so kowa ya zauna lafiya, da sauran kalamai munana marasa dad'in saurara.
Da misalin qarfe uku na rana suka koma gida, Sultana ta so lokacin tashin su Mubaraka bai wuce ba su dauko ta, haka nan take jin son yarinyar, ta alaqanta hakan da ilimin da ta kula Mubaraka na da shi.
Sun isa gida sun tarar da Mubaraka ta kwaso wankin kayan sultana daga ɓangaren wanki na gidan, za ta mayar cikin gida.
Ko a fuska ran Lawwali bai ɓaci ba, tunda Mubaraka ma bata da damuwa akan hakan, shi dai ko ma mene zatai ya zama ta na son abun, da kuma dukkan alama ta na jin dadin aikin, ba bacin rai a fuskar ta, sai ma walwala.
Da hanzari ta aje kayan ta nufe shi, tare da yi musu sannu da zuwa baki dayan su, jakar Sultana ta amsa, sai sultana ta riqe, cikin murmushi ta ce,
"Na gode, na hutar da ke, kar gatan ya min yawa, ga wanki kin debo, a ina za ki riqe jaka? In yau kin kai min gobe wa zai kai min?"
"Ko Ni Kin kai wa izini har ciki sai in kai miki, ballantana Mubaraka,"
Kallon Lawwali Sultana ta yi, tare da sakin murmushi mai kyau, ta wuce ciki, ta na shiga suka tafa,
"Yah Auwal da alama Aunty Sultana na yin ka hwa, ka ga wani murmushi da tayyi maka?"
"Allah ya sa, wannan murmushi halayyar ta ne, kowa ma yi mishi ta kai, Allah shi nuna min ta yi min irin wanda ni kai mata,....ke ci abinci?"
"Ameeen Yah Auwal, eh na ci abinci ,kafin Mama(Mai Buruji) ta tafi gida ta ban abinci, nima na kusan gamawa, wankin sultana kawai zan je in isuwa"
"Tau ya yi, In ke qare ki yi min magana, zan jira ki can garka, mu tai gidana, da kai na zan maishe ki gida, dazu na tai gida ai"
Nan ya bata labarin me ya faru tsakanin shi da Lamishi, idanun ta ne suka kawo ruwa ta ce,
"Ni dai dama baka tai ba wallah, yanzu ta na iya gwada min bone kan haka da kai, ya kamata ka rage kulawa da ni, tunda bata son haka nan"
Wani kallon baki da hankali ya mata, sannan ya duqa ya dauki kwandon wankin, ya dora Mata akai, ya tallabe qeyar ta cikin wasa, yar qara ta saki, ya mata gwalo ya tafi, tare da sanar da ita yana jiran ta, sultana da ke tsaye jikin window'n dakin ta ne,ta saki labule, ta na murmushi, su na burge ta sosai.
Har dakin sultana Mubaraka ta shiga, bayan ta yi sallama, ta bata izinin shiga, ita ta jera mata kayan inda ya dace ,sannan ta tambaye ta ko da abinda zata mata?
"Babu komai, amma ina so na tambaye ki,"
"Allah ya sa na sani"
"Inshaa Allah, kin ma sani, Ni kuwa na ce, ke da Auwal maman ku daya Abban ku daya?"
Da kallo Mubaraka ta bi Sultana........
Kallon da ya gajiyar da ni burutu😂😂
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 19:
"Yaya na ne, uwar mu guda uban mu guda da shi, amma ya girme ni sosai, mu na da wasu qannen maza ne su, guda biyu,"
Ajiyar zuciya sulatana ta sauke, sannan ta yi murmushin ta da ke qawata kyaun fuskar ta ta ce,
"Masha Allah, makarantar ku guda da qannen naki?"
"Ai su Jameelu ba su zuwa makaranta,yawon su kawai suke a unguwa, duk gidan mu ni kadai ta ka zuwa makaranta"
Gyara zama Sultana ta yi, cikin rashin fahimta ta ke kallon Mubaraka da ke mata bayani,
"Yah Auwal ya yi karatun allo, har ya kai ga sauke qur'ani, kamar yanda na ji labari, amma ban taba jin labarin ya yi boko ba, zama da masu ilimi na ya sanya shi koyon karatu da rubutu, sannan ya iya turanci kad'an, amma bai je makaranta ba, ni kuma kin ga wadda karatun nawa shi ke, yau in an bar ni na tai, gobe ba zani ba,su Jameelu kuwa ba su ko son zuwa makarantar Allah balle ta bature"
"Ikon Allah, zan so zuwa shiyyar ku niga wadda take, watarana"
"Kai ka kaiii, lallai ko da mun ji dad'i mara misali, ace ke da kan ki kin tai shiyyar mu,ko ba dan matsayin da ki ke da shi ba ma, domin kyawun halin ki da kullum Umman mu ke fad'a a shiyyar mu"
"Mubaraka kenan, to ni din wata ce daban? Ni ma mutum ce kamar kowa na duniya, a duniya babu wanda ya fi wani, sai wanda ya fi tsoron Allah, yawan dukiya, matsayi, muqami duk ba su na mutum ba, tsoron Allahn da bawa shike da shi, da kuma kyakkyawar mu'amala su ka yin mutum, ke gane?"
