komai fushin da take da shi, haramun ne matar nan ta qaurace wa mijin, in ta qaurace masa direct, ta ce ba zata ba, ko ta dinga yin wasu abubuwa indirectly har ya gaji da jiran ta ya yi bacci, to fa ta na cikin tsinuwar Allah da mala'ikun shi, har gari ya waye.
"Ni da kai akwai banbanci, domin kuwa na san Allah, na san dokokin da ya gindaya akan aure, kuma ina qoqarin kare kai na da take su, sai dai in da rashin sani, amma ka san wani abu, daga yanzu ba zan sake kwanciya da kai ba ba tare daka yi wanka ba, ba tare da ka wanke bakin ka da kyau ba, ba zan kwanta da kai ba ni ina cutuwa kai ka na mora ta ba wallah, an wuce wannan lokacin, in ka na buqata ta, ka tai zuwa wanka,in ka dawo ka wanke bakin ka, ban cuce ka ba na daina bari ka na cuta min wallah"
Komawa ta yi, ta yi wata iriyar kwanciya mai daukan hankali,a sukwane Isah ya bar dakin, ya shiga wanka, ya jima ya na dirzawa da cud'a jikin shi, sai da ya tabbata ya fita fess sannan ya dauraye jikin shi ya fita, abun ya bashi mamaki, da ya ga brush da toothpaste a ajiye a saman buta a qofar bayin, bai tsaya dogon bincike ba ya dauka ya wanke bakin shi tass, sannan ya koma dakin.
"Shin wai da ka taho ba alwala, ka yi sallar Isha'i halan?"
"Hansatu ba na jin sallah ta tana amsuwa innayi ta haka nan, dan Allah ki taimaka min"
"Watakam za ka iya yin wanka da brush dan biyan buqatar ka, amma ba zaka iya yin Sallah ba, dan cika umarnin Allah, lallai baka tashi kwana ba wallah"
Juyi ta sake, cike da kwarewa, sai da na dauki Style din juyin (lols) ta koma ta kwantar da kan ta a pillow, hankalin ta kwance.
Isah kuwa kuka ne kawai bai yi ba dan takaici, Gashi yanzu yanda ya ke hango rashin jin tsoron shi a idanun Hansatu, ba ya jin ko fada ya tsaya yi da ita zai samu riba.
Sallah ya je ya yi, a gurguje, ya koma dakin, gani ya yi ta kashe wutar dakin, a cikin duhun ya qarasa gadon......
Hansatu ta bawa Isah mamaki matuqa, ta shayar da shi zumar da ya dinga tunanin anya duk duniya akwai wadda ta fi Hanstun shi kuwa? Maqale ta ya yi gam da jikin shi, kamar ya na tsoron wani zai janye ta.
Ita kuwa kwace jikin ta tayi, ta tafi ta yi wanka, ta yi nafila raka'a biyu, tare da addu'ar Allah ya qara kawo mata zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan ta, sannan ta haye gado ta kwanta, kusa da Isah da ke ta sheqa munshari.
Da safe kuwa haka Isah ya debo kayan da ya samo a Makka wanda Larabawa suke bayarwa, sadaka, ya dinga bawa Hansatu ya na zuba mata qarya, ya na kurin shi ya siyo mata da kudin shi.
Ita kuwa fuskar ta ba walwala, ba fara'a take furta
"Na gode, Allah shi biya"
Isah dai ya qi shiru, sai zuba yake, qarshe da ta ga ba zai daina cika mata kunne ba, daki ta koma, ita da Ameenatu, suka bar shi da su Bilkisu a wajen.
Sai da ya ga Ahmad na qoqarin balle stone din wata riga, ya tattare duk haushin Hansatu da yake ji na qin kula shi da ta yi, ya gaurawa yaron mari, ai kuwa ya gigice, ya dinga zindima ihu, murmushin mugunta Isah ya yi, dan ya san zata je bada hakuri, ya qara bankawa yaro mari, Ameenatu na ta yi wa Hansatu magana akan ta je ta bawa Baban nasu hakuri, ta yi Murmushi ta ci gaba da gyara dakin ta abun ta.
Isan da yaga ba wanda ya kula shi sai ya hau masifa da zage zage, nan ma ba wanda ya ce masa ci kan ka.
Haka ya qaraci masifar shi ya bar gidan, tare da tabbatar mata da a sati na sama zai koma Makka,tunda abin nata iskanci ne.
Shirun da ta masa ne ya qara tunzura shi ya bar gidan gaba daya.
**************************
Ya kasa zaune ya kasa tsaye, saboda labarin da ya samu, Gwamna Halliru ya raba hotunan Mubaraka, ma jami'an tsaro dake tare motoci a hanya su bincika, ko da za a ga Mubaraka akai masa ita direct wajen shi, babban abun takaicin shi ne Dan Talo da kan shi ya bada hoton diyar tashi, ba tare da ya san me ke faruwa ba.
