Wannan kalamai sun sake birkita No 4, da kyar yake hadiyar yawu, zufa sai karyo masa take, a sati ukun nan, duk 'yar qibar ma da ya yi, saboda kudin da suke samu, duk ta zabge, ya fita hayyacin shi, ba wani kwanciyar hankali a tattare da shi.
Su Sultana kuwa a jikin motar shi, suka tsaya, su na magana, hira ce mai dadi,ta yaushe gamo suke yi, kusan kaso saba'in na hirar dukkan su akan Mubaraka su ke yi, Sultana na son mubaraka, ba wai dan ta na qanwar Lawwali ba,ah ah, yarinyar abar so ce ga duk mai hankali.
Shi kuwa a wajen shi Mubaraka ita ce rayuwar shi, a ganin shi ma ba zai taba samun kan Sultana ba in bata nan.
Bayan sun yi sallama za su tafi ne Sultana ta ce,
"Haka ake sallama da masoyi? "
Kallon yanda ta maida kai gefe ta yi, sai ta masa kyau, murmushi ya yi, kadan, wanda rabon shi da murmushi na gaskiya, ba na mugunta ba, tun kafin batan Mubarakan.
"Ya ya kamata masoyi ya yi sallama ?"
Dan rufe fuskar ta tayi da hannun ta kadan ta ce,
"Kamata ya yi ka ce, Sultana na tafi, zan dawo anjima, ina son ki"
Bude baki Lawwali ya yi, ya na dariya mai sassanyan sauti, ya ce,
"Kaiii ka kaiii ka kaiii, Baraka na ta ce man ke ustaziya ta wallah, ashe ke iya soyayya haka?"
Mayafin ta ta ja sosai ta rufe fuska sannan ta ce,
"To ai soyayya kowa na yi"
"Ok, to sultana Ina son ki,"
Wani irin dad'i ne ya ziyarce ta, musamman da ta kalle shi ta ga babu wasa a kalaman shi, iyakar gaskiyar shi yake fada, ta ji sautin Muryar shi, ba alamar gatse ko wasa, amayar da ta ta zuciyar ta ce,
"Auwal ina son ka, In na ce ina son ka, ba ina nufin ina son ka fiye da yanda kk so na bane, ina nufin ina son ka a kowanne hali, ina son ka ko da wani sabani ya haɗa mu, ina son ka ko da ka na cikin damuwar da ta sa ka nesanta da ni, ina son ka sama da nisan nan da ke tsakanin mu,ina son ka sama da yanda na ke jin zafin rashin ka a rai na, ina son ka sama da dukkan wani abu da zai qoqarin shiga tsakanin mu, ina nufin nafi son ka Auwal"
Ya Salam, Lawwali ya gama narkewa,kalaman sultana sun wanke masa wani kaso na baqin cikin da ke ran shi,dama haka take fata, shi ne dalilin da ya sanya ta cire kunya ta furta abinda ke ran ta, sai bayan ta gama kashe masa gabban jikin shi, ta juya da gudu gudu ta shige gida,dan kuwa kunyar shi ba zata bar ta ta tsaya jin me zai ce ba again.
Lawwali ya jima a wajen, kafin ya shiga motar shi, ya tada ya bar gidan.
Su No 1 kuwa ya na fita suma suka bar gidan, dan zuwa sauyawa su Mubaraka maboya kamar yanda Gwamna ya bada shawara, da kuma wajen zama.
Lawwali har ya isa gida bai dena murmushi ba, ya jima ya na dirzar dattin jikin shi,kafin ya samu abinci ya ci rabon shi da abinci sosai kamar na ranar ba zai iya fadin ga lokacin ba.
Ya na kammalawa ya kwanta, dan hutawa.
**********************
Vissa ta samu, na tafiyar Isah Saudiya, ana sauran kwana biyu tafiyar Isa, Hajiya ta sa Isan ya kai mata su Hansatu su gaisa, Hansatu ta sha mamakin jin duk abinda ke faruwa a bakin mahaifiyar ta, ace duk wadannan abubuwan na faruwa bata sani ba? Haka ta dinga yaqe ta na yabawa Isah ,tare da yanka qarya kala kala, dan ta kare shi, yaran ta na ta mamakin qaryar da take ta shinfidawa.
Ba daban ta basu tarbiyya mai kyau ba, tabbas da sun tona mata asiri, dan kuwa ba su so ta rufa masa asiri ba.
Isah kuwa sai murmushi yake ya na fadin,
"In ban muku ba wa zan wa?"
Yayan Hansatu ya qara masa dubu hamsin ya qara a kan jarin shi, sai godiya suke ta zabgawa.
Kafin tafiyar Isah ya yi qoqarin ajiye musu buhun shinkafa, ya aje musu galan din man gyada da manja, galan daya daya, ya sai masu maggi, wake,barkono, da gishiri, ya sai musu taliya, su omo da sabulun wanka da wanki, rabon Hansatu da ta ga irin wannan kayan a hade waje daya, tun sanda suka yi aure, sai yau, kuka take ta yi, saboda rabuwa da masoyin ta.