Daga kai Mubaraka ta yi, sannan ta ce,
"Aunty in tambaye ki? Dan Allah kar ran ki ya ɓaci da tambaya ta"
Kada kai Sultana ta yi, sannan ta bada hankalin ta ga kallon Mubaraka.
"Aunty yaushe na zaki aure?"
Dariya ce ta kwacewa sultana , ta ce,
"Mubaraka kenan, ni da ko saurayi ban da wa zan aura?"
Zaro ido Mubaraka ta yi cike da mamaki, sannan ta ce,
"Aunty ko dai ke ta baki kula su? Ko ni din nan, maza na cewa su na qauna ta, balle ke, aunty Sultana ke gane ki kuwa? Wa zai ce ba shi son mace kamar ki?"
Murmushi kawai sultana ta yi, domin ita maganar ma saurayi ko miji bata gaban ta tun da can, a kullum damuwar ta be wuce ta ga yanda zata fara aiki dan ta koyar da al'umma abinda Allah ya sanar da ita ba, sannan ta bude gidauniya ta na taimakon mutane, to yanzu ta samu buri d'aya ya cika, wataqila za ta duba maganar aure a nan gaba, domin maganar lecturing da take son yi da alama ba zai samu ba.
Lokaci Mubaraka ta kalla, ta ga ya tafi sosai, har hudu da rabi,da sauri ta miqe tsaye,
"Subhanallahi, na manta Yah Auwal na waje ya na jira na, na tsaya surutu"
"Jiran ki kuma? Yanzu ki na nufin sai mutum kamar Auwal ya tsaya jiran ki? Namiji ne fa, ba su son jira"
Murmushi mai dauke da tsantsar so da qauna Mubaraka ta yi, sannan ta ce,
"Aunty Sultana, ina so ki sa ido akan Yayana da kyau, a hankali za ki san wane ne wannan Auwal din, Yah Auwal daban shike cikin maza"
A bakin qofa Sultana ta tsaya, dan sauraron Mubaraka ba ta san ma ta na bin ta ba.
"Zan sa ido na biyu akan Yah Auwal din ki Mubaraka, sai gobe, ki gaishe da Lamishi da jiki"
"za ta ji"
A gurguje ta fita daga katafaren gidan, a zaune ta tadda shi a saman kujera ya na bacci, tsinke ta samu ta saka masa a hankali a qofar hanci, ai kuwa atishawa ya saki mai qarfi, miqewa ta yi ta na dariya, daga baya ta kama kunnen ta ta na bashi hakuri, kama ta ya yi, ya daga hannu kamar zai mare ta, cikin wasa ya san daki kuncin ta kadan, suka yi wa masu gadin qofar gidan da ke kallon su cikin sha'awa sallama, suka fita.
Sultana bata bar jikin window ba har sai da ta daina hango su, fuskar ta dauke da annuri ta fada wanka.
A hanya kuwa Mubaraka ta kwashe duk yanda sukai da Sultana ta sanar da Lawwali, murna a wajen shi kamar har ta ce masa ta na son shi.
Ko da suka isa gidan shi, sai da suka ci suka sha, ta yi wanka, ta maida kayan da ta cire, suka dauki yar qarama kuma tsadaddar motar shi da gwamna ya sai masa, tunda yanzu ba ya cikin tawagar su ta daji,ya na buqatar mota, ko da fitar gaggawa ta kama.
A motar suka isa gida, kafin su shiga Mubaraka ta lallaba shi ya sai balangu mutumin Lamishi, har da kaza da madara, suka isa.
Ko da suka shiga gidan shiruuu, ba kowa, ajiye ledojin hannun ta tayi, ta lelleqa, ba kowa da gaske, to ina suka je? Ina ita Lamishi me jinya?
Tsaki ya ja, sannan ya zauna su ka hau hira, ita kuma ta duba ko akwai abincin dare, ko se ta ɗora, gani ta yi akwai a flask, da zai ishe su, na gidan gwamna ne, dan haka ajiye naman ta yi, ta ce in sun dawo daga duk inda suka je an ci.
"Ke da kissani? Ta na can yawon gulma"
"Yah Auwal ina fada maka ka dinga tausasa harshen ka ga uwayen ka, umma ka ke fadin ta tai gulma"
Irin abun nan ya yi na 'yan mata masu yanga, ya murguda baki, ya yi fari, shi a dole an masa fada.
