ta na ringing, Sultan ne ke kiran ta, amsawa ta yi cikin sallama, da gaisuwa.
"Ok ina nan tafe ,bani minti biyar,"
Kashe wayar ta yi, cikin sauri da zare ido, ashe ta dauki lokaci mai tsawo haka? Lallai masu yin kwalliya su na cin lokaci, anyaa za ta dore kuwa? Kayan ta ta nema wanda ta saba sawa ko da yaushe, wato doguwar riga irin ta larabawa, in ta saka irin su su na amsar ta sosai, duk da ita din ba wata fara bace sosai, amma ba za a kira ta baqa ba, fatar ta na da haske sosai .
Ta na kammala shirya wa ta dauki jakar ta, ta sanya takalmin da ya zo da jakar ta ta, wayar ta riqe a hannun ta, ta na sake duba time din da ta bata.
Ta na daf da sauka daga yar matattakalar benen ne ta tsaya cak, Lawwali ta gani tsaye da Daddyn ta su na magana qasa qasa.
Daddyn ta da alama ya shiga damuwa sosai .
Da dan hanzari ta isa gare su, takun takalmin ta, da qamshin turaren ta ne ya sanar da su zuwan ta, Lawwali na dora idon shi a kan ta, ya ji kamar an zare masa dukkan wata damuwar shi,da lakar jikin shi, har wani lumshe ido ya ke.
Shi abinda ka ke so, Indai ka gan shi, komai munin shi kyakkyawa ne a wajen ka, ballan tana kyakkyawa ji za ka yi kamar ba abinda ya kai shi kyau a duniya.
Sultana kallon Lawwali ta yi, ta ga yanda yake kallon ta, kunya ce ta ji ta kama ta, sai ta ɗan sunkuyar da kan ta qasa, ta na murmushi, bai san sanda na shi ya bayyana ba, gaishe da Dad din ta tayi, sannan ta gaishe da Lawwali, da hanzari cikin girmamawa Lawwali ya mayar mata da gaisuwar.
"Daddy lafiya? Na ga hankalin ka a tashe?"
A dan daburce ya kalle ta, ya hau yaqe, ya na dafa kafadar ta, tare da shafa kuncin ta ya ce,
"Sulty baby ba abinda ke damu na, dama ina tsaye ne ina jiran ki fito, kowa yunwa yake ji, amma ba ki fito ba, sai kuma gashi masha Allah, na ga yau kin yi wata iriyar kwalliyar da ban taba gani kin yi ba"
Dan kwabe fuska ta yi, cikin shagwaba, wanda ya sanya Lawwali dan jingina da jikin ginin da ya ke tsaye a jiki ,tare da hard'e hannun shi a qirji,ya lumshe idanun shi a hankali ya sauke su akan ta.
"Daddyyy ban yi kyau ba ko? Let me go and clean my face, yanzu zan dawo"
Da sauri Lawwali ya ce,
"Wacce baki kyawu ba? Ke gane ki kuwa? Tunda ni ke duniya ban taba ganin mace kyakkyawa awakke ba"
Wani irin farin ciki ne ya lullube Sultana, har gwamna Halliru zai fassara maganar Lawwali, sai suka ji Muryar Sultan na fadin.
"Ba ka yi qarya ba Lawwali,bayan budurwa ta ban taba ganin kyakkyawar macen da ta hiki kyau ba Sulty Baby"
Dan tura baki ta yi kadan sannan ta ce,
"Wace budurwa ka ke da? Bayan tsoron mata ka kai"
Dariya aka sa a wajen, suka nufi dinning table, aka bar Sultan da son kare kan shi, shi ba tsoron mata yake ba, kawai dai tausayin su yake ji.
Hajiya Ikee ma zama ta yi ta na dariya, tare da taya Sultan kare kan shi.
"Sultan ai jarumi na wallah ,matar shi sai diyar sarki ko shugaban qasa"
Lawwali na gaishe ta ta yi kamar bata ji ba, ita ta qi jinin talaka, masu aikin ta kaf ba dadin ta suke ji ba,
Lawwali da ya ga ta qi amsawa hanyar fita ya kama abin shi,dan ya basu waje, sai ya ji Muryar Sultana na fadin
"Auwal ka ci abinci kuwa?"
Cikin jin dadi, ya juya ya kalle ta, a ranshi ya na ayyana ta na bashi abinci a baki, da sauri ya kawar da tunanin ya amsa da .
"Eh na ci,in ke qare ki dai yi min magana mu tai"
"Tau ya yi"
Fita ya yi,ya nufi can baya inda suke shanya a gidan ,waya ya dauka ya kira No 2, bata wani jima ta na ringing ba ya dauka, cike da damuwa da tsoron Ogan nasu.