Hajiya ta mata alqawarin zuwa da ita da yaran da Hajiyan kan ta,ta bata hakuri tare da lallashin ta akan ta bar shi ya tafi domin kasuwancin shi.
Yaran Isah kuwa murna suke da tafiyar tashi, har abun ya kasa boyuwa, garin murnar su da surutun da suke ne ya ja hankalin Yabbuga, da ta kasa kunne a cikin gidan, tun sanda ta ga ana shigar da kayan abinci.
Dan Jummaa ne ya wurge ta da dan qaramin dutse, ya ce,
"Ke hwasa zuwa gidan Kareema? Ina ta magana ke yi shiru"
"Bar tahiyar nan, zuwa gobe zan tai, wai shin dole na sai ka kaini? Mu na tahe saman mashin kamar 'yan bangar siyasa, ka yi tahiyar ka na yi tawwa"
"In baki hau bayan nawa ba, ai ke hau na wani qato, tau ki sani, walle baki zuwa ko ina in ba ni na zan kai ki ba, zancen banza zancen yohi"
Cikin fushi y fice ya bar gidan, Ita kuwa ko a jikin ta, kunnen ta na gidan Isah, so take ta ji kalmar da zata gama da wadda ta qunsa ta haɗa su bata ma'ana amma ta kasa.
Tsaki ta ja, ta zari mayafin ta, ta shuri takalman ta ta fice daga gidan ,ko jan qofa bata yi ba.
Ko sallama bata yi ba, haka ta afka gidan, karaf kuwa kunnen ta ya ji maganar Ahmad, ya na fadin, in baban su ya tafi Saudiya gobe a gado zai kwana.
Wani irin salati ta zabga, tare da tafa hannaye, Hansatu ce ta fito daga daki da gudu, ido ya mata jawur da alama kuka take.
"Lahiya? Mi ya hwaru halan? ",
"Yanzu ke Hansatu ina ganin ki shiru shiru ashe munahika ta? Ashe ke dauke ni maqiyyiyar ki da baki hwadi min mijin ki zai tahiya Makka, yau Allah ya sa ina da kunnuwan jin dumi, na jiyo daga wajen diyan ki, se qaqa?",
Cikin fushin da Hansatu bata san ta na da kalar shi ba ta kalli 'yabbuga ta ce,
"To sai qaqa kuwa? Ko ki na hana mai tahiyar na? Yo Ni na ji ikon Allah, komi na se na hwada miki? Tunda muke a matsayin ki na makwacciya ta ke taba zuwa ki tambayen shin na ci abinci Ni da diya na? Ko ke taba zuwa ki tambayen wane na abba lahiya cikin d'iya na ko niya? Haka d'ai ki dora min jidali? Don Allah dai ki barni na ji da abinda ka damu na"
Daga 'Yabbuga har yaran sai da mamakin Hansatu ya aure su, budar bakin Amina kuwa sai cewa ta yi,
"Kaiiii Umma ke burgeni wallah, dama haka nan zaki zanka yi wa Baba"
Wani kallo Hansatu ta mata, wanda ya sanya ta hadiye dariyar ta, suka shige ciki dukan su,
"In kin qare jin Isah zai tahiya Makka, sai a tai shiyya a baza"
Habaaa nan da nan kuwa 'Yabbuga ta hau bala'i ta na fadin yarinya qanwar bayan ta na kiran ta da munahika, a haka dai ta zare ta bar gidan, cike da borin kunya
Hansatu kuwa ta gama hada wa Isah kayan shi kafff a jaka, sabbin dinkunan da yayi, da takalma da duk wani abu da zai buqata su na akwati.
Shi kuwa ya gama hada goron shi da duk wani abu da zai buqata, ya daure ya aje, gobe kawai ya ke jira ta yi.
Daren ranar Isah ya mori jikin Hansatu kamar ba zai barta ba, Ita kuwa ta ci kuka kamar ba zata bar idanun ta su huta ba, zuciyar ta na matuqar zafi da quna, a duk sanda ta tuna gobe zai tafi, duk ta bi ta qular da Isah, amma ya danne, waya ya dauko aljihun rigar shi, yar qarama, me kyaun fasali, ya miqa mata.
Da a da ne ya bata da tayi murna, amma yau ji take kamar ya na bata takardar saki, ji take kamar ta na bankwana da shi na har abada ne, rabon Isah ya lallabata haka tun ta na amarya.
Ran Isah fa ya gama ɓaci yanzu, ya na bata waya ta na gani ta qi amsa ta na kuka, tsawa ya daka mata, sai da zanin da take ta share hawayen idanun ta ya kusan subucewa,
"Keeee ! Ki na barin kukan iskancin nan ko baki bari? Ban son shashancin banza da wofi za ki karba ko na ajiye aba ta?"
Hannu na rawa ta karba, tsabar kuka duhu duhu take gani, amma dole ta shanye shi, da alama ya gama kai wa maqura a hasala, kar kuma ya kai hannu.