Dariya ta yi, ta ce,
"Dama Aunty sultana ta gan ka"
"Ki na ganin duk mun ka hadu in yi mata haka nan? Za ta so ni?",
"Walle ba ruwa na, in tayi shiri shiri kwancin kwana ta shere ka mari, ka gan ka kuwa? Awab-budurwa wallah"(ba ruwa na in ta yi kwance kwance ta kwad'a ma mari, ka ganka kuwa kamar budurwa)
Dariya sukai ta yi, har Dan Talo ya shiga gidan a gaggauce, buta ya dauka dan zagawa, Lawwali na ganin shi,ya miqe ya daure fuska,
"Lawwali, ai na hango motar ka ne, muna dawowa daga garkar Yahai, nicce bari na zo, ko zan samu wani abu, bari na hito daga yauce, (bayan gida)"
Ya na fadawa bayi, Lawwali ya zaro dubu biyar ya ba Mubaraka Ya ce,
"Amshi ki ba uban nan nawa me kwadayi, in ya hito daga tutun wahala, ban jira nai wallah, na tafi nemo yaki halal yaki haram din da suka so"
Magana ya ke kamar da wasa, amma cikin zuciyar shi zafi take, a ce iyayen ka basu damu da inda ka ke samo kudi ba, kuma da ganin Lawwali sun san dai ba aikin jima yake ba ko kafinta, ko dako, balle aikin office, Amma kullum nema suke a wajen shi, kuma basu yake, manyan kudi ma kuwa, se kace wani babban ma'aikaci, ko babban ma'aikaci watarana ya na zama bai da shi.
Mubaraka da ke tsaye cikin tausayin Yayan nata ne ta amshi kudin, ta na so ta bashi ko da hakuri ne, dan ta san ya yake ji, amma ya fice, tun kan ta ce komai.
Dan Talo da ya fito ya ga ba Lawwali, a zaton shi ya tafi ne, nan da nan kuwa ya hau ashar, ya na kiran lawwali da sunaye marasa dadin ji.
"Gashi hwa, ya bar maka kuddin, ya dai tafi ne an kira shi ga waya"
Baki Dan Talo ya washe, ya na kuma godiya, soke su ya yi, a sassan aljihun jikin shi, sannan ya fita.
Girgiza kai Mubaraka ta yi kawai, ta na nema ma ahalin ta shiriya.
***********************
Su Lamishi kuwa su na gidan Isah, Yabbuga nan ta tattare su suka fada, har da Asshibi, yau ta samu leqa gidajen shiyya, duk gidajen mutuncin unguwar ba d'aya da Yabbuga ta raka ta, sai nasu ya nasu.
Qarshe da suka shiga gidan Lamishi suka gaisa shi ne suka rankaya gidan Hansatu gaba dayan su.
Sun tadda Isah na gida, sun gaisa su na ta wani hira kamar sun samu abokin su, kafin daga baya ya fada daki, da fita zai amma ya fasa,Hansatu kuwa ta gama dafa shinkafa da wake, ya ji yaji mai dadi, ga man ya samu matsayi har albasa aka saka masa.
Nan dai Yabbuga uwar kwadai ta hau yaba qamshin girkin, Ita kuwa Hansatu jin haka ya sa dole ta debar musu, haqqin su ne sun ji qamshi tunda akwai ta zuba musu. (Da damar mutane rowa ta saka ba su damuwa da haqqin maqoci, a yi girki mai dadi, me qamshi a lashe a sude hannu, wasu ma maqotan su talakawa ne, amma ba za su sammusu ba, duk da dai yanzu duniya ta sauya, ka na iya bawa mutum dan Allah da haqqin maqotaka, ya ce dan a san ka na cin dadi ka bayar, amma ka tsarkake zuciyar ka ka bayar, mutum shi ya sani da ya maka sharri, sannan wasu in suka ga ana basu, sai su fara zaqewa da roqo, har mutum ya koma boye abu ya na rowa, da ace kowa zai gyara da an zauna lafiya)
Su na kai loma su na zuba hira, rabi da kwatan hirar bata wuce ta auratayya ba, Isah na daki ya na jin su, ya na kuma jin dadin hirar saduwar auren da suke ta yi, Hansatu kuwa sai fada masu take, su yi a hankali mijin ta na ciki, Matar Yahai na bude baki kuwa, sai da ta fadi maganar da ta sa Hansatu shiga wani irin hali na matsananciyar kunya, su kuwa suka sheqe da dariya, Asshibi kuwa sai ta ji matan sun kwanta mata a rai,dan kuwa wajen hirar banza ta fi kauri dama.
Hansatu ta gaji da jin maganganun su, masu sanya ta kunya, cikin tattausan lafazi ta ce,
"Wai ku in tambaye ku? Me ne ne jigo a rayuwar aure ne?"
"Saduwa mana heeeeee casssss"
Suka yi shewa tare da tafawa, Isah kuwa dake daki, har sake gyara kwanciya ya yi, ya na sauraron su.
Zama Hansatu ta gyara ta ce,
"Tabbas saduwa daya ce daga jigon da ka sa a yi aure, amma ba ita kad'ai ba ce jigo a gidan aure ba, abubuwan na da yawa, su din ginshiqai na da ka riqon aure, in babu su da tuni aurarraki da dama sun watse.
Na farko akwai yin auren ma shi kan shi domin Allah, sannan Yarda, riqon amana, saduwa, ladabi, biyayyah, soyayya, qauna, tausayi, ciyarwa,tufatarwa, wajen zama,girmama juna, qimanta juna, mutunta juna, tausayawa juna,iya girki,da wasu mahimmai dai.
Wa'yanga abubuwa in suka hadu, aure ya ginu, ya zauna kenan sai dai in ajali nai na ya yi.