Sultana ce ta kwantar da kan ta a bayan shi, ta rasa da me zata kwantar masa da hankali, gaba daya naman jikin shi rawa yake, hankalin shi a tashe yake, damuwar shi what if aka kama su Mubarakan shi fa? Ina zai saka ran shi, ya zai ya cika mata alqawarin da ya daukar Mata na bata kariya? Daga shi har ita ba su da kowa mai qaunar su domin Allah sai junan su, in wani abu ya same ta ba zai taba yafewa kan shi ba.
Zama ya yi a qasa dabar, ya fashe da wani irin kuka mai ban tausayi, Sultana ma kukan take, duk ta bi ta rame, saboda rashin kwanciyar hankali.
Kallon ta ya yi, ya rungume ta sannan ya ce,
"Ki yahe min Sultana, ban zama miji nagari a gare ki ba, ban san ya zan da raina ba in wani abu ya same ta, kin dai san ta na shiga hannun mahaifin ki kashe ta zai ko? "
Ta na qoqarin kwatanta yanda yake ji a ran shi, amma bata san ya zata bayyana masa hakan ba, ba tare da ta yi tunanin komai ba, ta kai bakin ta nashi,wannan shi ne karo na farko da suka jima su na sumbatar junan su, kuma shi ne karo na farko da sumbatar ta zarce, har sultana ta cire duk wani tsoro, da tsaro, da kuma dokar da ta shimfida a tsakanin su, na sai ya fara sallah zata yarda ya Kusance ta, tunawa ta yi a ran ta cewar, ita addu'ar saduwa tsakanin ma'aurata, ba dole sai namiji ne kawai zai yi ta ba, mace da namiji duk ana so su yi, in daya be yi ba, saboda wani dalili, misali mantuwa, ko rashin iyawa, wanda ya iya zai iya yi shi.
A yammar Lawwali ya yi nasarar karbar haqqin auren shi a wajen matar shi ta sunnah kuma diyar fitaccen maqiyan shi,Lawwali bai taba hango cewar rayuwar aure dama haka take da wani sinadari, da dandano ba, sai a yau, wanda da ya san haka abun yake, da bai kai wannan tsahon lokacin ba, ba tare daya karbi haqqin shi a wajen Sulty Baby ba.
Lawwali ne ya taimaka mata ya maida ta saman gadon su, duk qasan carpet din ya ɓaci, cikin tausaya wa ya ce,
"Sannu Sultana, yanzu ya za mu yi? Na ga kin ji ciwo,ni ban san ya zan yi ba"
Duk da ciwon da take ji a jikin ta, bai hana ta, murmusa wa ba, tare da godewa Allah, da bai yi ta mazinaciya ba, hannun shi ta kama ta sumbata, shi kuma cikin damuwa ya kalle ta ya ce,
"Ki sanar da ni, mi zan yi yanzu? Ban san me zan ba, na ga har yanzu jini na zuba a jikin ki"
Cikin dasasshiyar murya ta ce,
"Ina so ka yarda da Allah,ka yarda Allah ne kawai zai iya bawa Mubaraka kariya ba kai ba, ka yarda cewar mubaraka ta na cikin kariyar ubangiji, ba wanda ya isa cuta mata sai idan Allah ya so,ina so daga yau ka min kyakkyawar kyautar da zata faranta raina,kyautar da har na koma ga mahalicci na ba zan daina jin dad'in ta ba"
Kafin ta sauke numfashi Lawwali ya ce,
"Na miki alqawarin baki duk abinda na mallaka, na kuma amince Allah shi ne kaɗai wanda zai kare min Barakana a duk inda take"
Murmushi ta yi, gefen idanun ta kuwa hawaye ne ke zuba da gudu,
"Ina so ka koma bautawa Allah, kamar kowanne musulmi cikakke, kuma nagartacce, wannan ita ce kyautar da nake so, a matsayi na na matar da ta kawo mutuncin ta gidan miji"
Lawwali bai san sanda ya rungume ta ba ya na kuka, tare da fadin
"Allah na tuba, Allah ka yahe min, ban san wanne aikin alkhairi na aikata ba ga rayuwa ta, da ka bani mace kamar wagga, Allah ka yahe min, Allah ka tausaya min ka yahe min ba dan hali na ba, Allah na san ka na so na da rahama ne ya sa ka azurta ni da mace kamar Sultana, Allah ka bani ikon sauya halaye na ka yi min afuwa"
Daga shi har ita kuka suke, da kyar suka lallashi kan su, suka yi shiru,
"Ka ce wa Barirah ta kawo ruwan zahi, kai kuma ka je ka yi wankan tsarki, ka shirya ka je gidan mu, ka taho da Sultan,ba tare da kowa ya sani ba, ka ce zaka kawo shi waje na mu gaisa, in ka yi haka, Daddy ya ji labari daga baya, ba zai sake ya cutawa Mubaraka ba har ta iso nan lahiya, ko ka na da wata shawara da ta hi wagga sauqi?"