"Hello, No 2 garin ya kuka bari ya gudu? Wanne irin daqiqanci ka damun ku? Dazu 1 ya kire Ni yacce min wai tsohon gwamna ya gudu, ka sani, duk kun ka bari ya hita dajin nan baku nemo shi ba, da hannu na zan halbe ku, dukan ku, umarni na ne, ku hita har da su Sa'adatu a nemo shi duk inda ya shiga, bai isa hita wajen nan ba yanzu, ku bazama da motoci a nemo shi, da kun ganai ku halbe shi, kar ku jira komai, kuma ku sani, zan bincika, duk wanda nikkama shi na da hannu a taimaka masa ya hita,.....duk wanda ya taimaka masa.....hummm sai na zo dai kawai,"
'Oga....'
Kafin No 2 ya yi magana Lawwali ya kashe wayar, cikin fushi ya tafi, ko daya je ya tarar Sultana na ta neman shi, dan sake fuskar shi ya yi,sannan ya je da sauri ya bude mata qofa, wayar shi ce ta yi qara ya duba 'Excellency' shi ne a jikin wayar, daga wa ya yi, tare da yin qasa da Muryar shi,
"Kar ka damu ranka shi dade, na bada umarnin a nemo shi, da na aje ta za ni nima"
'Ah Ah kar ka kuskura ka bar min yarinya ita daya, ka tsaya a wajen ta, ban yarda ka matsa ko ina ba,'
"Amma ranka ya dade..."
'Umarni nake baka ba shawara ba Lawwali'
"To ran ka shi dade,"
Kashe wayar ya yi, ya shige motar ya ja su suka bar gidan,ya kasa sake fuskar shi saboda bacin ran da yake ciki, rashin zaman da ba ya yi sosai a wajen yanzu ya sa su na sakaci da abubuwan da ya kamata su na bawa mahimmanci.
Sultana ta dan damu da ba ta ga ya kalle taba, sai ta samu kan ta da jin ba dad'in rashin kallon ta da ba ya yi a yau.
"Tsayar da motar,"
Ta madubi ya kalle ta, cike da mamaki, kauda kai ta yi kamar ba ita ta yi magana ba,
"Ran ki shi dade mi kicce?"
Dora idanun ta tayi a nashi sannan ta ce,
"Dan koma baya kadan, ka tsayar da motar daidai waccan matar mai suya qosai"
Komawa baya ya yi, ya tsayar da motar, tunda ya dora idon shi akan ta ya manta da tunanin da ke a zuciyar shi ,fita ta yi, matar na ta soya qosai, ba mutane sosai a wajen, saboda hantsi ya fara.
"Assalamu alaikum, baba a bani qosai na nera dari,"
"Wa'alaikumussalam, to yarinya ki dan jira ke ga ni dai akwai wasu gaban ki"
"To Baba"
Lawwali ne cikin hade fuska ya nufi wajen zai magana, Sultana ta marairaice ido, ta masa alamar ya bari, yanayin yanda ta yi ya shige shi, amma sai ya koma ya tsaya a gefen ta, Ita kuwa kallon unguwar take, ta na kuma wa, da alamar su na buqatar taimako,yara baja baja ba masu zuwa makaranta, ita fa ta na son makaranta ,ta na bawa makaranta mahimmanci, ta na son ganin yara na zuwa makaranta, ba ta son ta ga yaran da ya kamata ace su na aji, ta gan su su na wasa a unguwannin su.
Wani yaro ne da zai kai shekara goma sha daya, ya keto a guje ya tada qura, saura kadan ya fadi, cikin qiftawar ido Lawwali ya tare shi, sultana kuwa har ta rufe ido, dan kuwa ta saddaqar zai fadin, shiru ta ji, dan haka sai ta bude ido a hankali,
"Ke gani bai fadi ba? Yara irin wannan sun hi ki son jikin su,"
Cikin murmushi ya fadi hakan, Itan ma murmushi ta mayar masa, tare da maida hankalin ta kan yaron da ke raba ido a tsakanin su.
"Me ya sa ka ke wargi ba ka tai makaranta ba?" (Wargi wasa kenan)
"Zan gaishe da maman ka ne, na ce ta na da yaro mai hankali"
Shiru yaron ya yi, tare da saurin amshe hannun shi zai gudu, Lawwali ya riqe shi, ya daga fuskar shi, ya na kallon dan baqi kyakkyawan yaron,
"Ina za ka tai,ka rake mu gidan ku mana,"
"Mama ta ta mutu masu halbi na sunka halbe ta, baba na shi na inda likita da Goggo ta, an halbe shi a qafar shi guda,likita ya ce za a yanke,ba kowa gidan mu"
Sultana na jin wannan labari sai hawaye ya fara gangarowa saman kuncin ta, Lawwali kuwa ji ya yi kamar an dora masa wani abu mai nauyi a qirjin shi,tun da ya ke bai taba jin haka ba, ko dan bai taba tsayawa ya yi magana da wanda suke illatawa bane?
Gani ya yi Sultana ta ja yaron ta rungume a jikin ta, ko kula da dattin jikin shi ba ta yi ba.
Mutanen da ke wajen kallon ta suke da mamaki, da kuma birgewa, hankalin mutane ya fara yawa kan su Dan haka mota ta ja yaron suka nufa, ta zauna ya na tsaye gaban ta, ta kira Lawwali, ta bude jakar ta ta debi dubu goma ta ce ya bawa mai qosai, ta qara jari.