Na fahimci me ya sa kuke ganin kamar saduwa ita ce kad'ai abinda ka riqe aure, ba komai na yasa ba saboda fadi da ankai cewar,Aure shike hada wata alaqa, tsakanin mace da namiji, wannan shi na nufin hade rayuwarsu ta zama daya haka nan kuma makomarsu ta kasance guda daya. Kowacce irin al'ummah akwai irin matsayin da ta ba wa aure, Aure a musulinci wani daurine da shike halatta wa ma'aurata mace da namiji jin dad'i da junansu, ta hanyar saduwa irin ta jima'i,da sauran mu'amaloli na jin dadin saduwa, Allah (subbahanawu wa ta'ala) ya halicci mace daga hakarkarin namiji ya kuma sanya soyayya da tausayi a tsakaninsu.
Wannan babban dalili ne da zai sa ku ga kamar saduwa tahi komai a aure, amma duk wadda bata iya kula da miji ba, ta hanyoyi da dama, musamman iya girki, tsafta, kwalliya, ladabi da biyayya, bata iya magana ba, komi yattaho bakin ta hwadi takai, to wallahi mace na da saura a gidan aure ba ta iya komi ba"
Gaba dayan su har Isah da ke kwance, hansatu ta basu mamaki, ba mace ba ce me yawan Suratu, amma sai gashi yau ta yi magana cikin ilimi da nutsuwa da fasaha.
Mai Buruji ce ta fara yunqurawa ta miqe ta na sude hannu,
"Tauuuu, Mallamar gidan aure mun gode da wanga ilimi da munka samu, bari mu tai mu dora a gidan mu mu ma ko mun zam matan so ga mazajen mu kamar ke, mun gode da wake da shinkahwa ke iya girki, shi yasa Isah ba shi iya cin abinci ko ina, sai gida "
Dariya suka kwashe da ita, da shewa, dan kuwa magana Mai Buruji ta gaya wa Hansatu, ita da ake jibga kuma ake zagi kowa na ji, ita ke musu bayani haka.
Murmushi mai ciwo Hansatu ta yi, sannan ta ce,
"Ai duk abinda na fad'a maku ba qarya ciki, ballantana ki fad'a min magana, kuma ko da na fad'a ban ce ni ina aikata su ba,sannan ban ce ina da wani cikakken matsayi a wajen miji na ba, ballantana ya zama abin yi min arashi,"
Yabbuga ce ta taimaka wa Lamishi ta miqe, sannan ta kalli Hansatu ta ce,
"Keee wagga kwantas kin ga gida munkai yanzu, shiga daki ki lallaba Isah dan kuwa duk ya walqita ya ga ba shinkahwar ga se ke mance da kin taba sanin mi na na ma'anar aure a musulunci"
Dariya suka fita su na mata, kafin su rabu sai da suka yi ta gulmar ta, Yabbuga na basu labarin yanda yake dukan ta da zagin ta, akan abu qalilan.
*Shin a maganganun Hansatu akwai gyara ne mutanen kwarai? In akwai gyara ko qarin haske akan zamantakewar aure a qaro mana ilimi*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 20:
Mata kala kala ne a duniya, musamman ta bangaren kwalliya, da gyaran jiki, kowacce mace da hanyar da take bi dan ganin ta yi kyau.
Akwai wacce za ta yi gyaran jiki da kaya irin namu na gida da muke amfani da shi yau da kullum, kamar su lalle, dankalin turawa, sugar ,kwai, cucumber, tumatur, gwanda, Madara, lemo, zuma da sauran su, wadannan kadai sun ishe ta ba tare da ta yi kwalliya ba.
Wata ta kuma kayan wanka na Bature kawai sun ishe ta, ba tare da kwalliya ba.
Wata kuma ta na haɗawa duka , ta kuma qara da kwalliya.
Sultana na daga cikin matan da basu damu da gyaran jiki da kayan amfanin yau da kullum ba, ta fi amfani da kayan gyaran jiki na Bature, masu gyara asalin fatar mutum ba tare da ta sanya shi fari ba, (wannan shi ne aji da waye wa, bleaching qauyanci ne da zubar da kuma da mutunci ga mai hankali amma tare da nuna wa Allah be iya ba, ya tauye ki, ke bari ki wa kan ki abinda ya gaza wa'iyadhubillah).
Yau tun da Sultana ta fito daga wanka,ta ke tunanin wanne kaya za ta saka dan ta yi kyau, me za ta yi wa fuskar ta dan ta qayata ta?
Ta jima zaune a dan qaramin table din, ta na shafe shafen mayuka da turaruka masu sanyin qamshi, yau ce rana ta farko da ta fara shafa kwalli, tare da shafa powder har dikin wuyan ta, jan baki ta jera a gaban ta ta na tunanin wanne za ta shafa, kalar purple mai haske ne idon ta ya sauka akai, dauka ta yi ta goga kadan, sannan ta hade kyawawan labban ta, kallon kan ta tayi a madubi, ganin yanda ta yi kyau ne ya sanya ta sakin murmushi mai laushi.
Maskara ta shafa ma gashin idon ta mai yalwa, ta gyara girar ta, abun shafa powder ta sake dauka ta gyara ko ina na fuskar ta.