Lawwali sake fashewa ya yi da kuka, ya rungume Sultana, yau zuciyar shi ta koma danya shataff a gaban matar tashi,su na haka, ta koya masa yanda ake wankan, ya tafi ya yi, ya kuma bada umarnin a kula da ita, ya bar dajin.
Kamar yanda suka tsara kuwa haka aka yi, tun Sultan na ganin nisan waje,har ya fara tambayar shin ina za su ne? Lawwali kuwa budar bakin shi sai cewa ya
"Za mu tai ne ka ga inda Daddyn ku ya bamu dan mu zauna ni da mata ta"
Mamaki ne fal ran Sultan,yanzu duk gidajen da suke da shi a cikin gari a rasa inda Sulty Baby na ta zauna sai kauye?????......
*Hummmm Sultan kenan, U never see anything*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAEH
PAGE 51:
Mutanen da ya gani sanye da qananan kaya da bindigogi, sun tsoratar da shi matuqa,nan take ya tuno da kalaman iyayen shi akan Lawwalin, amma ya rasa dalilin da ya sa ya kasa gasgata maganar su a qasan ran shi, har yanzu ya na ganin Lawwali a matsayin mutumin kirkin da ya ke gani a baya.
Su na isa sansanin Lawwali ya bude mota ya fita, ya na jiran Sultan, Sultan cikin daurewar kai ya fito,kwakwalwar shi da kowacce gab'a ta jikin shi na so a masa qarin bayanin abinda idanun shi ke gani.
"Kar ka samu damuwa ran ka shi dade Sultan, mu je za ka san duk wani abu da ka ka buqata, Sultana na ciki na jiran mu"
"Wai dan Allah da gaske anan Sultana ke rayuwa? Ko dai wasa ka ke min, me ya had'a ku da irin wadannan mutanen?"
Gaisuwar da Sultan ya ga ana miqawa Lawwali ne ya sake sanya shi cikin rudani, sun kusan isa dakin su sultana, sultanan ta fito cikin wata iriyar kwalliya, mai ban sha'awa, ta yafa mayafin ta kalar shaddar da ke jikin ta, ta saka flat shoe, sai qamshi take zubawa, Lawwali na dora ido akan ta, ya ji duk wata soyayyar ta da yake ta qoqarin dannewa, da wadda bai ma san ya fara yi mata ba, ta taso ta lullube shi, wani qayatacce, kuma sassanyan murmushi yake zuba mata, Itan ma haka, sai dai kunyar shi ta fi yawa a tattare da ita a yanzu, bata iya hada kwayar idon ta da na shi, Sultan tsaye yake ya na kallon ikon Allah, cikin gyaran murya, da gyara tsayuwar shi ya ce,
"Baby Sulty ta dena so na yanzu,"
Da sauri ta kauda kan ta daga kallon qasan ido da take wa Lawwali, ta fara takawa, cikin tsananin kulawa dan kar su gane sauyawar tafiyar ta, ta isa gare shi, rungume ta ya yi, ita ma ta sa hannayen ta biyu ta rungume shi, sai da suka gama farin cikin ganin junan su, sannan Lawwali ya saqale hannun shi daya a qugun ta, sannan suka shiga ciki.
Lawwali ya yi mamakin yanda aka gyara wajen, sai kamshi ke tashi, ga abinci nan an kawo, da abun sha.
Aikin Barirah ne wannan.
Zama suka yi gaba dayan su, tare da yiwa Sultan Bismillah, kame hannayen shi ya yi, a qirjin shi, sannan ya ce,
"Ni fa ba zan iya sanya ko da ruwa ba ne a ciki na, ba tare da na san mi ya kawo ku dajin ga ba, shin sace ku an ka yi ko mi na na?"
"Mun yi maka kama da wanda anka sace?Kai dai aka sato, domin kuwa a yanzu haka in ba mun samu abinda muke so ba a wajen mahaifin ku, ba zaka koma cikin gari ba"
Wata dariyar rainin hankali Sultan ya yi, ya kalli Lawwali ya ce,
"Habaa habaa suruki na, ai ni nafi qarfin a sace ni, in ka ga an sace ni to qaddara ta ce ta zo da haka, ni da ka gane ni ban wasa da azkar, ban wasa da addu'ar hita da shiga gida, ka ko ga me sace ni sai ya shirya"
Sultana ce ta yi dariya ta ce wa Lawwali,
"Kira Daddy"
"Ban gane shi kira Daddy ba, me ke faruwa ne? Ku na ta sa wa kai na na daure wa,"
"Yah Sultan in har ka bamu goyon baya akan abinda muke shirin yi, na maka alqawarin sanar da kai komai game da iyayen mu, wanda nake boyewa ba na so ka sani, dan kar ka shiga damuwa"
Kallon su kawai yake, ya ma kasa magana, kenan ta tabbata sato shi aka je har qofar gidan su aka yi, kuma ya zo ba tare daya san sato shin akai ba.