************************
Da rana Hajiya ta aika mota, aka kwashi Isah da su Hansatu sai Sokoto, ta can za su tashi zuwa qasa me tsarki, Hansatu ta sha warning wajen Isah akan kukan da take, ya kuma shiga jikin ta da kyau ya zauna, dan haka ta kama bakin ta ta tsuke, ba abinda take da ya wuce addu'a.
Hansatu da yara basu koma gida ba, sai da Isah ya ga magariba ta kusa, shi ne ya ce a maida su, ai kuwa Hansatu me za ta yi in ba kuka ba, cikin jin haushin ta Isah ya ja hanun ta ya tura ta mota, duk ya matse mata hannun dan mugunta, amma bata kula ba.
Kudi ya debo a aljihun shi ya qirga dubu goma ya wurga mata, ya wuce abin shi, ba sallamar azziqi.
Hansatu kuwa tunda suka dau hanya take kuka, har suka isa gidan ta, Yaran kuwa farin ciki ne danqare a zukatan su, amma ba halin bayyanawa.
***********************
Bincike ya tsananta akan neman Mubaraka, hakan ya yi wa Lawwali dad'i, ya kuma kwantar masa da hankali, a qalla dai hukuma ta shiga lamarin, ya na saka ran za a gan ta.
Shi ma bai zauna ba, duk inda ya san ya dace ya je dan neman ta, bai gajiya ba, neman ta ya zama masa ibadar shi, tunda dama bai damu da ibadar ba.
Kwanan su uku basu hadu da Sultana ba, Ita kuwa ta na son ta dan ja aji ta ga ko zai neme ta, tunda ta gama bayyana masa me ke ran ta game da shi, amma shiru, ba waya ba saqo, ba kuma zuwa da kai.
Yau Lawwali a daji ya wuni, idanun shi na kan kowa da komai, ya kula da wani abu guda, wanda ya sanya shi zargin ko dai No 4 ba shi da lafiya, ko kuma ya na boye masa wani sirri, dan haka kiran shi ya sa a je a yi.
Lokacin da saqon kiran Lawwali ya riski No 4 ,ya shiga gingimemen tashin hankali, bai san sanda ya furta,
"Niiii? Mi an ka ce na yi???"
Da qarfi ya fadi hakan,
Da mamaki 'yar Aiken ta kalle shi, ta yi tafiyar ta.
Jikin shi na rawa zufa na digar masa ya tafi amsa kiran Oga.
Ko da ya shiga ya tadda Lawwali na qoqarin neman Network ya na son magana da Sultana.
Lawwali bai ko kalle shi ba ballantana ya san halin da yake ciki, cikin Muryar shi ta Oga Lawwali ya ce,
"Akwai matsala ne Taheer? Ina nufin gida lafiya suke ba bu matsala? Kwana biyu na ga baka cikin nutsuwar ka"
Wani qololo ne ya tokare wuyan No 4, da kyar ya furta,
"Ran ka shi dade Oga, diya ta ta ba lahiya, ina buqatar zuwa gida amma ba hali, Kuma kuddin waje na basu isa yin jinya"
Lawwali sai a lokacin ya kalle shi , akwai mamaki, wanne irin ciwo ke damun diyar shi da kudin da suke samu a kwanakin nan kamar hauka ba su isar shi? Lawwali bai tsananta bincike ba, ya miqe, ya bude inda yake aje kudi, ya ga babu, ya kai su can gidan shi na cikin gari.
"Baka da matsala, in dai kudi na Taheer, kar ka manta, tun ranar da mun ka hwara haduwa, na hwadi maka damuwar ka tauwa ta, ka zanka sanar da ni,mi zan yi da kuddi in ku baku wadata ba? Ka biyo ni gida na anjima mu tai ka amsa, kuma ka zauna wajen iyalin ka har sai sun samu lahiya"
Daga kai kawai No 4 ya yi, hawaye na zuba masa,tabbas in ya riqe wannan magana bai sanar da Lawwali ba, ya ci amanar Lawwali, domin shi ne ya jawo shi wannan harkar da suke samu, ya taimaka masa sanda mahaifiyar shi ba lafiya har aka mata dashen qoda,kuma shi ke temaka masa a duk sanda matsala ta iyali ta taso, amma ace a hada baki da shi a na cutar da shi?
Gashi in ya sanar da Lawwali sunan shi matacce, in ya bari Lawwali ya gano da kanshi su nan shi matacce, ya zai yi?
Jiki ba kwari ya fita, dukkanin abokan aikin shi sun kula da sauyin da ya koma da shi, ciki har da No 1 Dan haka waje ya ja shi, suka bar sansanin nasu gaba daya, su na zuwa qasan wata bishiya No 1 ya finciki No 4 su na fuskantar juna, ya ce,
"Ka sanar da oga komai ko?"
"Shi ne kai na da naka suke a jikin mu? Kai sake min taguwa ni, in ji da abinda ka damu na,"
Fizge kan shi ya yi, ya koma baya ya na shafa kan shi, cikin damuwa, da kyar ya furta,
"Na yi wa Oga qarya,...Oga ya min taimakon da ba wanda ya taba yi min shi a rayuwa, amma ina ha'intar shi, Oga ya min abinda ku ba ku min ba, yanzu ina cikin tsaka me wuya, in sanar da gaskiya in mutu, in yi shiru ya gano da kan shi in mutu, wa zai kula da ahali na?"