Sai ga Mai qosai ta debo qosai me yawa ta kawo ma Sultana ta na ta godiya kamar za ta kwanta mata, ita kuma tana nuna ba komai.
Amsar qosan ta yi, itama ta yi godiya, matar ta tafi, ta na ma Sultana addu'a.
"Ina ne makarantar ku? "
"Makarantar mu na can shiyyar mu, yawancin yaran shiyyar mu da na nan shiyyar ita suka zuwa"
"Za ka raka ni a mota ne ko da qafa?"
"Mu dai tai da qafa,"
Ya na dan dariya ya fadi hakan, Sultana ta fahimta ya na tsoro ne, ba ta ga laifin shi ba, zamani ya sauya, jakarta ta dauka da wayar ta, Lawwali ya kulle mota, suka taka.
Har zuwa makarantar yaran, ana ta karatu, makarantar ga ta nan ne dai kawai, kuma a haka ta kudi ce, sallama ta yi, ta nemi ofishin shugaban makaranta aka kai ta, bata fito ba sai da aka lissafa mata adadin yaran da ba su biya kudi ba, ta yi alqawarin biya, suka bata account No,ta tura musu, sannan ta ce a sanar da yaran su ci gaba da zuwa makaranta, za ta dawo ta duba ko sun dawo,sallama ta musu ta tafi
Lawwali mamaki ya hana shi ma bin ta su tafi, anya Sultana jinin Halliru da Ikeelima ce kuwa?
Tsayawa ta yi a gaban shi ta ce,
"In ka qare kallon nawa mu je ko?"
Murmushin gefen baki ya mata, sannan ya ce,
"Ai ke din ce Ran ki shi dade, bayan kyau da ki ke da shi,har da kyauwun zucciya, "
Kunya ce ta kama ta, ta sunkuyar da idanun ta daga kallon shi, su na tafe su na dan yin hira, ta na jin dad'i in ya yabi kyawun ta, bata sani ba ko dan bata saba jin haka bane oho, kawai dai ta san ta na jin dad'i.
Har suka isa mota, yaron na riqe da hannun Sultana,
"To yanzu ina ne asibitin da Baban ka yake?"
"Babban asibiti ne, amma ban san waje ba, Inna Rabi ta tassan waje,Ga gidan ta can, wancan me buhun"
Bata gaji ba, sallama ta yi suka gaisa da matan gidan, gida ne na haya, mai dakuna da yawa ciki,
Har qofar Innar shi Rabi ya kai ta, suka gaisa, ta mata bayanin haduwar ta da yaron, sai a sannan ne ta tuna bata san sunan yaron ba, Innar shi ce ta sanar da ita sunan shi Huzaifah, sultana sanar da ita tayi ta na son ta je duba mahaifin yaron a asibiti, ya za a yi?
"Dama an jima kadan zanna kai musu abinci, mu tai na rake ki"
Nan da nan ta shiga ta saka hijabi, ta kulle qofar ta, suka fita, motar da ta gani su na nufa ce ta dan tsorata ta, Sultana ta ce,
"In ki na ganin akwai matsala ki min kwatance, zan bide su"
Kunya ce ta kama Rabi ganin Sultana ta gano ta.
Nan dai ta shiga suka tafi har asibitin, ta ga mahaifin Huzaifah, ta biya duk wani abu da ake buqata, bayan nashi ma har da na wasu mutum shida.
Alqawarin sake komawa ta yi, watarana asibitin dan taimakawa masu jinyar.
Sai da suka isa office din su, Sultana ta ke nazarin abubuwan da suka faru, tabbas masu neman taimako na asibiti, da irin unguwannin su Huzaifah, unguwannin talakawa, lallai yau ta samu wata babbar nasara a abinda ta ke da buri, alqawarin taimakawa mabuqata da ta dauka da yardar Allah za ta yi qoqarin cika shi duk da ta sani ba zata iya taimakon kaff mutanen garin Zamfara ba, amma zata qoqarta taimakawa wanda ya samu.
(Shin irin su Sultana ne kawai ya kamata su dinga taimakawa talakawa? Ke me kike aikatawa na taimakon wasu? Kai fa? Mu tambayi kammu, a rayuwa kar mutum ya ce sai ya ci ya tada kai sannan zai bawa wasu, da kadan din da muke da shi da shi za mu taimaki wasu, masu kidnapping har gida wasu masu qarfin halin suke zuwa su yi su tafi, masu asiri da maita har gida suke bi su cutar da mutane, me ya sa masu taimakawa mutane ba su bi gida gida? Ba riya bane dan ka yi abu wasu sun gan ka sanda ka ke yi, niyyar ka ita ce ladan ka, baka sani ba da loma daya da zaka bawa wani ya ci Allah ya maka rahama ,mu kyautata niyya yayin yin aikin alkhairi, in dai mugaye za su bi gida gida su kashe, su sace, su cinye,to kuwa kai mai aikin alkhairi kai ka fi cancanta da ka bi gida gida dan kyautatawa, zamanin magabata na gari har gida suke bin wanda za su taimakawa, me ya sa muka daina? Ladan ne Bama so?)