"Excellency sir, ka na lahiya?.....yi hankuriii ba fada ne yasa na Kire ka ba, wasu kadarorin ka ne a waje na, wanda duk duniyar ga baka da kamar su, ina mai tabbatar maka da cewar in baka dakatar da neman qauna ta ba, ta iso gare ni lahiya, zan manta da wai an tai central mosque an daura min aure da diyar ka, zan sa bakin bindiga na halbe ta, d'anka da na tai na dakko dazu...."
Cikin wata iriyar tsawa Gwamna Halliru ya miqe tsaye daga saman dining table din da ya ke cin abincin dare shi kadai, ya ce,
"Lawwali kar ka kuskura, kar ka sake ka taba min yara na,....... kai wa Allah Lawwali ka dawo min da yara na lahiya, zan janye binciken da ake akan qaunar ka"
"Nooo ka ci gaba da yi min fadan mana, me ya sa ka dena? Ga Sultana na so ta yi magana da kai"
Wayar Lawwali ya miqa wa Sultana, tare da daga mata yatsan shi babba, cikin maqale murya da kukan qarya ta fara magana,
"Daddy ka zo ka cece mu, mutumin nan mugu na..."
Lawwali ne ya amshe wayar, ya kunna a handsfree ,Gwamna sai magiya yake, kamar zai kuka,
"Sultana are you ok? Ina d'an uwan ki shi ke? Lawwali kai wa Allah ka sake min yara na, zan janye duk wani neman qaunar ka da nake, kai zan manta ma da kai da rayuwar ka, zan kyale ka ka yi duk abinda ka ga dama, amma na roqe ka kar ka yi wa yara na komi"
"Amma dai ka san qa'idar aikin mu ko? Kai ne fa ka ce in mun amshi kuddi, in diyan 'yan siyasa ne,ko 'yan siyasan da kan su, mu kashe, kar mu bari da rai, yanzu kuma ka ke son sauya muna doka?"
"Lawwali na janye wannan dokar, ga sabuwar doka nan, Lawwali kai wa Allah ka sake min diya na lahiya, ina Sultan? Sultan..."
Sultan na zaune ya na saurara kuma ya na ganin abun kamar wasan yara, ah ah mafarki ne, bai ma san me ya dauki abun ba, gashi nan dai ne kawai.
"...Sultan ka yi min magana,Lawwali kaji tsoron Allah kar ka cutar min da yara na,ba su da haqqin kowa, kar ka cutar min da yara na, ka sanar da ni ko nawa ka ke so, zan baka, ka sake su"
"Ashe ka san Allah?Ka dai san na san kuddin ka kuddin sata ne ko? kuddin tsafi ne, to ni a yanzu mi zan da kuddin ka? Baicin na gama samun iya abinda nake buqata a wannan harkar, kawai yaran ka nika son kashewa, dan na rama lalata min rayuwa da ka yi, ai na fada maka, sai na dau fansar abinda ka yi wa qauna ta,da iya ni ka taba,da na kyale ka, tunda ni ma ina da laifi nawa na kai na,ni na kawo kaina gare ku dan neman taimako, ku ciyar da baki da tumbin da ke tsananin jin yunwa da qishirwa,amma me kuka yi? Sai ku ka jefa rayuwa ta cikin halaka da lalacewa, amma duk da na san mugayen halayen ku,na ci gaba da zama da ku, tunda in na yi abinda ku ke so ku na bani abinda zan ci har da iyaye na ma, da ace ni kad'ai ka tab'a a yanzu, wataqila da na hakura, amma qauna ta? Ka yi na farko, yanzu ka na so ka yi na biyu? Inaaa, ba zan iya hakuri ba sam sam"
Gwamna Halliru bai san ya na kuka ba tun farkon fara wayar, sai da kukan ya ci qarfin shi ya kufce masa da qarfi, tura kujerar da yake kai ya yi, ya durqusa da guiwar shi a qasa, ya na roqon Lawwali, da ya kyale masa yaran shi, kar ya cutar da su.
Lawwali ne ya bawa Sultan wayar, shi kuwa ya rasa me zai ce, kalma ɗaya ce ta fito daga bakin shi, wato,
"Daddy"
Haba mana Gwamna na jin Muryar Sultan da gaske sai ya sake rikicewa, domin sai ya ji Muryar Sultan kamar a wahale, bai san tsantsar mamaki ke damun Sultan din ba, ya nufi sama, a gigice, Hajiya Ikee na ta kyale kyale,duk da halin jimamin da ake ciki bai hana ta kwalliya ba.