"Kai banza na wallah, ka manta kuddin da Excellency yayyi muna alqawari,sun ninka wanda Oga ya taba bamu a rayuwa,"
"Amma wanda ya taimake ka lokacin da ka ka buqatar taimako ba ya shi a rayuwa"
Wata dariyar mugunta No 1 ya yi, sannan ya daki kafadar No 4, ya ce,
"In ka na ganin rayuwar ka bata da anhwani dan Allah tai ka sanar da Oga inda qauna tai take"
Ya na gama fadar haka ya bar wajen, No 4 kuwa qara ya yi ta saki, ya na kuka, ya rasa ina zai saka ran shi, me ne ne makomar shi in ya sanar da Lawwali?
*Ku ba wa No 4 shawara mutan group ya na cikin tsaka mai wuya*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 29:
Lamishi ce zaune ta buga uban tagumi, hankalin ta ya fara tashi a 'yan kwana biyun nan, wai a ce dan mutum a neme shi a rasa kamar kwabo a tsakanin barayi?
Sallamar qawa kuma aminiyar ta ta ji, wato 'Yabbuga, nisawa ta yi kafin ta amsa, cikin jimami, 'Yabbuga ta ce,
"Ohhh ki na nan zaune in da na barki? Hummm Allah dai shi kyauta muna wanga lamari,...dazu ina ta so na tambaye ki, wai an ce jiya da bani nan na tai gidan su Dan jumma, wai diyar gwauna ta zaka? Mi ta zo yi halan?"
Cikin sanyin murya Lamishi ta ce,
"Ta zo ta ji ko an samu wani labari akan wannan yarinyar, ke san da shike sun saba,ta na son Mubaraka kwarai aran ta, ko jiyan ma sai da tayyi kuka da ni ce har yanzu shiru"
"Allahu akbar, rayuwa kenan, za a gan ta,ni da zuwa nayi ki taimaki wagga farar qahwa tawa ki sa min lalle, amma fa a gida na, dan ka na zaune baka san wa zai fado ba, se de ka ji ana gahwara kayya kayya" (Lawwali)
"Mi ki ka nuhi? Gidan namu gidan qauraye na?"
Kama bakin ta 'yabbuga ta yi ta ce,
"Uhmm uhmmm, ba ki ji wanga batu daga gare ni ba, ki na samin ko ah ah?"
"Ban wallah bin ki gida sa lalle, in ki na zama nan na sa miki Lalle tauuu, in baki zama yi ta tahiyar ki"
Kyabe baki 'Yabbuga ta yi ta zauna, lokacin azahar ya yi, madadin su bari su fara sallah, sai suka yi kamar basu ji ma kiran sallah da ake ba,kwaba lallen Lamishi ta yi, Yabbuga na ta uban surutu, rabin surutun zagin Mai Buruji ne, dan ma Lamishi na taka mata burki, ta kan ce, ta tsani me zagin kishiyar ta, domin watarana zai zage ta ita ma.
"Ni hwa ban ga lallen ga na kamu ba" inji Lamishi, Yabbuga tace,
"Ke dai bari shi yi awa guda ki na ganin yanda zai yi kyawu kwarai"
Su na tsaka da saka lalle Mai Buruji ta dawo daga aiki, ga lalle an qunshe wa 'Yabbuga hannu da qafa da shi, ko da Mai Buruji ta dakko kwanukan cin abinci yawu ya fara ambaliya a bakin 'yabbuga, ta ji haushi saka lallan nan a hannu, da ta sani da a qafa kawai aka saka mata.
Ko da aka raba aka zo cin abinci sau biyu Mai Buruji ta bawa 'yabbuga a baki, suka yi ta cin abin su suna hira, Lamishi ta ce Allah shi kiyashe ta bawa qatuwa abinci a baki.
Ran 'Yabbuga in ya yi dubu ya ɓaci, ta kame bakin nan ta gume shi gum, a haka gyangyadi ya dinga dibar ta.
************************
Shigar su gidan Lawwali ke da wuya, ya qirga kudi dubu dari biyar ya bawa No 4, No 4 kuwa cikin dakiya, da danne abinda ke ran shi,ya dinga murnar dole ya amsa ya na godiya.
Lawwali na ta kallon shi, kallon da Lawwali ke masa ne ya fara shiga kowanne lungu da saqo na jikin shi,cikin hanzari ya fara qoqarin tafiya, Lawwali kuwa zama ya yi a daya daga kujerun da suka zagaye madaidaicin parlourn , ya dora qafar shi daya saman daya,No 4 na kallon zaman da Lawwali ya yi, ya tabbatar ba lafiya, cikin sarqewar murya ya ce,
"Oga na tafi..se..se..see da swahe,"
Hannu kawai Lawwali ya daga masa, idanun shi sun kad'a sun yi jawur, qafafun No 4 na rawa ya nufi bakin qofar, ko da ya murda
Showing 54001 words to 57000 words out of 150481 words
Wannan kalamai sun sake birkita No 4, da kyar yake hadiyar yawu, zufa sai karyo masa take, a sati ukun nan, duk 'yar qibar ma da ya yi, saboda kudin da suke samu, duk ta zabge, ya fita hayyacin shi, ba wani kwanciyar hankali a tattare da shi.