*Tambaya a gare mu baki daya*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 21:
Tafiya ya ke a cikin duhun dajin da suka yi wa hanyar mota da kan su, saboda yawan shiga da fita, babu hasken komai, sai hasken futilun motar, qarar tsuntsaye, da wasu dabbobin kawai ke tashi, bai tsaya a ko ina ba sai ginin da yake maboyar su, cikin hanzari ya fita daga motar ya shiga wajen, tun daga bakin qofa har ciki masu gadi ne riqe da muggan makamai, gaisuwa kawai suke miqawa wajen Ogan su da suka yi kewar gani kwana biyu, ya so ko da murmushi ne ya musu, amma bacin ran da ya ke ji ya hana shi sake musu fuska, sun kuma fahimci hakan.
Qofar da za ta sada shi da inda aka ajiye Tsohon Gwamana No 5 ya bude masa, bayan ya gaida shi, daga masa kai ya yi kawai ya shige, a wata kujera da aka tanadar masa ya zauna, tare da harde qafar shi daya saman daya, kallo ya kafe mutanen dakin da shi, ya jima ya na kallon su,daga baya ya ce,
"Wab-bud'e shi?"
(Waye ya bude shi)
Shiru wajen ya dauka, cikin bacin rai Lawwali ya zari bindigar qugun No 3 ya harbi qafar Tsohon Gwamna, wata iriyar qara ya saki, tin qarfin shi, jijiyoyin kan shi da na wuyan shi sun fita rudu-rudu, ya na so ya riqe qafar amma ba hali, saboda an daure hannayen shi, cikin rawar murya ya ce,
"Wata yarinya ce, ......na mata ...alqawarin....million goma....in ta kunce ni.."
Wata dariya Lawwali ya saki sannan ya ce,
"Ku je ku kawo min su Sa'adatu, na ji a cikin su wacce mai qarar kwanan ce tab-bude shi"
No 2 ne ya fita cikin sauri, Lawwali kuwa fada ya fara yi,
"Meye amfanin ka a nan Inuwa( No1) kai ne fa babba yanzu, ka na mi da an ka bude shi, ko ka san hitar shi daga nan, daidai yake da tonuwar asirin mu! "
'Yan mata ne guda uku suka shiga kowaccen su sanye take da kaya kamar mai shirin fita yaqi,a cikin matan da ke wajen, su aka bawa horon fita da mazan in za a je cikin gari sato mutane ko wani fada ko wata hatsaniya dai.
Daya daga cikin su sai rawar jiki take, hankalin ta a tashe, lokaci zuwa lokaci ta na daga kai ta kalli No 1, da alama ta na neman agaji ne a wajen shi, shi kuwa kauda kai ya yi kamar bai taba ganin ta ba.
Su na qarasa shiga Lawwali ya yi ido hudu da budurwar da ke rawar jiki, ya ce,
"Yaseerah kin bata wayon ki, shin kin manta million nawa Excellency ya ce mu karba wajen mutenen ga? Kudi na hwa masu yawa, me ya sa zaki zagaya ki aikata haka?"
"Oga.... Dama...."
Cikin sauri No 1 ya kalle ta, ya ce,
"Oga butulci ne irin na mata, bai kamata a barta ba, ya kamata a hukunta ta saboda ya zama izina ga na baya"
Kafin Lawwali ya bada umarni, ko ya yi magana, No 1 ya harbi Yaseerah, qarar bindigar da qarar ta kusan a tare suka karade wajen, gaba daya kallo kan No 1 ya koma, shi kuma ya fara wani murmushin jin dadi ya ce,
"Oga a min afuwa, irin haka ba za ta qara faruwa ba, zan sa ido sosai, ba a koma samun maci amana wajen ga na yi ma alqawari"
"Wa ya ba ka izinin yin halbi?"
"Oga a min afuwa, na zaci za ka yi hwarin ciki na kawar da maci amana, duk da ina son Yaseerah ba zan taba bari ta ci amanar mu ba,"
Yanda ya yi maganar ya sa Lawwali zaton ko No 1 na jin haushin cin amanar da Yaseerah ta yi ne, shi ya sa ya harbe ta.
Umarni ya bada akan a ɗauke ta, a binne ta a daren, sannan ya miqe kamar zai tafi ya saita Tsohon Gwamna ya saki kunamar bindigar a qirjin shi, sannan ya fice, No 2 na biye da shi a baya,
"Oga ka sani fa dangin shi ba su aiko kudin nan ba, sun ce su na nan suna haɗawa ne, yanzu da aka kashe shi ya za a yi?"