Yanayin da ta ga mijin nata ne ya sa ta sakin kwalbar turare a qasa, ta nufe shi zata kai masa cacuma ya bangaje ta, ya dauki sauran wayoyin shi zai fita, maganar da ta ji ya na yi ne ya sanya ta fahimtar inda aka dosa, cikin tsananin damuwa kuwa ta bi shi ta na kira, ko juyawa bai ba, sai da ya
Showing 108001 words to 111000 words out of 150481 words
"Ni da kai akwai banbanci, domin kuwa na san Allah, na san dokokin da ya gindaya akan aure, kuma ina qoqarin kare kai na da take su, sai dai in da rashin sani, amma ka san wani abu, daga yanzu ba zan sake kwanciya da kai ba ba tare daka yi wanka ba, ba tare da ka wanke bakin ka da kyau ba, ba zan kwanta da kai ba ni ina cutuwa kai ka na mora ta ba wallah, an wuce wannan lokacin, in ka na buqata ta, ka tai zuwa wanka,in ka dawo ka wanke bakin ka, ban cuce ka ba na daina bari ka na cuta min wallah"
Komawa ta yi, ta yi wata iriyar kwanciya mai daukan hankali,a sukwane Isah ya bar dakin, ya shiga wanka, ya jima ya na dirzawa da cud'a jikin shi, sai da ya tabbata ya fita fess sannan ya dauraye jikin shi ya fita, abun ya bashi mamaki, da ya ga brush da toothpaste a ajiye a saman buta a qofar bayin, bai tsaya dogon bincike ba ya dauka ya wanke bakin shi tass, sannan ya koma dakin.
"Shin wai da ka taho ba alwala, ka yi sallar Isha'i halan?"
"Hansatu ba na jin sallah ta tana amsuwa innayi ta haka nan, dan Allah ki taimaka min"
"Watakam za ka iya yin wanka da brush dan biyan buqatar ka, amma ba zaka iya yin Sallah ba, dan cika umarnin Allah, lallai baka tashi kwana ba wallah"
Juyi ta sake, cike da kwarewa, sai da na dauki Style din juyin (lols) ta koma ta kwantar da kan ta a pillow, hankalin ta kwance.
Isah kuwa kuka ne kawai bai yi ba dan takaici, Gashi yanzu yanda ya ke hango rashin jin tsoron shi a idanun Hansatu, ba ya jin ko fada ya tsaya yi da ita zai samu riba.
Sallah ya je ya yi, a gurguje, ya koma dakin, gani ya yi ta kashe wutar dakin, a cikin duhun ya qarasa gadon......
Hansatu ta bawa Isah mamaki matuqa, ta shayar da shi zumar da ya dinga tunanin anya duk duniya akwai wadda ta fi Hanstun shi kuwa? Maqale ta ya yi gam da jikin shi, kamar ya na tsoron wani zai janye ta.
Ita kuwa kwace jikin ta tayi, ta tafi ta yi wanka, ta yi nafila raka'a biyu, tare da addu'ar Allah ya qara kawo mata zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan ta, sannan ta haye gado ta kwanta, kusa da Isah da ke ta sheqa munshari.
Da safe kuwa haka Isah ya debo kayan da ya samo a Makka wanda Larabawa suke bayarwa, sadaka, ya dinga bawa Hansatu ya na zuba mata qarya, ya na kurin shi ya siyo mata da kudin shi.
Ita kuwa fuskar ta ba walwala, ba fara'a take furta
"Na gode, Allah shi biya"
Isah dai ya qi shiru, sai zuba yake, qarshe da ta ga ba zai daina cika mata kunne ba, daki ta koma, ita da Ameenatu, suka bar shi da su Bilkisu a wajen.
Sai da ya ga Ahmad na qoqarin balle stone din wata riga, ya tattare duk haushin Hansatu da yake ji na qin kula shi da ta yi, ya gaurawa yaron mari, ai kuwa ya gigice, ya dinga zindima ihu, murmushin mugunta Isah ya yi, dan ya san zata je bada hakuri, ya qara bankawa yaro mari, Ameenatu na ta yi wa Hansatu magana akan ta je ta bawa Baban nasu hakuri, ta yi Murmushi ta ci gaba da gyara dakin ta abun ta.
Isan da yaga ba wanda ya kula shi sai ya hau masifa da zage zage, nan ma ba wanda ya ce masa ci kan ka.
Haka ya qaraci masifar shi ya bar gidan, tare da tabbatar mata da a sati na sama zai koma Makka,tunda abin nata iskanci ne.
Shirun da ta masa ne ya qara tunzura shi ya bar gidan gaba daya.
**************************
Ya kasa zaune ya kasa tsaye, saboda labarin da ya samu, Gwamna Halliru ya raba hotunan Mubaraka, ma jami'an tsaro dake tare motoci a hanya su bincika, ko da za a ga Mubaraka akai masa ita direct wajen shi, babban abun takaicin shi ne Dan Talo da kan shi ya bada hoton diyar tashi, ba tare da ya san me ke faruwa ba.