Su Sultana kuwa a jikin motar shi, suka tsaya, su na magana, hira ce mai dadi,ta yaushe gamo suke yi, kusan kaso saba'in na hirar dukkan su akan Mubaraka su ke yi, Sultana na son mubaraka, ba wai dan ta na qanwar Lawwali ba,ah ah, yarinyar abar so ce ga duk mai hankali.
Shi kuwa a wajen shi Mubaraka ita ce rayuwar shi, a ganin shi ma ba zai taba samun kan Sultana ba in bata nan.
Bayan sun yi sallama za su tafi ne Sultana ta ce,
"Haka ake sallama da masoyi? "
Kallon yanda ta maida kai gefe ta yi, sai ta masa kyau, murmushi ya yi, kadan, wanda rabon shi da murmushi na gaskiya, ba na mugunta ba, tun kafin batan Mubarakan.
"Ya ya kamata masoyi ya yi sallama ?"
Dan rufe fuskar ta tayi da hannun ta kadan ta ce,
"Kamata ya yi ka ce, Sultana na tafi, zan dawo anjima, ina son ki"
Bude baki Lawwali ya yi, ya na dariya mai sassanyan sauti, ya ce,
"Kaiii ka kaiii ka kaiii, Baraka na ta ce man ke ustaziya ta wallah, ashe ke iya soyayya haka?"
Mayafin ta ta ja sosai ta rufe fuska sannan ta ce,
"To ai soyayya kowa na yi"
"Ok, to sultana Ina son ki,"
Wani irin dad'i ne ya ziyarce ta, musamman da ta kalle shi ta ga babu wasa a kalaman shi, iyakar gaskiyar shi yake fada, ta ji sautin Muryar shi, ba alamar gatse ko wasa, amayar da ta ta zuciyar ta ce,
"Auwal ina son ka, In na ce ina son ka, ba ina nufin ina son ka fiye da yanda kk so na bane, ina nufin ina son ka a kowanne hali, ina son ka ko da wani sabani ya haɗa mu, ina son ka ko da ka na cikin damuwar da ta sa ka nesanta da ni, ina son ka sama da nisan nan da ke tsakanin mu,ina son ka sama da yanda na ke jin zafin rashin ka a rai na, ina son ka sama da dukkan wani abu da zai qoqarin shiga tsakanin mu, ina nufin nafi son ka Auwal"
Ya Salam, Lawwali ya gama narkewa,kalaman sultana sun wanke masa wani kaso na baqin cikin da ke ran shi,dama haka take fata, shi ne dalilin da ya sanya ta cire kunya ta furta abinda ke ran ta, sai bayan ta gama kashe masa gabban jikin shi, ta juya da gudu gudu ta shige gida,dan kuwa kunyar shi ba zata bar ta ta tsaya jin me zai ce ba again.
Lawwali ya jima a wajen, kafin ya shiga motar shi, ya tada ya bar gidan.
Su No 1 kuwa ya na fita suma suka bar gidan, dan zuwa sauyawa su Mubaraka maboya kamar yanda Gwamna ya bada shawara, da kuma wajen zama.
Lawwali har ya isa gida bai dena murmushi ba, ya jima ya na dirzar dattin jikin shi,kafin ya samu abinci ya ci rabon shi da abinci sosai kamar na ranar ba zai iya fadin ga lokacin ba.
Ya na kammalawa ya kwanta, dan hutawa.
**********************
Vissa ta samu, na tafiyar Isah Saudiya, ana sauran kwana biyu tafiyar Isa, Hajiya ta sa Isan ya kai mata su Hansatu su gaisa, Hansatu ta sha mamakin jin duk abinda ke faruwa a bakin mahaifiyar ta, ace duk wadannan abubuwan na faruwa bata sani ba? Haka ta dinga yaqe ta na yabawa Isah ,tare da yanka qarya kala kala, dan ta kare shi, yaran ta na ta mamakin qaryar da take ta shinfidawa.
Ba daban ta basu tarbiyya mai kyau ba, tabbas da sun tona mata asiri, dan kuwa ba su so ta rufa masa asiri ba.
Isah kuwa sai murmushi yake ya na fadin,
"In ban muku ba wa zan wa?"
Yayan Hansatu ya qara masa dubu hamsin ya qara a kan jarin shi, sai godiya suke ta zabgawa.
Da yamma Hajiya ta sa mota ta maida su gida.
Tafiyar Isah Makka daiiii sauran kwana biyu, wace zata yi rakiya?????😂
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 28:
Kafin tafiyar Isah ya yi qoqarin ajiye musu buhun shinkafa, ya aje musu galan din man gyada da manja, galan daya daya, ya sai masu maggi, wake,barkono, da gishiri, ya sai musu taliya, su omo da sabulun wanka da wanki, rabon Hansatu da ta ga irin wannan kayan a hade waje daya, tun sanda suka yi aure, sai yau, kuka take ta yi, saboda rabuwa da masoyin ta.