Kallon wayar ta ta yi, ta ga
Showing 30001 words to 33000 words out of 150481 words
Da misalin qarfe uku na rana suka koma gida, Sultana ta so lokacin tashin su Mubaraka bai wuce ba su dauko ta, haka nan take jin son yarinyar, ta alaqanta hakan da ilimin da ta kula Mubaraka na da shi.
Sun isa gida sun tarar da Mubaraka ta kwaso wankin kayan sultana daga ɓangaren wanki na gidan, za ta mayar cikin gida.
Ko a fuska ran Lawwali bai ɓaci ba, tunda Mubaraka ma bata da damuwa akan hakan, shi dai ko ma mene zatai ya zama ta na son abun, da kuma dukkan alama ta na jin dadin aikin, ba bacin rai a fuskar ta, sai ma walwala.
Da hanzari ta aje kayan ta nufe shi, tare da yi musu sannu da zuwa baki dayan su, jakar Sultana ta amsa, sai sultana ta riqe, cikin murmushi ta ce,
"Na gode, na hutar da ke, kar gatan ya min yawa, ga wanki kin debo, a ina za ki riqe jaka? In yau kin kai min gobe wa zai kai min?"
"Ko Ni Kin kai wa izini har ciki sai in kai miki, ballantana Mubaraka,"
Kallon Lawwali Sultana ta yi, tare da sakin murmushi mai kyau, ta wuce ciki, ta na shiga suka tafa,
"Yah Auwal da alama Aunty Sultana na yin ka hwa, ka ga wani murmushi da tayyi maka?"
"Allah ya sa, wannan murmushi halayyar ta ne, kowa ma yi mishi ta kai, Allah shi nuna min ta yi min irin wanda ni kai mata,....ke ci abinci?"
"Ameeen Yah Auwal, eh na ci abinci ,kafin Mama(Mai Buruji) ta tafi gida ta ban abinci, nima na kusan gamawa, wankin sultana kawai zan je in isuwa"
"Tau ya yi, In ke qare ki yi min magana, zan jira ki can garka, mu tai gidana, da kai na zan maishe ki gida, dazu na tai gida ai"
Nan ya bata labarin me ya faru tsakanin shi da Lamishi, idanun ta ne suka kawo ruwa ta ce,
"Ni dai dama baka tai ba wallah, yanzu ta na iya gwada min bone kan haka da kai, ya kamata ka rage kulawa da ni, tunda bata son haka nan"
Wani kallon baki da hankali ya mata, sannan ya duqa ya dauki kwandon wankin, ya dora Mata akai, ya tallabe qeyar ta cikin wasa, yar qara ta saki, ya mata gwalo ya tafi, tare da sanar da ita yana jiran ta, sultana da ke tsaye jikin window'n dakin ta ne,ta saki labule, ta na murmushi, su na burge ta sosai.
Har dakin sultana Mubaraka ta shiga, bayan ta yi sallama, ta bata izinin shiga, ita ta jera mata kayan inda ya dace ,sannan ta tambaye ta ko da abinda zata mata?
"Babu komai, amma ina so na tambaye ki,"
"Allah ya sa na sani"
"Inshaa Allah, kin ma sani, Ni kuwa na ce, ke da Auwal maman ku daya Abban ku daya?"
Da kallo Mubaraka ta bi Sultana........
Kallon da ya gajiyar da ni burutu😂😂
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 19:
"Yaya na ne, uwar mu guda uban mu guda da shi, amma ya girme ni sosai, mu na da wasu qannen maza ne su, guda biyu,"
Ajiyar zuciya sulatana ta sauke, sannan ta yi murmushin ta da ke qawata kyaun fuskar ta ta ce,
"Masha Allah, makarantar ku guda da qannen naki?"
"Ai su Jameelu ba su zuwa makaranta,yawon su kawai suke a unguwa, duk gidan mu ni kadai ta ka zuwa makaranta"
Gyara zama Sultana ta yi, cikin rashin fahimta ta ke kallon Mubaraka da ke mata bayani,
"Yah Auwal ya yi karatun allo, har ya kai ga sauke qur'ani, kamar yanda na ji labari, amma ban taba jin labarin ya yi boko ba, zama da masu ilimi na ya sanya shi koyon karatu da rubutu, sannan ya iya turanci kad'an, amma bai je makaranta ba, ni kuma kin ga wadda karatun nawa shi ke, yau in an bar ni na tai, gobe ba zani ba,su Jameelu kuwa ba su ko son zuwa makarantar Allah balle ta bature"
"Ikon Allah, zan so zuwa shiyyar ku niga wadda take, watarana"
"Kai ka kaiii, lallai ko da mun ji dad'i mara misali, ace ke da kan ki kin tai shiyyar mu,ko ba dan matsayin da ki ke da shi ba ma, domin kyawun halin ki da kullum Umman mu ke fad'a a shiyyar mu"
"Mubaraka kenan, to ni din wata ce daban? Ni ma mutum ce kamar kowa na duniya, a duniya babu wanda ya fi wani, sai wanda ya fi tsoron Allah, yawan dukiya, matsayi, muqami duk ba su na mutum ba, tsoron Allahn da bawa shike da shi, da kuma kyakkyawar mu'amala su ka yin mutum, ke gane?"