"Ko sun kawo, ko basu kawo
Showing 33001 words to 36000 words out of 150481 words
"Ok ina nan tafe ,bani minti biyar,"
Kashe wayar ta yi, cikin sauri da zare ido, ashe ta dauki lokaci mai tsawo haka? Lallai masu yin kwalliya su na cin lokaci, anyaa za ta dore kuwa? Kayan ta ta nema wanda ta saba sawa ko da yaushe, wato doguwar riga irin ta larabawa, in ta saka irin su su na amsar ta sosai, duk da ita din ba wata fara bace sosai, amma ba za a kira ta baqa ba, fatar ta na da haske sosai .
Ta na kammala shirya wa ta dauki jakar ta, ta sanya takalmin da ya zo da jakar ta ta, wayar ta riqe a hannun ta, ta na sake duba time din da ta bata.
Ta na daf da sauka daga yar matattakalar benen ne ta tsaya cak, Lawwali ta gani tsaye da Daddyn ta su na magana qasa qasa.
Daddyn ta da alama ya shiga damuwa sosai .
Da dan hanzari ta isa gare su, takun takalmin ta, da qamshin turaren ta ne ya sanar da su zuwan ta, Lawwali na dora idon shi a kan ta, ya ji kamar an zare masa dukkan wata damuwar shi,da lakar jikin shi, har wani lumshe ido ya ke.
Shi abinda ka ke so, Indai ka gan shi, komai munin shi kyakkyawa ne a wajen ka, ballan tana kyakkyawa ji za ka yi kamar ba abinda ya kai shi kyau a duniya.
Sultana kallon Lawwali ta yi, ta ga yanda yake kallon ta, kunya ce ta ji ta kama ta, sai ta ɗan sunkuyar da kan ta qasa, ta na murmushi, bai san sanda na shi ya bayyana ba, gaishe da Dad din ta tayi, sannan ta gaishe da Lawwali, da hanzari cikin girmamawa Lawwali ya mayar mata da gaisuwar.
"Daddy lafiya? Na ga hankalin ka a tashe?"
A dan daburce ya kalle ta, ya hau yaqe, ya na dafa kafadar ta, tare da shafa kuncin ta ya ce,
"Sulty baby ba abinda ke damu na, dama ina tsaye ne ina jiran ki fito, kowa yunwa yake ji, amma ba ki fito ba, sai kuma gashi masha Allah, na ga yau kin yi wata iriyar kwalliyar da ban taba gani kin yi ba"
Dan kwabe fuska ta yi, cikin shagwaba, wanda ya sanya Lawwali dan jingina da jikin ginin da ya ke tsaye a jiki ,tare da hard'e hannun shi a qirji,ya lumshe idanun shi a hankali ya sauke su akan ta.
"Daddyyy ban yi kyau ba ko? Let me go and clean my face, yanzu zan dawo"
Da sauri Lawwali ya ce,
"Wacce baki kyawu ba? Ke gane ki kuwa? Tunda ni ke duniya ban taba ganin mace kyakkyawa awakke ba"
Wani irin farin ciki ne ya lullube Sultana, har gwamna Halliru zai fassara maganar Lawwali, sai suka ji Muryar Sultan na fadin.
"Ba ka yi qarya ba Lawwali,bayan budurwa ta ban taba ganin kyakkyawar macen da ta hiki kyau ba Sulty Baby"
Dan tura baki ta yi kadan sannan ta ce,
"Wace budurwa ka ke da? Bayan tsoron mata ka kai"
Dariya aka sa a wajen, suka nufi dinning table, aka bar Sultan da son kare kan shi, shi ba tsoron mata yake ba, kawai dai tausayin su yake ji.
Hajiya Ikee ma zama ta yi ta na dariya, tare da taya Sultan kare kan shi.
"Sultan ai jarumi na wallah ,matar shi sai diyar sarki ko shugaban qasa"
Lawwali na gaishe ta ta yi kamar bata ji ba, ita ta qi jinin talaka, masu aikin ta kaf ba dadin ta suke ji ba,
Lawwali da ya ga ta qi amsawa hanyar fita ya kama abin shi,dan ya basu waje, sai ya ji Muryar Sultana na fadin
"Auwal ka ci abinci kuwa?"
Cikin jin dadi, ya juya ya kalle ta, a ranshi ya na ayyana ta na bashi abinci a baki, da sauri ya kawar da tunanin ya amsa da .
"Eh na ci,in ke qare ki dai yi min magana mu tai"
"Tau ya yi"
Fita ya yi,ya nufi can baya inda suke shanya a gidan ,waya ya dauka ya kira No 2, bata wani jima ta na ringing ba ya dauka, cike da damuwa da tsoron Ogan nasu.
"Hello, No 2 garin ya kuka bari ya gudu? Wanne irin daqiqanci ka damun ku? Dazu 1 ya kire Ni yacce min wai tsohon gwamna ya gudu, ka sani, duk kun ka bari ya hita dajin nan baku nemo shi ba, da hannu na zan halbe ku, dukan ku, umarni na ne, ku hita har da su Sa'adatu a nemo shi duk inda ya shiga, bai isa hita wajen nan ba yanzu, ku bazama da motoci a nemo shi, da kun ganai ku halbe shi, kar ku jira komai, kuma ku sani, zan bincika, duk wanda nikkama shi na da hannu a taimaka masa ya hita,.....duk wanda ya taimaka masa.....hummm sai na zo dai kawai,"
'Oga....'