Sultana ce ta kwantar da kan ta a bayan shi, ta rasa da me zata kwantar masa da hankali, gaba daya naman jikin shi rawa yake, hankalin shi a tashe yake, damuwar shi what if aka kama su Mubarakan shi fa? Ina zai saka ran shi, ya zai ya cika mata alqawarin da ya daukar Mata na bata kariya? Daga shi har ita ba su da kowa mai qaunar su domin Allah sai junan su, in wani abu ya same ta ba zai taba yafewa kan shi ba.
Zama ya yi a qasa dabar, ya fashe da wani irin kuka mai ban tausayi, Sultana ma kukan take, duk ta bi ta rame, saboda rashin kwanciyar hankali.
Kallon ta ya yi, ya rungume ta sannan ya ce,
"Ki yahe min Sultana, ban zama miji nagari a gare ki ba, ban san ya zan da raina ba in wani abu ya same ta, kin dai san ta na shiga hannun mahaifin ki kashe ta zai ko? "
Ta na qoqarin kwatanta yanda yake ji a ran shi, amma bata san ya zata bayyana masa hakan ba, ba tare da ta yi tunanin komai ba, ta kai bakin ta nashi,wannan shi ne karo na farko da suka jima su na sumbatar junan su, kuma shi ne karo na farko da sumbatar ta zarce, har sultana ta cire duk wani tsoro, da tsaro, da kuma dokar da ta shimfida a tsakanin su, na sai ya fara sallah zata yarda ya Kusance ta, tunawa ta yi a ran ta cewar, ita addu'ar saduwa tsakanin ma'aurata, ba dole sai namiji ne kawai zai yi ta ba, mace da namiji duk ana so su yi, in daya be yi ba, saboda wani dalili, misali mantuwa, ko rashin iyawa, wanda ya iya zai iya yi shi.
A yammar Lawwali ya yi nasarar karbar haqqin auren shi a wajen matar shi ta sunnah kuma diyar fitaccen maqiyan shi,Lawwali bai taba hango cewar rayuwar aure dama haka take da wani sinadari, da dandano ba, sai a yau, wanda da ya san haka abun yake, da bai kai wannan tsahon lokacin ba, ba tare daya karbi haqqin shi a wajen Sulty Baby ba.
Lawwali ne ya taimaka mata ya maida ta saman gadon su, duk qasan carpet din ya ɓaci, cikin tausaya wa ya ce,
"Sannu Sultana, yanzu ya za mu yi? Na ga kin ji ciwo,ni ban san ya zan yi ba"
Duk da ciwon da take ji a jikin ta, bai hana ta, murmusa wa ba, tare da godewa Allah, da bai yi ta mazinaciya ba, hannun shi ta kama ta sumbata, shi kuma cikin damuwa ya kalle ta ya ce,
"Ki sanar da ni, mi zan yi yanzu? Ban san me zan ba, na ga har yanzu jini na zuba a jikin ki"
Cikin dasasshiyar murya ta ce,
"Ina so ka yarda da Allah,ka yarda Allah ne kawai zai iya bawa Mubaraka kariya ba kai ba, ka yarda cewar mubaraka ta na cikin kariyar ubangiji, ba wanda ya isa cuta mata sai idan Allah ya so,ina so daga yau ka min kyakkyawar kyautar da zata faranta raina,kyautar da har na koma ga mahalicci na ba zan daina jin dad'in ta ba"
Kafin ta sauke numfashi Lawwali ya ce,
"Na miki alqawarin baki duk abinda na mallaka, na kuma amince Allah shi ne kaɗai wanda zai kare min Barakana a duk inda take"
Murmushi ta yi, gefen idanun ta kuwa hawaye ne ke zuba da gudu,
"Ina so ka koma bautawa Allah, kamar kowanne musulmi cikakke, kuma nagartacce, wannan ita ce kyautar da nake so, a matsayi na na matar da ta kawo mutuncin ta gidan miji"
Lawwali bai san sanda ya rungume ta ba ya na kuka, tare da fadin
"Allah na tuba, Allah ka yahe min, ban san wanne aikin alkhairi na aikata ba ga rayuwa ta, da ka bani mace kamar wagga, Allah ka yahe min, Allah ka tausaya min ka yahe min ba dan hali na ba, Allah na san ka na so na da rahama ne ya sa ka azurta ni da mace kamar Sultana, Allah ka bani ikon sauya halaye na ka yi min afuwa"
Daga shi har ita kuka suke, da kyar suka lallashi kan su, suka yi shiru,
"Ka ce wa Barirah ta kawo ruwan zahi, kai kuma ka je ka yi wankan tsarki, ka shirya ka je gidan mu, ka taho da Sultan,ba tare da kowa ya sani ba, ka ce zaka kawo shi waje na mu gaisa, in ka yi haka, Daddy ya ji labari daga baya, ba zai sake ya cutawa Mubaraka ba har ta iso nan lahiya, ko ka na da wata shawara da ta hi wagga sauqi?"