Daga kai Mubaraka ta yi, sannan ta ce,
"Aunty in tambaye ki? Dan Allah kar ran ki ya ɓaci da tambaya ta"
Kada kai Sultana ta yi, sannan ta bada hankalin ta ga kallon Mubaraka.
"Aunty yaushe na zaki aure?"
Dariya ce ta kwacewa sultana , ta ce,
"Mubaraka kenan, ni da ko saurayi ban da wa zan aura?"
Zaro ido Mubaraka ta yi cike da mamaki, sannan ta ce,
"Aunty ko dai ke ta baki kula su? Ko ni din nan, maza na cewa su na qauna ta, balle ke, aunty Sultana ke gane ki kuwa? Wa zai ce ba shi son mace kamar ki?"
Murmushi kawai sultana ta yi, domin ita maganar ma saurayi ko miji bata gaban ta tun da can, a kullum damuwar ta be wuce ta ga yanda zata fara aiki dan ta koyar da al'umma abinda Allah ya sanar da ita ba, sannan ta bude gidauniya ta na taimakon mutane, to yanzu ta samu buri d'aya ya cika, wataqila za ta duba maganar aure a nan gaba, domin maganar lecturing da take son yi da alama ba zai samu ba.
Lokaci Mubaraka ta kalla, ta ga ya tafi sosai, har hudu da rabi,da sauri ta miqe tsaye,
"Subhanallahi, na manta Yah Auwal na waje ya na jira na, na tsaya surutu"
"Jiran ki kuma? Yanzu ki na nufin sai mutum kamar Auwal ya tsaya jiran ki? Namiji ne fa, ba su son jira"
Murmushi mai dauke da tsantsar so da qauna Mubaraka ta yi, sannan ta ce,
"Aunty Sultana, ina so ki sa ido akan Yayana da kyau, a hankali za ki san wane ne wannan Auwal din, Yah Auwal daban shike cikin maza"
A bakin qofa Sultana ta tsaya, dan sauraron Mubaraka ba ta san ma ta na bin ta ba.
"Zan sa ido na biyu akan Yah Auwal din ki Mubaraka, sai gobe, ki gaishe da Lamishi da jiki"
"za ta ji"
A gurguje ta fita daga katafaren gidan, a zaune ta tadda shi a saman kujera ya na bacci, tsinke ta samu ta saka masa a hankali a qofar hanci, ai kuwa atishawa ya saki mai qarfi, miqewa ta yi ta na dariya, daga baya ta kama kunnen ta ta na bashi hakuri, kama ta ya yi, ya daga hannu kamar zai mare ta, cikin wasa ya san daki kuncin ta kadan, suka yi wa masu gadin qofar gidan da ke kallon su cikin sha'awa sallama, suka fita.
Sultana bata bar jikin window ba har sai da ta daina hango su, fuskar ta dauke da annuri ta fada wanka.
A hanya kuwa Mubaraka ta kwashe duk yanda sukai da Sultana ta sanar da Lawwali, murna a wajen shi kamar har ta ce masa ta na son shi.
Ko da suka isa gidan shi, sai da suka ci suka sha, ta yi wanka, ta maida kayan da ta cire, suka dauki yar qarama kuma tsadaddar motar shi da gwamna ya sai masa, tunda yanzu ba ya cikin tawagar su ta daji,ya na buqatar mota, ko da fitar gaggawa ta kama.
A motar suka isa gida, kafin su shiga Mubaraka ta lallaba shi ya sai balangu mutumin Lamishi, har da kaza da madara, suka isa.
Ko da suka shiga gidan shiruuu, ba kowa, ajiye ledojin hannun ta tayi, ta lelleqa, ba kowa da gaske, to ina suka je? Ina ita Lamishi me jinya?
Tsaki ya ja, sannan ya zauna su ka hau hira, ita kuma ta duba ko akwai abincin dare, ko se ta ɗora, gani ta yi akwai a flask, da zai ishe su, na gidan gwamna ne, dan haka ajiye naman ta yi, ta ce in sun dawo daga duk inda suka je an ci.
"Ke da kissani? Ta na can yawon gulma"
"Yah Auwal ina fada maka ka dinga tausasa harshen ka ga uwayen ka, umma ka ke fadin ta tai gulma"
Irin abun nan ya yi na 'yan mata masu yanga, ya murguda baki, ya yi fari, shi a dole an masa fada.