Hajiya ta mata alqawarin zuwa da ita da yaran da Hajiyan kan ta,ta bata hakuri tare da lallashin ta akan ta bar shi ya tafi domin kasuwancin shi.
Yaran Isah kuwa murna suke da tafiyar tashi, har abun ya kasa boyuwa, garin murnar su da surutun da suke ne ya ja hankalin Yabbuga, da ta kasa kunne a cikin gidan, tun sanda ta ga ana shigar da kayan abinci.
Dan Jummaa ne ya wurge ta da dan qaramin dutse, ya ce,
"Ke hwasa zuwa gidan Kareema? Ina ta magana ke yi shiru"
"Bar tahiyar nan, zuwa gobe zan tai, wai shin dole na sai ka kaini? Mu na tahe saman mashin kamar 'yan bangar siyasa, ka yi tahiyar ka na yi tawwa"
"In baki hau bayan nawa ba, ai ke hau na wani qato, tau ki sani, walle baki zuwa ko ina in ba ni na zan kai ki ba, zancen banza zancen yohi"
Cikin fushi y fice ya bar gidan, Ita kuwa ko a jikin ta, kunnen ta na gidan Isah, so take ta ji kalmar da zata gama da wadda ta qunsa ta haɗa su bata ma'ana amma ta kasa.
Tsaki ta ja, ta zari mayafin ta, ta shuri takalman ta ta fice daga gidan ,ko jan qofa bata yi ba.
Ko sallama bata yi ba, haka ta afka gidan, karaf kuwa kunnen ta ya ji maganar Ahmad, ya na fadin, in baban su ya tafi Saudiya gobe a gado zai kwana.
Wani irin salati ta zabga, tare da tafa hannaye, Hansatu ce ta fito daga daki da gudu, ido ya mata jawur da alama kuka take.
"Lahiya? Mi ya hwaru halan? ",
"Yanzu ke Hansatu ina ganin ki shiru shiru ashe munahika ta? Ashe ke dauke ni maqiyyiyar ki da baki hwadi min mijin ki zai tahiya Makka, yau Allah ya sa ina da kunnuwan jin dumi, na jiyo daga wajen diyan ki, se qaqa?",
Cikin fushin da Hansatu bata san ta na da kalar shi ba ta kalli 'yabbuga ta ce,
"To sai qaqa kuwa? Ko ki na hana mai tahiyar na? Yo Ni na ji ikon Allah, komi na se na hwada miki? Tunda muke a matsayin ki na makwacciya ta ke taba zuwa ki tambayen shin na ci abinci Ni da diya na? Ko ke taba zuwa ki tambayen wane na abba lahiya cikin d'iya na ko niya? Haka d'ai ki dora min jidali? Don Allah dai ki barni na ji da abinda ka damu na"
Daga 'Yabbuga har yaran sai da mamakin Hansatu ya aure su, budar bakin Amina kuwa sai cewa ta yi,
"Kaiiii Umma ke burgeni wallah, dama haka nan zaki zanka yi wa Baba"
Wani kallo Hansatu ta mata, wanda ya sanya ta hadiye dariyar ta, suka shige ciki dukan su,
"In kin qare jin Isah zai tahiya Makka, sai a tai shiyya a baza"
Habaaa nan da nan kuwa 'Yabbuga ta hau bala'i ta na fadin yarinya qanwar bayan ta na kiran ta da munahika, a haka dai ta zare ta bar gidan, cike da borin kunya
Hansatu kuwa ta gama hada wa Isah kayan shi kafff a jaka, sabbin dinkunan da yayi, da takalma da duk wani abu da zai buqata su na akwati.
Shi kuwa ya gama hada goron shi da duk wani abu da zai buqata, ya daure ya aje, gobe kawai ya ke jira ta yi.
Daren ranar Isah ya mori jikin Hansatu kamar ba zai barta ba, Ita kuwa ta ci kuka kamar ba zata bar idanun ta su huta ba, zuciyar ta na matuqar zafi da quna, a duk sanda ta tuna gobe zai tafi, duk ta bi ta qular da Isah, amma ya danne, waya ya dauko aljihun rigar shi, yar qarama, me kyaun fasali, ya miqa mata.
Da a da ne ya bata da tayi murna, amma yau ji take kamar ya na bata takardar saki, ji take kamar ta na bankwana da shi na har abada ne, rabon Isah ya lallabata haka tun ta na amarya.
Ran Isah fa ya gama ɓaci yanzu, ya na bata waya ta na gani ta qi amsa ta na kuka, tsawa ya daka mata, sai da zanin da take ta share hawayen idanun ta ya kusan subucewa,
"Keeee ! Ki na barin kukan iskancin nan ko baki bari? Ban son shashancin banza da wofi za ki karba ko na ajiye aba ta?"
Hannu na rawa ta karba, tsabar kuka duhu duhu take gani, amma dole ta shanye shi, da alama ya gama kai wa maqura a hasala, kar kuma ya kai hannu.