Kafin No 2 ya yi magana Lawwali ya kashe wayar, cikin fushi ya tafi, ko daya je ya tarar Sultana na ta neman shi, dan sake fuskar shi ya yi,sannan ya je da sauri ya bude mata qofa, wayar shi ce ta yi qara ya duba 'Excellency' shi ne a jikin wayar, daga wa ya yi, tare da yin qasa da Muryar shi,
"Kar ka damu ranka shi dade, na bada umarnin a nemo shi, da na aje ta za ni nima"
'Ah Ah kar ka kuskura ka bar min yarinya ita daya, ka tsaya a wajen ta, ban yarda ka matsa ko ina ba,'
"Amma ranka ya dade..."
'Umarni nake baka ba shawara ba Lawwali'
"To ran ka shi dade,"
Kashe wayar ya yi, ya shige motar ya ja su suka bar gidan,ya kasa sake fuskar shi saboda bacin ran da yake ciki, rashin zaman da ba ya yi sosai a wajen yanzu ya sa su na sakaci da abubuwan da ya kamata su na bawa mahimmanci.
Sultana ta dan damu da ba ta ga ya kalle taba, sai ta samu kan ta da jin ba dad'in rashin kallon ta da ba ya yi a yau.
"Tsayar da motar,"
Ta madubi ya kalle ta, cike da mamaki, kauda kai ta yi kamar ba ita ta yi magana ba,
"Ran ki shi dade mi kicce?"
Dora idanun ta tayi a nashi sannan ta ce,
"Dan koma baya kadan, ka tsayar da motar daidai waccan matar mai suya qosai"
Komawa baya ya yi, ya tsayar da motar, tunda ya dora idon shi akan ta ya manta da tunanin da ke a zuciyar shi ,fita ta yi, matar na ta soya qosai, ba mutane sosai a wajen, saboda hantsi ya fara.
"Assalamu alaikum, baba a bani qosai na nera dari,"
"Wa'alaikumussalam, to yarinya ki dan jira ke ga ni dai akwai wasu gaban ki"
"To Baba"
Lawwali ne cikin hade fuska ya nufi wajen zai magana, Sultana ta marairaice ido, ta masa alamar ya bari, yanayin yanda ta yi ya shige shi, amma sai ya koma ya tsaya a gefen ta, Ita kuwa kallon unguwar take, ta na kuma wa, da alamar su na buqatar taimako,yara baja baja ba masu zuwa makaranta, ita fa ta na son makaranta ,ta na bawa makaranta mahimmanci, ta na son ganin yara na zuwa makaranta, ba ta son ta ga yaran da ya kamata ace su na aji, ta gan su su na wasa a unguwannin su.
Wani yaro ne da zai kai shekara goma sha daya, ya keto a guje ya tada qura, saura kadan ya fadi, cikin qiftawar ido Lawwali ya tare shi, sultana kuwa har ta rufe ido, dan kuwa ta saddaqar zai fadin, shiru ta ji, dan haka sai ta bude ido a hankali,
"Ke gani bai fadi ba? Yara irin wannan sun hi ki son jikin su,"
Cikin murmushi ya fadi hakan, Itan ma murmushi ta mayar masa, tare da maida hankalin ta kan yaron da ke raba ido a tsakanin su.
"Me ya sa ka ke wargi ba ka tai makaranta ba?" (Wargi wasa kenan)
"Ba a biya min kuddin makaranta ba"
"Ina ne gidan ku?"
"Shi na can bayan shiyyar ga"
"Me ya kawo ka shiyyar nan?"
"Wargi nittaho wajen diyoyin innata (wasa na taho wajen yaran innata)"
"Ohh su ma ba su tai makaranta ba kenan"
"Uhm"
"Ok to mu tai na ga gidan ku, za ka kai ni?"
"Mi za ki yi gidan mu?"
Dariya ta yi sannan ta ce,
"Zan gaishe da maman ka ne, na ce ta na da yaro mai hankali"
Shiru yaron ya yi, tare da saurin amshe hannun shi zai gudu, Lawwali ya riqe shi, ya daga fuskar shi, ya na kallon dan baqi kyakkyawan yaron,
"Ina za ka tai,ka rake mu gidan ku mana,"
"Mama ta ta mutu masu halbi na sunka halbe ta, baba na shi na inda likita da Goggo ta, an halbe shi a qafar shi guda,likita ya ce za a yanke,ba kowa gidan mu"
Sultana na jin wannan labari sai hawaye ya fara gangarowa saman kuncin ta, Lawwali kuwa ji ya yi kamar an dora masa wani abu mai nauyi a qirjin shi,tun da ya ke bai taba jin haka ba, ko dan bai taba tsayawa ya yi magana da wanda suke illatawa bane?
Gani ya yi Sultana ta ja yaron ta rungume a jikin ta, ko kula da dattin jikin shi ba ta yi ba.