Dariya ta yi, ta ce,
"Dama Aunty sultana ta gan ka"
"Ki na ganin duk mun ka hadu in yi mata haka nan? Za ta so ni?",
"Walle ba ruwa na, in tayi shiri shiri kwancin kwana ta shere ka mari, ka gan ka kuwa? Awab-budurwa wallah"(ba ruwa na in ta yi kwance kwance ta kwad'a ma mari, ka ganka kuwa kamar budurwa)
Dariya sukai ta yi, har Dan Talo ya shiga gidan a gaggauce, buta ya dauka dan zagawa, Lawwali na ganin shi,ya miqe ya daure fuska,
"Lawwali, ai na hango motar ka ne, muna dawowa daga garkar Yahai, nicce bari na zo, ko zan samu wani abu, bari na hito daga yauce, (bayan gida)"
Ya na fadawa bayi, Lawwali ya zaro dubu biyar ya ba Mubaraka Ya ce,
"Amshi ki ba uban nan nawa me kwadayi, in ya hito daga tutun wahala, ban jira nai wallah, na tafi nemo yaki halal yaki haram din da suka so"
Magana ya ke kamar da wasa, amma cikin zuciyar shi zafi take, a ce iyayen ka basu damu da inda ka ke samo kudi ba, kuma da ganin Lawwali sun san dai ba aikin jima yake ba ko kafinta, ko dako, balle aikin office, Amma kullum nema suke a wajen shi, kuma basu yake, manyan kudi ma kuwa, se kace wani babban ma'aikaci, ko babban ma'aikaci watarana ya na zama bai da shi.
Mubaraka da ke tsaye cikin tausayin Yayan nata ne ta amshi kudin, ta na so ta bashi ko da hakuri ne, dan ta san ya yake ji, amma ya fice, tun kan ta ce komai.
Dan Talo da ya fito ya ga ba Lawwali, a zaton shi ya tafi ne, nan da nan kuwa ya hau ashar, ya na kiran lawwali da sunaye marasa dadin ji.
"Gashi hwa, ya bar maka kuddin, ya dai tafi ne an kira shi ga waya"
Baki Dan Talo ya washe, ya na kuma godiya, soke su ya yi, a sassan aljihun jikin shi, sannan ya fita.
Girgiza kai Mubaraka ta yi kawai, ta na nema ma ahalin ta shiriya.
***********************
Su Lamishi kuwa su na gidan Isah, Yabbuga nan ta tattare su suka fada, har da Asshibi, yau ta samu leqa gidajen shiyya, duk gidajen mutuncin unguwar ba d'aya da Yabbuga ta raka ta, sai nasu ya nasu.
Qarshe da suka shiga gidan Lamishi suka gaisa shi ne suka rankaya gidan Hansatu gaba dayan su.
Sun tadda Isah na gida, sun gaisa su na ta wani hira kamar sun samu abokin su, kafin daga baya ya fada daki, da fita zai amma ya fasa,Hansatu kuwa ta gama dafa shinkafa da wake, ya ji yaji mai dadi, ga man ya samu matsayi har albasa aka saka masa.
Nan dai Yabbuga uwar kwadai ta hau yaba qamshin girkin, Ita kuwa Hansatu jin haka ya sa dole ta debar musu, haqqin su ne sun ji qamshi tunda akwai ta zuba musu. (Da damar mutane rowa ta saka ba su damuwa da haqqin maqoci, a yi girki mai dadi, me qamshi a lashe a sude hannu, wasu ma maqotan su talakawa ne, amma ba za su sammusu ba, duk da dai yanzu duniya ta sauya, ka na iya bawa mutum dan Allah da haqqin maqotaka, ya ce dan a san ka na cin dadi ka bayar, amma ka tsarkake zuciyar ka ka bayar, mutum shi ya sani da ya maka sharri, sannan wasu in suka ga ana basu, sai su fara zaqewa da roqo, har mutum ya koma boye abu ya na rowa, da ace kowa zai gyara da an zauna lafiya)
Su na kai loma su na zuba hira, rabi da kwatan hirar bata wuce ta auratayya ba, Isah na daki ya na jin su, ya na kuma jin dadin hirar saduwar auren da suke ta yi, Hansatu kuwa sai fada masu take, su yi a hankali mijin ta na ciki, Matar Yahai na bude baki kuwa, sai da ta fadi maganar da ta sa Hansatu shiga wani irin hali na matsananciyar kunya, su kuwa suka sheqe da dariya, Asshibi kuwa sai ta ji matan sun kwanta mata a rai,dan kuwa wajen hirar banza ta fi kauri dama.
Hansatu ta gaji da jin maganganun su, masu sanya ta kunya, cikin tattausan lafazi ta ce,
"Wai ku in tambaye ku? Me ne ne jigo a rayuwar aure ne?"
"Saduwa mana heeeeee casssss"
Suka yi shewa tare da tafawa, Isah kuwa dake daki, har sake gyara kwanciya ya yi, ya na sauraron su.
Zama Hansatu ta gyara ta ce,
"Tabbas saduwa daya ce daga jigon da ka sa a yi aure, amma ba ita kad'ai ba ce jigo a gidan aure ba, abubuwan na da yawa, su din ginshiqai na da ka riqon aure, in babu su da tuni aurarraki da dama sun watse.
Na farko akwai yin auren ma shi kan shi domin Allah, sannan Yarda, riqon amana, saduwa, ladabi, biyayyah, soyayya, qauna, tausayi, ciyarwa,tufatarwa, wajen zama,girmama juna, qimanta juna, mutunta juna, tausayawa juna,iya girki,da wasu mahimmai dai.
Wa'yanga abubuwa in suka hadu, aure ya ginu, ya zauna kenan sai dai in ajali nai na ya yi.