************************
Da rana Hajiya ta aika mota, aka kwashi Isah da su Hansatu sai Sokoto, ta can za su tashi zuwa qasa me tsarki, Hansatu ta sha warning wajen Isah akan kukan da take, ya kuma shiga jikin ta da kyau ya zauna, dan haka ta kama bakin ta ta tsuke, ba abinda take da ya wuce addu'a.
Hansatu da yara basu koma gida ba, sai da Isah ya ga magariba ta kusa, shi ne ya ce a maida su, ai kuwa Hansatu me za ta yi in ba kuka ba, cikin jin haushin ta Isah ya ja hanun ta ya tura ta mota, duk ya matse mata hannun dan mugunta, amma bata kula ba.
Kudi ya debo a aljihun shi ya qirga dubu goma ya wurga mata, ya wuce abin shi, ba sallamar azziqi.
Hansatu kuwa tunda suka dau hanya take kuka, har suka isa gidan ta, Yaran kuwa farin ciki ne danqare a zukatan su, amma ba halin bayyanawa.
***********************
Bincike ya tsananta akan neman Mubaraka, hakan ya yi wa Lawwali dad'i, ya kuma kwantar masa da hankali, a qalla dai hukuma ta shiga lamarin, ya na saka ran za a gan ta.
Shi ma bai zauna ba, duk inda ya san ya dace ya je dan neman ta, bai gajiya ba, neman ta ya zama masa ibadar shi, tunda dama bai damu da ibadar ba.
Kwanan su uku basu hadu da Sultana ba, Ita kuwa ta na son ta dan ja aji ta ga ko zai neme ta, tunda ta gama bayyana masa me ke ran ta game da shi, amma shiru, ba waya ba saqo, ba kuma zuwa da kai.
Yau Lawwali a daji ya wuni, idanun shi na kan kowa da komai, ya kula da wani abu guda, wanda ya sanya shi zargin ko dai No 4 ba shi da lafiya, ko kuma ya na boye masa wani sirri, dan haka kiran shi ya sa a je a yi.
Lokacin da saqon kiran Lawwali ya riski No 4 ,ya shiga gingimemen tashin hankali, bai san sanda ya furta,
"Niiii? Mi an ka ce na yi???"
Da qarfi ya fadi hakan,
Da mamaki 'yar Aiken ta kalle shi, ta yi tafiyar ta.
Jikin shi na rawa zufa na digar masa ya tafi amsa kiran Oga.
Ko da ya shiga ya tadda Lawwali na qoqarin neman Network ya na son magana da Sultana.
Lawwali bai ko kalle shi ba ballantana ya san halin da yake ciki, cikin Muryar shi ta Oga Lawwali ya ce,
"Akwai matsala ne Taheer? Ina nufin gida lafiya suke ba bu matsala? Kwana biyu na ga baka cikin nutsuwar ka"
Wani qololo ne ya tokare wuyan No 4, da kyar ya furta,
"Ran ka shi dade Oga, diya ta ta ba lahiya, ina buqatar zuwa gida amma ba hali, Kuma kuddin waje na basu isa yin jinya"
Lawwali sai a lokacin ya kalle shi , akwai mamaki, wanne irin ciwo ke damun diyar shi da kudin da suke samu a kwanakin nan kamar hauka ba su isar shi? Lawwali bai tsananta bincike ba, ya miqe, ya bude inda yake aje kudi, ya ga babu, ya kai su can gidan shi na cikin gari.
"Baka da matsala, in dai kudi na Taheer, kar ka manta, tun ranar da mun ka hwara haduwa, na hwadi maka damuwar ka tauwa ta, ka zanka sanar da ni,mi zan yi da kuddi in ku baku wadata ba? Ka biyo ni gida na anjima mu tai ka amsa, kuma ka zauna wajen iyalin ka har sai sun samu lahiya"
Daga kai kawai No 4 ya yi, hawaye na zuba masa,tabbas in ya riqe wannan magana bai sanar da Lawwali ba, ya ci amanar Lawwali, domin shi ne ya jawo shi wannan harkar da suke samu, ya taimaka masa sanda mahaifiyar shi ba lafiya har aka mata dashen qoda,kuma shi ke temaka masa a duk sanda matsala ta iyali ta taso, amma ace a hada baki da shi a na cutar da shi?
Gashi in ya sanar da Lawwali sunan shi matacce, in ya bari Lawwali ya gano da kanshi su nan shi matacce, ya zai yi?
Jiki ba kwari ya fita, dukkanin abokan aikin shi sun kula da sauyin da ya koma da shi, ciki har da No 1 Dan haka waje ya ja shi, suka bar sansanin nasu gaba daya, su na zuwa qasan wata bishiya No 1 ya finciki No 4 su na fuskantar juna, ya ce,
"Ka sanar da oga komai ko?"
"Shi ne kai na da naka suke a jikin mu? Kai sake min taguwa ni, in ji da abinda ka damu na,"
Fizge kan shi ya yi, ya koma baya ya na shafa kan shi, cikin damuwa, da kyar ya furta,
"Na yi wa Oga qarya,...Oga ya min taimakon da ba wanda ya taba yi min shi a rayuwa, amma ina ha'intar shi, Oga ya min abinda ku ba ku min ba, yanzu ina cikin tsaka me wuya, in sanar da gaskiya in mutu, in yi shiru ya gano da kan shi in mutu, wa zai kula da ahali na?"