Mutanen da ke wajen kallon ta suke da mamaki, da kuma birgewa, hankalin mutane ya fara yawa kan su Dan haka mota ta ja yaron suka nufa, ta zauna ya na tsaye gaban ta, ta kira Lawwali, ta bude jakar ta ta debi dubu goma ta ce ya bawa mai qosai, ta qara jari.
Sai ga Mai qosai ta debo qosai me yawa ta kawo ma Sultana ta na ta godiya kamar za ta kwanta mata, ita kuma tana nuna ba komai.
Amsar qosan ta yi, itama ta yi godiya, matar ta tafi, ta na ma Sultana addu'a.
"Ina ne makarantar ku? "
"Makarantar mu na can shiyyar mu, yawancin yaran shiyyar mu da na nan shiyyar ita suka zuwa"
"Za ka raka ni a mota ne ko da qafa?"
"Mu dai tai da qafa,"
Ya na dan dariya ya fadi hakan, Sultana ta fahimta ya na tsoro ne, ba ta ga laifin shi ba, zamani ya sauya, jakarta ta dauka da wayar ta, Lawwali ya kulle mota, suka taka.
Har zuwa makarantar yaran, ana ta karatu, makarantar ga ta nan ne dai kawai, kuma a haka ta kudi ce, sallama ta yi, ta nemi ofishin shugaban makaranta aka kai ta, bata fito ba sai da aka lissafa mata adadin yaran da ba su biya kudi ba, ta yi alqawarin biya, suka bata account No,ta tura musu, sannan ta ce a sanar da yaran su ci gaba da zuwa makaranta, za ta dawo ta duba ko sun dawo,sallama ta musu ta tafi
Lawwali mamaki ya hana shi ma bin ta su tafi, anya Sultana jinin Halliru da Ikeelima ce kuwa?
Tsayawa ta yi a gaban shi ta ce,
"In ka qare kallon nawa mu je ko?"
Murmushin gefen baki ya mata, sannan ya ce,
"Ai ke din ce Ran ki shi dade, bayan kyau da ki ke da shi,har da kyauwun zucciya, "
Kunya ce ta kama ta, ta sunkuyar da idanun ta daga kallon shi, su na tafe su na dan yin hira, ta na jin dad'i in ya yabi kyawun ta, bata sani ba ko dan bata saba jin haka bane oho, kawai dai ta san ta na jin dad'i.
Har suka isa mota, yaron na riqe da hannun Sultana,
"To yanzu ina ne asibitin da Baban ka yake?"
"Babban asibiti ne, amma ban san waje ba, Inna Rabi ta tassan waje,Ga gidan ta can, wancan me buhun"
Bata gaji ba, sallama ta yi suka gaisa da matan gidan, gida ne na haya, mai dakuna da yawa ciki,
Har qofar Innar shi Rabi ya kai ta, suka gaisa, ta mata bayanin haduwar ta da yaron, sai a sannan ne ta tuna bata san sunan yaron ba, Innar shi ce ta sanar da ita sunan shi Huzaifah, sultana sanar da ita tayi ta na son ta je duba mahaifin yaron a asibiti, ya za a yi?
"Dama an jima kadan zanna kai musu abinci, mu tai na rake ki"
Nan da nan ta shiga ta saka hijabi, ta kulle qofar ta, suka fita, motar da ta gani su na nufa ce ta dan tsorata ta, Sultana ta ce,
"In ki na ganin akwai matsala ki min kwatance, zan bide su"
Kunya ce ta kama Rabi ganin Sultana ta gano ta.
Nan dai ta shiga suka tafi har asibitin, ta ga mahaifin Huzaifah, ta biya duk wani abu da ake buqata, bayan nashi ma har da na wasu mutum shida.
Alqawarin sake komawa ta yi, watarana asibitin dan taimakawa masu jinyar.
Sai da suka isa office din su, Sultana ta ke nazarin abubuwan da suka faru, tabbas masu neman taimako na asibiti, da irin unguwannin su Huzaifah, unguwannin talakawa, lallai yau ta samu wata babbar nasara a abinda ta ke da buri, alqawarin taimakawa mabuqata da ta dauka da yardar Allah za ta yi qoqarin cika shi duk da ta sani ba zata iya taimakon kaff mutanen garin Zamfara ba, amma zata qoqarta taimakawa wanda ya samu.
(Shin irin su Sultana ne kawai ya kamata su dinga taimakawa talakawa? Ke me kike aikatawa na taimakon wasu? Kai fa? Mu tambayi kammu, a rayuwa kar mutum ya ce sai ya ci ya tada kai sannan zai bawa wasu, da kadan din da muke da shi da shi za mu taimaki wasu, masu kidnapping har gida wasu masu qarfin halin suke zuwa su yi su tafi, masu asiri da maita har gida suke bi su cutar da mutane, me ya sa masu taimakawa mutane ba su bi gida gida? Ba riya bane dan ka yi abu wasu sun gan ka sanda ka ke yi, niyyar ka ita ce ladan ka, baka sani ba da loma daya da zaka bawa wani ya ci Allah ya maka rahama ,mu kyautata niyya yayin yin aikin alkhairi, in dai mugaye za su bi gida gida su kashe, su sace, su cinye,to kuwa kai mai aikin alkhairi kai ka fi cancanta da ka bi gida gida dan kyautatawa, zamanin magabata na gari har gida suke bin wanda za su taimakawa, me ya sa muka daina? Ladan ne Bama so?)