Lawwali sake fashewa ya yi da kuka, ya rungume Sultana, yau zuciyar shi ta koma danya shataff a gaban matar tashi,su na haka, ta koya masa yanda ake wankan, ya tafi ya yi, ya kuma bada umarnin a kula da ita, ya bar dajin.
Kamar yanda suka tsara kuwa haka aka yi, tun Sultan na ganin nisan waje,har ya fara tambayar shin ina za su ne? Lawwali kuwa budar bakin shi sai cewa ya
"Za mu tai ne ka ga inda Daddyn ku ya bamu dan mu zauna ni da mata ta"
Mamaki ne fal ran Sultan,yanzu duk gidajen da suke da shi a cikin gari a rasa inda Sulty Baby na ta zauna sai kauye?????......
*Hummmm Sultan kenan, U never see anything*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAEH
PAGE 51:
Mutanen da ya gani sanye da qananan kaya da bindigogi, sun tsoratar da shi matuqa,nan take ya tuno da kalaman iyayen shi akan Lawwalin, amma ya rasa dalilin da ya sa ya kasa gasgata maganar su a qasan ran shi, har yanzu ya na ganin Lawwali a matsayin mutumin kirkin da ya ke gani a baya.
Su na isa sansanin Lawwali ya bude mota ya fita, ya na jiran Sultan, Sultan cikin daurewar kai ya fito,kwakwalwar shi da kowacce gab'a ta jikin shi na so a masa qarin bayanin abinda idanun shi ke gani.
"Kar ka samu damuwa ran ka shi dade Sultan, mu je za ka san duk wani abu da ka ka buqata, Sultana na ciki na jiran mu"
"Wai dan Allah da gaske anan Sultana ke rayuwa? Ko dai wasa ka ke min, me ya had'a ku da irin wadannan mutanen?"
Gaisuwar da Sultan ya ga ana miqawa Lawwali ne ya sake sanya shi cikin rudani, sun kusan isa dakin su sultana, sultanan ta fito cikin wata iriyar kwalliya, mai ban sha'awa, ta yafa mayafin ta kalar shaddar da ke jikin ta, ta saka flat shoe, sai qamshi take zubawa, Lawwali na dora ido akan ta, ya ji duk wata soyayyar ta da yake ta qoqarin dannewa, da wadda bai ma san ya fara yi mata ba, ta taso ta lullube shi, wani qayatacce, kuma sassanyan murmushi yake zuba mata, Itan ma haka, sai dai kunyar shi ta fi yawa a tattare da ita a yanzu, bata iya hada kwayar idon ta da na shi, Sultan tsaye yake ya na kallon ikon Allah, cikin gyaran murya, da gyara tsayuwar shi ya ce,
"Baby Sulty ta dena so na yanzu,"
Da sauri ta kauda kan ta daga kallon qasan ido da take wa Lawwali, ta fara takawa, cikin tsananin kulawa dan kar su gane sauyawar tafiyar ta, ta isa gare shi, rungume ta ya yi, ita ma ta sa hannayen ta biyu ta rungume shi, sai da suka gama farin cikin ganin junan su, sannan Lawwali ya saqale hannun shi daya a qugun ta, sannan suka shiga ciki.
Lawwali ya yi mamakin yanda aka gyara wajen, sai kamshi ke tashi, ga abinci nan an kawo, da abun sha.
Aikin Barirah ne wannan.
Zama suka yi gaba dayan su, tare da yiwa Sultan Bismillah, kame hannayen shi ya yi, a qirjin shi, sannan ya ce,
"Ni fa ba zan iya sanya ko da ruwa ba ne a ciki na, ba tare da na san mi ya kawo ku dajin ga ba, shin sace ku an ka yi ko mi na na?"
"Mun yi maka kama da wanda anka sace?Kai dai aka sato, domin kuwa a yanzu haka in ba mun samu abinda muke so ba a wajen mahaifin ku, ba zaka koma cikin gari ba"
Wata dariyar rainin hankali Sultan ya yi, ya kalli Lawwali ya ce,
"Habaa habaa suruki na, ai ni nafi qarfin a sace ni, in ka ga an sace ni to qaddara ta ce ta zo da haka, ni da ka gane ni ban wasa da azkar, ban wasa da addu'ar hita da shiga gida, ka ko ga me sace ni sai ya shirya"
Sultana ce ta yi dariya ta ce wa Lawwali,
"Kira Daddy"
"Ban gane shi kira Daddy ba, me ke faruwa ne? Ku na ta sa wa kai na na daure wa,"
"Yah Sultan in har ka bamu goyon baya akan abinda muke shirin yi, na maka alqawarin sanar da kai komai game da iyayen mu, wanda nake boyewa ba na so ka sani, dan kar ka shiga damuwa"
Kallon su kawai yake, ya ma kasa magana, kenan ta tabbata sato shi aka je har qofar gidan su aka yi, kuma ya zo ba tare daya san sato shin akai ba.