"Kai banza na wallah, ka manta kuddin da Excellency yayyi muna alqawari,sun ninka wanda Oga ya taba bamu a rayuwa,"
"Amma wanda ya taimake ka lokacin da ka ka buqatar taimako ba ya shi a rayuwa"
Wata dariyar mugunta No 1 ya yi, sannan ya daki kafadar No 4, ya ce,
"In ka na ganin rayuwar ka bata da anhwani dan Allah tai ka sanar da Oga inda qauna tai take"
Ya na gama fadar haka ya bar wajen, No 4 kuwa qara ya yi ta saki, ya na kuka, ya rasa ina zai saka ran shi, me ne ne makomar shi in ya sanar da Lawwali?
*Ku ba wa No 4 shawara mutan group ya na cikin tsaka mai wuya*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 29:
Lamishi ce zaune ta buga uban tagumi, hankalin ta ya fara tashi a 'yan kwana biyun nan, wai a ce dan mutum a neme shi a rasa kamar kwabo a tsakanin barayi?
Sallamar qawa kuma aminiyar ta ta ji, wato 'Yabbuga, nisawa ta yi kafin ta amsa, cikin jimami, 'Yabbuga ta ce,
"Ohhh ki na nan zaune in da na barki? Hummm Allah dai shi kyauta muna wanga lamari,...dazu ina ta so na tambaye ki, wai an ce jiya da bani nan na tai gidan su Dan jumma, wai diyar gwauna ta zaka? Mi ta zo yi halan?"
Cikin sanyin murya Lamishi ta ce,
"Ta zo ta ji ko an samu wani labari akan wannan yarinyar, ke san da shike sun saba,ta na son Mubaraka kwarai aran ta, ko jiyan ma sai da tayyi kuka da ni ce har yanzu shiru"
"Allahu akbar, rayuwa kenan, za a gan ta,ni da zuwa nayi ki taimaki wagga farar qahwa tawa ki sa min lalle, amma fa a gida na, dan ka na zaune baka san wa zai fado ba, se de ka ji ana gahwara kayya kayya" (Lawwali)
"Mi ki ka nuhi? Gidan namu gidan qauraye na?"
Kama bakin ta 'yabbuga ta yi ta ce,
"Uhmm uhmmm, ba ki ji wanga batu daga gare ni ba, ki na samin ko ah ah?"
"Ban wallah bin ki gida sa lalle, in ki na zama nan na sa miki Lalle tauuu, in baki zama yi ta tahiyar ki"
Kyabe baki 'Yabbuga ta yi ta zauna, lokacin azahar ya yi, madadin su bari su fara sallah, sai suka yi kamar basu ji ma kiran sallah da ake ba,kwaba lallen Lamishi ta yi, Yabbuga na ta uban surutu, rabin surutun zagin Mai Buruji ne, dan ma Lamishi na taka mata burki, ta kan ce, ta tsani me zagin kishiyar ta, domin watarana zai zage ta ita ma.
"Ni hwa ban ga lallen ga na kamu ba" inji Lamishi, Yabbuga tace,
"Ke dai bari shi yi awa guda ki na ganin yanda zai yi kyawu kwarai"
Su na tsaka da saka lalle Mai Buruji ta dawo daga aiki, ga lalle an qunshe wa 'Yabbuga hannu da qafa da shi, ko da Mai Buruji ta dakko kwanukan cin abinci yawu ya fara ambaliya a bakin 'yabbuga, ta ji haushi saka lallan nan a hannu, da ta sani da a qafa kawai aka saka mata.
Ko da aka raba aka zo cin abinci sau biyu Mai Buruji ta bawa 'yabbuga a baki, suka yi ta cin abin su suna hira, Lamishi ta ce Allah shi kiyashe ta bawa qatuwa abinci a baki.
Ran 'Yabbuga in ya yi dubu ya ɓaci, ta kame bakin nan ta gume shi gum, a haka gyangyadi ya dinga dibar ta.
************************
Shigar su gidan Lawwali ke da wuya, ya qirga kudi dubu dari biyar ya bawa No 4, No 4 kuwa cikin dakiya, da danne abinda ke ran shi,ya dinga murnar dole ya amsa ya na godiya.
Lawwali na ta kallon shi, kallon da Lawwali ke masa ne ya fara shiga kowanne lungu da saqo na jikin shi,cikin hanzari ya fara qoqarin tafiya, Lawwali kuwa zama ya yi a daya daga kujerun da suka zagaye madaidaicin parlourn , ya dora qafar shi daya saman daya,No 4 na kallon zaman da Lawwali ya yi, ya tabbatar ba lafiya, cikin sarqewar murya ya ce,
"Oga na tafi..se..se..see da swahe,"
Hannu kawai Lawwali ya daga masa, idanun shi sun kad'a sun yi jawur, qafafun No 4 na rawa ya nufi bakin qofar, ko da ya murda
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19 Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51