
Kukan shagwaba Sultana ta saka, ta na nuna Mubaraka,
"Ka gan ta ko? Har ta hwara yi min fatan kishiya ko shekara ban yi ba"
Dariya kowa ya ke yi a wajen,Sultan kuwa hankalin shi ya tashi, dan maganar da Mubaraka ta yi sai ya ji kamar da shi take, duk da bai ga alama ba,abinda bai sani ba kuwa shi ne, Mubaraka da shi take, amma ta yi kamar bata san ma ya na wajen ba, ta na so ta san shin hasashen ta gaskiya ne? Ya na son ta ko dan ta na son shi ne ya sa take ganin kamar ya na son ta?
Sallama Lawwali da Taheer suka yi, Taheer na qoqarin barin motar Mubaraka a nan, Lawwali ya ce ya je da ita, ya dinga kai yara makaranta, godiya ya dinga yi sosai, sannan ya cire yar qaramar jakar shi daga motar da za akai shi tasha ya mayar a wadda suka zo da ita.
Sallama ya dinga yi da mutanen wajen d'aya bayan d'aya,sai da ya zo kan Sultan ya rage murya ya ce,
"Kar ka tsaya kallon ruwa kwado ya maka qahwa wallah"
Kada kai Sultan ya yi, cikin yaqe, dan gaba d'aya hankalin shi ya tashi, ga dai Mubaraka ba wata babba ba, amma kwarjinin ta ya cika masa ido matuqa........
*Washhh na gaji,amma ya kuke gani mutanen kirki, shin ya kamata Sultan ya bayyana soyayyar shi a dajin Oga, ko kuma ya bari sai sun shaqi iskar gari???*
π π» *A GARIN MU* π π»
BY
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43 Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51