"Excellency sir, ka na lahiya?.....yi hankuriii ba fada ne yasa na Kire ka ba, wasu kadarorin ka ne a waje na, wanda duk duniyar ga baka da kamar su, ina mai tabbatar maka da cewar in baka dakatar da neman qauna ta ba, ta iso gare ni lahiya, zan manta da wai an tai central mosque an daura min aure da diyar ka, zan sa bakin bindiga na halbe ta, d'anka da na tai na dakko dazu...."
Cikin wata iriyar tsawa Gwamna Halliru ya miqe tsaye daga saman dining table din da ya ke cin abincin dare shi kadai, ya ce,
"Lawwali kar ka kuskura, kar ka sake ka taba min yara na,....... kai wa Allah Lawwali ka dawo min da yara na lahiya, zan janye binciken da ake akan qaunar ka"
"Nooo ka ci gaba da yi min fadan mana, me ya sa ka dena? Ga Sultana na so ta yi magana da kai"
Wayar Lawwali ya miqa wa Sultana, tare da daga mata yatsan shi babba, cikin maqale murya da kukan qarya ta fara magana,
"Daddy ka zo ka cece mu, mutumin nan mugu na..."
Lawwali ne ya amshe wayar, ya kunna a handsfree ,Gwamna sai magiya yake, kamar zai kuka,
"Sultana are you ok? Ina d'an uwan ki shi ke? Lawwali kai wa Allah ka sake min yara na, zan janye duk wani neman qaunar ka da nake, kai zan manta ma da kai da rayuwar ka, zan kyale ka ka yi duk abinda ka ga dama, amma na roqe ka kar ka yi wa yara na komi"
"Amma dai ka san qa'idar aikin mu ko? Kai ne fa ka ce in mun amshi kuddi, in diyan 'yan siyasa ne,ko 'yan siyasan da kan su, mu kashe, kar mu bari da rai, yanzu kuma ka ke son sauya muna doka?"
"Lawwali na janye wannan dokar, ga sabuwar doka nan, Lawwali kai wa Allah ka sake min diya na lahiya, ina Sultan? Sultan..."
Sultan na zaune ya na saurara kuma ya na ganin abun kamar wasan yara, ah ah mafarki ne, bai ma san me ya dauki abun ba, gashi nan dai ne kawai.
"...Sultan ka yi min magana,Lawwali kaji tsoron Allah kar ka cutar min da yara na,ba su da haqqin kowa, kar ka cutar min da yara na, ka sanar da ni ko nawa ka ke so, zan baka, ka sake su"
"Ashe ka san Allah?Ka dai san na san kuddin ka kuddin sata ne ko? kuddin tsafi ne, to ni a yanzu mi zan da kuddin ka? Baicin na gama samun iya abinda nake buqata a wannan harkar, kawai yaran ka nika son kashewa, dan na rama lalata min rayuwa da ka yi, ai na fada maka, sai na dau fansar abinda ka yi wa qauna ta,da iya ni ka taba,da na kyale ka, tunda ni ma ina da laifi nawa na kai na,ni na kawo kaina gare ku dan neman taimako, ku ciyar da baki da tumbin da ke tsananin jin yunwa da qishirwa,amma me kuka yi? Sai ku ka jefa rayuwa ta cikin halaka da lalacewa, amma duk da na san mugayen halayen ku,na ci gaba da zama da ku, tunda in na yi abinda ku ke so ku na bani abinda zan ci har da iyaye na ma, da ace ni kad'ai ka tab'a a yanzu, wataqila da na hakura, amma qauna ta? Ka yi na farko, yanzu ka na so ka yi na biyu? Inaaa, ba zan iya hakuri ba sam sam"
Gwamna Halliru bai san ya na kuka ba tun farkon fara wayar, sai da kukan ya ci qarfin shi ya kufce masa da qarfi, tura kujerar da yake kai ya yi, ya durqusa da guiwar shi a qasa, ya na roqon Lawwali, da ya kyale masa yaran shi, kar ya cutar da su.
Lawwali ne ya bawa Sultan wayar, shi kuwa ya rasa me zai ce, kalma ɗaya ce ta fito daga bakin shi, wato,
"Daddy"
Haba mana Gwamna na jin Muryar Sultan da gaske sai ya sake rikicewa, domin sai ya ji Muryar Sultan kamar a wahale, bai san tsantsar mamaki ke damun Sultan din ba, ya nufi sama, a gigice, Hajiya Ikee na ta kyale kyale,duk da halin jimamin da ake ciki bai hana ta kwalliya ba.
Yanayin da ta ga mijin nata ne ya sa ta sakin kwalbar turare a qasa, ta nufe shi zata kai masa cacuma ya bangaje ta, ya dauki sauran wayoyin shi zai fita, maganar da ta ji ya na yi ne ya sanya ta fahimtar inda aka dosa, cikin tsananin damuwa kuwa ta bi shi ta na kira, ko juyawa bai ba, sai da ya
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37 Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51