Na fahimci me ya sa kuke ganin kamar saduwa ita ce kad'ai abinda ka riqe aure, ba komai na yasa ba saboda fadi da ankai cewar,Aure shike hada wata alaqa, tsakanin mace da namiji, wannan shi na nufin hade rayuwarsu ta zama daya haka nan kuma makomarsu ta kasance guda daya. Kowacce irin al'ummah akwai irin matsayin da ta ba wa aure, Aure a musulinci wani daurine da shike halatta wa ma'aurata mace da namiji jin dad'i da junansu, ta hanyar saduwa irin ta jima'i,da sauran mu'amaloli na jin dadin saduwa, Allah (subbahanawu wa ta'ala) ya halicci mace daga hakarkarin namiji ya kuma sanya soyayya da tausayi a tsakaninsu.
Wannan babban dalili ne da zai sa ku ga kamar saduwa tahi komai a aure, amma duk wadda bata iya kula da miji ba, ta hanyoyi da dama, musamman iya girki, tsafta, kwalliya, ladabi da biyayya, bata iya magana ba, komi yattaho bakin ta hwadi takai, to wallahi mace na da saura a gidan aure ba ta iya komi ba"
Gaba dayan su har Isah da ke kwance, hansatu ta basu mamaki, ba mace ba ce me yawan Suratu, amma sai gashi yau ta yi magana cikin ilimi da nutsuwa da fasaha.
Mai Buruji ce ta fara yunqurawa ta miqe ta na sude hannu,
"Tauuuu, Mallamar gidan aure mun gode da wanga ilimi da munka samu, bari mu tai mu dora a gidan mu mu ma ko mun zam matan so ga mazajen mu kamar ke, mun gode da wake da shinkahwa ke iya girki, shi yasa Isah ba shi iya cin abinci ko ina, sai gida "
Dariya suka kwashe da ita, da shewa, dan kuwa magana Mai Buruji ta gaya wa Hansatu, ita da ake jibga kuma ake zagi kowa na ji, ita ke musu bayani haka.
Murmushi mai ciwo Hansatu ta yi, sannan ta ce,
"Ai duk abinda na fad'a maku ba qarya ciki, ballantana ki fad'a min magana, kuma ko da na fad'a ban ce ni ina aikata su ba,sannan ban ce ina da wani cikakken matsayi a wajen miji na ba, ballantana ya zama abin yi min arashi,"
Yabbuga ce ta taimaka wa Lamishi ta miqe, sannan ta kalli Hansatu ta ce,
"Keee wagga kwantas kin ga gida munkai yanzu, shiga daki ki lallaba Isah dan kuwa duk ya walqita ya ga ba shinkahwar ga se ke mance da kin taba sanin mi na na ma'anar aure a musulunci"
Dariya suka fita su na mata, kafin su rabu sai da suka yi ta gulmar ta, Yabbuga na basu labarin yanda yake dukan ta da zagin ta, akan abu qalilan.
*Shin a maganganun Hansatu akwai gyara ne mutanen kwarai? In akwai gyara ko qarin haske akan zamantakewar aure a qaro mana ilimi*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 20:
Mata kala kala ne a duniya, musamman ta bangaren kwalliya, da gyaran jiki, kowacce mace da hanyar da take bi dan ganin ta yi kyau.
Akwai wacce za ta yi gyaran jiki da kaya irin namu na gida da muke amfani da shi yau da kullum, kamar su lalle, dankalin turawa, sugar ,kwai, cucumber, tumatur, gwanda, Madara, lemo, zuma da sauran su, wadannan kadai sun ishe ta ba tare da ta yi kwalliya ba.
Wata ta kuma kayan wanka na Bature kawai sun ishe ta, ba tare da kwalliya ba.
Wata kuma ta na haɗawa duka , ta kuma qara da kwalliya.
Sultana na daga cikin matan da basu damu da gyaran jiki da kayan amfanin yau da kullum ba, ta fi amfani da kayan gyaran jiki na Bature, masu gyara asalin fatar mutum ba tare da ta sanya shi fari ba, (wannan shi ne aji da waye wa, bleaching qauyanci ne da zubar da kuma da mutunci ga mai hankali amma tare da nuna wa Allah be iya ba, ya tauye ki, ke bari ki wa kan ki abinda ya gaza wa'iyadhubillah).
Yau tun da Sultana ta fito daga wanka,ta ke tunanin wanne kaya za ta saka dan ta yi kyau, me za ta yi wa fuskar ta dan ta qayata ta?
Ta jima zaune a dan qaramin table din, ta na shafe shafen mayuka da turaruka masu sanyin qamshi, yau ce rana ta farko da ta fara shafa kwalli, tare da shafa powder har dikin wuyan ta, jan baki ta jera a gaban ta ta na tunanin wanne za ta shafa, kalar purple mai haske ne idon ta ya sauka akai, dauka ta yi ta goga kadan, sannan ta hade kyawawan labban ta, kallon kan ta tayi a madubi, ganin yanda ta yi kyau ne ya sanya ta sakin murmushi mai laushi.
Maskara ta shafa ma gashin idon ta mai yalwa, ta gyara girar ta, abun shafa powder ta sake dauka ta gyara ko ina na fuskar ta.
Kallon wayar ta ta yi, ta ga
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11 Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51