*Tambaya a gare mu baki daya*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 21:
Tafiya ya ke a cikin duhun dajin da suka yi wa hanyar mota da kan su, saboda yawan shiga da fita, babu hasken komai, sai hasken futilun motar, qarar tsuntsaye, da wasu dabbobin kawai ke tashi, bai tsaya a ko ina ba sai ginin da yake maboyar su, cikin hanzari ya fita daga motar ya shiga wajen, tun daga bakin qofa har ciki masu gadi ne riqe da muggan makamai, gaisuwa kawai suke miqawa wajen Ogan su da suka yi kewar gani kwana biyu, ya so ko da murmushi ne ya musu, amma bacin ran da ya ke ji ya hana shi sake musu fuska, sun kuma fahimci hakan.
Qofar da za ta sada shi da inda aka ajiye Tsohon Gwamana No 5 ya bude masa, bayan ya gaida shi, daga masa kai ya yi kawai ya shige, a wata kujera da aka tanadar masa ya zauna, tare da harde qafar shi daya saman daya, kallo ya kafe mutanen dakin da shi, ya jima ya na kallon su,daga baya ya ce,
"Wab-bud'e shi?"
(Waye ya bude shi)
Shiru wajen ya dauka, cikin bacin rai Lawwali ya zari bindigar qugun No 3 ya harbi qafar Tsohon Gwamna, wata iriyar qara ya saki, tin qarfin shi, jijiyoyin kan shi da na wuyan shi sun fita rudu-rudu, ya na so ya riqe qafar amma ba hali, saboda an daure hannayen shi, cikin rawar murya ya ce,
"Wata yarinya ce, ......na mata ...alqawarin....million goma....in ta kunce ni.."
Wata dariya Lawwali ya saki sannan ya ce,
"Ku je ku kawo min su Sa'adatu, na ji a cikin su wacce mai qarar kwanan ce tab-bude shi"
No 2 ne ya fita cikin sauri, Lawwali kuwa fada ya fara yi,
"Meye amfanin ka a nan Inuwa( No1) kai ne fa babba yanzu, ka na mi da an ka bude shi, ko ka san hitar shi daga nan, daidai yake da tonuwar asirin mu! "
'Yan mata ne guda uku suka shiga kowaccen su sanye take da kaya kamar mai shirin fita yaqi,a cikin matan da ke wajen, su aka bawa horon fita da mazan in za a je cikin gari sato mutane ko wani fada ko wata hatsaniya dai.
Daya daga cikin su sai rawar jiki take, hankalin ta a tashe, lokaci zuwa lokaci ta na daga kai ta kalli No 1, da alama ta na neman agaji ne a wajen shi, shi kuwa kauda kai ya yi kamar bai taba ganin ta ba.
Su na qarasa shiga Lawwali ya yi ido hudu da budurwar da ke rawar jiki, ya ce,
"Yaseerah kin bata wayon ki, shin kin manta million nawa Excellency ya ce mu karba wajen mutenen ga? Kudi na hwa masu yawa, me ya sa zaki zagaya ki aikata haka?"
"Oga.... Dama...."
Cikin sauri No 1 ya kalle ta, ya ce,
"Oga butulci ne irin na mata, bai kamata a barta ba, ya kamata a hukunta ta saboda ya zama izina ga na baya"
Kafin Lawwali ya bada umarni, ko ya yi magana, No 1 ya harbi Yaseerah, qarar bindigar da qarar ta kusan a tare suka karade wajen, gaba daya kallo kan No 1 ya koma, shi kuma ya fara wani murmushin jin dadi ya ce,
"Oga a min afuwa, irin haka ba za ta qara faruwa ba, zan sa ido sosai, ba a koma samun maci amana wajen ga na yi ma alqawari"
"Wa ya ba ka izinin yin halbi?"
"Oga a min afuwa, na zaci za ka yi hwarin ciki na kawar da maci amana, duk da ina son Yaseerah ba zan taba bari ta ci amanar mu ba,"
Yanda ya yi maganar ya sa Lawwali zaton ko No 1 na jin haushin cin amanar da Yaseerah ta yi ne, shi ya sa ya harbe ta.
Umarni ya bada akan a ɗauke ta, a binne ta a daren, sannan ya miqe kamar zai tafi ya saita Tsohon Gwamna ya saki kunamar bindigar a qirjin shi, sannan ya fice, No 2 na biye da shi a baya,
"Oga ka sani fa dangin shi ba su aiko kudin nan ba, sun ce su na nan suna haɗawa ne, yanzu da aka kashe shi ya za a yi?"
"Ko sun kawo, ko basu kawo
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12 Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51